Showing 129001 words to 132000 words out of 185502 words

Chapter 44 - Matar Mutum Book 1 Hausa Novel Complete

20 Dec 2024

505

zazzabga miki bulalar da zata fahimtar dake me nake nufi."

Tsaf ta had'e kuka tayi k'asa da kanta, nuna mata k'ofar ban d'aki yayi yace "Maza je kiyi wanka kiyi alwala kiyi sallah."

Jiki na kakkarwa ta shiga saukowa daga kan gadon, saidai allurar da har yanzu bata gama sakin jikinta yasa k'afafunta kasa d'aukarta, shirin fad'uwar da tayi yasa shi azamar tallabota jikinshi, cak ya d'auketa ya nufi ban d'akin da ita yana kallon fuskarta fuskarshi a had'e yace "Yarinya sai taurin kai, bakya gane magana cikin sauk'i."

Tsayar da ita yayi ya shiga cire mata kayan jikinta, nok'ewa ta shiga yi ita ma hakan yasa shi d'aga kai ya kalleta yace "Miye na kunyar kuma? Ba mun zama d'aya ba?"

D'auke kanta tayi tana kumburo baki, murmushi yayi yace "Shikenan bari ki gani, aidai zakiyi k'orafin na kalleki babu kayana ne ko? To bari muyi wankan a tare."

Kar-kar-kar! Jikinta ya fara ta shiga taka k'afafunta zata fita a ban d'akin, rik'ota yayi ya had'ata da k'irjinshi yana kallon fuskarta yace "To miye a ciki? Ni ba naki bane?"

Ko kallonshi ba tayi ba ta shiga sinne kan ta k'asa, b'alle botir d'in rigar yayi tare da tattarota daga k'asa yayi sama da ita, yanda ta ganta kwance a k'irjinshi da babu riga sai kwantaccen bak'in gashin daya kusa mamaye knirjin mai sulb'in gaske kamar na kan shi yasa ta saurin juya baya, hakan ya bashi damar k'arasa cire...馃槑 ya jawota ya had'a da jikinshi, yanda yaji jikinta ya fara d'aukar zafi da gaske ga rawar da yake mata yasa shi sakin murmushi ya d'ora hab'arshi a kafad'arta cikin kunne ya rad'a mata "Ryam ga ki da tsoro amma kuma ke ma kina bada tsoro."

Kakkaucewa ta shiga yi saboda kayan jikinta daya fara shirin cire mata, bai bata damar matsawa nesa da shi ba saida ya rabata da kayanta, yanda jikinsu ke gugar na juna tana jin duk wata hallita ta bawan Allahn nan a fatar jikinta sai ta nemi numfashi ta rasa, gaba d'aya ta sarewa lamarin mutumin ko ta ce lamarin maza.

Duk girmanshi, duk shekarunshi, duk matsayinshi yanzu nan ya aje su gefe har ya tsaya gabanta babu kaya zasuyi wanka? Tunda taja numfashinta sama bata maido shi ba ita dai ta k'ame wuri d'aya ta rintse idonta dan b芒 zata iya kallonshi ba. Sheikh ko a jikinshi, wanka yake musu sosai cikin nutsuwa tare da wasa da ita, Mimi dai abun jin shi take wani iri, ita dake burin d'an k'aramin mijinta suyi wanka tare sai gashi yau old man ne ke mata wanka kamar baby.

Tana jin sanda ya kashe panpon ruwan suka tsaya, jim kad'an taji yana saka mata rigar wanka, kamo hannunta yayi suka fara takawa tana jin k'asanta na d'an mata zuzar zaren d'inkin nan hakan kuma na k'ara mata rad'ad'i.

Kan kujera ya zzunar da ita gaban madubi, mai ya d'auka ya durk'usa ya fara shafa mata man, kallonshi take yanda har yanzu towel ne a k'ugunshi, sam sai yake mata kamar ba tsoho ba, yanda yake d'aukarta da yanda yake sarrafa jikinshi ba alamar manyanta irin ta tsofaffin da zaka ga suna fama da ciwon baya k'afafu da sauransu. Yanda take kallonshi idonta bud'e yasa shi sakin murmushi yace "Inna Issa har yanzu ba zaki min magana ba."

K'in d'auke idonta tayi a kan shi, d'an murmushi kawai ya sake saki ya ci gaba da murza mata mai, yana gamawa doguwar riga abaya ya d'auko a cikin kayan daya k'ara zuba mata na ban mamaki, pant ya d'auko da bras ya sake durk'usawa ya zura mata k'afafun, kamata yayi ta mik'e zai k'arasa saka mata sai kuma ya kalleta, d'an sosa kai yayi da irin alamar jin kunya yace "Yan matan tsohonta, anya kuwa wannan zai isheki? Ni fa kallon baby nake miki."

D'auke idonta tayi daga kan shi ta k'arasa saka wandon, tam ya mata alamun dai ya matseta sosai, d'aukar bras d'in tayi ta saka ita ma haka ta mata kip, d'aukar rigar tayi ta saka da sauri ya zaunar da ita kan kujerar, macaji ya d'auka ya fara caje mata gashinta, tsaf ya d'aure mata shi da mad'auri sannan ya d'auki kallabin rigar ya fara yane mata kan cike da k'warewa, yana gama mata ya tallabo fuskarta ya sumbaci goshinta sannan ya nuna mata sallaya yace "Kiyi sallah, zan je na saka kaya nima."

Takawa tayi ta k'arasa gaban sallayar, tana ganin fitarshi a d'akin tayi saurin cire pant d'in nan dan yana tab'ata a jikinta sosai tana jin zafi saboda d'inkin da aka mata, sallah ta kabbara shi kuma ya shiga d'akinshi dake nan b'angarenta dan shiryawa.



*Asa-Ma'u*


Tunda Asma'u ta zauna jiran Mimi ta ga ba alamarta sai kawai ta ma Hafsat sallama suka taf tare da Kabiru, ita ma suna zuwa gidan suka had'e da Asas, ita kanta sai ta ji kunya da suka had'u da shi ba'a gida ba, a d'arare ta bishi suka nufi na su gidan suma.

A daren kam tasha abubuwa da dama, kunya, fad'uwar gaba, farin ciki da kuma bak'ar wahala, dan kuwa Asas ya nuna mata ya samu lafiya, sun sha amarci sosai da kuma soyayya har garin Allah ya waye, daga wajen Hajia kawai yasa aka kawo musu abinci suna ci ya dunk'ule matarshi a bargo suka shiga ramuwar bacci.

Sake matseta yayi a jikinshi yace "Husna."

A hankali ta amsa da "Na'am."

Cikin taushin murya yace "Kina so na?"

Sinne kanta tayi a k'irjinshi tana d'an shafa cikinshi da hannunta ke kai tana murmushi, cikin shafa bayanta yace "Ina jinki mana, ko ba kya so na?"

Girgiza kai tayi a hankali tace "Ni ban ce ba."

"To me kika ce kenan?" Ya fad'a kai tsaye, cike da jin kunya tana b'oye fuskarta a jikinshi tace "Taya zan ce bana son mijina wanda a yanzu ya zama sirrina, a yanzu fa babu wani abu daya mana shamaki ni da kai, ko na so ka ko na k'i ka ka riga daka zama wani b'angare na jikina."

Matseta yayi sosai ya sumbaci kanta cikin dadad'an murya yace "Ina sonki *Asmy* na, ina sonki sosai, Allah barmu tare."

Cike da jin ya k'arawa kanta girma da farin ciki ta matseshi ita ma cike da jin kunya murya k'asa k'asa tace "Ni ma haka."


D'an tsakulkuli ya mata yana dariya yace "Ke ma me? Sai kin fad'a fa malama ko nima na dawo da kayata na rik'e."

Cikin bille bille ta shiga k'yalk'yala dariya tana fad'in "Nima haka, na fad'a to na fad'a."

Dakatawa yayi yace "Me kika fad'a to? Fad'i ko kuma na sake juyewa a kan ki yanzun nan, dama ba isata kikayi ba dan naji kin k'ara wani irin dad'i."

Dukanshi tayi a k'irji cike da kunya tace "Kai wallahi, haba dai."

Cikin dariya yace "Gaskiya na fad'a ai, na tabbata shirya min kanki kikayi kafin dawowata."

Girgiza kai tayi tace "Ni ba abinda nayi."

"Kin tabbata?" Ya tambaya yana lek'an fuskarta, jinjina kai tayi alamar eh, murmushi yayi yace "To yanzu fad'a min na ji, ke ma kina so na?"

Turo baki tayi tace "To wai me yasa ka damu da sai na fad'a maka nima? Ka yarda da abinda na fad'a maka mana."

Mak'ale kafad'a yayi yace "Um um! Kawai ki fad'a min Husna ko nayi kuka."

Waro ido tayi ta kalleshi da mamaki yanda kam duk ya kyab'e fuska shi shagwab'abb'e, kunya tasa ta rufe fuska tace "To ni ma ina sonka."

Sake k'amk'ameta yayi yana murmushi yace "Ko ke fa, har na ji dad'i."

Cikin farin ciki suka samu baccinsu a nutse suna k'amk'ame da juna kamar dama can asali masoya ne.




*Mim-Sheikh*


Cikin wata dakakkiyar shadda ya shigo d'akin wacce ta sa shi bayyana sak a angonshi, fara ce shaddar ga rigar daya d'ora irin ta malamai ga hula da takalmi k'afa ciki, shagala tayi da kallonshi dan gaskiya da zata iya bud'a baki a wannan lokacin tayi magana to zata ce "Kayi kyau." Ne, amma data ga yana mata murmushi saita d'aure fuska har saida ya tsaya gabanta yace "Zamu iya tafiya?"

Mik'ewa kawai tayi ta nufi hanyar fita, rik'e hannunta yayi suka kalli juna, ba alamar sakin fuska yace "Bana son jin shirun nan idan muka fita, zan d'auki wannan shirun ne kawai saboda ni na ja, amma iyalina ki girmama min su ta hanyar bud'a baki kiyi magana idan sun miki, Hafsat a gaba take da ke, karki jira sai ta gaisheki kafin ki gaisheta."

Shafa kumatunta yayi yace "Kin gane?"

Sunkuyar da idonta tayi saboda k'wallar da taji sun cika mata ido, tallabo fuskarta ya sake yi cikin sanyin murya yace "Kiyi hak'uri kinji, nayi alk'awari na yau kawai zan baki lokaci na gaba d'aya, zan sa ki fara tunanin tsohonki a zuciyarki, sannan nayi alk'awarin saka murmushi a fuskarki yau d'in nan."

Kama hannunta yayi suka shiga takawa a nutse, ta k'ofar waje suka fita kafin ya zagaya ta k'ofar shiga falon Hafsat, saida ya d'an k'wank'wasa sau uku kafin ya shiga da sallama a bakinshi yana sakin hannun Mimi, yaran dake zaune dukansu falo suna karatu ne suka juya suna kallonshi da amsa sallamarshi, da k'yar da lahaula ta cira labb'anta ta furta "Assalama alaikum."

Ido suka fara zuba mata da d'an mamakin nan ta kwana ko me? Sai kuma suka amsa mata sallamar suna gaishe da mahaifinsu a ladabce, cikin k'arfin hali Mimi ta kallesu da fara'a tace "Karatu ake."

Kallonta suka sake yi dukansu sai Munzeer dake k'arami daya washe mata baki yace "E aunty."

Sheikh ne ya kalleshi yace "Ina mamanku?"

Nuna d'akinta yayi yace "Tana ciki."

Hanyar nufa d'akin Hafsat yayi sai kuma ya kula da wani kallo da Aisha da Heezam suka rakashi kallo ne mai tattare da "Abienmu me kake nufi? Yarinyar nan anan ta kwana? D'aki guda kai da ita?"

Sai kawai ya ji ya tsargi kansa, saidai baiji kunya ba dan ita ma matarsa ce, halalinsa ce ba kuma haramun ya aikata da ita ba. Tsaye yayi dan sai yake ganin kamar zasu iya dakuwa da ita idan ya matsa, Mimi kuma da tsayuwar ta gundureta zaune tayi a kan kujera tana kallonsu ita ma.

Zai sake nufa d'akin Hafsat sai gata ta fito da hijab d'inta a jikinta, duk zuba mata ido sukayi har ta k'araso da sakin fuska tana kawar da komai daga ranta tana fad'in "Mimi da safe haka aka taso ki? Amma dai sheikh ka shiga lokacinta."

Duk murmushi sukayi sai Mimi data sunkuyar da kai tace "Ina kwana aunty."

Da fara'a tace "Lafiya lau Mimi, antashi lafiya?"

Da kunya ta amsa da "Lafiya lau."

D'orawa tayi da "Ya kwanan bak'unta kuma?"

D'an murmushin yak'e kawai tayi sai muryar Munzeer da suka ji yace "Amie gidanmu aunty ta kwana?"

Da fara'a Hafsat ta kalkeshi tace "E."

Aswan kam kamar da gangan kamar sub'utar baki sai cewa yayi "A b'angaren Abie ta kwana?"

Kallonshi duk sukayi sai Mimi da taji kamar ta k'urma ihu, a tsawace Hafsat ta kalleshi tace "Aswan wace maganar banza ce wannan? Ina ruwanka to?"

A tsorace ya kalli Hafsat yace "Amie kiyi hak'uri dan Allah, ba zan sake ba."

D'auke kanta tayi ta kalli sheikh daya tsurawa Aswan ido yana tunanin dole yayi wani abu gaskiya, Aisha dake mace zai matsar da ita dan za'a fi samun matsala da ita saboda mace ce, mazan kuma dama dai lokacin karatunsu yafi yawa akan lokacinsu na zama gida, dan haka zaiyi k'ok'ari yaga raini bai shiga tsakaninsu da matarshi ba.

Kallonta sheikh yayi yana k'ak'aro murmushi yace "Manga kin tashi lafiya?"

Da fara'a tace "Lafiya lau, antashi lafiya?"

Da fara'a shi ma ya amsa da "Lafiya lau."

A ladabce tace "Ya gajiya kuma?"

Kashe mata ido yayi yana murmushi amma bai ce komai ba, girgiza kai tayi tana murmushi ita ma ta d'auke idonta daga kanshi, d'orawa yayi da fad'in "Manga zamu fita da yarinyar nan mu dawo, ba wara matsala?"

Murmushi ta fad'ad'a tace "Ba matsalar komai sheikh, Allah ya tsare hanya, sai kun dawo."

Mik'ewa Mimi tayi tana d'an cije baki, kallonta Hafsat tayi tana sakin murmishi tace "A dawo lafiya?"

Da murmushi ita ma ta amsa da "Allah yasa, mun gode."

Gaba Mimi tayi sheikh ya ma yaran addu'a kamar yanda ya saba kafin ya bi bayanta yana duba agogon hannunshi ta azurfa data nuna k'arfe *06:20* na safe, da kanshi ya bud'e mata gaban motar ta zauna ya rufe kafin ya zagaya ya shiga suka bar gidan.



*Sorry mutane na, wlh gaba d'aya ne aka d'auke mana network.*




*Alhamdulillah*
06/08/2021 脿 11:57 - Mme Ishaq馃拑馃グ: 馃懇鈥嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈�
*MATAR MUTUM*
_(K'abarinsa)_
馃懇鈥嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈�

*NA*


_SAMIRA HAROUNA_


*SADAUKARWA*


_GA DUKA_

*'YAN AMANA TA*


馃挮鉁� *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*馃専
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_馃

鈽� *[ T.M.N.A]* 鈽� 馃摉馃枈锔�

https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/

_Bismillahir rahamanir rahim_


*43*



Wani k'ayataccen gida ya sauketa da gaba d'ayanshi bai wuce zaman mace d'aya, tun wajen gidan take kallo kamar wata bak'auya, komai na gidan sai taji ya birgeta daga tsarin gidan zuwa kayan cikinshi, a matsakaicin falonta zaunatana kallo ya shiga ciki, ta d'an jima zaune kafin ta ji bud'e k'ofa alamar zai fito.

Sunkuyar da kanta tayi saida ta ji shi tsaye a kan ta yana fad'in "Ryam me zaki ci na dafa miki?"

Da sauri ta d'aga kanta ta kalleshi jin wai yace ya dafa mata, k'walalo ido tayi da matsanancin mamakin ganin shi da k'ananan kaya, riga da wando masu kamar na sport kamar kuma na bacci, amma irin kayan da yan zamani har fita suke dasu idan suka saka, wani irin kyau daya mata da kayan yasa ta saurin had'e mamakinta ta mayar da kanta k'asa a ranta tana fad'in "Oh Allah, wai me ye haka? Shi ma dai d'an duniya ne ashe."

Gaban tv ya k'arasa ya kunna mata wani caset naa wa'azin Hafsat wanda tayi shi ne lokacin auren wata daga cikin d'alibanta, dake magana ce tsantsa akan zamantakewar aure shiyasa ya kunna mata shi, dawowa yayi gabanta ya sunkuya ya rik'o hannayenta yace "Ryam, ni ne ba zaki ma magana ba?"

Lumshe ido tayi alamar eh, marairaicewa yayi yace "Saboda me? Dan na kaiki mataki babba?"

Jinjina kai tayi alamar e, numfashi ya sauke yana murmushi yace "To na ji kiyi hak'uri, yanzu fad'a min me zaki ci na kawo miki, idan kin gama kinga ke ma saiki rama ko? Haka ya miki?"

Girgiza kai tayi tana kawar da kan ta, wata ajiyar zuciya ya sauke kafin ya mik'e zai shiga k'aramar madafar, hannunshi da har yanzu bai k'arasa sakin na ta ba tayi saurin rik'ewa gam, juyowa yayi yana kallonta, cikin had'e fuska ta kawar da kai tace "Ni gida nake so ka kaini."

Sake sunkuyawa yayi yana kallon fuskarta yace "Me zakiyi a gida idan na kaiki Ryam? Ba kya jin kunyar Mama ne ke?"

Turo baki tayi gaba cikin shagwab'a tace "To ai ba zan fad'a mata komai ba."

Murmushi yayi ya girgiza kai yace "Ryam, ko ni dake namiji idan na kalli mace ina iya fahimtar halin da take ciki, bare kuma uwa mace, dole mama na kallonki zata fahimci me ya faru da ke? Ko kina so ki ce min Mama bata tab'a saka miki ido bane?"

Jim tayi kamar mai tunani hakan yasa shi fad'in "Idan kina so zan kira miki Abbanki sai na baki shi ku gaisa."

Had'e yawu tayi sai kuma ta jinjina kai alamar to, murmushi yayi na jin dad'i ya shafi kuncinta yana fad'in "Yarinyar kirki kenan."

Mik'ewa yayi yana zame hannunshi a nata yace "Ina zuwa."

D'akin daya shiga ya koma jim kad'an ya dawo da waya a hannu, yana zuwa ya mik'a mata yace "Gashi sai ki kira."

Karb'a tayi shi kuma har ya juya sai kuma ya tsaya yace "Fad'a mine zaki ci to?"

Sake turo baki tayi gaba ta nok'e kai tace "Ni bana cin girkin maza, mazan ma wanda basu da k'warewa."

Fad'owa yayi kan kujerar ya mata rumfa kamar zai tausheta yana mata wani shu'umin kallo, had'ewa tayi a jikin kujerar tana sinne kan ta, cikin wani irin salo yace "Ni ne ban da k'warewar? Fad'i abinda kike so na girka miki idan ba tsoro ba."

Cikin sissine kai tace "Indomie."

Wani murmishin gefen labb'a yayi yace "Taliyar yara zaki ce, to kazarki kuma fa?"

D'an d'aga idonta tayi ta kalleshi da alamar tambaya, d'aga mata gira yayi yace "E, kazar amarcinki fa? Na kawo miki ne ki ci?"

Shiru tayi sai turo baki da take yi gaba, caraf ya damk'i leb'enta na k'asa yasa a bakinshi ya tsotsa kamar wata alawa, saida ya ja leb'en kamar zai cirashi ya sakar mata baki yana fad'in "Bani minti biyar yan matan tsohonta."

Yana fad'a ya shige madafar, da kallo ta rakashi tana jin kanta na neman fashewa saboda abubuwan da tsohon ke zuwa mata da su, a gaskiya sai ta ga ya koma mata wani sharaf da shi a cikin k'ananan kayan, sai ta rantse kamar bai tab'a kyau irin na yanzu ba, ko kuma dai bata saba ganinshi da irin kayan bane?

Wayar dake hannunta ta shiga saka lambar Abba, tsaf lambar ta fito da sunan *vieux* (tsoho), bata san lokacin data mik'e tsaye ba ta dafe k'ugu tace "Lallai ma!"

Ai da sauri tsabar jaraba ta nufi madafar, tana isa k'ofar a bud'e take yana tsaye yanaa aiki kam tuk'uru, cike da yarinta ta nuna wayar tace "Yanzu Abban na wa ne tsoho?"

Juyowa yayi yana kallonta da mamaki sai kuma ya d'aga kafad'a yace "Gare ni na ji."

Cikin turo baki tace "Kamar ya gareni? Ni fa Abba nake cewa."

Juyowa yayi da kyau yace "Ranar aurenmu na ji kince tsoho ne, shiyasa ni ma na rik'e a kai na."

Shiru tayi alamar tunani, sai yanzu ne ta tuna sanda tace ta so nemawa Abbanta auren Asma'u saboda nagartarta, tab'e baki tayi ta murgud'ashi tace "Ai dai Allah bai ce hakanan ba, ina laifin ma

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login