Showing 24001 words to 27000 words out of 185502 words

Chapter 9 - Matar Mutum Book 1 Hausa Novel Complete

20 Dec 2024

480

shiga caracterta ta jiya a gaban ustazu tayi shiru, daga b'angarenshi ne ya rangad'a sallama a sanyaye sosai, saida ta kalli Jamila kafin tace "Wa'alaikumus salam, barka."

Da sauri Asma'u ta k'yafaceta a kafad'a tana mata nuni da ido da hannu "Sheikh d'in zaki ce wa barka?"

Yatsina fuska tayi da sauri ta kalli wayar tana sauraren yana fad'in "Ryam antashi lafiya?"

A sanyaye ta amsa da "Lafiya lau sheikh."

A hankali yace "Ba sheikh ba, Abdul, ki kirani da Abdul Ryam hakan zai sa na ji nima bawa kuma ba kowa ba."

Da ido ta musu alamar ba kun ji ba? Ai na fad'a muku, jinjina kai sukayi suka sake kafe kunnuwansu, a nutse cikin murmushi tace "Wacece ni da zan sake maimaita wannan kuskuren, na jiya ma sub'utar baki ce."

D'an murmushi yayi har tana jin sautinshi kafin yace "Na so hakan, kuma akwai lokacin da zai zo na tursasaki fad'ar Abdul."

Da alamar tambaya duk suka kalli junansu, a nutse suka sake jin muryarshi yace "Ryam Abbanki ya dawo ne?"

Cikin rarraba ido tace "A'a bai dawo ba."

Rik'e hab'a Asma'u tayi alamar mamakin nan tana kallonta, cikin taushin murya yace "To me yasa kika kirani?"

Cikin murmushi tace "Tun jiya da kuke kira ne sai naji bana jin dad'in ganin lambarku a jan rubutun nan, shiyasa na karb'i wayar a hannun mama na kira."

Duk mamaki ne ya kusan kashe su Asma'u dake kallonta da saurarenta, ita kam ko a jikinta saima saurarenshi yana fad'in "Ba kina islamiyya ba?"

Da "Eh ina yi." Ta amsa, kallon agogo yayi a lokacin yace "Amma naga 10:14, kuna hutu ne ko?"

Jinjina kai tayi tace "Eh dake yau ban je islamiyya ba, saboda k'anina da baya da lafiya, jiya ma magani na siyo mishi muka had'u, shiyasa na zauna taya mamana aiyukan gida da kula dashi."

Cikin jin dad'i yace " Masha'Allah, Alhamdulillah, na ji dad'i sosai da kika kirani, na kuma gode."

A ladabce tace "Nima nagode, muna barar addu'a."

Lumshe ido yayi daga inda yake, to wai me yasa kowa ke fad'an hakane? Shin bakinshi yafi na kowa tsarki ne? Ko kuma waliyi ne shi da aka bugawa hatimin waliyantaka? D'an sauke ajiyar zuciya yayi yace "Insha'Allah, nima ina barar addu'arki."

Tana cikin k'yak'yabta ido yace "Zan sake kiranki anjima, ina wajen aiki ne."

A sanyaye ta amsa mishi sukayi sallama ta kashe kiran, cike da kuri da k'apapa ta shiga kallonsu a sama tana fad'in "Me na fad'a muku? Mak'aryaciya kuka d'aukeni ba."

K'wafa tayi ta mik'e tsaye cikin takon kuri da isa da k'asaita ta fita a ajin dan neman abinda za ta ci, kallon da Asma'u ta bita dashi ne yasa Jamila fad'in "Ke daina kallonta, Allah ne ya bata farin jinin nan sai hak'uri."

Harara ta galla mata tace "Na ce miki ina haushin hakane, ai baiwarta a jikinta take."

Sai lokacin kawai Aisha ta samu damar fad'in "Wallahi ni har birgeni take, farin jini ne da ita kamar k'asa mai tsarki, da babba da k'arami da tsoho da yaro mai kud'i da talaka kowa son ta yake."

Jinjina kai Asma'u tayi tace "Shiyasa ai take murza kambunta yanda take so."

Jamila ce tace "Kamar yanda idan ta shiga gidan sai labari ba."

Asma'u ce tace "Gaskiya ne kam, dan tana aure komai zai zama tarihi."


*Asas*


Kafeshi tayi da ido har ya gama d'aure takalminshi k'afa ciki ya mik'e yana sake nad'e hannun rigarshi, girgiza kai tayi tace "Yanzu Ashraf idan ka fita a haka waye zai kalleka yace d'an musulmi ne kai? Me yasa ba ka jin magana a kan saka k'ananan kayan nan."

Kallon kanshi yayi ya langab'e kai yace "Hajia basu min kyau bane?"

Hararanshi tayi tace "Wane maganar kyau ina maka maganar kimarka? Kasan da ko sheikh ya sha yi maka magana a kan saka irin kayan nan amma ka k'i ji."

Numfashi ya sauke ya had'e hannaye yace "Zan daina Hajiata."

"Yaushe?" Ta fad'a cike da katsalandan, murmushi yayi yace "Da zaran nayi aure, dan bana so 'ya'yana su tashi su ganni a haka."

Wata hararar ta masa tace "Oho! Kenan kai ma kasan ba abun kirki kake yi ba?"

Girgiza kai tayi ta dora da fad'in "Allah ya sawak'e."

Saida ya matsa kusanta ya sumbaci kuncinta kafin yace "Hajia zan tafi saina dawo."

Cike da gargad'i tace "Ashraf, bana so ka jima a wajen nan kamar yanda kayi jiya, ka dawo da wuri kaji."

Girgiza kai yayi yace "Hajia, me yasa kike damun kanki dani kamar wani k'aramin yaro? Na fad'a miki a茅roport kawai zan je saboda maganar tafiyarmu, daga nan kuma gida zan dawo."

Cikin rashin yarda ta nuna shi da yatsa tace "Da gaske zaka dawo yanzu?" Rik'e yatsarta yayi yace "Da gaske hajiata, wai me ye duk na damuwar nan? Naji sauk'i fa sosai Hajia, kuma ba gashi jiya har na samo miki wacce zata zama sarakuwarki ba."

Turo baki tayi irin shagwab'ar nan tace "Ba wani nan, har yanzu bata zama ba tunda sheikh yace sai ya gamsu da tarbiyarta."

Mik'ewa yayi tsaye daga rank'wafawar da yayi yana fad'in "Zai ma gamsu Hajia, na yarda da yarinyar sosai."

Jinjina kai tayi tace "Ashraf ina sake jadadda maka karka jima, idan ka wuce azahar zan fita nemanka da kaina."

Zaro ido yayi yace "Hajia nema na kuma? Anya kuwa zan iya yin aure nayi nesa dake?"

A marairaice kamar zatayi kuka tace "Nima abinda na fara tunani kenan, Ashraf larurar ciwon cikin nan naka ne yafi komai d'aga min hankali, shekara bakwai kenan ana fama babu likitar da bamu je ba, magani babu daga k'asar da ba'a aiko mana ba amma shiru, idan kayi aure kuma ba kowace mace ce zata iya jinyar ka ba, dan haka zan so ka zauna kusa dani, yanzu kaga fa wata biyu daya wuce daga waje abokanan ka suka kaika asibiti a some baka san inda kake ba."

Tallabo kumatunta yayi duka biyu yana fad'in "Hajiata, ki kwantar da hankalinki dan Allah, ina ji a jikina auren da zanyi shine silar warakar duk wani ciwo nawa insha'Allah."

Jinjina kai tayi tace "Da gaske haka kake ji?" Jinjina mata kai yayi alamar eh, ita ma jinjina kai tayi alamar shikenan tare da fad'in "Allah ya yarda."

Lumshe ido yayi yace "Ameen, saina dawo ko?"

D'aga kai tayi tana kallon fuskarshi, juyawa yayi zai fita ya d'aga mata hannu yace "Banda yawan kirana kuma karki fito nemana Hajiata." Dariya tayi ta gyara zamanta a kan kujerar tana girgiza kai.



*Maryam*


Kwana biyun da bata lek'a ba yasa Maimuna aiko yaro kiranta, mik'ewa tayi duk da magriba ta kawo kai ta shiga gidan, da alama ta gama duk aikin gidanta zaune take ita kad'ai, dama bata tab'a haihuwa ba in kaga yara na mak'wabta ne.

Da sallama ta shigo hakan yasan Maimuna amsawa tana fad'in "Mimi ina aka shiga kwana biyu shiru ba'a lek'o ba?"

Dariya tayi tana zama kusa da ita tace "Wallahi aunty Maimuna karatu ne, kuma kinsan ni bana zuwa haka kawai in ba wani film ake mai kyau ba."

Ita ma dariyar tayi tace "Na sani, shiyasa ma da naga sun saka wannan nace su kiraki, nasan ke gwanar kallon film d'in india ce saboda soyayya."

Murmushi tayi tana kallon tvn data nuna mata, tabbas tana son film d'in sosai saboda soyayyarshi da kuma nishad'i da yake sakata a ciki, amma fa ita bata cika son mai-mai ba, bata son ta kalli abu yau ta kalla gobe, dan haka tayi shiru kawai ba tace komai ba, Maimuna ce ta mik'e tana fad'in "Bari nayi alwala an kusa kiran sallah."

Ita ma mik'ewa tayi tana fad'in "Aunty bari nima na tafi nayi sallah saina dawo anjima."

Kallonta tayi a maraice tace "Haba Mimi ki zauna mana kiyi sallahn a nan, wallahi gidan shiru ban da abokin hira duk ba dad'i."

Murmushin yak'e kawai ta mata ta jinjina kai, cire hijabinta tayi dan ita ba mutuniyar son zama da hijabi bace tana fad'in "Bari nayi alwala to."

Da kallo Maimuna ta bita, kai ita dai wallahi hallitar yarinyar na birgeta, kukkukup da ita digir-digir, kawai abinda ta fahimta Mimi irin mutanen nan ne da ko dusar dabbobi suka ci sai sunyi b'ul-b'ul, kumarinsu ba daga cin abinci bane hallita ce kawai. Dan yanzu ma riga da zane ne simple d'inki a jikinta, amma zanen sai ya mata hegen kyau k'ugunta na kad'awa sosai, ga rigar kamar dai sauran rigunanta ne masu tsayawa a iya kumkumi kawai. Farfajiyar ta fita tayi alwala a bakin panpo ta dawo ta d'auki hijab d'inta a lokacin an fara kiran sallah, sallaya ta d'ora suka kabbara sallah a tare har aka idar, suna gamawa Maimuna tare "Mimi zaki ci abinci?"

Girgiza kai tayi tace "A'a Alhamdulillah."

Mik'ewa tayi tace "Ina zuwa to." D'akinta ta shiga ita dai tana kallonta, jim kad'an ta dawo ta zauna tana aje wasu kaya a gaban Mimi tace "Mimi zab'a min wanda suka fi kyau a ciki? Ku ne yan zamani fa."

Dariya tayi tana k'arewa kayan baccin kallo, a hankali ta shiga dubawa saida ta cire guda uku ta mik'a mata tace "Aunty Maimuna kamar wannan sun fi ko? Kinga kalarsu ma ta dace da yanayin dare da kuma d'aukar hankali namiji, sannan sun fi sauk'i yakicewa a jiki."

Da mamaki Maimuna ta kalleta tace "Haka abun yake Mimi?"

Kunya ce ta kamata ta rufe ido tace "Haka dai nake tunani."

Jinjina kai tayi tace "To zab'a min wanda zan saka yau, kinsan fa Alhaji baya nan yayi tafiya amma zai shigo anjima."

Da tsantsar kunya ta nuna mata kalar fari tace "Ki saka wannan aunty, sannan ki shinfid'a zanin gadon da zai dace da kalar kayan, har labulenki ma idan zai yiwu komai ya zama kala d'aya."

Da farin ciki tace "Da gaske?" Jinjina mata kai tayi, cikin rarrashi tace "To mimi ko zamu je ki tayani saina canza d'in, na gyara komai wannan ne daai banyi tunani ba."

Murmushi ta mata tace "Ba komai aunty."

Mik'ewa sukayi inda Mimi ta sake cire hijab d'inta ta aje suka shiga d'akin, komai a gyare yake a kimtse, dan Maimuna kam ba k'azama bace ko wata wawuya, farin zanin gado mai kyau ta mik'owa Mimi ta karb'a ta d'auke waccen ta d'ora farin, ita kuma ta taka kujera ta cire labulayenta ta saka farare dan dama guda biyu ne a d'akin, bakin k'ofa da kuma tagar dake jikin bayan gado, suna gamawa Maimuna tace "Shikenan?"

Da d'an mamakinta ganin ko ba komai fa shekararsu shida da aure amma tana tambayarta ita da bata da auren, cikin rashin sakewa tace "Eh to ai har kun gama girki, zaku iya zuba abincinku a kwanukan da zasu dace da wannan kalar ma, sannan kuyi shigar da kuka san zata faranta mishi kuma yake so."

Fita sukayi daga d'akin da haka a sannu sannu har saida suka sha aiki ba kad'an ba, dan har jus saida Mimi tasa suka had'a, ita fa ba k'warewa tayi ba, kawai a harkar kalle kalle ne da karance karance duk ta iya wani salon kinibibi, da kuma wannan take tak'ama ko yau aka kaita gidan mai mace uku zata iya zama kuma ta birge.

Amir ne ya shigo da sallama suka amsa mishi, kafin yace komai Mimi tace "Kira na ake?"

Girgiza kai yayi yace "Mama ce ta ce na zo na duba idan kina nan, sannan na ji wai aiki kika ma aunty Maimuna."

Da fara'a Maimuna tace "Allah sarki, Amir ka fad'awa Mama aiki ne take kama min, amma har mun kusa kammalawa ma."

Juyawa yayi yana fad'in "To." Da kallo Mimi ta bishi yanda yake tafiya da k'arfinshi k'undul k'undul, mayar da hankalinta tayi kan lomar da take tace mata dafaffiyar mazark'waila da karanfani. Mik'ewa Maimuna tayi tana fad'in "Bari na shiga ko wanka nayi kafin ki tace na fito sai ki tafi gida Mimi tunda an fara nemanki."

Jinjina kai tayi alamar gamsuwa, shigewa tayi ita kuma ta ci gaba da tacewa, tana idawa ta d'auki madara peak d'in ta fasata ta juye mata a ciki haka ma maltina, d'auka tayi ta kai mata fridge ta aje, kankanar da suka yanyanka ta d'auki yanka d'aya ta juyo tana kai wa bakinta hannunta d'aya kuma tana gyara gashinta daya d'an sauko mata a kan goshi duk ya jik'e da gumin da take yi kasancewarta mai yawan gumi a kai musamman idan bata da kitso.

Cak ta tsaya tana neman sark'ewa saboda ido hud'u da sukayi da Alhaji Saminu, kallon tashin hankali daya wuce k'a'ida ne yake mata kamar zai afka mata, ya kasa ko motsawa bare ya had'a ko da yawu. A gaskiya dole ya samu yarinyar nan dan in ya rasata zai shiga matsala a yanda ya jima da soyayyarta, indai kud'i na samawa mutum alfarma to ba shakka zai kashe ko nawa ne ya sameta, ta mishi a yanda yanzu yake son ganin mace, komai na ta birgeshi yake, uwa uba wasu wadatattun mazaunai da Allah ya bata.

Da k'yar cikin k'osawa da tsaarguwa tace "Sannu da zuwa, ina wuni."

Da sauri ta dawo dashi hayyacinshi yana washe baki da fad'in "Sannu Mimi, aiki ake ne? Sannu ko? Kina lafiya?"

D'an murmushi kawai ta yak'o masa tace "Um."

Takowa ta fara yi dan ta d'auki hijabinta ta bar gidan, amma saiya gyara tsayuwa ya shiga k'ure gabanta da kallo zuwa wuyanta dake wani mul-mul dashi. Saida ta zo daf dashi zata wuce duk da kuwa kayan data gani a hannunshi nik'i-nik'i kawai ta ji ya rik'e hannunta ram a ciki na shi yana binta da wani kallo.

A tsorace kuma a gigice ta kalleshi tace "Subhanallah, kawu..."

Bai bari ta k'arasa ba ya aje ledojin hannunshi ya damk'a mata wata ledar yana sake murza hannunta yace "...



*Asma'u*
*Aminatu*
*Rabi'atu* (Bintu Yusuf)
*Yagana ta*
*Rahamah* (Mom)
*Maryam* (Mom)
*Pretty Aeeshartyy*


_Sannunku da k'ok'ari, Allah ya saka muku da alkairi, comment d'inku yafi na kowa._



*Alhamdulillah*
06/08/2021 脿 11:52 - Mme Ishaq馃拑馃グ: 馃懇鈥嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈�
*MATAR MUTUM*
_(K'abarinsa)_
馃懇鈥嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈�

*NA*


_SAMIRA HAROUNA_


*SADAUKARWA*


_GA DUKA_

*'YAN AMANA TA*


馃挮鉁� *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*馃専
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_馃

鈽� *[ T.M.N.A]* 鈽� 馃摉馃枈锔�

https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/

_Bismillahir rahamanir rahim_


*10*



Bai bari ta k'arasa ba ya aje ledojin hannunshi ya damk'a maya wata ledar yana sake murza hannunta yace " Wannan na ki ne Mimi, ki rik'e kinji karki ce a'a."

Da k'arfi ta ja hannunta ta raba da nashi tana binshi da wani fitanannen kallon mamaki, sake matsawa yayi daf da ita murya k'asa k'asa yace "Mimi lafiya? Kinga ki saurareni, indai zaki amince ki aureni wallahi zan miki komai a rayuwar nan, zan d'auki nauyin karatun k'annanki, zan canza muku gida na sabinta muku rayuwarku, Mimi amincewarki kawai nake buk'ata."

Da sauri ta ja baya saboda hannunta da yayi k'ok'arin kamowa, a razane cikin al'ajabi tace "Aure na fa? Ni d'in? Aunty Maimuna fa?"

Sake matsawa yayi ya samu kusanci da ita sosai yana fad'in "Mimi ai ba haramun bane, ina sonki wallahi kuma zan aureki, ki amince kin ji."

A kid'ime ta girgiza mishi kai tace "Gaskiya ba zan iya ba, kayi hak'uri kawu."

Da sauri ta k'arasa kan kujerar da hijabinta yake zata d'auka, tana juyowa suka had'e dan yana biye da ita ne, kamar jira yake dama a samu wannan tsautsayi sai kawai ya k'arasa rumgumeta jikinshi har rawa yake kar-kar-kar dan jaraba, dan shi fa irin mazan nan ne da kalami kawai zai iya tsumasu bare su ganki zahiri, ji yake kamar ya shige da ita d'akinshi ya samu sauk'i da sukuni, yana hawaltuwa sosai da azabtuwa akan yarinyar, siririyar ihu ta k'walla dan a rayuwarta haka bai tab'a faruwa ba sai yau, da sauri ya d'ora hannunshi ya rufe mata baki yana fad'in "Shiiiii! Haba mimi kamar ba wayayya ba."

Iya k'arfinta ta saka ta tureshi tare da fita a guje rik'e da hijabinta tana kukan takaici, duk da nauyin jikinshi bai hanashi shiga tashin hankalin da shi ma ya bi bayanta ba yana kiran "Tsaya, tsaya na ce."

Ganin bata saurarenshi yasa shi hangen mai gadi yace "Karka bari ta fita."

A gigice ta tsaya ta juyo ta kalleshi saboda mai gadin daya shiga kakkarwa rufe k'aramar k'ofar, kar ta fita yake nufi? Me zai mata? Tana ganin ya kusa k'arasowa ta durk'usa tana kuka tace "Dan Allah ka k'yaleni na tafiyata gidanmu, ni ba zan koma zuwa nan ba."

Yana zuwa sunkuyawa yayi ya kamo hannayenta ya mik'ar da ita tsaye, janye jikinta tayi daga na shi ta ja baya, cikin sigar rarrashi yace "Mimi ba zaki aureni bane? Ina sonki wallahi so na aure, ki fad'a min duk abinda kike so a duniyar nan zan miki shi da yardar Allah."

Girgiza kai tayi hankali a tashe tace "Ba zan iya ba, ba zan iya aurenka kawu, bamu dace ba ko kad'an."

Numfashi ya sauke yace "Kar ki ce haka mana Mimi, miye a cikin rashin dacewar m没 to? Ina sonki kuma ke ma zaki soni da mun yi aure, ina da kud'i zan iya baki komai kike so."

Cikin b'arin jiki ta kalli fuskarshi tace "Kud'i basu dameni ba, dacewata da mutum ita tafi komai mahimmanci a gareni, ba zan iya auren wanda bamu dace ba."

Juyawa yayi ya kalli k'ofar d'akin saboda tunanin kar Maimuna ta fito sannan ya kalleta yace "Yanzu dai ki tafi kinji, zamuyi magana dake a waya, bani lambarki?"

Ya fad'a yana mik'a mata wayarshi, a tsorace ta kalleshi tace "Ni bana da waya ai."

Wani sakaran murmushi yayi yace "Mimi ni ba kamar sauran mutanen bane da kike ninkesu ta baibai, nasan kina da waya wacce saurayinki ya baki, ki saka min lambar a nan kin ji."

Rarraba ido tayi cikin rashin gaskiya ta karb'i wayar tana fad'in "Dan Allah to karka fad'awa Abbana, wallahi hushi zaiyi dani."

Girgiza kai yayi yace "Karki damu, bana son abinda zai b'ata miki rai ai."

Saka mishi lambar tayi ta mik'a mishi

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login