Showing 183001 words to 186000 words out of 230725 words

Chapter 62 - Karfen Kafa Book 1 Hausa Novel Complete

Unknown   

06 Jan 2025

1077

har abada ba zan taɓa bari wata alaƙata shiga tsakanin ni da yara da ba'a san asalinsu ba! Aminu dai ya zo ya kawomana karuwarsa ya kuma tafi ya bar munda bara gurmi a cikin zuri'armu. Na ji! Amma ba wanda ya isa ya yi min dole kan na karɓe su. Shi kuwa Tahir yau ko ni ko shi tunda ya zaɓi zama da su a kaina! Zan nunamasa ni ne nan ubansa!"

Kawu Modibbo na kai wa nan ya mike ya nufi ɗaki, ransa idan ya yi dubu ya ɓaci, ga Bokansa ya tabbatar masa babu sauran ƙofar da wani asiri zai shiga jikin Hussein da sauri sai dai a sannu. Yanzun ya gama gane ba iyakar tsana kawai ya yiwa zuri'arnan ba, har da bakin ciki da kuma jin tsantsar hassadar yanda ba su rayu a wulakance kamar yanda shi da Innarsa a baya suke fata ba. Sai ya kasance koyaushe sai dai ya yi ta jin labarin nasarorinsu. Ga dai yaransa nan amma kowanne da kalar shashancin da ya sa gaba, kalilan ne a yaran suka kama dahir. Wato dai suka yi karatu kuma su ke aiki, aikin da bai kai darajar na AlHassan ba. Ko iyaka nan aka tsaya ya san za su yi mishi dariya, abinda ba zai jure ba kenan.

***
"Ya akai ɗan uwa?" AlHassan ya fadi kai tsaye daga ɗayan ɓarin. Hussein ya kara gyara zaman wayarsa duk kuwa da cewar tuƙi ya ke yi.

"Lafiya, batun maganar da muka yi, yaushe za ka zo?"

Murmushi mai sauti AlHassan ya yi.

"Ai ka ji, dama sai da na ce maka ka yi hakuri mu taho tare komai zai fi bada ma'ana, yanzu gashinan tun ba ka tafasa ba za ka ƙone."

Hussein ya ɗan cire hannunsa saman sitiyari ya shafi sumar kai yana murmushi kafin ya mayar.

"I'm sorry, ka san.."

"Ko ba ka faɗa ba na sani. Na san kuma dalilinka. Hakan ma ya yi daidai. Fadamin, me ka zo ka tarar?"

Tiryan-tiryan ya ba shi labari, AlHassan ya yi dariya.

"Alhamdulillah. Wannan ma nasara ce. Zeenatu get ready."

Suka ɗan taɓa hira abinsu suka yi sallama.

***
Da yammacin ranar juma'a, tana zaune saman kujera suna hira da Baban Hanif, damuwa karara ta bayyana saman fuskarsa.

"Mamin Affan, ban san dalili ba, amma gabana faduwa ya ke, sai na ga kamar zan rasaki, sai naga kamar duk wannan rawar ƙafartawa zai zama mafarki."

Ta ɗago kai da zummar ba shi amsa da ɗan murmushi saman fuskarta, ya yi daidai da bude ƙaton kyauren gidan, motar Hisham ce ta shigo sai dai a gefensa mai zaman banza, Hussein ne.

Kauda idanu ta yi gami da danne bugun da kirjinta yake ba tare da fuskarta ta nuna ba.

"Me zai sa ka fargaba? Akwai wani lamarin da ya fi karfin addu'a? Komai na Allah ne."

Ya jinjina kai, har sannan bai ji zuciyarsa ta sake ba. Yana son faɗamata sakamakon da binciken tarihinta ya ba iyayensa amma ya danne a ransa har zuwa sadda zai kammala nashi binciken ya gane gaskiyar lamari.


Daga cikin motar kuwa, Hisham ji ya yi wani murmushi ya suɓuce masa, abinda ya fi dadi, ya ji na zuwan da ya yi da Hussein gidannan. A farko Hussein bai yi niyyar zuwa ba, sai dai kwadayin ladan da ke cikin ziyartar iyaye da ma yan uwa da asibitoci a ranar juma'a yasa shi cewa su je din. Sai da suka soma zuwa gidan iyayen Hisham din suka ci abinci kafin su zo gaisuwar surukai kuma yan uwa a wajensu yanzun. A farko Hussein gardama ya ke mishi kan zuwa ziyartar Kawu Modibbo da Hisham ya ke so su yi a ranar, sai dai shigowarsu gidan da mummunan tozalin da ya yi ya sa shi yin ɗif har hakan ya ankarar da Hisham shima ya kai idanunsa garesu.

"Muje ko?" Hisham ya katse tunaninsa yana kara nazartar yanayin sauyawar fuskarsa. Babu annuri.

"No, shiga ka fito."

Dariya mai karfi ta kama Hisham sai dai dakyar ya haɗiye, idanun Hussein din akan Baban Hanif yana son tuna inda ya taɓa ganinsa.

"Ah, wai Hajiya Ramlatu kake kallo? Kai wai dama Haris ne? Bari na je mu gaisa."

Hussein a sannan ne ya watsawa Hisham banzan kallo kafin ya ja tsaki, kusan a tare suka fito daga motar. Baban Hanif na ganinsu ya taso da fara'a ya karaso. Maimakon Hussein ya tsaya kawai sai ya yi gaba yana shan murr ko inda suke bai kalla ba. Baban Hanif ya bishi da ido sadda hannunsa ke cikin na Hisham su na musabaha. Ramlat ta dora kafa daya kan daya tana fitar da wani irin murmushi mai kama da yaƙe. Sauyawar Hussein ya mugun kasheta da ba ta mamaki.

"Ranki ya dade, girman kujerarki."

Sai a sannan ta sauke ƙafar ta gaida Hisham fuska a sake. Daga bisani shima ya yi ciki.

Kusan mintuna sha biyar suka kwashe a cikin gidan kafin Ramlat ta shigo. Kiciɓus suka yi a bakin ƙofar. Kallon da ya watsamata ne yasa ta hadiye gaisuwar a fatar bakinta. Ganin shi bai ba ta hanya ba kuma bai ce uffan ba yasa cikin dakiya bayan ta saukar da kanta ta gaishe shi.

"Ba girin-girin ba dai, ta yi mai."

Ya fadi a sanyaye amma zafin maganar ya fi komai buga zuciyarta. Ta dubeshi, ya kauda kai ya bi gefenta ya wuce. Ta bi bayansa da kallo cikin rashin gane inda zancensa ya dosa.

"Ah Hajajju, har kin gama taɗin?"

Ta juyo ta dubi Hisham tana murmushin hadiye damuwa.

"Har za ku wuce?"

"Eh kinsan da yake ba iyakar nan muka tsaya ba. Yau dai ladan juma'ar muke kwadayi."

Ta jinjina kai.

"Allah Ya saka da alheri."

Ya amsa da amin. Wani wawan hon da Hussein ya yi sai ya ba Hisham dariya.

"Kinga bari na tafi kafin na ba shi haushi ya koma Adamawa a ƙasa."

Ta yi dariyar da ta tsaya a fatar baki. Hanya ta ba shi ya wuce.

***
BANKWANA DA MASOYI....





I just published "BABI NA HAMSIN DA BIYAR" of my story "Ƙarfen Ƙafa". https://www.wattpad.com/1015298066?utm_source=android&utm_medium=com.whatsapp&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=Rufaida-Umar&wp_originator=APuHCxKNugEN8dtZunyL4O%2FJKBns%2FO08vTjSCIlxF7AhR%2BRuxyUYJF8vGaw9PlhcYs%2Fd5Guq41cilqJPUF4w8sQuGhQdsC6bSLWR4oVKhbuxPFsqscrPZn1s%2BR6QxkUd





🕯️ *ƘARFEN ƘAFA*🕯️

_*Rufaida Umar*_

Bismillahir Rahmaanir Raheem.

55)


"Na kasa gane kanka. Wai me ya sauyaka haka?"

Hussein wanda ke jin kirjinsa har wani zafi yake ya kasa magana sai guntun tsaki da ya ja.

"Allah Ya kyauta. Amma idan har dagaske kana son Ramlat toh ya kamata ace zuwa yanzu ka bada kai bori ya hau. Bana son wannan zurfin cikinnaka alhalin ni na sani wallahi ko mijinta na farko sai an yi dagaske zai kamo ka a son da ka ke mata."

Nan ma dai shirun ya kara samu maimakon amsa, Hisham dole ya ja baki ya yi shiru don ya soma jin haushi.

"Zamu je Yakasan?"

Ya tambaya bayan ya yi tuƙi mai ɗan tazara daga gidan su Ramlat. Ajiyar zuciya ya saki ya dubeshi da jajayen idanun da ɓacin rai ya rinar.

"Ba zan iyaba. Mu yi hakuri ko zuwa gobe ne, ba ta ɓaci ba."

"Ok!" Yanda Hisham din ya amsa sai ya tabbatar da fushi ne don haka ya yi ɗan murmushi.

"Ka yi hakuri."

Shima Hisham don ya rama sai ya shareshi, a karshe ma ɗaya daga cikin waƙoƙin Breaker ya kunna mai suna So.

A hankali Hussein ya lumshe idanu yana sauraron waƙar, wani abu ke ratsa zuciya da gangar jikinsa sai dai kuma yana ji a jikinsa ba mai yiwuwa bane. Daga yau zai mishi iyaka da zuciyar da gangar jikinsa har sai ya ga abinda hali ya yi.

***
Hajiya Zeenatu ta ƙara buɗe zanin jikinta, fitowarta daga banɗaki kenan. Hankalinta idan ya yi dubu ya tashi, maimakon da ta soma shafa cream na ƙuraje da likita ya ba ta, kurajen su mutu sai abin ya kara yin gaba. Don a farko iyakar cinyarta ne kadai, yanzun kuwa har su na kokarin dabaibaye dukkan wata gaɓa daga ƙugunta zuwa ƙasa. Ta kuma lura da wani abu guda, ko yaya ruwan ya taɓa jikin fatarta sai wani kurjin ya fito.

"Na shiga uku ni Zeena! Me zan gani?!"

Ta dora hannu a kai nan da nan idanunta suka fito ƙululu kamar za ta yi kuka. Wato dai don bakin ciki cuta bai tashi yi mata kamun kazar kurkuku ba sai da ta ke dab da more rayuwarta da miji? Sai da komai ha daidaita babu tsafi balle asiri?

Wani irin miƙewa da ta yi sai da zanin ya faɗi, ba ta bi ta kai ba ta karasa sif na kayanta, doguwar riga ta sauya hannunta har wani irin rawa ya ke yi, ta gwammace yau ta je babban asibitin Malam ta ga likitan fata. Tana ji a jikinta abin daga fatarta ne. Ba ta yi tunanin ciro waya ta kira Hussein da zummar neman izni ba, sai da ta shiga mota, koda ta fadamasa a dawo lafiya kawai ya ce daga nan bai ƙara uffan ba, itama ba ta son ya kara don yanzu ta lafiyarta ake. Babban tunaninta yanzu komai na tafiyarsu London ya zama ready, ga samu ga rashi. Haka ta ke ji a ranta.

***
Yau kwanaki biyu kenan da Yusufa ke zaryar gidan su Ramlat sai dai ba ya samunta. A karshe dai ya nemi lambar wayarta ya kira. Bayan sun gaisa ya yi kata kwatancen ko waye shi. Jin ya ce shi ɗin ƙanin Halima ne yasa ta maida hankali ga sauraronsa.

"Aunty maganar ba ta waya ba ce, saƙo ne daga Yaya Halima, tun ba yau ba ta ban ta ce na isar gareki. Na so ajiyewa wurin Maigadin gidanku amma kuma bana so ya kasance bai isa hannunki ba."

Da mamaki Ramlat ta gyara zama saman kujerar Office din.

"Kana ji? Ko zan maka kwatancen ofishin da nake aiki sai ka kawomin."

Cikin zumudin hakan ya amsa da toh ya kuma yi mata godiya.

Wuraren karfe biyar da  mintoci na yamma sai ga Yusufa. Da kanta ta fita suka gaisa, sau ɗaya ta taɓa ganinsa, rashin lafiyar Kakar Halimar da ya tashi suka je dubiya asibiti daga tsohuwar ma'aikatarta. Suka gaisa kafin ya ciro takarda a ninke ya miƙa mata.

"Ki yi hakuri wallahi saƙonnan ya fi sati a hannuna, rasuwar Kakarmu ce ta sanya ban kawomaki ba sai yanzun.  "
Cike da jimami ta ce.

"Kaka ta rasu? Allahu Akbar, Allah Ya yi mata rahma. Yasa aljanna makoma. "

Yusufa ya amsa da amin. Daga haka suka yi sallama bayan ta mishi ihsani.

Kasancewar an kusan tashinsu daga aiki yasa kawai ta jefa a jakarta.

Ba ita ta samu damar warware takardar ta karanta ba sai bayan Magriba. Lokacin ta samu nutsuwar wanka har ma da na cin abinci. Ga abinda ta kuntsa.

_*Assalamu alaikum Ramlat.*_
   
     _*Da farko zan soma da ba ki hakuri, haƙiƙa na sani ni Halima ban cancanci komai daga gareki ba ballantana har ki yafemin. Sai dai duk da haka ina mai nadama da dana sanin abinda na aikata gareki. Ni mai laifi ce, ina neman gafararki Ramlat. Hassada da son abin duniya irin nawa ya kai ni ya baro. Yau ganinan a gidan da ko a mafarki ban taɓa zaton zuwansa ba.*_

_*Na aikata bisa tursasawar Hajiya Zeenatu da kawarta Hajiya Batulu. Duk irin tsanar da na yi maki ba zai sa na yi yunkurin kashe ki ba. Duniya aka kwaɗaitamin, ni kuma na karɓa da gaggawa ba tare da tunanin abinda zai je ya dawo ba. Ina neman gafararki. Ki yafemin domin Allah Ramlat. Wallahi a yanzu haka na tsani kaina. Ba ni da kwanciyar hankali daidai da kwayar zarra. Ki yafemin ko zan samu ganin haske a rayuwata da kuma mafarkaina. Na gode.*_

_*Halima Shehu.*_


Ajiyar zuciya ta saki sannan ta ninke takardar, a hankali ta sanya bayan hannu ta share hawayen saman fuskarta. Ba ta taɓa kawowa Hajiya Zeenatu ce ta sa Halima kasheta ba. Sai dai tayar da zancen ta san ba shi da amfani, ta bar wa Allah komai.

Ta ƙurawa takardar idanu sai kuma ta yi murmushin yaƙe ganin cewar Halima ba ta da masaniyar ita ta jima da yafemata ma. Gefen dirowar gadon ta buɗe ta cilla.

"Mami! Mami!"

Ansar ne ya shigo hannunsa riƙe da wayar Hajiya yana game.

"Wai Hajiya ta ce ki zo, ga Baba Dakta ya zo."

Ta ji kirjinta ya buga. Ta amsa da toh sannan ta mike ta yafa mayafin doguwar rigar da ke jikinta. Hajiya na zaune ta sha lulluɓi su na ɗan taɓa hira. Ta karasa ta durkusa ta gaidashi. Ya kalleta da fara'arsa. Ta mike ta koma kicin ta kawomishi ruwa da lemu. Sannan bisa umarnin Hajiya, ta ja yaran zuwa ciki don su yi magana.

Hankalinta ya kasa kwanciya a dakin, zirga-zirga kawai ta shiga yi, ganin an kwashi mintuna yasa ta kasa hakuri sai da ta ɗan kasa kunne. Ta ji Hajiya da na fadin.

"Ai wannan ba a bukatar jin ta bakina ko ita Ramlatun. Ramlatu da Amrah duk daya ne. Dukkan hukuncin da ku ka yanke a kanta nasan ba za ta taɓa yin da na sanin zaɓinku ba in sha Allahu. Balle kuma dama akwai fahimtar juna tsakanin yaran. Ni dama hankalina ya fi kwanciya da shi tunda ko ba komai ba wannan ne aurensa na farko ba. Allah Ya sanya alheri. Ya sa ayi muna raye."

Ramlat tuni ta ji wani gumi na tsastsafo mata, kirjinta ya tsananta bugu, ta ji Baba Dakta na kara godiya da yiwa Hajiyar addu'a. A karshe ma yake batun zai je takanas can Yakasai ya ga su Kawu su yi magana. Gwuiwa a sake ta juya ta koma saman gadon, Affan ya damu da kai ƙarar Ummi ta ɗauki wayar Mamin, ba ta san sadda ta dakamasa tsawar da dukkan yaran sai da suka tsorata ba. Ta ja guntun tsaki ta riƙe kai, salati kawai ta ke yi da addu'ar Allah Yasa hakan ya zamemata alheri. Ta dafe saitin kirjinta, ba ta taɓa zaton lamarin aurenta da Baban Hanif zai zo mata da yanayin ɓacin rai kwatankwacin na Hilal ba sai yanzu. Sai dai wannan karon alƙawari ta yiwa kanta, ko me zai je ya zo, za ta rungumi zaɓin iyayenta da hannu bibbiyu.

"Ki godewa Allah da zaɓinSa. In sha Allah jikina yana bani wannan aurennaki shi zai zama na dindindin duk kuwa da cewar sai an yi hakuri kuma an kai zuciya nesa saboda kananun maganganun da kan iya tasowa."

Wannan shi ne kadai abinda ta ji a bakin Hajiya, nan ta tuna wayarta a safiyar yau da Baban Hanif, inda cike da damuwa yake sanarmata irin tashin hankalin da yake fuskanta daga iyayensa game da aurenta da ya yi niyyar yi. Labari ya zo musu cewar ta taɓa yunkurin kisa a aurenta na farko. Wannan ne dalilin da yasa gaba ɗaya a kwanakin ta kasa gane inda ya nufa.

Ramlat ta dubi Hajiya karo na ba adadi tun zamanta a falon, waya Hajiya ta shiga yi da Munir, ta kasa kunne amma a karshe ma sai Hajiyar ta miƙe ta nufi ɗaki. Ranta sai ya soma ɗan baci. Ko ba komai ba wannan ne aurenta na farko ba, ya kamata ta san wa za ta aura ai. Hakan kuma bai nufin jayayya za ta yi da su. Ko kadan, ta rantse koma waye ta yarda kuma ta amince da aurenta da shi, kawai dai tana son sanin waye. A gefe guda kuma jikinta yana ba ta cewar ta yi BANKWANA DA HUSSEIN. Bankwana na har abada.

"Mami! Wayarki."

Ta sa hannu ta karɓa a hannun Ummi. Baban Hanif din ne kuwa ya kira don haka ba ta jira ya kara ba ta bi bayansa. Sai da ta shiga daki ta rufe kafin ta amsa sallamarsa. Bayan sun gaisa a gaggauce ta ce.

"Kun yi magana da Baba Dakta ne?"

"Eh ya kirani dazunnan da yamma, mun yi magana sosai da shi. Labari ya zo maki kenan?"

Ta kasa magana kawai sai ta kashe wayar gaba daya, kai ta dora saman gwuiwar ƙafafunta ta shiga rera kuka. Kukan jin zafin Hussein da ya kasa kallonta matsayin masoyiyarsa. Ta gasƙata cewa yanzun babu wani abu da zai ƙara shiga tsakaninta yanzun. Ta ji kuma ta hakura da zaɓin Allah. Dakyar ta iya miƙewa ta faɗa ɗakin yaranta, kowannensu ta gyarawa gado don yanzun ta sauyamusu da gado kanana na yara kowanne da na shi. Ta kakkaɓe, ta ba su umarnin kwanciya. Kasancewar sun saba da baccin wurin hakan yasa su na kwanciyar bayan ta sa sun yi addua, bacci ya ɗauke su.

Ta yi shiru tana kallonsu bayan ta gama kwashe shirgin kayan da suka zubar a ƙasa ta ninke kayan sif din da ya lalace. Aliyunta ne ya faɗomata, zuciyarta ta ƙara karyewa, nan ta shiga rera wani sabon kukan. A karshe don kanta ta rarrashi zuciyarta ta share sannan ta fita ta ja musu ƙofar.

"Ashe AlHassan ya zo garinnan?"

Ta dubi Hajiyar da le tambayarta, robb ta ke faman shafawa a ƙofofin hancinta.

"Ban sani ba wallahi. Yaushe?"

Murmushi Hajiya ta yi.

"Ai da Husseini muke waya, sai ya ba shi muka gaisa. Wai jiya-jiyan nan. Amma ya cemin zuwa gobe zai shigo in sha Allahu."

"Allah Ya nunamana."

Ta fadi a ɗan gaggauce don ji ta ke yi kamar ta fashe da wani kukan.

Hajiya na lura da ita kuma abin na ba ta mamaki amma ba ta ce uffan ba. Ta san dai idan ma da wani abu na daban a zuciyar Ramlatun, dole yanzu ta yi kokarin kawar da shi tunda dai bakin alƙalami ya riga da ya bushe.

***
Tun sadda Hajiya ta shaidamata cewar ana nemanta a Yakasai, Kawunnanta, kirjinta ke bugu da sauri. Affan wannan karon maƙalewa ya yi zai bi ta, dole ta shirya shi suka fita tare. Adaidata Sahu suka hau kasancewar motarta ta samu matsala.

A hanyar ma babu cikakkiyar nutsuwa tattare da ita sakamakon tunanin abinda zai biyo baya da ta sa a rai. Kiran ko kusa bai ba ta mamaki ba, ta san dama tunda har aka ce an mata miji to komai ma za ta gani. Har dai suka iso ba ta jin ta ba Affan kwakkwarar amsar tambayoyinsa na shirme da ya ke mata. Karshe ma da ya dameta cewa ta yi za ta bar shi a cikin Napep din dole ya ja baki ya yi shiru.

Ɓangaren Baba Dije ta soma shiga. Bayan sun gaisa ta ce.

"Ina tayaki murna ƴarnan,

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login