Showing 150001 words to 153000 words out of 185502 words
ne suka tsaya suka karya kumallo, suna gamawa suka fita Mimi na musu a dawo lafiya, saida suka fita ta nufi d'akin Hafsat da sallama a bakinta, zaune ta sameta bakin gado da wayarta a hannu, k'asan mak'oshi ta amsa sallamarta, bata damu ba haka ta k'araso tsakiyar d'akin tace "Aunty Hafsat abincinki na ce ko na kawo miki nan? Na ga baki fito ba yau."
Yatsina fuska Hafsat tayi tace "A'a ki barshi ma na k'oshi."
D'an satar kallonta tayi sai kawai ta jinjina kai tana murmushi tace "Shikenan, na barki lafiya."
Fita tayi a d'akin tana jinjina kai a ranta tana fad'in "Ku kaini bango kuka aiki da cikawa."
Fita tayi ta kai wa sheikh na shi abinci yana gama ci sukayi sallama ya fita. Haka har rana ta dora girki ta gama bata ga Hafsat ba sai zuwan yaran daga makranta ta dinga jin hayaniyarsu a d'akinta, tana gama aikinta ita dai ta shige d'akinta uta ma da abincin dan tayi niyya bama zata fito ba sai yamma in zata d'ora girki.
*Dare* ma haka suka kasance kasancewar sheikh bai shigo da wuri ba Mimi ta nemi su ci abinci, kowa ya zo amma ban da Aisha da Hafsat, saida ta gama zubawa su Heezam ta kallesu tace "Ina zuwa, bari na kira aunty."
Jinjina mata kai sukayi alamar to, tana zuwa ta fara k'wznk'wasa k'ofar tana sallama, jin ta amsa yasa ta turawa a hankali ta shiga, da ladabi tace "Aunty Hafsat ina kwana?"
"Lafiya lau." Ta amsa ba yabo ba fallasa, sharewa Mimi tayi tace "Abinci na ce ko zaki ci?"
Yatsina fuska tayi tace "Um um! A ci lafiya."
Ita ma yatsina fuskar tayi ta juya dan fita, k'wafa Hafsat d'in tayi ta jin haushin takurawar Mimin, juyowa Mimi tayi cike da shak'iyanci tace "Magana kike?"
A gatsala ita ma tace "Kika ji nayi?"
D'aga gira tayi tace "Ok, Allah ya kyauta."
Juyawa tayi amma dake Hafsat dama can fin k'arfin zuciyarta ne takeyi sai kawai tace "Ke! Rashin kunya zaki min?"
Juyowa Mimi tayi cike da rashin tsoro tace "Rashin kunya kuma? Kika ga alama zan miki?"
Sai kuma ta gyata tsayuwarta tace "Wai tsaya, ko dai haushina kike ji saboda na daki 'yata? To ai ke ma na ga kamar uwa kike gareni kina iya rama mata."
Mik'ewa tayi tsaye ta nunata da yatsa tace "K'arya kike wallahi, Aisha ba 'yar ki bace, da 'yarki ce ai da baki mareta a fuska ba, saboda baki san darajar haihuwa ba."
Bushewa tayi da dariya tace "Haihuwa? To ai ban tab'a yinta bane shiyasa, amma kwana nawa ne ya rage ni ma na haifo nawa."
Ta fad'a tana shafa mararta, girgiza kai Hafsat tayi tace "Dama da ganin idonki zakiyi fitsara, to ki ji da kyau karki k'ara dukar min yarinya dan b芒 jakarki bace, da fari na so baki girma da darajar da zasu dinga kiranki da Amie, amma tunda baki da mutumci na fasa."
Gaba d'aya jikin Mimi ne yayi wani irin sanyi har tsakiyar ranta ta ringa jin wani iri, yau gata ta daki yarinyar data mata rashin kunya a kan gaskiyarta amma mahaifiyarta da take jin k'aunarta a zuciyarta tamkar 'yar uwarta har tana jin ta samu 'yar uwa ta kalleta ta wulak'antata a kan hakan, anya kuwa idan jininta ce koma ta ce idan 'yar uwarta ce ko zane mata 'ya ta yi zata kula? Zata d'aga kai ta kalleta? Duk da zamani ya cenza amma akwai na kirki har yanzu, akwai zumunci har yanzu.
Shin Hafsat bata ganin irin abinda 'yarta ke yi ta katseta tunda wuri ko hakan na mata dadi? Shin Hafsat so take su fara zaman kishi da juna ko menene? A matsayinta na babba, babbar ma wace ta san ba haka kawai ta d'auko kanta ta kawo gidan mijinta ba a ganinta ya dace ta mata adalci.
Muryarta a sanyaye ta d'ago tana kallon Hafsat cikin ido tace "Allahn da ya baki aunty nima bai manta da ni ba, kuma ina rok'onsa idan ya tashi bani ya bani masu tarbiyar da ko da Abdul na da damar k'ara wani auren nan gaba su kirata da Amie, bare kuma ke, ke ina so yarana su kiraki da Mama, haka kawai na ga kin isa ki zama uwarsu dan a d'an zaman da na yi da mijinki sai nake ji da kuma ganin girma da darajar wani ma wanda ya rab'e shi bare matar daya hayayyafa da ita."
Suna tsaka da muhawarar nan sheikh ya shigo, rashin sa'a kuma shi ne daidai Mimi ta kuma sakin wani murmushi tana girgiza kanta ta bud'i bakinta zata yiwa Hafsat wata maganar wacce Hafsat d'in kuwa gaba d'aya yanayi na b'acin rai ya saka har wata k'walla da b'acin rai sun nuna a tare da ita, uwa uba a yau idonnta ko kwali babu tsabar ta sakawa kanta damuwa bayan ba haka Hafsat take ba, hakan ya saka hankalinsa tashe ya kuma nazartarsu kafin muryarsa kamar a d'an kausashe yace "Ryam, rashin kunya kika zo har d'aki kike yi wa matata ko me? Shin rashin kunya kike yi wa Hafsat? Kin kuwa san zan iya take komai na had'iye komai na danne komai amma banda cin zarafin uwar gidana? Kar na ji, kar na gani kar na ji kar na gani ko da wasa kar ki saki ki kuskura na kama ki da y iwa matata fitsara domin zaki yi mamakina Nana."
Da mamaki take kallonsa, yanayi na yarinta da d'anyen kai da b'acin rai ne ya sakata kuma kallonsa idanunta a bayyane tace "Wato ni ga matar kutse ko Abdul? Ni matar haye? Allah ya sa nima ce min aka yi jeki ga mijinki ba hauka nake a kanka ba bare daga kai har matarka ku wulak'antani!"
Ta karashe tana mai danne muryarta dake rawa sakamakon b'acin rai da kukan dake son k'wace mata.
Ransa ne ya b'aci saboda jin ya ya zata ringa maida masa magana ta wani siga wai kenan shi ga sakarai shi da bata so ko? Ransa b'ace ya nufota yace "Me kike nufi da maganarki? Kenan kina so ki nuna ni d'in banza wofi ne a wurinki? Ya zaki nemi raina min matata na miki magana kuma ki nemi yi min fitsara."
Cikin d'aga murya da kwaratsi Mimi ta ja baya tace "Ya isa! Ya isa haka."
Kallonshi tayi tana sako hawayen da take rik'ewa tace "Kowa sai ya dinga kirana da fitsararriya ko marar mutumci, to na gaji kunji na fad'a muku, idan zaman gidan nan ba zai yiwu ba ka sallameni na tafiya ta mana, a'ah, wai ana dole ne?"
Da wani irin sauri ya kai hannu zai shak'o wuyanta ya gaura mata mari, sai kuma ya tsaya tare da dunk'ule hannunshi yana kallon fuskarta, girgiza kai yayi ya feso iska dan maganar sakin nan na tab'a mishi zuciya wallahi, kai dole ma ya zauna zama na musamman da ita ya nuna mata babu kyau abinda take fad'a, wani numfashi ya kuma saukewa yana ci gaba da kallonta yace "Ryam ban tab'a dukan mace ba, ba zan fara yau ba, amma ki sani ita mace da kika gani kamar abun tuk'i ce, idan har kika zamar min mummunan abun tuk'i har tuk'inki ya k'wace min zan zama sakarai kuma malalaci, a gaskiya ba zan bari haka ta faru ba."
Ja baya yayi sosai ta yanda yake hangensu tsaye dukansu kuma yana kallon kowace yace "Na yardaina sonki ne daga lokacin da muka fara zama a matsayin ma'aurata, soyayyata ta farko gareni na farata, k'aunarki na gaba d'aya zuciyata saboda ke d'in nan ke ce b'angare na jikina, zubar hawayenki ba k'aramin d'aga min hankali yake ba, karki so kiji yanda zuciyata ke bugawa musamman dana shigo d'akin nan na fahimci ba kya cikin farin ciki, ina son ki, na fad'a miki haka bila-adadin, ki yarda, ki yarda da ina sonki kinji."
Kamar shed'an nan da aka tofawa a'uziya haka duk suka zuba mishi ido sukayi tsuru, kowace tana d'aukar kalamai tana d'orasu a muhalli, saidai kuma wani b'angare na zuk'atansu na sa musu wasi-wasin da wa yake a ciki? Musamman Mimi da tafi raja'a ce wa da Hafsat yake, a wajen k'arshen ne kawai zata ce da ita yake dan yana yawan fad'in yana son ta kuma ta yarda. hafsat kam ta yarda tabbas da ita yake, tafi kokonton me yasa bai tsayar da kallonshi kan ta kawai ba.
Mimi kam juya baki tayi tace "Ni da ba'a so sai naje na nemi mai sona ai."
Tsai yayi yana kallonta, "Inna lillahi wa'inna ilaihi raju'un." Ya fad'a a zuciyarshi, wallahi wani irin gudu zuciyarshi tayi sanda ta anbaci ya sallameta, anya kuwa ba mutuwa zaiyi ba ko kuma dai yarinyar nan ce hawan jinin shi ba? Kasa maganar da yayi yasa ta kallonshi tace "Ba ma kada lokaci na ko? Shikenan ka tura min takardata a gidanmu."
Juyawa tayi zata fita ya rik'o hannunta a mugun firgice, kallon juna sukayi tana kallon yanda yake sauke numfashi. Sautin kukan Hafsat daya ji ya dawo dashi daga shirin fad'in "Ryam kiyi hak'uri, karki tafi dan Allah."
Kallon Hafsat yayi cikin fizgo kalamai yace "Me ya had'u Manga? Ban san ki da rikici ba."
Da sauri ta nuna Mimi tace "Ka tambayi dak'ikk'iyar yarinyar nan mana."
Kallonta Mimi tayi da mamaki tace "Dak'ikk'iya kuma?"
Kallon sheikh tayi tana jiran ta ga me zaiyi amma sai wani kakkawar da kai yayi kamar mai kokarin b'oye kukanshi, fizge hannunta tayi ta kallesu da kyau tace "A tare na sameku dama, zan tafi na barku yanda na ganku, ni ma Allah zai had'ani da wanda zai iya kare kima da darajata, amma wannan ba gidan zama bane."
Tana fad'a ta juya da sauri ta fita a d'akin wanda kowane tako ke sauka kan k'irjin sheikh, iya yanda mazaunanta ke juyawa cikin tafiyar b'acin rai yasa jinin jikinshi rage saurin gudu. Juyawa yayi ya kalli Hafsat dake ta sharar hawaye, wani iska ya feso dan gaskiya zuciyarshi na son ya bi *yarinyarshi*, amma kuma ga Sawwama na kukan b'acin rai wanda bai tab'a ganin hakan daga gareta ba, duk da bai san asalin me ya kawota d'akin ba yasan dai zaiyi wuya a ce bata da gaskiya.
Zaunar da Hafsat d'in yayi ya zauna gefenta yana shafa bayanta ya kasa ceewa komai dan hankalinshi da nutsuwarshi na wani wurin gaskiya.
Mimi kam na fita ai kuwa da gaske take dan akwatin da aka mata na lefe ta d'auko guda a ciki ta shiga zuba mata kaya saida ta mata nak da kaya ta d'auki hijab ta saka ta fito, su Heezam na zaune suka ga fitarta babu wanda ya mata magana saidai suna fatan ba matsalar Aisha ce ta jawo wannan babbar matsala ba.
*Alhamdulillah*
06/08/2021 脿 11:58 - Mme Ishaq馃拑馃グ: 馃懇鈥嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈�
*MATAR MUTUM*
_(K'abarinsa)_
馃懇鈥嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈�
*NA*
_SAMIRA HAROUNA_
*SADAUKARWA*
_GA DUKA_
*'YAN AMANA TA*
馃挮鉁� *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*馃専
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_馃
鈽� *[ T.M.N.A]* 鈽� 馃摉馃枈锔�
https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/
_Bismillahir rahamanir rahim_
*50*
Jin yanda zuciyarshi ke ta buga mishi da sauri har sai ya bud'e baki yake sauke numfashi yasa shi d'an janye Hafsat daga jikinshi ya mik'e, zai fita ta rik'o hannunshi ya juyo suka kalli juna, cikin dakusashiyar murya tace "Kayi hak'uri idan na b'ata maka rai."
Kasak'ai yayi yana kallonta kamar baya hayyacinta sai kuma ya kawar da kan shi yace "Ya zanyi idan ba hak'urin ba, tunda kun sani mun taru mun wa yarinya rashin adalci, mun nuna mata mu jahilai ne marasa tunani..."
Sab'ule hannunshi yayi daga rik'on data mishi ya juya ya bar mata d'akin, da kallo ta bishi tare da jin wata matsananciyar kunya ta rufeta, sai ta samu kan ta da jin nauyin kan ta da kuma mijinta da Mimi, tabbas tasan abinda ta aikata har da rashin fitar da abinda ke ranta da tayi na wani lokaci, shiyasa yanzu ta fake da abinda ya faru ta d'an furzar da abinda ke ranta, gashi sun tafi sun barta da tunani kamar kan ta zai fashe. Alamu sun nuna sheikh yayi hushi da ita, ga kuma mamakin yarinyar da take kallon fuskar mijinta tana kiranshi da Abdul.
Wani lallausan murmushi ta saki ta furta "Har yanzu bana iya kiransa da sunan Abdul Waheed ko da bayan idonsa ne, amma ita kai tsaye a gabanshi take kiran Abdul Abdul."
Yana fita a rud'e ya nufi d'akin Mimi, ganin bata nan sai kaya dake kan gado a barbaje yasa shi durk'ushewa ya kifa kanshi a gadon yana furta "Inna lillahi wa'inna ilaihi raju'un."
Ya maimaita haka sau uku kafin ya mik'e yana lalubar wayarshi tare da fita a d'akin ya nufi waje, d'aya daga cikin jami'anshi na ganinshi ya taso a sukwane, da sauri ya tara masa hannu yace "Makulin mota?"
Da girmamawa yace "Sheikh mu je sai na sauk..."
Bai gama fad'a ba a tsawace yace "Ka bani makulli bana so."
Da sauri ya mik'a mishi yana ja baya da d'umbin mamaki, tunda suke haka bai tab'a faruwa ba sai yanzu, bak'ar Mercedes ya shiga yana d'ora waya a kunne yana kiran lambarta, data fara k'ara sai ta kashe kiran hakan ya k'ara d'imauta tunaninshi, yana fita dama ya nufa da fatan had'uwa da ita, saidai sam bai ga alamarta ba har saida ya iya kwanar unguwarsu.
K'ofar gidan ya k'urawa ido yana kallo dan yasan dai nan zata zo, amma shiru bai ga alamarta ba saida ya d'auki waya ya sake danna kira, k'it ta datse kiran da sauri ya shiga rubuta mata sak'o kamar haka _"Ryam ki rufa min asiri, karki d'ora min hawan jini da tsufana, dan Allah na rok'eki."_
*Mimi* kam ta jima da shiga gida dan haka ma bai ganta ba, tunda ta shiga taxi take kuka kamar an mata mutuwa, tana fita ta mik'awa mai taxi jaka guda ta shige gida da jakarta, Abba dake shirin fita kicib'us sukayi a k'ofar shiga, kaucewa yayi a hanye ta wuce yana d'aga kai sosai yana kallonta da fad'in "Ke daga ina? Uwata anya kuwa baki da aljanu? Me ya fito dake yanzu daga gidanki?"
Durk'ushewa tayi ta fashe da wani kukan ba tayi magana ba, sake gusawa yayi a bakin k'ofar yace "Ina zaki da k'atuwar jaka haka?"
Had'a kanta tayi da gwiwa cikin kuka tace "Abba ni gidanmu na dawo, Abba na ba zan iya zama a gidan Abdul ba, wallahi bak'in cikin 'ya'ya..."
Da k'arfi ya kai mata bugu a baki yana fad'in "Astagfirullah! Uwata sheikh d'in ne Abdul kai tsaye? Ban gane ba zaki iya zama ba ?"
Juyawa yayi ya kalli k'ofar d'akinsu ya k'walla kiran sunan Mama da "Rabi, Rabi'a kina ina? Zo nan zo kiga haukan 'yarki."
Da sauri Mama ta fito k'undul k'undul kamar zata fad'uwa tana fad'in "Malam lafiya?"
Nuna mata Mimi yayi data rufe bakinta daya buga yace "Ga ta nan ta fad'a miki kiji."
Kallon Mimi tayi hankali tashe tana jin wani suka a zuciyarta bakinta na hard'ewa tace "Mimi lafiya? Me ya faru?"
Abba ne yayi tsal yace "Ba wani lafiya, wai fad'i take ba zata iya zaman gidan sheikh ba, ke dan Allah a nan gidan ba hak'uri kike dani ba ?"
Sunkuyar da kai Mama tayi tana jin kamar tace mishi ya fita ya barsu ita da 'yarta ta ji me ye matsalarta, amma yanda ta ji ya fara fad'in "Ke Maryama bana son shashancin banza da wofi, ni zaki mayar k'aramin mutum da bai san me yake ba, duka yaushe kika tare a gidan na ki da zaki fara min yaji, kenan kinfi k'arfin a b'ata miki rai ke 'yar gwal? Yanzu haka ma ba da izinin gafarta malam kika taho ba, to ni ba za'ayi haka dani ba, maza tashi ki koma gidanki kamar yanda kika kawo kan ki, ba zan zauna na baki mafaka a gidana ba kwana kad'an ki fara min laulayi kamar yanda uwarki ke fama da na ta laulayin."
Da sauri Mimi ta d'aga kai ta kalleshi sai kuma ta kalli Mamanta, a ranta tace "Mama ciki ne da ita?"
Sai kuma ta yatsina fuska tace "Allah sawak'e ma na d'auki cikin mutumin nan, tsoho kawai da wata akwalar matarshi da 'ya'yanshi marasa kunya."
Had'e fuska ta sakeyi ta kalli Abba ta marairaice tace "Abba dan Allah karka koreni a gidan nan, Abba ka ga fa da shi da matarshi da 'yarsu suka min taron dangi, ni wallahi Abba..."
Takalminshi ya cire yana fad'in "Ke in ban kakkarta miki..."
Ganin Mama ta juya tana rufe bakinta dan dama ya gama kasheta da kunya tunda yayi maganar cikin nan yasa shi binta da kallo, Mimi da tuni ta mik'e da gudu ta fita waje ta fashewa da kuka, akwatin ya kama da nufin cilla mata ita saidai ta fi k'arfinshi dan a tsayi ma kusan kansu d'aya da akwatin, turata ya dinga yi saida ya fito mata da ita ya nunata da yatsa tana tsaye nesa da shi yace "Wallahi kika bani na d'aga murya a kan ki ba zakiji dad'i ba uwata, har gidan na ki zan sameki na zazzabga miki dukan mutuwa."
Cikin sand'a ta jawo akwatin na ta tana kallonshi ya koma cikin gidan yana fad'a, had'e hawayenta ta kalli unguwar ta su da kyau, duk da ba dare bane sosai amma babu mutane sai masu wucewa, numfashi ta sauke cikin disassashiyar murya tace "Kayi hak'uri Abba na ka yafe min, amma ba zan iya komawa gidan Abdul yanzu ba, idan na koma kamar ban da zuciya ne da kuma gata, ku a wajenku haka da kukayi shine daidai, amma ni tunda ni ke zaune dashi dole na bi kowaxe hanya dan samawa kai na mutumci a gurinshi, Mama na ta fad'a min na koyi yanda zan kula da kai na, kuma na yi alk'awarin zan k'watarwa kai na 'yancina ba tare da taimakon kowa ba."
A hankali ta ja akwatin na ta ta d'auki