Showing 153001 words to 156000 words out of 230725 words

Chapter 52 - Karfen Kafa Book 1 Hausa Novel Complete

Unknown   

06 Jan 2025

1063

akan lamarin aurenta da Chairman.

"Kunne ke ji, kuma na saurareka. Ka yi kokari."

Harara Hisham ya watsamasa yana danne tausayinsa.

"Shi ne za ka share ni? Nima fa takanas na taso don wanke laifin Ramlat amma ina da abin yi ai. Aikina na baro na zo."

Wannan ne karon farko da ya yi murmushi daga jiya zuwa yanzun, Hisham yana da raha. Ko ya ya ka zauna da shi sai ya sanyaya ranka.

"I'm travelling to London."

"For what?!"

Yanda Hisham ya nemi sani a hargitse, hakan ya ba Hussein mamaki har ya kalleshi, ganin ya zaro ido sai ya buɗe tafukan hannu gami da ɗaga gira cikin dakiya.

"Me akai na razanar? Tafiya ce kawai ta 3months."

"Gwara da Allah Yasa na zo." Hisham ya faɗi a fili kuma a hankali. Da ace ba su haɗu ba ba zai sani ba kenan. Lallai dole su yi komai cikin gaggawa.

"Me ka ce?"

Hussein ya tambaya. Girgiza kai ya yi.

"Ba komai. Yaushe za ku wuce?"

Damuwa ƙarara a fuskar Hussein sai dai ba ƙaramin ƙoƙorin dannewa ya ke ba.

"Ba na jin za mu wuce satinnan. Ya dai danganta da samun Visa."

Ya faɗi a sanyaye.

'Innalillahi wa inna ilaihir raajiu'un!'

Hisham ya ambata a zuciya gami da mikewa.

"Ok ok, Allah Ya nunamana. Bari na wuce sai mun haɗu anjima."

Hussein ya bishi da kallo har ya fita. Abinda ya kawo a rai shi ne damuwa ce tsantsa na ganin za su yi nesa da juna. Ya dafe kai da hannu. Shi kansa damuwar ce ke cinsa, tunanin tafiya ya bar Ramlat da Chairman kan ci masa tuwo a kwarya. Sai dai ya tabbatar furta wata kalma a kanta zai zama kamar barazana ga rayuwarta. Hajiya Zeenat ta sha faɗamasa gami da cin alwashin kashe duk wata mace da za ta shiga rayuwarsa. Ba a bayan idanunsa ba, a gabansa ta ke faɗi ya na kuma ji a jikinsa fiye da hakan ma za ta aikata. A hankali ya ɗauki waya ya kunna Data wacce rabonsa da whatsapp tun ranar da Hajiya ta kwace wayar. Saƙonni suka shigo har da nata. Ya shiga ya karanta. Gaisuwar safe ce ta mishi gami da tambayar ko lafiya. Ya dinga binyana karanta hirarsu da bai fi a ƙirga ba. Murmushi sosai ya ke yi san nan ya bude hotonta yana kallo. Ya kai kusan minti biyar ba'a hayyaci ba, tashin hankalinsa ya ƙaru. A hankali ya rufe hoton ya aikamata saƙo.

-*"Ki sa ranki Hussein ɗan uwanki ne. Ya na buƙatar addu'arki a duk inda zai je. Akwai wani duhu da na kasa fita, ke na gani kin fitar da ni kin sadar da ni da haske. Ina fatan mafarkina wataran ya tabbata. Ban ce ina sonki ba, ban kuma ce ina tsananin kishinki ba, amma ina roƙonƙi akan kar ki yi garajen aure. Nemi zaɓin Allah. Ke ba yarinya ba ce. Ina miki fatan alheri koyaushe."*_

Ya aikamata ya kashe datar, dakyar ya ci gaba da abinda ya ke ransa a jagule.

***
Kawu Modibbo tsaye a tsakar falonsa. Safa da marwa ya ke yi yana ƙarawa. Babu wani cikin iyalinsa da ya yi ƙoƙarin dosar inda ya ke, Amarya kanta haƙura ta yi da kwanan ta koma sashinta ta kwana.

*_"Kamar wuta da ruwa, haka ta ke barazana ga ayyukanka. Na sha faɗanaka, ba kai ɗaya ke aikin ba, akwai masu yi. Naka kan rinjayesu ne wani lokacin, kamar yanda nasu kan rinjayi naka aikin. Ina tsoron shaida maka muddin ba'a kawar da yarinyarnnan ba, aikin shekara da shekaru zai lalace. Za'a rasa dukkan wata nasara a kansa. Abubuwan da ka ke gudun afkuwarsu a rayuwarka, za su afku!"_*

Waɗannan jawabi na Tsoho, shi ke yawo a kwanyar Kawu Modibbo suka kuma hanashi sukuni daidai da sakan. Daren jiya kasa runtsawa ya yi balle har ya samu damar baccin. Idan komai ya lalace, hakan na nufin bayyanuwar komai.

"Lokaci ya yi da za mu haɗa ƙarfi da ƙarfe da ke ZEENATU."

Ya furta a fili kafin ya samu wuri ya zauna kamar kayan wanki.

***

ƘARFE BIYU...
Ta karanta saƙon Hussein sau ba adadi, sai dai ba ta fahimci komai ba. Cewar ba ya sonta ba kuma ya kishinta wannan ya haifar mata da matsananciyar damuwa. Kukan da ta yi ya jazamata tsananin ciwon kai. Hajiya na ganin haka ta tsorata, abinda ya faɗo a ranta kada ace wani mummunan abin ya sami Ramlatu sanadin wannan yaro, bayan ta taimaka mata ta sha magani ta shiga tofe ta da addu'a. Ummi kam su na Islamiyya ba su da labarin wainar da ake toyawa.

Wuraren ƙarfe huɗu da mintuna ne. Wayarta ta yi ƙara, dakyar ta iya ɗagawa. AlHassan ne.

"Na shigo Kano, ina hanyar gidanku."

Ta amsa da toh, a daddafe ta miƙe, babu laifi kan ya daina sarawa. Ta shiga ta yi brush ta kama ruwa ta yi alwalar jiran la'asar. Fitowa falon ta yi bakinta duk jikinta ya yi mata nauyi. Hajiya na zaune tana amsa waya.

"Ita Ramlatun?!"

Hakan da Hajiyar ta faɗi ya ɗau hankalinta, ba ta katse ta ba har ta kammala wayar.

"Ke da kanki ki ka ba shi Dikko damar turo kuɗi? Yaya Bello ya shaidamin ai sun ma gama magana ya turomaki kudin aurenki ta akawun dinki da ki ka aikamasa."

Dafe kanta ta yi tana salati, kirjinta na bugu da sauri-sauri.

"Ni kuma Hajiya? Wallahi ban.."

Ɗif ta yi, sai lokacin ta tuno da kuɗin da ya turomata account. Ranta idan ya yi dubi ya ɓaci. Ta faɗawa Hajiya gami da nunamata sannan ta ƙara da faɗin.

"Amma wallahi ban san inda ya samu lambar account ɗina ba. Ban sani ba. Me ake nufi da ni wai?"

Ta karashe hawaye na son zubomata. A fusace Hajiya ta mike tana faɗa.

"Bari na je gidan! Ba su suka haifarmin ke ba don haka ba zan zauna rayuwarki ta ƙare haka ba Ramlatu! Idan shi Munirun ya kasa ni zan je na same su."

Daga haka Hajiya ta faɗa ɗaki ta bar Ramlatu da ruɗewa da kuma hawaye. Waya ta ɗauka ta kura Zulaihat ta sanarmata komai, itama hankali a tashe ta ce za ta je can gidan su Dada kar abin ya ɓaci. Hajiya ta fito ta kama hanya ta fita.

Mintuna talatin bayan fitar ta sai ga kiran AlHassan yana shaidamata zuwansa ƙofar gidan. Ta mike ta shiga ciki ta gyara fuskarta da ta kumbura. Dole haka ta haƙuranta fita hakan. Tuni an gyaramasa ɗakin Muniru na baya, ta yi mishi iso ya shiga yana bin ta da kallo.

"Lafiya dai ko?"

Ta yi murmushin yaƙe.

"Lafiya kalau. Sannu da zuwa."

Ya amsa karo na biyu, shi ba wannan ya ke da muradi ba. Labarin Hajiya Zeenatu da adireshinta ya ke da buƙata.

Abinci ta kawomishi ta kuma ce ya yi hakuri har su yi sallah tukunna. Daurewa ya yi ya amsa da toh sannan ta fice.

***
"Rai kan ga rai?" Hajiya Zeenatu ta faɗi tana murmushi da wani irin mamaki shimfiɗe a fuskarta tana duban Kawu Modibbo da ke zaune a ofishinta na A&Z. Ya share goshi.




I think you'd like this story: "Ƙarfen Ƙafa" by Rufaida-Umar on Wattpad https://my.w.tt/rSOQW4y2Gcb




🕯️ *ƘARFEN ƘAFA*🕯️

_*Rufaida Umar*_

Bismillahir Rahmaanir Raheem.

46)


"Kin san dai ruwa ba ya tsami banza. Kamar yanda kin sani, na sani, komai nisan jifa ƙasa zai faɗo. Toh idan ba mu yi dagaske ba, asirinmu na dab da tonuwa."

Nan da nan ta haɗe rai.

"Me kake nufi?"

Kawu Modibbo ya gyara zama yana mata kallon ƙyar.

"Wata yarinya ta zo min da zancen da ya rushe dukkan walwalata. Tana ƙoƙarin shaidamin cewar ta san inda Husseini yake, duk da ba ta fito fili ta yi bayanin komai ba, amma daga yanda ta ambaci shi Hassan ta alaƙantashi da Husseini shakka babu akwai babban al'amarin da ta sani."

"Ya sunanta?" Hajiya Zeenatu ta nemi sani a hanzarce yayinda kirjinta ke bugu, tana tsoron kar hasashenta ya zama gaskiya. Sai dai abinda ta guda shi ya faru, sunan da ta ke fatan kar ta ji, shi dai ta ƙara tsinkaya daga bakin Kawu Modibbo.

"Ramlatu ta ce sunanta."

Wani miƙewa da Hajiya Zeenatu ta yi sai da shi kansa Kawu ya ƙara tsorata. Jikinta ya shiga rawa nan da nan idanunta suka kaɗa.

"Baƙa ce, ba ta da jiki sosai kuma.."

"Abinda ya tunkaro mu, ya fi ƙarfin mu tsaya ɓata lokaci a kan suffantawa ba. Ki faɗi kai tsaye idan kin santa."

Ya faɗi cike da ƙagara. Ta haɗiyi miyau tana goge gumin goshi.

"Tsinanniyar yarinyar da aka sha yimin gargaɗi a kanta kenan! An tabbatarmin muddin ban nisanta Hussein daga duniyarta ba, to shakka babu komai zai lalace. Kenan yanzu ta gano dangin Hussein? Wannan mayyar ina ce?!"

"Mafita za mu nema. Kin sani, baragurbin kwai idan ya fashe, yakan shafi kowa ba mutum guda ba. Za ki fi ni shiga matsala. Kin san komai don haka a bar kaza cikin gashinta. Tun lokaci bai ƙure ba ya kamata a ɗau mataki."

"Kasheta zan sa a yi."

Kai tsaye ta furta tana fidda hucin ɓacin rai. Kawu ya dubeta sosai, duk da cewar yana shuka abubuwa a doron ƙasa, bai taɓa tunanin ya kashe rai ba. 

"Kina ganin hakan zai haifar da ɗa mai ido?  Kisa na nufin abubuwa da dama ciki kuwa har da rabuwarki da shi Hussein don za ki ƙare a kur..."

"Dakata, ai ba ni zan kashe ba. Zan saka a kashe ne. Mace ƴar uwarta zan saka, ita kanta ba za ta fahimci komai ba. Na santa a bakin Dikko, mayyar kuɗi ce da za ta iya aikata komai saboda shi. Don haka ka bar min wuƙa da nama yanda ka ce, za ka sha mamaki nan da awannin da suka rage kafin safiya."

Kawu ya jinjina kai, suka ƙara shawarwarinsu sannan ya fice.

A gaggauce Hajiya Zeenat ta kira Hajiya Batool ta ba ta labarin komai har shawarar da suka yanke.

"Wannan ya yi kuma ina goyon baya dari bisa dari. Gwara tun wuri a yi ta kuma ta ƙare."

Da wannan suka yi sallama ta kira Chairman a waya. Cikin gaggawa ta ce

"Ka turomin lambar yarinyarnan."

"Wa?" Ya nemi sani.

"HALIMA."

Dariya ya ɗan yi mai sauti, sanadin Halima ya san duk wani tarihi na Ramlatu, duk da cewa ya san da biyu ta faɗamasa, amma ya zamar masa tamkar ƙarin makaman yaƙi a wurin iyayen Ramlatun har ya same ta. Sanadin wannan ne ya sanya har holewa ya yi da ita na sati kafin ya biya ta da maƙudan kuɗaɗen da suka kusa zautar da ita.

"Wani abu ne ya taso?"

Ya nemi sani.

A ɓangaren Hajiya Zeenat ta ja tsaki.

"Wankim hula ke neman kai ni dare, turomin yanzu-yanzu."

Daga haka ta katse kiran ta kwashi tarkacenta ta fita. Ba zai yiwu su tattauna da Halima a wurin ba. Hussein zai iya shigowa kowane lokaci.

Tun kan ta kai motarta lambar Halima ya shigo. Kai tsaye ta ɗauka ta kira bayan ta daidaita zama cikin mota ta rufe.

"Hello."

Halima ta furta.

"Kina magana da Hajiya Zeenatu mamallakiyar A&Z."

Hajiya Zeenatu ta yi shiru don ba ta san ta ya za ta soma bayani ba. Ga mamakinta sai ji ta yi Halima ta ce.

"Lah, na san wurin ai ina zuwa lokaci -lokaci. Ai kin taɓa zuwa inda nake aiki kwanaki can kika biya kudin haraji. Na sanki sosai. Ranki ya dade, Allah Ya ƙara girma."

Murmushi Hajiya Zeenatu ta yi, dagaske ba za ta samu matsala da wannan ba. Don haka ta muskuta.

"Halima ina son ganinki, idan ba damuwa a yau kuma a yanzu."

"Aa babu wata damuwa Hajiya, ki fadi inda zan zo na sameki kawai."

Nan Hajiya ta yi mata kwatancen gidan Hajiya Batool. Ta dinga amsawa daga bisani suka yi sallama bayan Halima ta tabbatar mata yanzun za ta taho.

***
  Hajiya ta isa unguwar Yakasai ranta a tsananin ɓace, ko sashin Hajja ba ta shiga don tasan tsaf za ta hanata tada kowace magana. Kai tsaye ta wuce rumfar Malam Bello inda anan ne yawanci Kawunnan ke zama a sha hira kuma a tattauna matsaloli. Da yake rana ce, aikuwa ta ci sa'a ganinsu a rumfar. Su biyar zaune, Kawu Bello, Kawu Sunusi, Kawu Jamilu, Haruna sai Usman.

Kawu Bello na ganinta ya haɗe gira, ta ƙarasa ta zauna aka gaisa.

"Sai kuma kika ji an turo kuɗin Ramlatu ko?"

Kawu Usman ya furta yana washe haƙora da duk goro ya ɓata. Ta haɗe gira.

"Na ji Yaya, sai dai sam ba'a kyauta ba. Ba ku yiwa yarinya daidai ba. Kada ku manta Ramlatu ba yarinya ba ce yanzu, addininta ya ba ta damar zaɓen miji a karon kanta. Idan ma ku ka dauke batun ta, na tabbatar ku kanku ba ku tsaya wani dogon bincike a kan mutuminnan ba saboda.."

"Saboda yana da kudi ko? Haka kike so ki ce! Wato mu gamunan mayun kudi? Rabi yaushe kika sauya haka? Kina son ki nunamana ke da Khalid ku ka haifi Ramlatu?"

Kawu Bello wanda tun zuwanta ya ke a fusace shi ne ya hau wannan kumfar bakin. Hajiya ta ɗago ta dubeshi don tuni ta soma hawayen idanun sun ƙanƙance.

"Ba iko nake nunamaku da Ramlatu ba, amma fisabilillah duk irin munin ɗabi'u  mutuminnan da na lissafamaku a baya bai hana kun murzawa idanunku toka ba kun ba shi damar ya turo kuɗi. Wannan auren ba zai taɓa yiwuwa ba idan har ina raye, ku gafarce ni amma Ramlatu ba za ta auri Chairman ba."

"Yanzu na fahimci inda Ramlatu ta ɗauko kafiya da taurin kai. Ashe ba a ƙasa ta kwasa ba, a nono ta tsotsa. Wato yanzu da babu ran Malam shi ne ki ka samu kwarin gwuiwar cin karenki babu babbaka Rabi. A baya ke yarinya ce mai takatsantsan da ɓacin ran ƴan uwanki, amma saboda kin haifa, kina kuma taƙama da dukiyar marayun yaranki da ubansu ya bari, shi ne za ki wulaƙantamu. To gwara da aka yi tusa ai halin kowa ya fito."

Sosai kalaman Kawu Haruna sun soki zuciyar Hajiya kamar mashi, ta kalleshi ta kasa magana. Sai Kawu Usman ya sa baki

"Ni abinda ban gane ba Yaya Bello, kai da bakinka ka tabbatarmin da yardar Ramlatu a auren wannan mutumin, yanzu kuma sai na ke jin sabon labarin da ya sha bamban da wanda na sani. Wato dai dole ne za ku yiwa yarinya? Wannan ai ba girmanmu ba ne."

Ya fadi a sanyaye amma ransa a ɓace, haka yake mutum mai hakuri da gudun duniya. Sai a lokacin Kawu Sunusi ya tanka ta hanyar zubawa Usman daƙuwa.

"Ka ci ƙaniyarka Usmanu, mu sa'anninka ne da za ka yi fito na fito da mu? Ai ko Murja ba za ta yi mana haka ba."

Kawu Usman jin Kawu Haruna yana sanya Yayarsa ciki ya sa shi jan baki ya yi shiru sai dai ya rantse ba zai ƙara sa hannu a cuci yarinya ba.

"Aa Haruna, zancen Usmanu gaskiya ne, ni kaina ai shi Bello cemin ya yi da amincewar yarinya aka yi komai. To ba za ta saɓu ba, ke Rabi ki je. Ni da kaina zan yi kiran shi Dikkon na ba shi hakuri. Ita Ramlatu ta je ta ciro kudin ta turomin da hannuna zan ba shi."

Kawu Jamilu ke maganar a daure, kasancewar shi ne babbansu  a wurin don daga Kawu Yakubu sai shi, kuma bai fiye magana ba sai ta ɓaci wannan yasa suke ɗan shakka-shakkarsa. Kawu Bello ya soma share gumi, babu abinda ke ba shi tsoro sai yanda zai yi ya biya kuɗaɗen da ya ci na Chairman. Ƙananun filaye har biyu ya siya ba tare da sanin ƴan uwannasa ba. Wannan tashin hankalin ya sa ya kara magantuwa.

"Haba Yaya, ka mance da auren Ramlatu na baya? Ka mance irin tijarar da ta yi mana? Yanzu Rabi ke har kin mance kina ɗauremata gindi?"

Hajiya wacce ta ke jin ya zamemata dole ta koma wajen Malam Mu'azzam ƙanin babansu na Daura ta yi shiru ba ta ce masa uffan ba. Suka ci gaba da ja in ja, daga ita har Kawu Usman ba wanda ya ƙara tankawa. Kawu Jamilu ya kafe lallai a mayar da kudi yayinda Bello da Haruna suka ce sam ba zai yiwu ba. Wannan ne karon farko da suka yi mishi musu a rayuwa. Ko ba komai shima Haruna ya ci rabonsa. A karshe dai Hajiya ta mike ta wuce sashin Hajja ina ta tarar da Zulaihat zaune su na tattauna maganar.

"Aa, kenan dagaske dai Uwani ta ke za ki zo?"

Hajiya ta harari Zulaihat wacce ita kuma yanda idanun Hajiyar ya yi ja ya ɗaga hankalinta. Ta koramusu duk yanda aka yi. Hajja ta yi salati.

"Ke Rabi! Ban ce ki bari zan je na same su da kaina ba?"

Hajiya ta girgiza kai.

"Ki bar ni kawai Hajja, ni yanzu gobe ma Daura na nufa zan je na sami Baba Mu'azzam da kaina mu tattauna."

"Hakan ya kamata ki yi tun farko ba yanzu da muka dawo ba. Meyasa tun acan shi ba ki mishi bayani ba sai yanzu da ki ka je kike kokarin rushe zumuntarku da ƴan uwanki."

Hajiya ta kalli Mahaifiyarta da mamakin furucinta, ga dai Hajja girma ya ja amma kyawun jikinta yasa ta ke nan ƙyam da ita tubarakAllah.

"Ƙarya na yi kike kallona Rabi? Meyasa za ki tunkare su, ni ban isa ki zo ki fara shawarta ta ba shi ne za ki yi gaban kanki. Yanzu idan wannan ya haɗaku rikici fa? Mun cika alƙawarin da muka ɗaukarwa Babanku kafin rasuwarsa na ganin zumuncinku ya kara ɗanko?"

Hajja ta karashe gami da fashewa da kuka. Hankalin Hajiya da Zulaihatnya tashi, suka shiga ba ta hakuri da neman gafara, dakyar ta sauko ta kuma yi mata fada sosai.

"Idan irin haka ta faru ba'a yanke hukunci cikin fushi. Hakuri ake yi da kuma kai zuciya nesa."

Ta amsa da toh tana sharar kwalla.

***
Zufa sosai ya shiga ketowa Halima, kirjinta na dukan tara-tara. Da gaskiyar ƴar uwarta da ta taɓa gargaɗinta akan son abin duniya.

_*"Watarana idan ba ki yi hankali ba Halima, son kudinki zai kai ki ya baro. Kuɗi sheggun abu ne da idan har ka sa a ranka za ka aikata komai don ka same

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login