Showing 189001 words to 192000 words out of 230725 words

Chapter 64 - Karfen Kafa Book 1 Hausa Novel Complete

Unknown   

06 Jan 2025

1385

hijabi ta hau sallar isha'i. Hajiya ta shigo har sau biyu tana magana. Na farko ta shigo tana wanka, na biyun kuwa yanzun tana sallah. Koda ta idar a gaggauce ta ninke dardumar ta fita. Ba ta son Hajiyar ta ƙara dawowa a karo na uku ta san rai ne zai ɓaci. Ba tare da ta cire hijabin ba ta fita.
Su biyu ne da shiga iri ɗaya, shadda ce ruwan blue, hatta da karamin aikin da aka yi musu iri guda ne. Hular kansu ma hakan ta ke, sun yi kyau har sun gaji. Su biyun ne kadai a falon, Hussein na zaune a ƙasa yayinda AlHassan ke saman kujera yana danna waya su Ummi zagaye da shi. Sallamarta ya sanya shi ɗago kai ya dubeta. Ta wani ɗaure fuska babu wani zumudi balle har ta kalleshi. Sai kawai shi din ya ci gaba da kallonta ƙasa-ƙasa yana kokari ya ga sun hada idanu. So ya ke ya karanci idanun ko zai gane manufar sauyawar fuskarta. Ta karaso gami da zama a hannun kujera ta gaishesu.

"Ranki ya dade Mrs Hussein, girman kujerarki ne ai. Idan laifi muka yi a yafemana, irin wannan shan ƙamshi, fitowar sai an ga dama?"

Kalaman AlHassan suka sa ta murmusawa, tana jin nauyinsa hakanan kawai.

"Ba haka bane, sallah na tsaya yi ne."

"To dafatan an samu a addu'a? Allah Ya amsa."

"Amin. Ina zuwa."

Daga haka ta mike ta nufi kicin, sarai ta na kallon Hussein ta gefen idanu, kallonta yake sosai, ta yi mamaki kwarai ganin ba ya daga cikin ɗabi'unsa.
Kayan abincin ta hada komai a tebur har ruwa da lemu ta ajiye kafin ta dawo falon ta yi musu iso zuwa saman teburin.

"Nikam da dai za ki sa a ƙasa ya fi min dadi. Kai fa?"

AlHassan ya fadi gami da duban Hussein. Ya gyada kai alamar hakan ma ya yi. Ta amsa da toh sannan ta koma kicin ta dauko katuwar ledar abinci wacce da wuya su yi amfani da ita idan ba azumi ne ya taho ba. Yanzun kam gashinan a kusa-kusa. Falon ta dawo ta matsar da centertable sannan ta shimfida. Bisa kuskure idanunta ya kai kansa, ta kauda kai lokaci guda tana kara hade fuska. Juyawa ta yi bayan ta ba Ummi umarnin bin bayanta. Marasa nauyin ta dinga ba ta ta kawo falon, ita kuma ta ji da masu nauyin. Komai ta jera, tuni AlHassan ya sauko, tana ji yana jan Hussein da hira amma yana amsawa tamkar ba ya so, a karshe sai shima ya kama girmansa ya watsar da shi ya maida hirar ga Ramlatu don tuni ta kora yaran ɗaki da kallo kawai. Sun san halinta, muddin aka yi baƙi zasu ci abinci to fa basu isa su zauna ba musamman ma tunda sun ci.

"Wai nikam Ramlat a ina kika koyi girki haka? Kamshin kadai ya mamaye hancina har yawuna ya tsinke tun kafin na kai baki."

Ba ta san sadda ta yi dariya har fararen haƙoranta na fitowa ba.

"Wurin Hajiyata mana. Amma dai ka bari ka ci kafin ka yanke hukunci."

Ta karashe gami da turamasa plate din da ta shaƙe da shinkafa ta kuma ɗoramasa kifin a gefe, ga zoɓo har turiri yake a kofi.

AlHassan ya jinjina.

"Gaskiya ne. Amma ko a ido ai an san mai dadi."

Ba ta ce komai ba banda murmushin, ta ja plate ta shiga zuba wa Gogannata wanda ya hau danna waya amma kacokan hankalin a kan hirarsu yake, shi kansa ƙamshin abincin dukan kofofin hancinsa yake yi, ya haɗiyi miyau ya fi a ƙirga. Ƙamshin zoɓon da ya ji citta da abarba da su flavour, yana kara kwaɗaitamasa son sha.

"Bismillah."

Ta fadi da wani salon kashe murya kamar ba ita ba. Ya ɗago kai ya dube ta. Hankalinta na ga zoɓon da take tsiyayawa a kofi ammafa kirjinta wani bugu yake don ta san idanunsa a kanta su ke kamar yanda jikinta ya ba ta.

"Na gode."

Ya fadi a ciki-ciki, ta ajiyemishi zoɓon, ta mike ta bar falon. Koda ta kai ƙofa, ta dan saci kallonsa, har sannan ita ya ke bi da ido duk kuwa da cewar ya kafa kofin zoɓon a baka. Mamaki ya sa ta saurin kauda ki ta shige daki.




Wani dadi ranta ya yi tana jin kamar ta zuba ruwa a ƙasa ta sha. Wato dai haka Hussein ke ji idan ya na mata wannan shan ƙamshin. Ta yi dariya ita ɗaya a ɗaki kafin ta kife saman gadon cikin annashuwa. Sai da aka kwashe mintuna talatin sannan Ummi ta shigo kiranta. Ta maida hijabin ta fito, sun kammala har ma Hajiya ta fito, kayan kuwa ta tabbatar Ladidi ce ta kwashe tunda ba ta kai ga tafiya ba.

Hussein ya miƙe ya fita tare da Ansar, zuwa can sai ga Ansar din ya dawo.

"Mami, ki zo inji Uncle."

Ta dan saci kallon Hajiya da AlHassan, hira suke abinsu kamar uwa da ɗa, ganin ba su damu da kallonta ba yasa ta miƙewa ta shiga daki. Sai da ta ɓata mintuna fiye da biyar ba don kuma wani abun ta ke shafawa ko gyarawa ba, can kuma ta fito ta fice.

Yana tsaye a jikin motarsa ya harde kafafu hakanan hannunsa a harɗe a kirji. Tun tahowarta ya ke kallonta. So da kaunarta na ratsa dukkan wani ɓangare na zuciy da gangar jikinsa sai dai shafe mintocin da ta yi ba ta fito ba ya yi masifar sosa ransa. Don haka koda ta tsaya sai shima ya ja baki ya yi shiru. Ramlat ta soma gajiya da tsayuwar don haka ta dubeshi babu fara'ar a zo a gani.

"Shikenan ina iya tafiya?"

Kallon da ya watsamata yasa ta kallon gefe guda.

"Idan har ba ki daukeni a bakin komai ba, kina iya tafiyar."

Shiru ya biyo baya, jin ba ta ce komai ba sai ya sauke ajiyar zuciya.

"Akwai abinda na yi maki? Ko kuwa duk baƙin cikin na rabaki da masoyinki karo na biyu ne?"

"Komai nufin Allah ne. Haka ya tsaramin a rayuwa. Na kuma karɓa da hannu bibbiyu."

"Hakane, sai dai kina nufin ba da son ranki ba?"

Yanda ya yi maganar da wani irin sanyi, yasa ta yin murmushi kadan.

"Kamar yanda kaima ba da son ranka ba, haka nima yake a wurina. Ina ganin dai mun yi anko."

"Yaushe kika fara duba? Me kike nufi da mun yi anko?"

Daga muryarsa ta gane ɓacin ransa, ta kara gyara tsayuwa gami da ɗan dubansa.

"Daga ni har kai, mun yarda da kaddara mai kyau da marar kyau saboda mu din musulmai ne. Kamar yanda na ji batun aurenmu da kai daga sama, haka Allah Ya bani ikon karɓar lamarin matsayin kaddarata kuma mai kyau. Ko ba komai na shaida kana da ɗabi'u masu kyau daidai gwargwado. Hakanan iyayena da suka haɗa ni da kai, na tabbatar ba za su cutar da ni ba har abada. Bana so na ƙara yin gangancin saɓa umarninsu."

Tana kaiwa nan ta sunkuyar da kai don ba ta kaunar kallon da yake jifanta da shi da ta kasa ganewa.

"Ba wannan na tambayeki ba. Tambayar da na maki, kenan ba...Shikenan dai. Hakan ma is good."

Ya fasa nanata tambayar, sai ya share. Can kuma ya kara magana.

"Ku mata kun fi kaunar wadanda za su tsaya su na furtamaku kalaman so a baki alhalin idan aka yi auren ba lallai su iya tafiyar da lamuranku yanda ake so ba. Ina da tabbacin har da wannan a bahagon tunaninki."

"Me ya kawo batun so? Ai bana jin akwai shi a tsakaninmu. Ba ka san cewa ko ba aure ana yin so ba?"

Ya ji zafin kalamanta don haka shima ya shirya ramuwa.

"Shiyasa ki ka kasa hakuri da auren da babu so?"

Ta dubeshi, wani murmushi ya ke ganin ya ci galaba ta fusata. Ta kasa haɗiye maganar da ke cinta, ta maida mishi martani nan take.

"Yanzu ai gashinan zan yi. Ko ba komai a rayuwa ana koyon darasi, da auren so da wanda ma babu soyayyar, duk darasi ne a gareni. Na kuma gani. Idan a baya na yi na soyayyar, yanzu na hakura zan jarraba wanda babu soyayyar na ji yanda ake ji. Ko itama tana dauwama ko aa."

Tana kaiwa nan ta soma tafiya da zummar barin wurin, ya riƙo hannunta ta dawo baya. Ta juya da sauri gami da kokarin janyewa amma ina karfin ba ɗaya ba.

"Ka cikani tunda dai ka riga ka san cewa haramun ne."

Idanunsa tuni sun kaɗa. Shi Ramlat ke nufi da ba ta so ko me?

"Idan wasa ki ke yi, bai miki kyau ba. Ina miki rantsuwa da Allah, ko yankar naman jikin Hussein za ki dinga yi kullum kina gasawa tsabar ƙiyayya, sai kin zauna da ni muddin aka ɗaura aurenmu. Idan kika ga kin fita daga gidana, to ki sa a ranki, ƙasa ce za ta zama makwancinki a ranar. Babu fitar yaji ko kuma saki. Kar ki shigo gidana da makami, zan miki tanadin kala-kala sai wanda kika zaɓa. Zan iya mutuwa, amma har abada kar ki ji a ranki za ki shigo gidana kuma na rabu da ke. Har abada Ramlat."

Ta dubeshi da idanunta da suka cicciko, ba karamin fusata ya yi da zantukanta ba. Jikinta ya yi sanyi, ya saki hannunta ya faɗa motar gami da rufewa da karfi. Ta ci gaba da tafiya kamar wacce kwai ya fashewa a ciki ta bar harabar wurin zuwa ciki.




I just published "BABI NA HAMSIN DA BAKWAI" of my story "Ƙarfen Ƙafa". https://www.wattpad.com/1018053716?utm_source=android&utm_medium=com.whatsapp&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=Rufaida-Umar&wp_originator=H1vXb7%2FW6A2U5P8fFwbtuiA8loSGt%2B%2BNft8tDKy3EJM810crtMGUnxqUIIutxZI04rTU84moV3sLlZ4ErYDW%2BHsUJ6yuYaxKr9kgvrgaa2%2BsQQrAwLvUCmdmO42m8ACV





🕯️ *ƘARFEN ƘAFA*🕯️

_*Rufaida Umar*_

Bismillahir Rahmaanir Raheem.

57)


Kiciɓus ta yi da Alhassan dake fitowa, ta yi saurin sunne kai kamar mai jin kunya. Shi kuwa a fisge da suka hada ido ya gane kamar ranta a ɓace yake.

"Har ka fito?"

Ta furta cikin dakiya, ya dan yi dariya.

"Na fito Amarsu, zan wuce. Gobe dai zan koma Adamawa sai ranar daurin aure in sha Allah."

"Allah Ya tsare hanya. A gaidamin su Aunty Kausar da Fatima."

"Zasu ji in sha Allahu."

Daga nan suka yi sallama ta shige ciki shi kuma ya nufi wurin motar yana ta tunani. Koda ya shiga, ya dubi Hussein da ya ɗago kai daga saman sitiyari.

"Lafiya? Na ganka wani iri kamar yanda itama Ramlatun na lura da damuwa a fuskarta. Meyafaru?"

"Nothing."

Ya amsa a gajarce sadda ya tayar da motar suka bar harabar gidan. AlHassan bai kara magana ba banda baki da ya taɓe. Sai da suka yi nisa ne kafin ya ji ya kamata ya ce wani abu ko da shawara ce sanin halin mutumin.

"Idan mutum yana son mace, kwantar da kai ya ke yi ya nemi soyayyarta. Mace ba ta son gadara ko taƙama, mace kulawa ta ke so da kuma a nunamata soyayya a fili kuma a gaban kowa. Ban san me ya haɗaku da Ramlatu ba, amma na kalli abin a mahangar ba ka taɓa soyayya ba, asalima matan ke binka a baya kana yanƙwana su. Idan har ka ce ta wannan hanyar za ka siye zuciyar Ramlatu, abun zai ba ka wuya daga kai har ita. Kar ka yi wasa da damarka."

Hussein tun soma maganar ɗan uwansa, bai katse shi ba, kamar yanda kunnuwansa ba su bar sauraronsa ba. Sai da ya kai karshe ne ya ɗan yamutse fuska.

"Su matan ba za su iya hakuri da kowace kulawa ta biyo bayan aure ba? Dole burinsu tun su na waje a nunamusu?"

Abin ya ba AlHassan dariya.

"Ka taɓa ganin inda aka yi cinikin biri a sama? Ko kuwa su matan kana tunanin sun san gaibu da nan take za su karanci halayyar mutane irinku? Su ba wannan a gabansu, su dai su gani a ƙas. Kuma dama ai amfanin taɗin kenan, a fahimci juna a kuma ga ko za'a iya zama a jure halayyar juna. Na tabbatarmaka idan ka ci gaba da tafiya a wannan shan ƙamshin naka da rashin maida hankali, za ka sha wuya a hannun Ramlatu bayan aurenku."

Murmushi Hussein ya yi don shi mamaki ma maganar ya ba shi.

"Wai zan sha wuya hannun Ramlat? Anya? Don Allah na yi kama da mazan da za su sha wuya hannun mace?"

Murmushin shima AlHassan ya yi gami da gyara zaman gilashinsa.

"Da sauranka ɗan uwa. Bari na kyaleka, gani ya kori ji. Nidai idan ta fara gasa maka aya a hannu, kar na ganka a ƙofar gidana."

Suka yi yar dariya a tare. Shi Hussein dariya yake don ganin hakan yake kamar wani almara ko tatsuniya. Bai ce Ramlatun ba ta da kyau ko tsarin da namiji zai rikito a kanta ba, tunda shi shaida ne, ganinsa da ita tun farko ya ji kawai ta burgeshi kafin ya tantance abinda ya ke ji taƙamaiman a kanta, sai dai ya na da ja akan cewa akwai macen da za ta iya juyashi ba tare da asiri ba kamar dai Hajiya Zeenatu a baya. Amma zai jira ya ga irin juyawar ta Ramlatu. Kulawar ba zai nuna ba kamar yanda dan uwansa ya buƙata har sai bayan aurensu.

***
  Tana tuƙi a hanyarta na zuwa Ofis bayan ta sauke yara a makaranta, tana tunanin zantukan Hajiyarta.

_*"Magidannaki fa ya bukaci ki bar aiki hakanan tunda can Adamawa za ki zauna. Ko ba don haka ba dama na fadamaki duk radda kika tashi aure idan mijin da za ki aura bai amince ba, to za ki bar aiki."*_

Sauke ajiyar zuciya ta yi. Kenan dai rabuwarta da yaranta ya zo, wani kewarsu ta ji ya kamata. Dama tasan aiki ko ba dade ko ba jima za ta bar shi kamar yanda suka yi da Hajiya a farko. Hon da aka cikamata kunne da shi yasa ta kara nutsuwa a tuƙinta, ganin ma ba wani tare hanya ta yi ba sai abin ya yi mata zafi, ta cikin gilashi ta ke duban motar, sam ba ta ganeta ba. Don haka ta yi gefe ta ba mai motar hanya. Ido suka hada ya yi mata murmushi ita kuwa dubansa ta shiga yi baki a sake sai kuma ta dara.

"Hilal?" Ta furta a bayyane, a hankali ta ga ya ja gefe ya yi parking, itama dolenta ta tsaya don su gaisa. Ba ta kai ga fitowa ba ya rigata isa wajenta.

"Ranki ya daɗe."

"Yaya Hilal?  Saukar yaushe a garin?"

Ya yi ƴar dariya.

"Ko kwanaki uku ban yi ba da zuwa, shima daurin auren abokina ne ya kawoni, amma nan da jibi zan koma in sha Allah."

Ta yi murmushi.

"Allah Ya nunamana. Ya Fa'iza da Ɗiyarmu?"

"Suna nan kalau. Ai nake gidan Sis Bilki jiya, na ji kuma abin alheri. Allah Ya sanya albarka. Yasa zamu gani."

Ba ta yi mamakin yanda aka yi Bilkisun ta sani ba, tana da tabbacin daga bakin Mijinta ne. Amma faɗawa Hilal sai ta gani kamar da biyu ne. Cike da jin nauyinsa ta amsa.

"Amin. Ina godiya. Wato dai da ace ba mu haɗu ba anan sai dai mu ji labarin ka tafi ko?"

Dariya ya yi.

"Ni na isa na shigo garin nan ban je na ga Hajiyarmu ba? Aa sam. Wallahi yau nake cewa zan shiga zuwa yamma haka."

Ta jinjina kai.

"Allah Ya nunamana."

"Amin amin. Bari na bar ki kada na sa ki makara. Sai na shigo din."

Ta amsa da toh gami da yi mishi fatan alheri, ya rufemata murfin motar sannan ya wuce zuwa tashi motar. Ta ja numfashi ta furzar, Hilal kenan, mutumin da ya kaunaceta don Allah. Gaba daya ya sauya ya ajiye kumatu. Ga duk wanda ya gan shi zai fahimci yana cikin jin dadi da kwanciyar hankali. Wayarta ce ta yi ringing daidai sadda ta ke kokarin hawa titi. Ba tare da ta duba ba ta daga gami da karawa a kunnen da sallama.

"Ke da waye tsaye a titi?"

Tambayar da aka watsomata ba tare da an amsa sallama ba yasa ta gane ko waye. A hankali ta ɗaga kai ta dubi mirror, motarsa na nesa kaɗan da nata. Ta fi kyautata zaton daga wurin motsa jiki ya ke. Murmushi ta yi daidai sadda ta hau titi ta harba motarta.

"Ba ka da hurumin sanin da wanda nake magana. Kar ka manta ban kai ga zama matarka ba."

"Hakane, ba ki kai ga zama ba. Amma kin manta cewa haramun ne nema cikin nema? Ke musulma ce."

Dariya ya ba ta jin yanda ya zaƙalƙale.  Yanda ta ke tafiya a sannu, haka yake biye da ita da motarsa a sannun. Ta kauda kai kamar ba ta san da shi din ba.

"Babu wanda ba ya kuskure."

"Haka kika ce? To naga kin ƙara tsayuwa da wani ɗan iskan! Duk abinda na yi mishi, ke kika ja. Sannan lokacin da za ki ajiye yawon gantalin aikinnan ya yi! Ba zan lamunta ba."

"Wannan kuma ba ka da hurumi a ciki, ajiye aiki sai lokacin da naga dama. Ka bar tada jijiyoyin wuya tunda har yanzu aure bai tabbata ba tsakaninmu. Akwai sauran lokaci."

Tana kaiwa nan ta katse wayar ta taka motarta, sai dai ba ta je ko'ina ba ya zo ya gifta ta har yana kokarin buge wani ɗan sahu. Bai ko tsaya ba ya yi gaba. Ta bi shi da kallo tana dariyar farin ciki, ko ba komai ta san ta ba shi aiki. Wannan nishadin yasa ta ware waƙar Breaker na Jarumar Mata tana saurara har ta karasa wurin aiki.

Hussein bai kara kiranta ba kwata-kwata a wannan ranar.

***
Bisa umarnin Yayanta Munir, ta rubuta takardar barin aiki. A wannan satin Rafee'ah ke zuwa ta kai ta gidan mai gyaran jiki. Ya kasance Ramlat ba ta da lokacin kanta balle na yara, ɗawainiyarsu ta koma hannun Hajiya da direba mai safa da marwar kai su makaranta da daukowa. Waya ba ta kara shiga tsakaninta da Hussein ba sai dai kokari kawai ta ke yi itama don tana kewarsa. Ya aiko da wani leshi mai tsadar gaske da kuma atamfofi har kala uku suma masu tsada sai mayafai da jaka da takalma, sai kuwa tsarka kala biyu da abin hannu duk na fitar biki. Ba ɓata lokaci aka kai wurin dinki tare da wanda Munir ya siyamata.


  "Wai ke angonnaki yana zuwa hira kuwa? "

Ta dakatar da shafa man da take yi a jiki ta dubi Amrah wacce ke zaune saman gado tana shayarwa. Taɓe baki ta yi.

"Mutumin da ko waya ba ya kirana."

Da mamaki Amrah

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login