Showing 93001 words to 96000 words out of 230725 words
To wa ma za ta tunkara cikinsu.
Ajiyar zuciya ta saki ta koma cikin ƴan uwanta ba ta ko kula jan da suke yi mata ba. Murmushi kawai ta yi don tasan ba wannan ne a gabanta ba.
***
Ranar juma'a aka sanya Amarya a lalle, sai da ta je wurin aiki ta dawo ta iske farfajiyar gidannasu da aka ƙawata da kayan kyale-kyale, ya yi kyau sosai. Babu batun anko, kowa kayansa ya sanya.
Ta hade abinta tsaf cikin atamfa Batik kalar orange mai surkin ja. Ba ta yi wani kwalliyar a zo a gani ba, yanda dinkin ya zauna ɗas a jikinta ba karamin kyau ta yi ba. Kai ba ka ce ta haifi yara uku ba.
Anyi lalle lafiya, an ci an sha. Amrah da Muhibbat sun zo dukkansu, anyi hira da dariya abinsu tsaf. Sai da Magriba ta doso kafin a soma tafiya yin Sallah, tuni Muhibbat ta wuce. Ramlat kuwa kasancewar ba ta da Sallah yasa ta miƙewa ta zauna, dole ta tashi ba don ta so ba don Amrah ta rantse sai sun je ta taimaka mata da cirewa Zaituna famfas don tunda ta zo bikin, yarinyar sai ta ƙi zama wurin Ummanta, ta naniƙe mata.
"Kedai wallahi kin shiga uku da kwuiyar masifa, ace famfas dinma ba za ki iya fiddawa yarinya ba?"
"Naji ko me za ki ce, ki yi ta faɗa. Nidai ki cire din."
Fadin Amrah, murmushi kawai Ramlat din ta yi. Suna shiga dakin, ta ji kamar ta juya. Bilkisu ce zaune sai kanwarta Salma, sai wata budurwa da ba ta sani ba. Suna daga gefe zaune yayinda Zulaihat ke dakin tana sallah. Sanin da ta yi ta gaisheta ne yasa ta yi gaba zuwa banɗaki ta bar Amrah suna gaisawa.
Ta cirewa Zaituna famfas ta fito daidai sadda Bilkisu ke tambayar Amrah.
"Ni kuwa don Allah ba Muhibbat ce tsohuwar matar Aliyu na ganku tare ba?"
Amrah ta saci kallon Ramlat da ta dauke kai tana maidawa Zaituna wando kamar ba ta san me suke ba, ta kara duban Bilkisu da murmushin yaƙe.
"Eh ita ce."
Taɓe baki Bilkisu ta yi.
"Shi ne har da zuwa gayyar soɗi? Kai wasu ma akwai karfin hali, wato har gayyatar ta aka yi?"
"Gwara da kika gyara Anti, kin yi kiɗanki kuma kin yi rawarki. Ba gayyar soɗi ta zo ba, Ramlat da kanta ta kai mata katin gayyatar."
Amrah ke maganar tana murmushin tura haushi. Maimakon haka sai Bilkisu da Salma suka tuntsira dariya.
"Wai, Sis? Dan adam ma bai da kunya wallahi."
Salma ke fadi tana duban Bilkisu. Ramlat ta dubi Amrah.
"Malama kin fasa alwalar ne? Zan koma can kya iskeni."
Daga haka ta sa kai za ta fita, maganar Bilkisun ta dakatar da ita.
"Yanzu ke Ramlat tsabar rashin ta ido, matar da kika yiwa kwace ita ce yanzun kika dawo kina wani zumuncin neman suna da ita? Ta dai bi a hankali kar a maimaita ƴar gidan jiya."
Cak ta kasa koda motsi, juyowa ta yi ta dawo da baya. Ta san take-taken Bilkisun. Tun safe take jefa habaici, ta zagi dangin miji ta zagi kishiya, duk don Yaya Munir zai ƙara aure ne. Zuwanta gidan bikin kusan da biyu ta yi.
"Ramlat, fita daga dakin nan."
Ta dubi Zulaihat wacce idar da sallarta kenan, ta kara da roƙarta.
"Don sonki da Allah da ManzonSa s.a.w nace ki fita."
"Ki kyaleta mana, au karya aka fada? Da ta tsayamin kerere tana da bakin magana ne?"
Bilkisu ta fadi har tana fidda huci da girgiza ƙafa, dama kiris take jira ta yi musu tas don yanzun cikinsu ta tsani kowa, kallonsu kawai take yi. Mijinta zai ƙara aure tasan har da amincewarsu da na uwarsu.
Maimakon Ramlat ta yi magana sai ta fasa gami da kara rike Zaituna a jikinta su bar dakin.
Koda ta koma farfajiyar gidan, kurawa ƴanmatan dake rawa kawai ta yi amma ta kasa cewa uffan. Tunani ta fada, ba Bilkisu ce farkon fadin hakan ba game da alaƙarta da Muhibbat, akwai sadda mahaifiyar Muhibbat din ta isketa a gidan ƴarta, tana jin sadda ta ke yiwa ƴar faɗa akan don me za ta dinga jawota gidanta. Wannan abu ya yi mata ciwo, yana daga dalilan da yasa ta janye jiki daga Muhibbat din, sai dai matar na mata kauna ta don Allah, wannan tasa ba ta rabo da taɓota ta whatsapp ko ta aikomata saƙon gaisuwar juma'a ta text. Dalilin kenan da yasa itama ke ganin kirkinta. Ji da ta yi an taɓa kafaɗarta ne yasa ta kallon mai shi, Amrah ce. Zama ta yi.
"Kar fa maganar waccan banzar ya dameki, ai bayan fitarki kamar su doki juna ita da Maman Twins. Wallahi tas ta yi mata har da cewa aure kamar Munir ya yi ya gama. Matarnan ta yi jijjiga da zuba ruwan bala'i, ke da tana da iskokai a ta tayar. Ashe itama Maman Twins ciki take da ita, da safe wai ta mata magana ta dauke kai kamar ba ta ji ba. Sau kusan uku suna hakan, kuma ta ji ƙananun maganganun da take game da auren Yaya Munir tana zagin dangin miji."
Murmushi Ramlat ta yi.
"Ya ci ace na daina damuwa da lamarinta, na lura ba na ƙare bane."
"Atoh, ashe dai kin gane. Ya kamata ki yiwa kanki fada. Damuwa ba ta maganin komai."
Gyada kai kawai ta yi, zuwan su Naja'atu ne yasa su sakin zancen a ci gaba da raha.
***
Washegari tun safe suka tashi aka shiga aikace-aikace, sauƙinta ɗaya, wasu ayyukan na abinci, Hajiya bayarwa ta yi order. Kamu da yini ne wanda za'a fita a yi a wani katafaren event centre na masu faɗa a ji. Ango da kansa ya kama wurin.
Karfe uku aka sanya, sai dai halin mutanenmu, ba'a soma tafiya ba sai bayan la'asar.
Ƴan matan Amarya ankonsu daban, wata Atamfa ce kalar fari da blue. Fadin irin kyan da suka yi ma ɓata baki ne. Hakanan a ɓangaren ankon sisters, maimakon su uku, (Ramlat, Zulaihat da Rafee'ah), sai ya kasance su duka suka yi har su Naja'atu su Amrah da ma wasu cikin ƴan uwansu na cikin gari. Atamfa ce su ma blue zallah mai adon fari kaɗan kaɗan ba kamar na ƴanmatan ba. Wannan karon sosai Ramlat ta yi kwalliya domin mai kwalliyar aka dauko ta musamman har gida ta yiwa jama'a da dama. Amarya da ƙawayenta kuwa fita suka yi.
Wurin ya cika taf, Amarya da Angonta Hisham sun yi kyau har sun gaji. Maza da mata ne a wurin kowanne da nashi ɓangaren. Shiga take tana fita ita da Rafee'ah da su Naja. Amrah karamin cikinta mai ɗan karen laulayi yasa ta samun gefe ta yi zamanta tare da Affan da Zaituna ba tare da ta biyemusu ba. Takan kalli Ramlat akai-akai ta yi murmushi. Ita kanta aminiyarta ta yi mata kyau.
Ta jima rabon da ta ganta cikin walwala da farin ciki irin haka, sai ta dawomata Ramlat dinta sak da suna ƴanmata kafin komai ya sauya.
Ita kuwa Ramlat, waje ta nufa ta tarbo matan ofis dinsu da suka zo mata takanas bikin A'isha. Halima, Naja'atu Azare, Fa'iza da Zuhra.
Halima sai cin magani take don tun a motar Zuhra da ta nemi ayi gulmar Ramlat din, suka ƙi bada fuska ta cika ta yi fam. Yanzun kuwa ganin irin masu hannu da shuni da aka tara a wurin sai jikinta ya yi sanyi, ko ba komai wutsiya raƙumi ta yi nesa da ƙasa. Ramlat suna da kudi daidai gwargwado, kamar yanda ta lura, dangin Angon su ma ba baya ba. Har suka karasa suka nemi wurin zama ba ta bar mamakin yanda wurin ya haɗu ba.
"Malama rufe bakin." Muryar Samira ta katse tunaninta, ta harareta.
"Bana son iskanci." Suka yi dariya, ita kuwa Ramlat bayan sun gaisa gaba ta yi ta kyalesu don samar musu abinci.
"Hali Dubu!"
Halima ta juya tana neman mai kiranta, ido hudu suka yi da Salma ƙanwar Bilkisu, kuma abokiyar karatunta. Nan da nan ta saki fuska ta mike ta nufi wurinta, itama Salma ta nufota suka rungume juna kafin a saki ana shewa da murnar ganin juna.
"Kai Salma, dama kina duniya?"
Salma ta yi dariya, kiɗan da aka kunna ne yasa ta jan hannun Halima suka ɗan fita daga hall din.
"Halima Halee Baby! Kin kama ƙasa kin yi bakam ba'a ji da ganinki kwana biyunnan har a whatsapp."
"Wane kama ƙasa aikin da bai taka kara ya karya ba Salma? Kedai muna fatan nan gaba mu kama ɗin, mu samu wani mai hannu da shunin."
Suka yi gami da kara cafkewa.
"Family din Ango kike ne?"
Salma ta tambaya tana dubanta. Taɓe baki ta yi.
"Ko ɗaya, yayar Amaryar ce ta gayyacemu. Abokiyar aiki na ce. Ofis din mu ɗaya."
"Ramlat?"
Fadin Salma cike da mamaki. Itama Halimar kallonta take gami da ba ta dukkan hankalinta.
"Kwarai ita fa."
Yamutse fuska Salma ta yi.
"Amma dai ba ƙawarki ba ce?"
"Meyasa ki ka yi wannan tambayar?"
Cewar Halima cikin zaƙuwa.
"Tab, kin tuna auren wani Cousin brother dina da na ba ku labari a WhatsApp? Wanda nace maku matarsa ta kusa kashe shi ranar da aka kai ta gidansa?"
Da sauri Halima ta shiga gyada kai kamar ƙadangaruwa.
"Yes yes, na tuna!"
"Toh ai ita ce. Sanadin da ya saketa kenan, ta dage da auren wani Aliyu. Na fadamaki sai ya yi shaye-shaye ya zo ya yi mata tsinanan duka ya kyaleta ba ci ba sha. Dakyar dai ta samu salama bayan mutuwa ta rabasu. Ni naji ma Anti Bilki na cewa wai Ƙanjamau ta kasheshi."
Halima ta saki baki da hanci kafin ta yi wata dariya.
"Ke Salma! Ki rantsemin da Allah."
Salma ta ja tsaki.
"Na taba yi maki irin wannan wasan? Lallai ma, ai yanzu ta ƙi auruwa kowa tsoronta yake ji. Ku dai bi a hankali da ita ko a ofis kar ta shafamaku mugun abu."
Halima wani dadi da farin ciki ya mamayeta, wannan labarin ya fi komai yi mata dadi. Ko ba komai anan za ta huce haushin tsanar da ta yiwa Ramlat da cin mutuncin da ta ja mata a ofis.
Suka yi sallama da Salma suka dawo wurin bikin, a hanyar ma sai ƙaramata gishiri da siga ta ke yi. Abinda aka yi da wanda ma ba'a yi ba duk ta haɗa ta faɗawa Halimar. Burinta itama ta ɓatawa Ramlat suna a ko'ina.
Koda Salma ta koma mazauninta, gaba daya ta kwashe yanda suka yi da Halima ta fadawa Bilkisu. Dadi kamar ya kasheta. Har kyauta ta ce za ta yi mata. Suka yi ta dariya ransu fari ƙal.
A ɓangaren Ramlat kuwa, haka ta yi ta hidima da ƴan ofis dinsu har suka tafi, ta yi mamakin yanda Halima ta sakarmata kamar ba ita ba. A karshe ta yi musu rakiya har wurin mota bayan ta kaisu sun gaisa da Hajiyarta sun mata fatan alheri.
"Amma zaku zo dinner goben ko?"
Ta fadi sadda ta kama murfin motar tana dubansu.
"Me zai hana? Za mu zo." Halima ta fadi cikin sauri. Duk suka dubeta. Ba wanda ya yi magana suka amsawa Ramlat da cewa zasu zo. Ta kuwa ji dadi ta yi godiya. Daga nan suka ja suka bar wurin ta koma ciki.
***
WASHEGARI...
LAMIƊO CI just published "BABI NA ASHIRIN DA TARA" of my story "Ƙarfen Ƙafa". https://my.w.tt/FLZKsoqJJab
🕯️ *ƘARFEN ƘAFA*🕯️
*_Rufaida Umar_*
Bismillahir Rahmaanir Raheem.
29)
LAMIƊO CRESCENT
A hankali ya ɗago kai daga kallon jaridar da ya ke ya maida saman fuskar wayarsa dake faman ruri a saman tebur. Murmushi ya yi, irin murmushin da idan har ka gani saman fuskarsa to bai ɗauki mutum nan kusa ba. Ko sallama bai kai ga yi ba ya soma yi mishi mita.
"Kai dai wallahi anyi ɗan iska, wato dagasken dai ba za ka zo ɗaurin aurena ba ko? Ni za ka yiwa wannan tsiyar!"
Dafa goshinsa ya yi gami da ɗan runtse ido.
"Oh no, dagasken gaske na mance fa. Yi hakuri."
"Hakuri kake bani? Ba zan hakura ba wallahi muddin ban ga ƙeyarka a dinnerparty ɗina ba! Ka kyauta sosai!"
Hisham bai jira cewarsa ya katse wayar, sakaka ya bi wayar da kallo kafin ya ajiye yana murmushi.
Tunda ta soma taka matattakalar benen idanunta gaba daya a kansa, yanda yake murmushi ya sanya ta jin wani abu mai kama da kishi ya soki ƙahon zuciyarta. Kaf duniya ba ta jin akwai wanda ya isa shiga rayuwar mijinnata har ya sanyashi ya murmusa idan ba ita ba. Tunaninta gaba daya ya tafi ga zargi kamar yanda ta saba, wato da mace yake waya. Wannan ya ƙaramata saurinta ta shiga haɗa step bibbiyu tana saukowa, ikon Allah ne ya kawo Hajiya Zeenatu cikin falon ta yi mishi kerere a ka.
Ya ɗago ya dubeta gami da lumshe idanu ya bude.
"Me akai?" Ya nemi sani cikin halin ko'inkula. Hannu ta kai ta ɗauki wayarsa ta shiga sarrafawa don tunda suke bai taɓa sanya password lock a wayarsa ba, koda zai sanya, Hajiya Zeenatu ta san mabuɗan, abin da ke ba shi mamaki, ba shi da hurumin da zai ɗauki wayarta ya sarrafa yanda ta ke sarrafa nasa.
Bai katseta ba har ta gama shiga da ficenta, asalima maida hankali ya yi ga jaridarsa, zuciyarsa na jin ciwon abinda ta ke aikatawar, bakinsa ya kasa motsawa balle ya tsawatarmata, bai ji yana da jarumtar da zai ce ba ya so ba.
Zama ta yi gefensa gami da riƙo hannunsa tana murmushi, ya dubeta ya maida martani wanda ya fi kama da yaƙe.
"Ashe fa Hisham an yi aure? Gaskiya bai kamata ace ba ka je daurin aurensa ba."
Ya jinjina kai yana dan yaƙe.
"Hakane, yanzun ma ya ce lallai fa sai naje mishi Dinner."
Ta yamutse fuska.
"Wane irin dinner kuma? Salon ka je wata ƴar iska ta ganka ta nuna tana sonka? Abinda ba zai yiwu kenan ba, ya yi hakuri daga baya idan sun tare sai muje har gida mu ga Amarya."
Ya dubeta ya ɗan ɗaure fuska, yana jin kamar ta ragemishi wani farin ciki a rayuwa, sai dai ita din ba ta laifi koda ace uwa da ubansa ta zaga.
"Shikenan, duk yanda kika ce, hakan daidai ne."
Hajiya Zeenatu ta yi murmushi mai kyau har ruwan ɗorawar hakoranta suka bayyana. Ya kauda kai, ta shafi gefen fuskarsa.
"Shiyasa nake ƙara sonka mijina ni kaɗai! Zan fita sai na dawo."
Gyada kai kawai ya yi sannan ta mike, doguwar rigar shadda ce a jikinta sai wani karamin mayafi da ta yafe kanta da shi, san shigar bai mishi tsarin da matar aure za ta fita da shi ba. Ya kauda kai gami da sauke ajiyar zuciya. Inda za ta je ma bai sani ba, ba jimawa dai ya ji tashin motarta. A hankali ya kwantar da kai jikin kujera gami da lumshe idanu. Yana bukatar tunani, sai dai tunanin ya jima da gushewa. Duk kokarinsa, duk irin yaƙin da yake da zuciya da kwakwalwarsa, sun kasa ba shi haɗin kai. Kamar yana aka saba ne ya afku, matsanancin ciwon kai wanda ya sanyashi hakurin dole ya miƙe ya haye sama.
***
Tun ƙarfe takwas na dare farfajiyar ƙawataccen Event Centre din na Marhaba, ya cika ya batse da yan mata da samari matasa sai tsirarun iyaye. Kwalliya iri-iri kawai ka ke gani. Wasu tuni suka shige dakin taron yayinda wasu suka tsaya ƙyam jiran saukar Amarya da Ango. Tana daga can gefe tsaye cikin wani arnen baƙin lace, ta ɗora silver head. Ummi kadai ce ta biyota wurin taron, zaman ɗankwalinta take gyaramata tana faɗan muddin ta ƙara cirewa sai dai ta nemi mai ɗauramata don ita ba baiwa ba ce.
"Ni kuma bawa ne, na yarda na amince idan har ƙarƙashinki zan yi aiki zan yi din koda ba biya."
Tun soma maganar ta juya tana kallonsa. Ya haɗe cikin wata gogaggiyar shaddarsa ruwan ƙasa, murmushi kawai ya ke yana dubanta babu ko kyaftawa.
"Uncle Hilal!" Faɗin Ummi kafin ta fisge jikinta daga na uwar ta yi gaba a guje ta rungumeshi. Ya durkusa yana mai ɗago fuskarta yana dariya, dariyar ba ta komai ba ce sai na ganin yanda Ramlat ta haɗe fuska don Ummi ta tafi ta bar ta da ɗankwali a hannu wanda ya warware gaba daya sai jerin ƙananun kalbar da aka yi mata ke yawo a iska.
"Kin ƙara yiwa Mami laifi. Kinga."
Ya yi mata nuni da Ramlat, ganin haka Ramlat ta kauda kai bayan ta watsawa Ummin harara, ta rufe motarta ta jefa muƙulli jaka ta nufosu. Ganin hakan yarinyar ta tsorata ta yi bayan Hilal da sauri gami da fadin.
"Mami please ki yi hakuri, sunan Hajiya fa ne da ni."
Kusan da hakan ta saba cin galabarta, Ummi akwai wayo da saurin ba da hakuri bisa laifi. Kusan dariya ta basu daga ita har Hilal din. Ya mike tsaye bayan ya yakice Ummi dakyar a jikinsa.
"Ba za'a yi mata afuwa ba?"
Ta ɗan harareshi tana murmushi, ya lumshe idanu ya budesu a kanta, sai kuma sannan ta farga da katoɓarar da ta yi, ko meye na yi mishi murmushin? Da saurinta ta kauda kai ta soma tafiya da nufin barin wurin. Riƙon da ya yiwa ɗankwalin Ummin ne yasa ta kallonsa, kasancewar ya tarkata dukkan nutsuwarsa a kanta yasa kai tsaye idanunsu suka sarƙe cikin juna, ta yi saurin janye nata idanun.
"Ana kallonmu fa."
Ta furta a ƙagauce, zuciyarta har zafi ta soma. Takaici da haushin kanta ne ke mamayeta. Wani sashi na zuciyarta ihu yake mata, yana mata tunin bai kyautu ace har ta mance baya ba. Bai kyautu ta saurari kowane namiji ba, ko ba komai ta yiwa kanta alƙawarin gudanar da rayuwarta babu aure, ta raini yaranta har su zamo abin alfaharinta duniya da lahira.
"Lah, Yaya Hilal?" Kusan a kidime ta kai duba ga mai maganar, Salma ce tare da Halima. Zuwan su Halimar kenan ta ha hannunta don ta yi mata hotuna.
"Ramlat?" Fadin ita Halimar. Lokaci guda Hilal da Ramlat suka dubi juna kafin ta kauda kai da sauri ta sakarmasa ɗankwalin Ummin ta yi gaba wurin Halima. Murya na rawa ta ce.
"Ha..lima., yaushe ku ka zo?"
Halima wacce a farko bakin cikin