Showing 54001 words to 57000 words out of 230725 words

Chapter 19 - Karfen Kafa Book 1 Hausa Novel Complete

Unknown   

06 Jan 2025

1057

su a daren jiya har da zagin iyayenta sun fi komai tsayuwa a ƙahon zuciyarta. Ta haɗiye komai ta danne, ita kanta yanzun tana bukatar a duba lafiyarta, tana jin jikinta kamar babu jini balle ruwa, kamar ma a yau ɗin za ta mutu.

***
"Congratulations, kina da ciki wata biyu."

Kalaman da ke fitowa daga bakin likitiyar suka sanyata jin hanjin cikinta kamar zasu tarwatse.

"Ciki kuma? Dama haka ake cikin?"

Abinda ta fadi ya sanya daga Aliyun har Likitar dubanta, shi Aliyu ko fuskarsa kadai ka kalla za ka san yana murna da hakan duk da cewa yana auna yanda nauyi zai ƙara hawa kansa.

"Yes ciki, haka report ya nuna. Yaushe rabon da ki ga al'adarki?"

Tsabar rudewa ma ta mance da wani batun al'ada, ita tun zuwanta gidan Aliyu ba ta taɓa ganin jini ba. Shima Aliyun sai a sannan ya ankara da hakan. Maimakon ta yi murna, maimakon a ga tana dariya sai ta rike cikin tana kuka kamar wacce aka fadawa ranar da za ta mutu.

"Bana so, wallahi bana so! Dr ki zubar da shi."

Wani wawan mari Aliyu ya dauketa da shi. Ta rike ƙuncin a zabure ta mike tana dubansa cike da dumbin mamaki.

"Haba Malam, matarka ta sunnah? Ita za ka mara? Wane rashin hankali kenan? Koda ta yi kuskure ba ka ganin yarinya ce, bai kyautu ka lallaɓata ba? A ina aka taɓa marin mace, matar ma ta sunnah?"

Bai ko kalli Likitar ba wacce haushi da takaicinsa ya kamata. Ta zagayo ta kama hannun Ramlat da gaba daya ta gigice kukan ma ya tsaya cak. Ashe dai akwai marin da ya fi karfin kuka.

"Please get out. Ka bamu wuri."

Yana huci ya yi kwafa gami da hadata ita da Ramlat din ya watsamusu wani banzan kallo, har ya kai ƙofar ya juyo ya hau magana.

"Kika kuskura kika yi gangancin zubarmata da ciki, daga ke har ita sai na yi shari'a da ku!" Daga haka ya fice gami da banko ƙofar da ƙarfi har iskar na bugunsu. Dr Sadiya ta zauna kujerar da Aliyu ya mike, sannan ta maida Ramlat din mazauninta suna fuskantar juna.

'Ga ta a haka yarinya mai hankali da nutsuwa, sai dai da alama ba ta yi dacen miji ba.' Cewar Dr Sadiya a ƙasan ranta. Tausayin Ramlat ya kamata,ta danne ta soma yi mata nasiha.

"Ramlat ke fa musulma ce, cikinki koda shege ne ya haramta ki zubar balle kuma cikin sunnah. Ba ki yi kama da mutuniyar banza ba, ba kuma ki yi kama da mata ballagazazzu ba wadanda basu je makaranta ba. Ko mene ya yi zafi a rayuwarki, ki dinga tunawa da Allah. Shi ne Mai yaye dukkan wani azaba. Ki kwantar da hankalinki, idan ma haihuwa kike tsoro ki miƙa lamuranki ga Ubangiji, In sha Allah sai kiga kin haihu lafiya. Mutum nawa ne za ki ga su na neman haihuwar ba su samu ba? Wata ma da kudi za ki ga ta zo nan tana neman maganin da za ta sha ta samu ciki. Wata kuwa har kuka take yi tana faɗin yanda miji da danginsa ke wulaƙanta ta duk akan ba ta haihu ba. Ke kuma da Allah Ya ba wa cikin ma na sunnah ki ce bakya so? Kenan kina nunawa Ubangiji ba ki yi murna da kyautarSa ba?"

Ta girgiza kai tana share hawayen da sai a sannan suka zubo, so ta ke ta ce ba haka bane, so ta ke ta ce yaron ko yarinyar da ke cikinta, ba ta so su dauki ɗabi'un mahaifinsu, sai dai kuma ba za ta iyaba. Ko ba komai wannan sirrinsu ne.

Dr Sadiya ga ci gaba da lallaɓata da ba ta shawarwari har sai da Aliyu ya gaji ya dawo ofishin.

"Wai me ake yi? Ni fa zan iya barinki ki kwana anan idan ba ku kammala ba."

Ya yi maganar a fusace, Ramlat ta mike ta yiwa Dr Sadiya godiya, ita kuwa ta miƙa wa Aliyu file din suka fita. Tun a asibitin tana jinsa yana jan tsaki har dai suka siya magani suka fito yana mitar kudinsa sun kare.

"Wallahi injin ma na fasa kunnawa, kudin sun ƙare. Zan dai siyamaki kazar tunda na sakamaki rai."

Gyada kai ta yi kamar kadangaruwa, fuskarta duk ta kumbura saboda kuka. Bini bini sai ta shafi cikinta. Iskar mashin na neman yi mata yawa don haka sai ta dukunkule ta kwantar da kai kadan a gadon bayansa. Hakan da ta yi dukkansu sai suka ji wani sanyi da kaunar junansu yana kara ɗarsuwa a zuƙatansu.

"Ina sonka Sweet Aliyu, ba zan iya rabuwa da kai ba."

Ta furta a hankali, kalaman sun ratsashi. Ya yi murmushi gami da ɗan rage gudu.

"Baby wa ya ce miki zan iya rabuwa da ke? Ai mai rabamu sai mutuwa Baby. Don ina shaye-shaye addu'a za ki yimin har na daina, kin ji?"

Ya ji sadda ta gyada kai a jikinsa, kusan a tare suka yi murmushi. Murmushin tana yi hawaye na zuba, zuciyarta ta kasa tsanar Aliyun. Soyayyarsa da na abinda ke cikinta suka haɗarmata. Ta kuma daura ɗamarar faɗa wa Allah matsalarta akan Ya shiryamata mijinta.

Sai gashinan Gen din da yake cewa ba zai tayar ba, sai da ya siya mai rabin galan ya kunna suka ga haske. Ranar tattalinta ya dinga yi gami da fadamata karya da gaskiya duk don ta ji tausayinsa ta kuma yarda ba'a son ransa ya soma shaye-shaye ba. Ya kuwa ci galabar hakan.

***🕯️ *ƘARFEN ƘAFA*🕯️

*_Rufaida Umar_*

Bismillahir Rahmaanir Raheem.

_Assalamu alsikum ƴan uwana. Na gode sosai da addu'oinku. Allah Ya bar zumunci. Ameeen ameeen._


17)


Tun fitowarsu take bin bayanta, har suka bar wurin jama'a sosai. Tsayawa ta yi cak gami da juyowa a fusace.

"Wai Malama bibiyar ta menene? Me kike nufi? Kin san ni ne?"

Maganar ko kadan ba ta fusata Ramlat ba. Asalima hawaye ta soma ƙoƙarin zubarwa. Amrah da sauri ta kauda kai gefe, ba ta son ko kusa ta karya zuciyarta, ita kanta ta yi kewar aminiyarta sai dai kuma tunda har hakan ta zaɓamusu zai fi.

"Kiyi hakuri, don Allah ki yi hakuri ki yafemin Amrah. Kowa yan guduna, idan kema kin gujeni wa nake da shi? Da ke kadai na saba shawara, ki yi hakuri ki yafemin kuskuren da na maki."

A ɗan sace Amrah ta kalleta.

'Ta rame.' Ta ayyana a ranta. A fili kuwa ƙara tamke fuska ta yi gudun kada ta nuna rauninta a fili.

"Ai ba ki yimin laifin da na riƙe ki da komai ba. Mutum duk abinda ya zaɓarwa kansa, sai a zuba ido a bar shi da zaɓinsa. Ba ma miki mummunan fata ko kadan."

Ta juyo don ta san idan ta ci gaba da tsayuwar tsaf Ramlat za ta kalamance ta. Yanzun sai ta sauya dukkan ra'ayinta.

"I am pregnant."

Ta furta a hankali bayan ta kara matsawa gaba kadan. Cak kuwa Amrah ta tsaya, ta juyo tana dubanta. Gyada kai ta shiga yi tana share fuska.

"Eh Amrah."

Har ga Allah jin cewa tana da ciki ya sanyayawa Amrah jiki.

'To ko wannan shi ake kira rabo? Wannan auren kaddarar Ramlat ce.'

Ta yi maganar a zuciya, ganin jama'a na kallonsu ya sanya Amrah magana.

"Allah Ya raba lafiya. Na miki murna sosai. Kinga ana kallonmu, ki wuce gida kawai, gobe ma hadu a makaranta. Na yafemaki."

Ta ƙarashe da dan murmushi. Ramlat ta ɗan rungume kafaɗarta tana ƴar dariya. Ko ba komai za ta maido amintarsu.

Tare suka jera suka fita waje, abin hawa ne ya rabasu. Hatta Amrah sai sannan zuciyarta ta yi sanyi.

***
  Kofar falon a bude, wannan ya kara tabbatar mata da zargin maigidan na nan, tun a bakin ƙyauren ta ga motar da a yanzun ta shaida na abokinsa G Baba ne. A gajiye take lis amman murnar shirinta da Amrah ya mantar da ita hakan.

  Tun kafin ta saka ƙafa a falon, ƙaurin sigari da kuma hayaƙinsa ya baƙunci hanci da idanunta. Hira suke suna haɗawa da ashariya. Ji ta yi zuciyarta na tashi. Ta daure ta karasa shigowa falon da sallama. Suka dubeta. Aliyu ya saki murmushi.

"Baby, kin dawo?"

Gyada kai ta yi, don takaici ko kallon G Baba ba ta tsaya yi ba balle su gaisa ta yi ɗakinta. Zama ta yi bakin gado ranta na wani irin zafi. Kallon agogon bangon ta yi, shida na dab da yi. Kwafa ta yi ta rage kayan jikinta fa faɗa wanka.

  A falon kuwa, G Baba ya zuƙi sigari ya fesar.

"Madam dinka fa ba ta yi murnar ganina ba. Hala ba ta son wannan hayaƙe-hayaƙen?"

Wani tsaki Aliyu ya ja, ɓacin rai sosai Ramlat ta jazamishi.

  "Don uwarta an fadamata ni ban isa da gidana bane? Ko an fadamata shashashan miji ne? Zan je na sameta ai! Sa'arta ɗaya tana dauke da Baby."

Wani mugun kwarewa G Baba ya yi, Aliyu ya tsaya cak yana kallonsa.

"Lafiya? Ka zuƙa over Malam."

Sai da G Baba ya kora ruwa sannan ya samu nutsuwa. Ya ɗan dubi kofar dakin sannan ya juyo ya kalleshi.

"Ciki? Kai murna kake Madam dinka ta haihu yanzu? Kasan irin nauyin da zai ƙara hawa kanka kuwa? Wani fita eh yane, wani hawa gajimare duk raino zai sa ka daina. Kai Zaki! Yawane wallahi! Nawa kake ma yanzu? Gaskiya ku san abin yi game da cikin."

Aliyu ya daure fuska kamar bai taɓa dariya ba.

"Malam kar ka kara yimin zancen banza! Shege ne da za ka ce kar na bari ya fito duniya? Kai ka fi kowa sanin duk iskancina bai wuce zuƙe-zuƙe da ƴar romance ba, amma bana babbar harka balle a samu akasi. Toh don me za'a haifarmin ɗan sunnah ka nemi ka kashen gwuiwa. Ba dan iskan da zai sa na zubar da cikin Baby."

Ya ƙarashe gami da watsawa G Baba harara. Shi kuwa G Baba ya kara yarda da irin son da Aliyu ke yiwa Ramlat. Ya tabbata shi ya shafi abinda ke cikinta. Aliyu kaifi daya ne idan ya ga dama, idan har ya yi irin tsaurinnan to ba mai juyamishi ra'ayi wannan ta sanya ya ja bakinsa ya wayance da yi mishi kirari hadi da fadin.

"Ko ba komai ai ma zo mu ƙarawa sama ado."

Suka cafke gami da wata irin dariya.

***
  Ramlat zamanta ta yi a dakin bayan ta idar da sallar La'asar da ba ta yi kam lokaci ba. Tana jin yunwa, sai dai ba ta kaunar ganinsu. Kwantar da kai ta yi a saman hannunta jikin gado tana daga zaune saman darduma, tunani mai zurfi ta faɗa gami da riƙe cikinta. Har sannan tana kara jinjina lamarin, wai ciki ne da ita. 

'Cikin mashayi.' Wani bangare na zuciyarta ya ayyana mata, ta jima anan zaune har wahalallen baccin da ba ta samu yinsa da safe ba ya soma fisgarta sai dai cikinta na ta ƙara saboda yunwa.

A hankali ta ji hannu saman fatar cikinta. Firgigit ta bude idanu, Aliyu ne durkushe ya daga rigar yana shafa cikin. Suka hada ido, murmushi ya sakarmata. Ita kuwa warin sigari ke tayarmata da zuciya don haka ta mike da sauri ya riko hannunta gami da miƙewar shima.

"Baby lafiya?"

Ta rufe baki da hancinta da hannu ta shiga tureshi tana girgiza kai.

"Don Allah ka fita, warin taba, zan yi amai wal..."

Yunkurin aman ya katseta, da sauri ta faɗa banɗaki shi kuwa ya fita daga dakin. Ba wani abin kirki ta amayar ba, ta wanke baki ta fito, ganin baya dakin yasa ta daukar turare mai sanyin kamshi a bakin madubi ta ɗan fesa a jikin wani dan handkerchief ta toshe hancin sannan ta bude winduna  dakin.

Kiraye kirayen sallar Magriba ne ya sa ta mike ta zura hijabinta. Sai da ta yi sallah sannan ta mike ta nufi falon don Aliyun ya shigo har sau biyu kafin ta idar. Maimakon ƙamshin sigari, sai ta ji ƙamshin turaren wuta. Ba kowa a falon hakan ya bata tabbacin Aliyun ne ya kunna. Ta saba duk sadda ya gama busa hayaƙinsa za ta yi azamar daukar kaskonta ta kunna gawayi ta saka turare. Sai ta ji hakan da ya yi ya burgeta, kaso hamsin na damuwarta ya yaye. Sai a sannan ta ci dora abinci mai saukin dahuwa ta ci, ta shiga karatu.

***
Washegari da ɗokinta ta fita daga gidan. Aliyu ne ya kai ta saman mashin dinsa.
   Koda ta shiga Malami ya shigo basu sami damar gaisawa da Amrah ba sai dai wannan karon sun samu zama wuri guda. Ana tashi, kowa ya fice daga ajin suka yi zamansu.

"Mai ciki ba za ki ci komai ba? Rana fa ta yi." Fadin Amrah cikin murmushi. Harararta ta yi sannan ta ja guntun tsaki.
  "Ni har tsoron haihuwar ma nake."

"A gidan Aliyun ko kuwa me?"

Tasan Amrah da biyu ta yi tambayar, ba kuma ta so ta bada kofa yanzu Amrah ta san sirrin gidanta. Ta fi kaunar Amrah ta dawo da tausayi da kaunarta a zuciya kamar dai a baya.

"A'a, kada na mutu wurin haihuwa."

Dariya Amrah ta yi.

"Sai kuma aka fadamaki haihuwar ƙarar kwana ce? Addu'a za ki yi, In sha Allah za ki haihu lafiya. Af, ga saƙon Umma ma. Ta cemin ki dinga shan kayan marmari da abinci lafiyayye. Kar kuma ki yawaita daukar abu mai nauyi. Kuma wai ko nan gaba za ta aikomaki mene? Oho na manta. Ta ce dai na miki albishir tana nan zuwa."

Dadi, farin ciki da annashuwa suka cika zuciya da fuskar Ramlat. Daga washe haƙora tana dariya sai ga hawaye na fita. Hawayen tana da wata uwa da ba ita ta haifeta ba, amman ta tuna da ita. Tana kokarin ba ta kulawa irin ta uwa.

"Meye abin kukan?"

Fadin Amrah da ke jin zuciyarta itama na neman karyewa. Ta daure ta tattaro dauriyar wuri guda, ta shiga zolayarta.

"Oh, wa ya ga Ramsy da ɗa? Naga yanda za ki yi raino. Wai har ki shayar."

Ta ƙarashe gami da sanya dariya, itama ba ta san sadda ta dara ba ta hau share fuskarta.
 
"Kema ai kamar yau ne."

Taɓe baki Ramlat ta yi.

"Ni da aure sai na kammala karatu in Sha Allah."

Murmushi Ramlat ta yi kafin su taɓa hira, so take Amrah ta jefomata tambayar da ta shafi gidanta ko dangin mijinta, sai dai ta lura kokarin kaucewa hakan ma Amrah ke yi. Don haka itama sai ta kara rufe cikinta ba ta kaunar su sami wata matsalar.

***
   Bayan sati biyu hankalin Ramlat a kwance, za ta yi waya da Abbanta da kuma Hajiya wacce a sannan ta ɗan sassauta kadan. Umman Amrah kuwa kiranta take sosai su yi hira ta yi ta kwantar mata da hankali. Ta dauketa kamar ƴar da ta haifa a cikinta. Bangaren Aliyu, ya rage zuwa ya yi mata shaye-shaye a gida kamar yanda ya daina shigomata a buge. Hakan ya kara kwantar da hankalinta ba kaɗan ba. Abinda ke yawan bata mamaki ya daure mata kai, banda Abulle babu wani ko wata a dangin Aliyu dake zuwa gidanta, zargin ba sa kaunarta ya kara tabbata a kansu. Don haka ta ja jikinta ta kama kanta. Hakan bai hana ta kira mahaifin Aliyun ta gaidashi, shi kam lafiya sumul yake amsamata.
 
   A yammacin juma'a ta fito falon bayan ta yi wanka ta shirya cikin riga da wando Pakistan. Tashinta daga bacci kenan bayan ta dawo daga makaranta. Kicin ta shiga ta hau kiciniyar yin tuwon semo da miyar kuka kasancewar hakanan ta ji tana sha'awarsa. Sai dai me? Babu gas.

"Ya Salam." Ta furta a fili. Jiki a sanyaye ta fito falon tana jan tsaki, waya ta dauka ta lalubo lambar Aliyu ta kira.

  "Kamar ya babu gas? Har gas din gidan ya ƙare?"

Shi ne tambayar da ya jefomata bayan ya saurari bayaninta. Ta ciji leɓɓanta ta kasa cewa komai. Sai kuma ta ji ya ja tsaki kafin ya ce.

"Nidai wallahi banda kudi, kema kin sani kuma. Yanzu haka ganinan wani banza dan gin..."

Kiit, ta katse kiran, a duniya ta tsani ta ji yana ashariya. Abin na ƙona ranta.

"Allah Ka shirya." Ta firta a fili, ita kam yunwa ta ke ji don haka ta mike. Ta tuna da lemun da ta gani Aliyu ya ajiye a fridge da safiyarnan, sadda aka kawo wuta. Ta soma shiga kicin ta dauko ragowar bireda ta fiddo lemun. Tun kafin ta ƙaraso ta bude ta shiga kwankwada. Sosai ya yi mata dadi. Tana zama ta hau tauna biredin, idanunta na kan wayarta dake ƙara kuma sanin Aliyun ne ta ƙi ɗagawa. A hankali kuma ganinta ya soma zama dishi-dishi. A kokarinta na  ajiye robar lemun saman Centretable sai ya zube a ƙasa.

"Innalillahi wa inna ilaihir raajiun! Mene haka?"

Ta fadi cike da karfin hali. Ita ta san me take ji. Jirin na kwasarta, yana kokarin fitar da ita daga hayyacinta. A hankali ta kai hannu ta dauki wayar ta danna. Cikin muryar ƴan maye ta soma magana.

"Aaaaaliiii."

Ba ta ji me yake cewa ba ta wurgar da wayar, ta mike ta na tafe tana rangaji da zagaye falon, ba ta yi aune ba ta ci uban tuntuɓe da takalminta ta bugi gefen mararta da tv stand ta zube anan. Duk da ba'a hayyacinta take ba sai da ta saki ƙara.

***
A hargitse ya banko kofar falon ya shigo. Kallo ɗaya ya yiwa robar lemun ya san abinda ke faruwa. Jijjigata ya soma.

"Baby! Baby! Ramlat!"

Ya rasa na kira, cak ya ɗagata ya fita. Ba kuma zai yiwu ya sanyata a mashin ba, dole ya dawo da ita ya fita ya taro ɗan sahu suka bar gidan zuwa asibiti.

***
"Ka yi hakuri, cikinta ya riga da ya zube."

Bayanin Dr Lamin kenan bayan ya gama faɗawa Aliyu cewa a jininta da aka auna an samu tabbacin ta sha kwaya mai ƙarfi, ya kuma yi faɗan meyasa ya bar ta yin shaye-shaye duk kuwa da sanin da ya yi tana da ciki. Ga mamakin shi kansa Aliyu ya kasa cewa komai, har Likitan ya yi faɗa ya kammala. Batun zubewar cikin ya fi komai ɗagamishi hankali. Idanunsa suka kaɗa.

'Ko mene laifinka ne ai! Da ba ka ajiye a gidan ba, ta ina za ta gani ta dauka tunda

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login