Showing 45001 words to 48000 words out of 230725 words
wa Dr Sunusi cewa kar ya bar kowa ya shiga wurin Abba daga nan suka yi sallama ya sauya location zuwa asibitin.
***
_*Bayan Cudewar Awanni*_
Safiya ce, garin ya yi sanyi kuma ya yi luf-luf kamar a lokacin wani hadarin ne zai hadu ruwa ya ƙara sauka kamar yanda aka kwana ana yinsa.
Kamar wacce laka ya fashewa a ciki, haka ta shiga taka barandar asibitin. Idan yaro zai yi mata kallo ɗaya, nan take zai ayyana a ransa cewa mahaukaciya ce. Ga duk mai hankali kuwa zai ga tsantsar tashin hankali da damuwa cike fal shimfide a saman fuskarta.
"Mutuwa akai mata da alama."
Ta tsinci muryar wasu mata a gefe, ba ta kallesu ba balle ta tofa. Ba kowa ta ke ganewa ba,ba kuma kowa take gani ba. Abbanta kawai take son sanyawa a idanu. Da shi ta kwana kuma ta tashi.
Hijabin jikinta duk ya cukurkuɗe ya yi jirwaye na ruwan hawayen da ta dinga gogewa da shi. Silifas ne a kafarta na baƙin gidansu, ba ta san inda nata yake ba. Ta dai tuna da shi Hajja ta yi amfani wurin dukanta. Fuskarta yatsun Amrah ne kwance a samansu wadanda har yanzu basu baje ba. Tana fashin sallah, wannan yasa ba ta kalli gabas ba balle fuskar ta ci darajar wanki. Ta dai tsarkake inda ya zamemata dole saboda kyankyami irin nata, ko ba komai kula da lafiyar jikinta ne. Ta shanye komai a awannin da suka biyo baya. Zagi, tsinuwa da ma duka, duk ta dauka daga dukkan wadanda acewarta sun kai su yi mata su. Ta ji ta dau komai idan har za'a bar ta ta ji da abinda ke cin ranta.
Har ta iso dakin da Abba ke kwance tana tunani mai zurfi, ta gane dakin a dalilin hango Mijin Rafee'ah, Isma'il da ta yi zaune a saman kujera, gefensa Yaya Munir ne su na magana.
Yaya Munir na kallonta tana kallonsa.
_"Ban yarda ɗayanku ya taɓa lafiyarta ba, kar wanda ya tuhumeta akan abinda ta yi, ni da kaina zan auramata wanda take so. Na dauki laifina na yi mata auren dole kamar yanda ta ce."_
Ya tuna kalaman Abbannasu a jiya ga Hajiya, Zulaihat da kuma shi Yaya Munir din. Sai dai ya yiwa kansa alkawarin babu shi babu Ramlat. Don haka ya kauda kai kamar bai ganta ba. Isma'il ne ya tsayar da ita suka gaisa yana mata fadan ba ta kyauta ba, tsam Yaya Munir ya mike.
"Muje ga Rafee'ah ko?" Ya katse Isma'il. Hakan yasa shima ya mike suka tafi. Ta bisu da kallo idanun taf da kwalla sannan ta murda kofa ta shiga dakin Abban da sallama.
Babu kowa a ciki sai Abban dake kwance ya yi shiru idanunsa biyu. Ya juyo ya dubeta, ga mamakinta murmushi ya yi mata. Ta sunkuyar da kai ta ji saukar hawayen da take riƙewa a saman kuncinta. Hannu ya miko.
"Zo nan Ramlatu."
Tana tafiya kamar a iska tsabar ramar da ta yi ta zauna saman kujerar gefensa ta rike hannun sai kuka.
"Abba don Allah ka yafemin. Abba na tsani kaina, na kasa rankwafar da zuciyata na yi maku biyayya. Abba ka yafemin na tuba. Na shirya zama da Hilal kamar yanda ku ke so. Ku ce ya maidani. Wallahi zan zauna."
Murmushi Abba ya yi, ya shiga girgiza kai.
"Kin ji nace ba zan ba ki Aliyu ba? Ko wani ne ya ce hakan? Ki yi shiru ki daina kuka, ni na yi laifi da na dage wurin yi miki aure da wanda bakya so. Ki yi hakuri ki yafemin kinji? Zan aura maki Aliyu cikin satinnan in sha Allahu. Yau zan koma gida ba zan ƙara kwana a asibitin nan ba. Idan har Khalid na raye, sai kin auri zaɓinki. Ki daina kukan. Na yafemaki duniya da lahira. Allah Ya yi maki albarka."
Ya ƙarashe da rarrashi, ta kasa gane zantukan Abban suka dosa. Ta kasa gane dagaske yake maganar ko kuwa mai harshen damo ne? Don haka ta bi umarninsa ta share hawayen. Ya dinga jan ta da hira har ta yi dariya. Hankalinta ya ɗan kwanta. Amman maganar Abban ta shiga yawo a kwanyarta cike da rashin gamsuwa. Maimakon ma ta yi murna, sai ta shiga firgici da kuma faduwar gaba.
Daga nan ta karasa dakin Rafee'ah, ba ta shiga ba, ta hango baby mai kyau dai, ta yi murmushi sannan ta koma ga Abban.
***
Kwana biyu da sallamar Abba, ya sallami dukkan baƙi ƴan Daura, ya basu hakuri akan abinda Ramlatu ta yi. Daga nan ya tara iyalinsa ya tsawatar akan bai yarda ko maganar banza wani ya yiwa Ramlat ba.
Abba da mahaifin Amrah, da ma wasu a ƴan uwa, suka dunguma har gidan su Hilal. Suka ba iyalinsa hakuri cike da nadamar abinda Ramlatun ta aikata don tuni sun ji abinda ta yi har ya saketa. Bai ɓoye wannan ba. Wannan ya ɗan sassauta ran iyayen Hilal, ko ba komai iyayen Ramlat sun nuna ba hannunsu. Basu nemi sulhun kome ba, koda sun nema iyayen Hilal sun yanke wannan alaƙar. Hatta Alhaji Aminu mahaifin Hilal wannan karon ya yi Allah wadai da irin Ramlatu. Toh Abban ma bai da ra'ayin komawarta.
Washegari kuwa kamar yanda suka nemi iyayen Aliyu, sai gasunan sun zo. Ba ɓata lokaci Abba ya karbi sadakin ƴarsa. Nan aka daura auren Aliyu da Ramlat don duk wani bincike an yi ta hanyar Yaya Munir an kuma tabbatar daga Hilal har ita Ramlatun babu idda a kanta.
"Ga sadakin aurenki Ramlatu, na auramaki Aliyu. Ina fatan wannan zai faranta ranki. Zai sa ki dawo da walwalarki. Ki kuma maido soyayyarmu a zuciyarki?"
Ta ɗago ta dubi Abba tana hawaye. Abban murmushi yake har hakoransa tana hangowa. Ita ya kamata ta yi irin wannan kalar fara'ar, sai ya kasance ita ce mai kuka, Abban da mutan gidan na dariya.
Hajiya ma sosai ta sakarmata fuska.
"Ramlatu matar Aliyu. Allah Ya baku zaman lafiya."
Wannan ne kalaman Hajiyar kafin ta fita zuwa asibiti wurin Rafee'ah duba lafiyarta.
Ramlat ta shiga daki ta zauna, ta yiwa kudin da Abba ya damƙamata kuri da idanu, abin mamaki su dinma jiƙasu ta soma da hawayenta. Ranar da ya kyautu ta yi rawa da juyi, ranar da ya kyautu ta fi kowa farin ciki. Abin mamaki kuma ya sanyata, kukan ta shiga yi kuwa iyakar ƙarfinta, koda za'a shaƙeta ba za ta ce ga dalili ba.
Ba ta da masaniyar cewa Mafarin kenan!!!
***
https://my.w.tt/iRW2CA35T9
🕯️ *ƘARFEN ƘAFA*🕯️
_*Rufaida Umar*_
Bismillahir Rahmaanir Raheem.
15)
Kallo ɗaya za ka yi mishi ka hango farin ciki tsantsa da walwala marar misaltuwa a saman fuskarsa. Sigari ya sanya a bakinsa yana zuƙa lokaci daya yana fesarwa. Ihu da kurantawa shi kawai ke tashi daga bakin maza da matan wurin.
"Cau cau Aliyu Angon Ramlat!"
Fadin G Baba. Hakan sai ya kara tunzura Aliyu har sai da ya zuƙe kara biyu cikin ƙanƙanin lokaci kafin ya kwantar da kai yana kallonsu ƙasa-ƙasa yana doka murmushi. Ko ba komai yau burinsa ya cika. Ko ba komai ya mallaki abinda ya jima yana dakonsa. Ya na a jingine da kujera cikin club ɗin, yana kallon yanda ake rawa da rausaya mata da maza. Duk ana yi don tayashi farin cikin samun cikar burinsa. Hannu ya zura a aljihu ya ciro bandir din dubu daya ya bude ya watsamusu. Aka hau kwasa ana ihu da kara korantashi. Abin na mishi dadi. Wayarsa dake saman tebur ya duba, kira ke shigowa ba kuma na kowa ba sai na Granny. Ya mike tsaye ya yi musu bankwana ya fice. Yau bai sha abin maye ba don ya fi son a yi komai cikin hayyacinsa ya gani.
Bai daga kiran ba har sai da ya bude sabuwar karamar motarsa Honda wanda Abulle ta sanya aka siyamishi ya shiga. Ya soma tuki a nutse kafin ya dauki waya ya kira Granny.
"Ina ka shiga wai? Ka zo mu tattauna game da lefen."
Ya yi murmushi gami da kara lumshe lumsassun idanunsa.
"Ina hanya Kakus, gani nan tafe."
Ya kashe kiran bayan ta mishi addu'ar zuwa lafiya. Ya kai duba ga agogon dake daure a tsintsiyar hannunsa. Karfe tara da mintoci na dare. Buga sitayari ya yi gami da sakin ƴar ƙara da furta.
"Yes!!" Cike da nishadi ya kara gudun motar gami da ware kiɗa. Har ya isa gidan bai kashe kidan ba duk kuwa da hango iyayensa maza da ya yi zaune a saman tabarma ƙasan ƴar rumfa a farfajiyar gidan. Duk sadda irin hakan ta kasance, tattaunawa suke game da wani abun mai muhimmanci.
Kallonsa suke har ya kashe motar ya fito zai nufi cikin gida ba tare da tunanin gaishesu ba. Idan da sabo ya ci ma su saba.
Malam Abdussalam cike da takaicin halin ɗannasa ya sunkuyar da kai.
"Kai! Aliyu?!"
Fadin Kawu AbdulRashid wanda ke bi wa Malam Abdussalam a haihuwa. Aliyu ya maido akalar tafiyar garesu.
"Gani. Sannunku."
Yanda ya gaishesu kerere ya fi komai baƙanta ransu. Daƙuwa Justice ya wurga mishi.
"Ungo wannan! Yanzu kai tsabar iskanci da rashin kunya mu kake yiwa gaisuwa irin na ƴan iska?"
Nan ya gane kurensa, sai ya durkusa yana shafar suma. Dama ya riga yasan har gobe dattijon haushin sakin da ya yiwa ɗiyarsa yake. Yana cikin farin ciki yau, don haka bai shirya wani abun ya ɓata ransa ba.
"Ku yi hakuri." Ya ce kai tsaye cikin tausasa murya. Banda warin taba ba abinda ke tashi a jikinsa. Sun gaji da magana daya akansa.
"Allah Ya shiryeka Aliyu, Yasa wataran ka sauya." Cewar Kawu AbdulRashid ransa na zafi.
Nan Justice ya shiga magana.
"Yarinyar nan mun ji labarin abinda ta aikata, kuma ta yi a bakin duniya duk don ta aureka. Ta yi laifi, ta yi kuskure. Mahaifinta ya damƙa amanarta gareka, da kunnenka ka ji kalamansa."
Aliyu ya gyada kai cikin son tuna abinda Abban ya furta gareshi ranar da ya karbi sadakin Ramlat a hannun magabatansa.
*"Ramlatu amana ce Allah Ya ba ni, yanzu kuma amanar za ta koma kanka. Ban ce lallai sai ka kyautata mata ba, ban kuma ce lallai sai ka yi mata adalci a rayuwa ba, duk wannan hakki ne da ya rataya a wuyanka ko ban faɗa ba. Ka ji tsoron Allah a lamuranka, kar ka manta zai tambayeka duk wani abu da ka aikata a rayuwa."*
Bai mantawa a lokacin murmushi ya yi kawai.
*'Ba dai haka ka so ba Abbanmu. Sai dai ba za ka hana abinda Allah Ya yi ba.'*
Nan take ya ce a cikin ransa.
"Don ubanka ina magana kake dariya? Wane raini kenan?"
Kalaman Justice suka katse tunaninsa, ya ankara da murmushin da yake zabgawa har haƙoransa na bayyana.
"Ayi hakuri." Ya kara fadi.
Kowanne ya tofa albarkacin bakinsa kan ya riƙe amanar yarinya, daga nan ya yi musu godiya ya mike da uzurin Abulle na nemansa. Mahaifinsa ya bishi da kallo gami da addu'ar shiriya. Yaran ka haifa ba ka isa ka saita halayyarsu ba.
Kiciɓus suka yi, ba haka ta so ba. So ta yi da sauri ta bar dakin Abulle kafin ya cimmata. Shigarta dakin Abulle don kai mata goron da ta dauko a dakin Daddynta. Jin Abulle na mitar Aliyun ya zaunar da ita zaman jiransa ya sa ta katse hirartasu ta yi mata sallama ta fito tana sauri ta bar bangarennata. Sai dai kuma ba yanda ta iya tunda gashinan gabanta. Ta daure ta haɗiye komai dake tasomata.
"Ina wuni Yaya Aliyu."
Bai san yana da kunya ba sai a yanzun, ya kauda kai daga kallonta.
"Lafiya. Ya kike?"
Ba tare da ta amsa ba ta wuce da sauri ta yi hanyar kofar sashinsu. Bayanta ya bi da kallo, Muhibbat kenan. Ya sa kai dakin Abulle.
Salati ta shiga yi kafin ta hau yi mishi fadan sigari da ya sha. Taɓe baki ya yi, ya mance da hakan shaf bai jefa alawa bakinsa ba, bai kuma fesa turare ya tsaye a waje na mintoci ba kafin ya hau mota ya tuƙo. Ya mance rabon da ya shigo gidan yana warin taba.
"Wai ni don Allah ki bar kunnena ya huta. Shikenan don kin ji warin abu a jikina sai ya kasance sha na yi? Ko a addini an hana irin wannan yanke hukuncin. Idan ina sha tsawon lokacin nan ba za ki sani ba sai yanzu? Mtsw, Abokina ne ya sha, shi na ziyarta shi ne ƙamshin ya biyoni."
Hakan da ya faɗa sai kuma ta gyara zama ta hau jijjiga kai.
"Kuma fa hakane. To ka kara kiyayewa dai. Raɓar abokai ɓata gari ba naka bane. Na soke abotar. Yanzu dai ya batun lefe? Mahaifinka cewa ya yi na farko an maka, na biyu kai za ka yi. Duk da haka Alƙali da sauran kawunnanka sun ɗan ba ka wani abin ka haɗa ka yi."
Murmushi ya yi.
"Lefen Baby ina son ya fi na kowa. Ina son a bude a kirashi da lefe. Masu yi mata habaici da zagi a kan aurena su daina. Don haka da kaina naji zan hada abina koda ace hakan na nufin karyewar jarina."
Baki sakaka Abulle ta saki tana kallonsa kafin ta magantu.
"Um um dai Zakina, ba za'a yi haka ba. Ƴar dangi ma ba ka ce hakan ba sai akan bare? Ina rabaka fa."
Ya yi dariya.
"Abulle tawa ni kadai, Baby ai ta isa na yi mata komai. Koda kuwa komai nawan zai ƙare a kanta."
Ta taɓe baki.
"Fadi dai sunanta na zahiri, shi zan fi fahimta. Ramlatu ko? To naji, ungo nan."
Ta daga filo ta fiddo damin kudi ta mikamasa. Ya karba ya zura a aljihu.
"Wai nikam me zai hana ka mayar da yarinyarnan ɗakinta ne? Naga dai tsiraicinka yafi rigar aro ta mutane."
Miƙewa ya yi tsam!
"Sai da safe Kakus. Kwanta ki yi bacci abinki. Nima na tafi nawa lissafin."
"Ai fa, ba dama a dauko magana sai ka kauce. Toh har gobe ban ga wata ɗiya da za ka kawo na ji ina sonta a raina ba irin Muhibba."
Daga kafada ya yi alamar ke ta shafa ba kuma tare da ya komai ba ya fice daga dakin. Ko a ransa bai ƙara tada zancen Muhibbat din ba.
***
"Kai Allah Ya rayamana mai sunan Abba."
Fadin Zulaihat kenan cikin waya tana murmushi ranta fari ƙal. Ramlat na daga kicin tana dahuwar indomie ta ji wannan kalamin. Anan ta fahimci sunan Abba ɗan Rafee'ah ya ci. Kwalla suka tarar mata, a yanzu ba ta rabo da hakan. Tunda aka daura aurenta da Aliyu, komai ya daina yi mata dadi. Ba kuma don ba ta sonsa ba, har gobe tana jinsa a ranta. Wuyarta ya kira wayarta ko kuma ta kirashi, za ka ganta cikin farin ciki da annashuwa. Kalamansa masu taushi da dadi, wanda ke nuni da nutsuwa da kuma cikar hankali, sun fi komai yi mata dadi a ranta. Sai dai ba ta nufin ta rabu da yan uwanta a dalilinsa, duk suna amsamata idan ta yi magana, sai dai irin amsawar da gwamma kar su yi. Babu fara'a babu sakin fuska. Sama-sama suke amsawa kamar ba sa so.
An kwaso kayanta kaf a gidan Hilal, a daren jiya ya zo har gidan ya riski Abba a falonsa. Sun jima suna magana sannan ya tafi. A hirar Zulaihat din da Hajiya ta ke jin cewa hakuri ya ba shi. Hakuri bisa sakin ƴarsa da ya yi.
"Ke wane rashin hankali ne za ki kunna gas har abu ya ƙone haka? Gobara kike son jazamana? Ko mu dinma kashemu za ki yi?"
Ta waiga ta dubi Zulaihat s'ilin da ta sanya hannu ta kashe gas din.
"Hajiya ta ce ki yiwa Mijinki magana za'a je a yi jere don Abba ya ce a satinnan za ki tare. Ya kawo muƙulli."
Tana kaiwa karshe ta fice a kicin din, kawai sai Ramlat ta fashe da kuka. Haka to za su ci gaba da yi mata?
Indo ta risketa tana kuka, ganin ta dage wurin rarrashinta duk kuwa da haushinta itama ta ke, ya sa ta daukar wayarta ta bar kicin din. Abincin da ba ta ci ba kenan.
***
Akwati takwas cif Aliyu ya shaƙe da kaya na gani na faɗa. Yakasai gidan su Hajja aka kai lefen kamar yanda Abba ya bada umarnin a yi.
"Anya Rabi'atu wannan yaron ba ya cin haram a aikinsa? Wannan wane irin kaya ne ya shaƙowa yarinyarnan?"
Hajja da mamaki ya kasheta a zaune ke wannan furucin cikin waya ga Hajiya. Hajiya ta yi murmushi mai ciwo.
"Ko ya ya dai Hajja ai ita yarinyar ta fi kowa sanin yanda aka haihu a ragaya. Tunda ya kawo lefe an karɓarmata shikenan. Ta je ta yi ta sakamishi."
"Kai Rabi, na rabaku da irin wannan fushin fa. Meyasa Khalid ya biyewa yarinyarnan bai yi bincike ba? Har da gwal a sarkokin."
"Hajja ina zuwa zan kiraki."
Hajiya na fadin hakan ta katse kiran. Ba wai don abin bai tayarmata da hankali ba, sosai hankalinta ya tashi. Yaron da aka ce a kasuwar ma ba wani mayar da hankalin a zo a gani yake ba. Ba ta son tunkarar mijinta da wannan batun, don ta lura yana cikin damuwar auren Ramlatun har lokacin. Wannan ta sa ta kira Munir. Kafin ma ta yi nisa ya katse zancen.
"Hajiya ke mahaifiyata ce. Don girman Allah kiyi hakuri ki bar min zancen Ramlat. Hajiya ki zubamata ido tunda kun mata abinda take so. Ku yi hakuri ku bi ta da addu'a idan da bukatar hakan. Ba ita kadai ku ka haifa ba, muna raye zamu share kukanku. Ki yi hakuri, ki sanya a ranki hakan ya zama alheri ba sharri ba."
Da wannan ya samu ya zame kansa daga abinda Hajiyar ta kawomishi, na bincike akan harkar Aliyu.
'Wane bincike bayan mai afkuwa ta afku? Komai ta fanjama fanjam!'
Ya fadi a kasan ransa.
***
"Ai yanzu kin girma, kin mallaki hankalin kanki, ba kya bukatar nasiha daga gareni. Duk abinda kika aikata ga rayuwarki daidai ne."
Kalaman Hajiya suka shigeta sosai, ta cikin laffayar da Zulaihat ta naɗeta a ciki, kuka take. Ba ta san sadda ta bude lulluɓin ba ta karasa ta dafa cinyar Hajiyarta.
"Don son Annabin Rahma s.a.w Hajiya ki yafemin. Ki yafemin ko zan ga haske a rayuwata. Na yi miki