Showing 144001 words to 147000 words out of 230725 words
hannunta da ya sha lalle idanu, mutuwa mai tonon silili. Hakan ta ayyana yayinda hawaye nta suka soma ɗiga.
***
Tafe yake cikin shiga ta alfarma, a gefensa Hajiya Zeenatu ce tana zabga uban murmushi. Hannuwansu sarƙe cikin juna.
"Husseini!" Ya ji wata murya ta kwalamasa kira, kusan lokaci guda suka juya shi da Hajiya Zeenat. A fuskar Hajiya Zeenatu, tashin hankali ne tsagwaronsa, idan ka ɗauke Hussein wanda idanunsa suka kaɗa suka yi jazur. Damƙe hannunsa da Hajiya Zeenatu ta ƙara ya sanyashi dubanta a hargitse.
"Husseini kai ne?!" Ya juya ga matar da ke tsaye tana dubansa dakyau.
I think you'd like this story: "Ƙarfen Ƙafa" by Rufaida-Umar on Wattpad https://my.w.tt/i7Akdw4Ovcb
🕯️ *ƘARFEN ƘAFA*🕯️
_*Rufaida Umar*_
Bismillahir Rahmaanir Raheem.
43)
_*Tafe yake cikin shiga ta alfarma, a gefensa Hajiya Zeenatu ce tana zabga uban murmushi. Hannuwansu sarƙe cikin juna.*_
_*"Husseini!" Ya ji wata murya ta kwalamasa kira, kusan lokaci guda suka juya shi da Hajiya Zeenat. A fuskar Hajiya Zeenatu, tashin hankali ne tsagwaronsa, idan ka ɗauke Hussein wanda idanunsa suka kaɗa suka yi jazur. Damƙe hannunsa da Hajiya Zeenatu ta ƙara ya sanyashi dubanta a hargitse.*_
_*"Husseini kai ne?!" Ya juya ga matar da ke tsaye tana dubansa dakyau.*_
_*"Kar ka je gareta! Zo mu tafi!"*_
_*Hajiya Zeenatu ta furta iyakar karfinta. Matar na jin haka ta taho gadan-gadan da zummar nufar Hussein kai tsaye tana fadin.*_
_*"Ni ce Husseini! Dadarka ce! Ka manta ni?"*_
_*Ba ta kai ga ƙarasawa ba ta ci uban tuntuɓe za ta faɗi. Sai dai caraf aka riƙeta. Hussein ya dubi mai shi, mace ce cikin fararen kaya. Daidai sadda Hajiya Zeenatu ta soma jan hannunsa, hawaye yake fitarwa yana dubansu da wacce bai san ko wacece ba. Caraf aka riƙe hannunsa, dole suka tsaya cak. Fuskar Ramlat ya gani na wani haske da kyalli, murmushi ta ke yi madadin kukan da Dada da kuma shi suke yi, ta ɗago hannunsa ta sanya a cikin na Dada ta matse su.*_
_*"Har abada babu wani ko wata da zai ƙara shiga tsakaninku."*_
_*"Ƙarya kike!" Hajiya Zeenatu ta furta tana ihu.*_
***
"Innalillahi wa inna ilaihir raaji'un!"
Ya furta a fili yana maida numfashi kamar wanda ya yi tsere, jikinsa gumi yake fitarwa duk kuwa da sanyin da ke a ɗakin. Kirjinsa bugu yake da sauri-sauri. Ya kai duba ga makwancin Hajiya Zeenatu. Bacci take ta lulluɓe har kai da bargo. A hankali ya dauki wayarsa a gefen gado ya kalli agogo, biyar saura mintuna, tabbacin Asuba ce. Don haka ya mike yana juyayin mafarkinsa.
'Dada?' Ya maimaita a zuciyarsa yana juya sunan, yana da wata mai suna Dada? Kuma a ina? Tunani ya yi mishi yawa har ya ɗaura alwala ya fito, kansa wani irin sarawa ya ke. Me mafarkinsa ke nufi? Ramlat ya gani, ihun kuma da Zeenatu ta yi na menene?
Babu mai amsa masa, wannan tasa ya fice daga dakin zuwa falo gami da shimfida darduma ya yi nafila. Bayan idarwa ya yi addu'a. Masallaci zai fita, don haka sai ya koma dakin ya tashi Hajiya Zeenat sannan ya fita. Ta bishi da kallo har ya fice sannan ta ja tsaki tana miƙa, ta lura da wani ustazanci da ya soma. Sallah a masallaci ya daina wuce shi, ita dai tana jin tsoron ibadar da ya soma maida hankali a kai. Ko ba komai ai ta sani wutsiyar raƙumi ta yi nesa da ƙasa. Ƙarfin ikon Allah da addu'a ya shallake dukkan ƙarfin mai ƙarfi.
Jiki a sanyaye ta miƙe tana tunanin mafita.
'Ku bar ƙasar zuwa wata ƙasar kawai!'
Wani ɓangare na zuciyarta ya shawarceta. Sai dai tana tunanin ta yanda za ta sa Hussein ya amince da wannan shawarar da tun ba yau ba ta ke ƙoƙari a kai.
***
Misalin shida na safe, iyalan gidan Alhaji Khalid Mu'azzam sun fito fess sun sha wanka har da yaransu idan ka dauke Ramlat da nata yaran ke gidan Muhibbat. Dalilin yaran ne Ramlat ta yi ƴan soye-soye na snacks da zasu ci a hanya.
Ta sha adon doguwar rigar atamfa kalar ruwan toka da sirkin ja da yellow an mata dinkin Bubu. Ta ɗora ƙaramin mayafi kalar ja a samansa. Murmushi ta ke sai dai iyakarsa leɓɓanta bai kai ga shiga zuciyar ba. Tunani goma da ashirin take duk ita daya, rayuwar yaranta, auren Chairman, soyayyar Hussein da ta ke ji kamar Son Maso Wani ta ke yi kawai. Wannan ne yasa da safe ta tashi idanun ƙozai-ƙozai shaidar bacci bai wadaceta ba.
Bayan sun ɗuru a motar da Munir yasa aka hayo musu ta kasuwa, tana daga can baya tare da yara sai Hunainah a ɗayan gefen. Ta bude whatsapp, ta gwada yiwa Hussein sallama sannan ta sanarmasa da tafiyar da za ta yi zuwa Daura. Daga nan ta sauka online ta kira Amrah suka ƙara sallama. Ba ta son yi mishi text gudun kada ya faɗa hannun Hajiya Zeenat.
'Koda shi ne abu na ƙarshe da zan maka, in sha Allah zan yi Hussein. Zan sulhuntaka da ƴan uwanka.'
Abu na farko da ya faɗo ranta bayan wannan tunani, shi ne Kawunsa da aka ce yana zama a Kano. Da dabara za ta nemi cikakken sunansa a wurin Hafsat, sauƙinta ma unguwarsu ɗaya da kakanninta (Hajja).
Ta toshe kunnuwanta da earpiece tana sauraron Suratul Maryam tana bi a hankali idanunta a lumshe. Wakokin soyayya ba ta da muradinsu a lokacin kasancewar ba karamin ingiza zuciyarta suke yi ba akan Hussein.
Tafiya ta yi nisa, shiru na ƴan sakanni, karatun ya tsaya, ta duba. Kira ne daga Hussein. Kirjinta ya bada dam! Ta ɗaga ta yi sallama a hankali tana mai satar kallon su Hajiya, hirarsu suke yi na dangi yayinda Hunainah ta rufe kanta da mayafi alamun bacci ya ɗauketa ko zai ɗauka, ba ta da tabbaci.
"Tafiya ba sallama? Ba ki faɗamin ba sai yau?"
Daga yanda ya yi furucin za ka fahimci ɓacin ransa.
Daƙyar ta iya motsa leɓɓan.
"Ka yi hakuri."
Shiru ya biyo bayan can kuma ya sauke ajiyar zuciya.
"Naso yau na ganki."
Ta yi luum da idanu, ta kasa yarda da abinda kunnuwanta suka jiyemata.
"Uhm?" Ta nemi ba'asi.
"Hoton zan karɓa ta ƙarfi tunda an hana ni."
Ya faɗi a shagwaɓance, ya sanyata murmushi tana mai sunkuyar da kai kamar yana gabanta.
"Zan turomaka."
"Promise?"
"Yes."
"Kinsan hoto ɗaya rowa ce ko?"
Ta ƙara faɗaɗa murmushinta.
"Uku fa?"
Tana jin sautin murmushinsa. Can ya amsa.
"Thanks. Allah Ya kaiku lafiya."
Bai jira amsarta ba ya katse kiran, karatun ya ci gaba. Kaso saba'in na damuwarta ya ragu, ta ji wani kwarin gwuiwa. Nan da nan ta shiga Gallery dinta ta hau kallon hotuna. Duk wanda ta ga shi ya dace ta aika sai ta ga kamar bai kai ba. Ruwan ido, abinda ta tsana ta ke jin haushi a wurin Amrah, ita ce yau ta ke yinsa. Dakyar ta haƙura ta zaɓi wasu guda uku ta aika kasancewar da network a wurin da suke nan da nan ya je, ba ta jira godiyar ba ta sanya wayar a Airplanemode tana murmushi.
Koda suka isa yan uwan sun sha mamakin sauyawarta. Ƙofar Baaru kusa da gidan Sarkin Daura, nan ne ainahin gidan iyaye da kakannin su Abba da Hajiya yake. Gida ne babba na gandu, zaman iyaye da ƴaƴa. Sun tarar da su Nusaiba mutan Kano duk an hallara. Hajja da abokiyar zamanta ma suna nan. Gida ya cika da ƴan uwa gwanin dadi. Sashen Ƙanin Malam Abdullahi kakanta nan ta yada zango wurin su Nusaiba sa'anninta, don ba ta kaunar zama da su Rafee'ah, zancen dai daya ne, na Chairman. Ta fiddo miji ta gujewa aurensa.
Karshe ta watsar da duk wani tunani ta rage sutura ta shiga wanka. Bayan ta fito ta tarar su Nusaiba gaba daya na zaune ana kari da doya da kwai da shayi wanda ya ji citta da kanumfari.
"Ke kuwa Ramlatu yaushe za mu sha naki bikin?"
Ta yi kamar ba ta ji maganar Gwaggo Hansai ba, ta ci gaba da goge ruwan jikinta. Ba ta ce uffan ba. Duka Dije kanwar Gwaggo Hansai din ta kai mata bakinta cunkushe da burodi.
"Ja'ira, ai tana jinki. Ta fi kaunar muje ana daurin aure ta dawomana. Maimaita tarihi ko? Toh dagaske banni ƙara zuwa bikinta."
Aka yi dariya don an san zolaya ce ta Dije, ita dai Ramlat ta kara tamkewa ta mike ta kwashi kayanta, ta fasa shirin a falo, ta koma uwar ɗaka.
***
Kamar wanda aka daskarar da jinin jikinsa haka ya yi ɗif, a hankali ya sauke ƙarfen da ke hannunsa yana maida numfashi, gumi kam kamar ruwa haka yake ɗiga daga cikin gashinsa, saman fuska har zuwa jikinsa. Kallon Hisham ya ke yi da wani irin faɗuwar gaba. Hisham ya toshe kunnuwansa da earpiece yana gyada kai alamun waƙar da yake ji na tsumashi sai dai kacokam hankalin yana ga Hussein. Yana sane ya fesamasa batun auren Chairman da Ramlat duk kuwa da cewar yasan maganar rawa take yi ba ta tabbata ba. Amma ɗan hakin da ka raina ai shi ke tsonemaka ido. Gwara tun wuri ya yiwa abin tufka, ko ba komai zai ƙara karantar inda Amininnasa ya dosa.
Tasowar ta Hussein, da kuma fisge Earpiece din daga kunnensa duka-duka abin ya zamewa Hisham kamar kiftawar idanu. Ya haɗiye dariyarsa ya kara daure fuska.
"Lafiya Malam? Me ya yi zafi? Daga cewa Chairman Aliyu Dikko zai au.."
"Kar ka ƙarasa." Ya fadi a kausashe yana nunashi da yatsa idanun sun kaɗa cike da wani irin matsanancin kishin da bai san mafarinsa ba. Hisham ya cika da mamaki don bai zaci abin zai kai haka ba. A hankali Hussein ya zauna a gefensa ya yi shiru, can kuma ya dubeshi a sanyaye.
"Wasa ka ke yi, sai dai irin wannan ba maganar wasa ba ce. Please kar ka ƙara."
Hisham ya karkace yana dubansa.
"Don me? Toh kai mene naka ciki? Me zai dameka? Menene haɗin biri da gada?"
Ran Hussein ya yi tsananin ɓaci.
"Ni ka ke kira biri? Hisham har wuyanka ya kai tsaikon da za ka haɗani da biri?"
Dariyar Hisham ta kasa ɓoyuwa, lallai ya ƙara yarda Hussein bai iya Hausar ba. Dariyar ta kara fusata Hussein wanda dagaske ya ji zafin birin da Hisham ya ambata. Abin ya haɗemishi biyu don haka ya mike ya dauki jakarsa don suturta jiki. Hisham ya bishi da kallo yana mai ba shi tausayi. A yanzu ba shi da abar kauna sai Ramlat, sai dai ya rasa dalilin abokinnasa na ƙin ba wa zuciyarsa abincinta. Ko a ɗazun, kasancewar Hussein ya rigashi zuwa wurin motsa jikin, kama shi ya yi dumu-dumu da hoton Ramlat din yana kallo yana murmushi. Ganinsa ya wartsake ya sanya wa wayar muƙulli.
Yana nan zaune ya fito, madadin gajeran wando, ya sanya dogo mai santsi fari ƙal mai haɗe da riga. Ya sanya baƙin gilashi yanda idanun suka ɓuya.
"Sai Allah Ya kaimu."
Ya furta can ƙasan maƙogwaro yana duban Hisham din a fisge. Hisham ya rike hannunsa.
"Haba abokina, ka yi hakuri idan ɓacin ran da na jefaka ya kai girman haka. Karin magana na yi maka, haka Bahaushe ke karin maganarsa. Ba wai da gayya na haɗaka da dabba mafi muni ba."
Hussein ya sa hannu ya dan ja karan hancinsa kaɗan yana duban gefe.
"Wani abu na ƙara faɗi?"
Hisham ya dubeshi dakyau.
"Ba ka faɗa ba, amma ba haka muka saba sallama ba. Mafi yawan lokuta tare muke fita. Yau kuma ba alamar za ka jirani."
Guntun tsaki Hussein ya ja.
"Sauri nake."
Ya furta kai tsaye har da duban agogonsa kalar silver.
"Karin maganar ce ko damuwar Ramlatu ce?"
Ya ji tambayar Hisham kamar daga sama, shiru ma mintuna kafin ya dubi Hisham ta cikin gilashin.
"Abinda ka fadi gaskiya ne?"
Yanda ya yi maganar a sanyaye, sai hakan ya sanyaya jikin Hisham. Shirun da ya yi, Hussein ya samu amsarsa.
"Sai da safe."
Daga fadin haka ya yi gaba. Murmushi Hisham ya dan yi. Shakka babu da Ramlatu za ta samu Hussein ba karamin farin ciki zai mata ba. Yana matukar son ganinsu tare sai dai kuma sanin tarihin Ramlatun kan sanyaya masa jiki. Anya Hussein zai gan ta da gashi?
***
_*Nan kusa za'a yi bikin Ramlat da Chairman Aliyu Dikko don na ji labarin zai kai kuɗi.*_
Wannan kalaman ke yawo a kwanyarsa har ya hanashi maida hankali ga tuƙin da ya ke yi. Dole ya gangara gefen titi ya kashe wayar ya kwantar da kai bayan kujera. Runtse idanu ya yi na ƴan mintoci kafin daga bisani ya ƙara fiddo waya ya buɗe hotunan Ramlat yana ƙaremusu kallo. Saura ƙiris ta zama mallakin Chairman yana nufin abubuwa da dama. Shugabanta wurin aiki, wanda ya fi shi kudi da muƙami, wannan na nuna kwaɗayi ƙarara. Hira da ita da ma kallon hotunan har da ganinta a zahiri zai zama haram a gareshi, wannan ma wata damuwar ce mai zaman kanta.
Ransa idan ya yi dubu to ya ɓaci, kirjinsa zafi yake. Mafarkinsa na ƙara yawo a kwanyarsa, gaba daya ya hargitse lokaci guda. Ya tuna abu daya kwakkwara da ya danganci rayuwarsa ya kasa. Neman haske cikin duhu yake amma abin ya gagara. Koda ya tsananta tunani, kansa ya ci gaba da sarawa da ƙarfi, cikin dauriya ya kai hannu ya kunna CD na karatun Al-kur'ani da ke kan rediyon. A hankali ya soma samun nutsuwar zuci da na gangar jiki, ɗif, sai ya nemi yanayin ya rasa. Wannan kadai ya tabbatar da zargin da ya sha yiwa kansa a baya, wato ba shi da lafiya, kuma ya zamar mishi dole ya ga likita.
Ya kwashe mintuna biyar a wajen yana kallon motocin da ke safa da marwa kafin daga bisani ya ci gaba da tuƙinsa.
***
BAYAN KWANAKI UKU..
ADAMAWA
Tun fitowarta daga ɗakin ta ke ƙunƙuni tana zuba abincin zuciyarta na tuƙuƙi ga wani ƙololon abu dabya tokaremata ƙahon zuciya. Tahir kallonta yake kamar ya haɗiye, nan duniya ba ya jin akwai wacce zai so sama da Hafsat. Aure ne yana ji a jikinsa tamkar an yi an gama.
"Kin yi kyau."
Ya faɗi kamar mai raɗa bayan ya ƙaremata kallo cikin riga da siket din jikinta na Atamfa. Harara ta watsamasa, ba don ta so ba ta dawo gidan don a farko tattarawa ta yi ta koma gidam AlHassan da zama. Ya yi murmushi madadin hararar ta ƙona ransa, wannan ya ƙara ba Hafsat haushi, ta ja tsaki. Ita kuwa Dada ta ci gaba da hirarta da Tahir ranta na mata wani irin dadi. Kusan yanzun ta saba da shi sosai don kamar ba yaron da a baya ya ke wucesu kerere babu ko gaisuwa ba. Ta kuma ƙara fahimtar ɗabi'un yaron, jikinta na ba ta cewar duk wani mugayen halayensa akan waɗanda ba ya so ya ƙare. Kuma zuga ce kawai.
"Dada anya ba nan zan dawo da zama na dindindin ba?"
Ya fadi yana mai kallon Hafsat, ta dubeshi da sauri, ya kashemata ido ɗaya, ta mike sadda Dada ke ba shi goyon bayan maganarsa fuskarta a sake.
Ya yi daidai da sallamar AlHassan. Suka amsa, Tahir ya gaisheshi, ya amsa a ɗan sake don yaron ya soma ɗan sakin jiki da shi, ya fahimci koda yana da matsalar, a yanzun ta kau.
"Ke kuma zo dama ina nemanki."
Muryar AlHassan ya katse Hafsat daga tafiyar da ta soma. Ta ji kamar ta sa ihu, Tahir kam ransa ya ƙara fari ƙal sadda ya soma kai lomar abincin da ta girka da hannunta. Ta dawo ta zauna ta gaidashi kamar ta yi kuka. AlHassan ya murmusa don yasan kanun zancen.
"Jiya ina kika je? Na zo ance kin fita."
Ta ɗan tura baki.
"Gidan su Iklima na je."
Ya ɗan ɗaure fuska.
"Kuma ai na hanaki zumuncin da yarinyar ko kin manta?"
"Ka yi hakuri."
Ta faɗi a ƙagauce don Allah-Allah ta ke yi ta shiga ciki don tserewa kallon da Tahir ke mata.
"Shikenan, je ki."
Ya ba ta umarni lura da ya yi har sannan babu wata shaƙuwa tsakaninta da yaron. Shima ya fi kaunar hakan ko don gudun abinda zai je ya zo. Wayarsa ta yi ƙara, ya duba, Rasheed ne daga Saudia.
Ya ɗaga suka gaisa a mutunce.
"Ina ta so na kiraka sai dai Allah bai ban iko ba sai yanzu. Ya su Dada?"
Alhassan ya murmusa.
"Alhamdulillah, gamunan duka lafiya. Nima rashin lambarka ne ya sa na hakura. Fatan ka iske mutan gidan lafiya?"
"Duka kowa lafiya. Akan Hussein ne nayi kiranka. Na tuna wani abu."
Jin haka AlHassan ya miƙe da sauri har Dada da Tahir na binsa da kallo.
"Lafiya?" Dada ta tambaya. Ya ɗan dubesu.
"Babu komai Dada, bari na amsa waya ina zuwa."
Daga nan ya fita waje da sauri-saurinsa. Hannunsa har rawa ya ke yi.
"Ina jinka Rasheed, me ka tuna?"
Rasheed ya ba shi labarin kaf abinda ya faru a ranar da suka yi bikin kammala makarantarsu a DUBAI shi da Hussein. Bai ɓoyemishi wani labari da Hussein ya ba shi ba a ranar har suke dariya.
Safa da marwa AlHassan ya fara gami da dafe goshi.
"Innalillahi wa inna ilaihir raajiun!Meyasa ban tuna da hakan ba? Meyasa muka kasa tunawa da cewar itama za ta aikata?!"
Rasheed ya amsa.
"Nima ban tuna da lamarinta ba sai yanzun da Mamina ta ankarar da ni!"
Cikim gigicewa AlHassan ya ƙara jefamasa tambaya.
"Maminka? Ta santa?"
"Eh ta san ta, farin sani ma! Zan tambayi dukkan wani bayani game da ita zuwa safiyarku zan kiraka, ina ji a jikina ɓatan Hussein nada alaƙa da ita. Mu binciki inda take don mu tabbatar."
Gumi sosai AlHassan ke yi, kirjinsa na bugu da ƙarfi. Ya dafe goshi karo na biyu.
"Please kar ka ɓata lokaci Rasheed."
Ya fadi kamar zai yi kuka.
"Na damu da Hussein, na daukeshi dan uwa ba aboki ba. In sha Allahu komai zai zo karshe. "
Jinjina kai AlHassan ya yi cikin son gasƙata hakan. Daga bisani suka yi sallama.
"Meyasa ban tuna da ita ba?!" Ya fadi a fili zuciyarsa na wani zafi. Kamar faifan bidiyo haka komai ya shiga dawomasa filla-filla. Ya runtse idanu yana addu'ar neman dacewa.
***
DAURA..
Idan Ramlat ta ce bikin ya yi mata dadi toh fa ƙarya ce kawai saboda kusan faɗa iyayen aka yi game da aurenta da Chairman wanda ba su da labarin zuwansa har Daura gaida tsoffin sai a sannan. Hankalinta da na yayyun ya tashi.
"Wato dai Chairman makircinnasa ya kai inda