Showing 42001 words to 45000 words out of 271643 words
Chapter 15 - Wani Gari Book 1 Complete Hausa Novel
kumfa ba, a take yaji ya shige masa a idon, a nan yaji wani sabon amai na taso masa yana ta jin kyankyami a jikinsa, tun da yake a rayuwar be taba wanka tara at the same time ba sai yau, ba wanka iya na sabulu ba har da na tsarki sai da yayi ba kuma dan yayi komai ba, sai dan ganin Waira da yayi da tabata da carpet din yake ji ba kamar ma har da wankan tsarki yana bukata saboda kazantar ta yi jawa wata kila idan be yi wankan tsarki ba zai iya jawa kansa matsala aki karbar sallah shi.
Ya san yadda Hajiya Jamila take sakawa a tsabtace komai na dakinsa amman hakan be kwantar masa da hankali ya taba tawul din dake aje a bathroom din ba, haka ya fito ya nufi gurin da tufafinsa suke aje ya dauko sabbi fil ya saka sannan ya shafama jikinsa mai ya saka turare, talkami ya saka ya sauko fito daga dakinsa zuwa falon Hajiya Jamila tea ta fara tarbonsa da shi sannan ta zuba masa soyayyaen nama domin ya san yadda yake son naman da aka soya suya mai kyau, doya ta sarrafa masa da miyar kabeji wanda ta ji kaza, tun kan ta kawo masa abincin kamshi ya cika hancinsa. Lafiya lafiya ya fara cin abincin kamin ya tuna da kazantar Waira sai gashi ya tashi da sauri ya nufi bathroom din Hajiya Jamila cikin tashin hankali ta bi bayansa tana tambayar ko abincin ne be masa dadi ba ko kuma wani abun ya gani a ciki. Haka ta tsaya a bayansa tana kallonsa har ya gama aman ta kunna fanfo ta tara masa ruwa ya wanke bakinsa.
“Wani abu ka gani a cikin abincin ne?”
“No inda na tafi ne na ga wata kazanta da ban taba gani a rayuwata ba”
“Ina kaje Ameer?”
“Wani daji ne, a KT”
Bedroom suka dawo, ya zauna ya labarta Hajiya Jamila duk abun da ya faru ciki har da motar da Nimra ta bashi and da reason din da yake ganin ya saka ta ba shi motar. A yanayin yadda ya bata labarin ta gama fahimtar bashi da gaskiya domin shi ya fara tsokanar abokin nasa amman tsoron bacin ransa ya saka ta kasa nuna masa sai tausarshi take kar ya aikata abun da zai zame masa matsala.
“Da ka yi hakuri ka kyaleshi Ameer idan ma ya ci amanarka zai gani a nan gaba, zalinci ba shi da kyau idan ka zalinci mutum komai ta dade sai hakkinsa ya fita, ka saka masa ido kana zaune hakkinka zai ita matukar ya zalince ka Allah ba zai bar shi ba”
“Ni ko ba a taba ni ba, kin san zan taba balle kuma an taba ni, bana bari ga Allah”
Ya amsa mata kai tsaye, numfashi ta sauke a hankali ta mike tsaye.
“A dauko maka wani abincin?”
“Na koshi, a sama min flight din da zai tafi Abuja anjima zan kwanta yanzu idan babu kuma zan je da mota”
“Ba zaka kwana a nan ba?”
“No ina son na je na duba jikin Daddy hankalina ba zai kwanta ba sai na ganshi”
Hajiya Jamila ta shafa kansa, sannan ta fice cike da damuwar da ita kadai ta santa. Kwanta yayi saman lafiyayyen gadon abun ka da wanda ya marmarin bachi nan da nan bachin yayi gaba da shi.
Mafarkinsa gaba daya akan yarinyar da tunaninta ke saka shi tashin zuciya da mai ne, ba mafarkin abun da ya faru a dajin yake ba, mafarki yake akan wata yarinyar da aka tsabtace ta sha ido da kwalliya, kamshi ta ko'ina ta ratso taron jama'ar da ake gabatar da Event din da be san na minene ba, ta iso gare shi, sai ya risina kamar mai jiran isowarta ta saddan kansa kasa alamar girmamawa a gareta ita kuma ta cire wani zare a hannunta ta daura masa a wuya ta yi mashi murmushi, sannan ta juya ta fice daga taron a zuwa wani dakin dake da icen tuffa ga kuma wani itacen na dogon yaro (Dalbejiya or Bedi) a tsaye. Can kuma mafarkinsa ya sake daukarsa zuwa gidansu Nimra, kuka ya hango tana yi tana fadar shi yayi kisa ba ita ba, hakan ya sake haddasa fada a tsakaninsa da mahaifinsa har ya sake korarsa a karo na biyu...! Firgigit ya farko daga bachin na rana ya yarfar da hannu ya shafe wuyansa, tsabar kyamar Waira da yake ko a mafarki ya ga ta taba shi kazanta yake ji, Even though ya san mafarki ne amman hakan be hana shi sake yin wani wankan ba, har mamaki yake in wanda haukar mafarki da kwashe kwashe shi miye hadinsa da kazama da har zai kawo masa ita a bachi, ba kawo ta ne kawai matsalar ba daura masa zaren dake hannunta da tayi a wuya shi ne matsalar domin jinsa yake kamar gaske.
Tsaki yaja yana shafa turare a wuyansa, lallai ya yarda mummunan mafarki daga shaidan yake, domin idan ba shaidan ba ta ina za a ga wannan yarinyar kazama ta yi wanka ta yi kyau tsabtsab da ita har su kamshi, a yau kam ya tabbatar da mafarkin rana shirme ne. Sai da ya saka wasu tudafin sannan ya sake komawa bathroom din yayi alwala ya fito ya karbi key din motar Hajiya Jamila ya fice daga gidan, gida biyar ya wuce sannan ya isa inda masallacin unguwar yake, yin Sallah in time kuma cikin jam'i is one of his favorites, sai dai baya jerawa da mutane sai dai ya tsaya a gafe daya, idan kuma ya samu Masallaci ya cika sai yayi sallah a waje, Saboda kar jikinsa ya taba na wani indai ba abokansa ba, sai kuma mahaifinsa da mutanen da yasan suna tsabta a yadda yake so, haka Allah yayi shi akan kyamar mutane da yake har warinsu yake ji wani lokacin.
Bayan an sallame ya fito ya dawo gida, a nan ya samu Hajiya Jamila na hada masa cake, bayan ta gama take fada masa ba za a samu flight zuwa Abuja da yamma nan ba, amman ta masa Booking din Private jet, kuma ya jidadin haka cake din kadan ya ci daman he's not that foodie abu kadan idan ya ci ya ishe shi wani lokacin ma Lemu kawai zai wuni a cikinsa.
Karar tsayawar motar YaYan Hajiya Jamila ya tuna masa da sarewa, da sauri ya saka hannunsa aljihu yana lalabe kamar a ciki ya aje ta.
“Oh...”
Ya furta hakan yana jin wani sabon bakinciki.
“Lafiya?”
“Sarewata na bari a motar yarinyar can Wallahi”
“Mantuwa ka yi?”
“Eh ban tuna ba sai yanzu”
“Sai siyen wata kenan?”
“Ba za a samu mai kyau irinta a yanzu ba, and akwai wanda ya saka min wani abu a sarewar nan wanda idan na busa take tafiya yadda nake so”
Zanjabil da yar'uwarta Hurriyya ne suka shigo falo, suna ganinshi suka yo kansa da gudu suna murna, sai dai bacin rasa sarewarsa ya saka be wani sake musu fuska sosai ba, tunaninsa na yadda zai dawo da barsa hannunsa ne, ya san zai sha fama amman haka zai dawo da ita ko da kuwa yakin duniya na uku ne zai afku.
©Khadeeja Candy
©®Copyright
2023
*⚜️ ...WANI GARI... ⚜️*
_©Khadeeja Candy_
1️⃣5️⃣
Daddy na kokarin mikawa yarsa tea cup din dake hannunsa Momy ta turo kofar dakin ta shigo, tun daga yanayin annashuwar da ya gani a fuskarta ya san akwai labari mai dadi, domin samun saukinsa kawai be isa ya saka ta farinciki har haka ba. Kamin ta karaso inda yake zaune Ameer ya shigo dakin. Wani sanyi ne ya ziyarci zuciyar Daddy a take ya ji kamar ya warke daga ciwon da yake, cikin yanayi na damuwa da halin da Ameer yake ciki yake kallonsa har ya karaso kusa da shi, Kanwarsa ma kallon mamaki take masa domin babu wanda yayi tsammanin dawowarsa so soon haka, duk a tunaninsu sai mahaifinsa yaje nemansa. For the first time Ameer ya ji yana dan jin nauyin mahaifinsa har ya kasa hada ido da shi.
“Ina shirye shiryen zuwa nan ya Hajiya Jamila ta kira ni ta ce gata ita da yaranta sun raka Ameer Airport jirginsu zai sauka 5:30 na tura mota ta dauko shi Airport, ni naje daukarsa da kaina domin na san kai yake son gani”
Momy ce take labartawa Daddy haka tana murmushi, Ameer ya saka hannayensa aljihu.
“I'm just care about you, an fada min jikinka ya tashi”
Daddy yayi murmushin da shi kadai ya san na minene ya ma dansa mazauni a kusa da shi.
“Ba ma iya rabuwa da juna Ameer mutuwa ce kawai ke iya raba ďa da mahaifi, ba zaka iya rayu idan babu a tare da kai ba, haka nima bana jindadi komai idan baka kusa da ni, Allah ya maka albarka ya shirya ka”
Momy da Kanwarsa suka amsa da Ameen, shi kuma ya kara matsawa jikin Daddy kamar wani karamin yaro, they miss each other irin na uba da ďa, a asibitin ya raba dare sannan ya karbi key din Momy ya fita daga Asibitin, family house dinsu ya nufa yana yin horn aka bude masa makeken gate din, ya kunna kai harabar ya faka motar ya fito ya fito ya shiga falon, kamshin gidansu na dabam balle kuma dakinsa da doka ce a saka masa turare sama da kala daya.
“What a blessing”
Ya furta yana jin yadda ya shaki iskar yanci a yanzu kamar wanda ya fito daga gidan yari. Kan gadonsa ya fadi kwance ya ware hannayensa yana jin marmarin macen da addinin musulunci be halal ta masa ba, abun bakinciki kuma babu wayarsa a kusa da shi, Sim din ma sai am masa welcome back domin ba zai iya komawa daukarsa ba he don't think ma idan ya koma zai samu liyin a gurin. Tashi yayi zaune ya nufi gurin da yake aje wayoyinsa ya dauki wanda and ya manta when last yayi amfani da ita ya kunna, sai dai ba shi da liyin da zai yi amfani da shi ya kirata a yanzu, domin liyi biyu yake amfani da su, kuma ya fasa wayar ya bar Sims din a can. Fitowa yayi dakinki ya sauko kasa falon ba kowa daman dare ya raba mutanen kirki duk sun yi bachi. A dole ya zauna akan kujera ya lumshe ya san idan yaje gidanta a yanzu ba lallai ta iya fitowa ta bude masa ba, kuma gashi sisters dinsa duk sun yi bachi balle ya ari Sim dinsu ya saka ya kirata, by this time kuma ya san kowa ya rufe shagonsa. Ba dan Allah ya hakura ba sai dan babu yadda zai yi sai karfe biyu da minti biyar ya tashi falon ya haura sama ya shiga dakinsa, wanka ne first abun da ya fara yi sannan ya saka kayan bachi ya kwanta. Hankali kwance bachi ya dauke shi be farka ba sai da Asuba, gidansu ya shan banban da wasu sauran gidajen da suke Abuja, domin akwai karamin Masallaci a na su gidan ba kamar gidajen sauran masu kudin ba. Da shi aka yi jam'in Sallah Asuba sai dai bangarensa da dabam da yake tsayawa yayi Sallah. Dakinsa ya sake dawowa ya kwanta sai a yanzu yana tunanin ko ya Nimra zata yi idan har yarinyar da ya dauko aka ce ta mutu a motarta? At least ya rage zafi domin ya san zai jefata a matsala, be zama lallai mahaifinta da Maleek da ta hada kai da shi ya bari a hukuntata ba, kamar yadda ya san mahaifinsa ba zai yarda ya bar shi ya amsa sunan kiran kai ba, ko da ta fadi cewar shi ta bawa motar a dole ita za a dorawa laifi, balle kuma shi a yanzu ya shirya karyatata idan har tace shi ta bawa motar.
Kamar an tsikare shi ya tashi ya cire tufafin jikinsa ya shiga yayi wanka ya shirya akansa sai kamshi yake ta ko'ina, key da ya shigo da sho ya sake dauka ya fita, Babu wanda ya san da fitarsa a gidan sai masu aikin da suka farka tun da Asuba suka fara aikinsu Momy bata dawo ba saboda kwana da ta yi Asibitin kanensa kuma duk bachi suke. Motarta ya shiga sanin halinsa ya saka masu gadin suka bude masa gate tun kamin ya iso. Tafiyar awa daya yayi sannan ya isa wani madaidaicin Gida da aka kawata da kayan alatu, tsayawa yayi da motarsa yana kallon yarinyar dake kokarin rufe gate din da ke nuna alamar motar da ta wuce ta gabansa a gidan ta fito, ita ma tsayawa ta yi rike da kofar tana kallonsa hanjin cikinta na kadawa domin ta ga fuskar ko waye duk da kasancewar ba da motar da ta sani ya zo ba. Ji yayi ba zai iya shiga ciki da motar ba sai ya bude ya sauko yana kallonta sai wani sham kamshi yake zuciyarsa na halbawa da mugun karfi, cikin wani irin taku na daukar hankali da gwarewa irin ta yan duniyar da take murza musu kambu yadda suke so, Angel ta je a gareshe tana tarbunsa with surprise.
“Don't touch me”
Tana isowa ya dakatar da ita, ta fi kowa sanin idan ya ce kar ta aikata abu he meant it tana aikatawa za su samu matsala.
“I miss you Ameer”
“Waye ya fita da mota yanzu?”
Ya wani yi kamar bata fahimce ba, sai kuma ta yi dariya tana kokarin yi masa wasa da hankali.
“Oh... Kawata ce Nanita”
“Really? Kina tunanin ni wawa ne?”
Ta mika hannu zata fara yaudararsa da kalamanta, ya daka mata tsawa.
“Na ce karki taba ni, kin fi kowa sanin abun da nake kyama shi ne sharing, and because of that na ware miki komai, na dauke miki komai ashe bayan idona kina iya cin amanata?”
“Nono karka je da nisa Ameer wannan fa kawata ce ta kwana nan ne, yanzu nan ta fita kai kasan ba zan iya cin amanarka ba God Forbid ni zan aikata haka ba, yanzu dai shigo ciki mu yi magana”
Harara ya watsa mata tun daga saman kanta har kasa, sannan ya kara ja baya.
“Kin yi sa'a ina jin kyamarki a yanzu, idan ba haka ba, Wallahi sai na kusa kasheki a gurin nan, but matsalar ba zan iya taba ki da hannuna ba ne, ki hada duk wani abu da kika san naki ne ki bar gidan nan we done”
Ko bahaushiyace ba zata yarda ta rasa wannan gatan na Ameer ba balle kuma inyamura da suka fi kowa sanin zafin neman kudi, zubewa ta yi kasa ta fara rikonsa tana dukan kanta da ke a haske kamar na maza, ko kadan be saurareta ba ya juya ya shige motarsa motar ma da take kokarin tarewa sai da yayi cikinta da ita, da bata yi hanzarin kaucewa ba kadeta zai yi yayi tafiyarsa. Bacin ransa ya karu he never thought Angel zata iya cin amanarsa a bayan idonsa kamar haka, duk da be tabbatar ba amman yasan ta aikata domin akwai alamun rashin gaskiya a tare da ita, idan ba haka ba wace kawace zata zo ta kwana a gidan ta fita a irin wannan time da da sasafe kamar an koreta? Kamin bata taba fada masa kawarta ta zo ko zata zo ba, and shi da idonsa Namiji ya gani a motar ba mace ce, duk kudin da yake kashe mata yana yi ne saboda ta tsare masa mutunta ta hana kowa kanta sai shi, a tunaninsa matan hausawa su da rikon amana kamar na kafirai wannan ya saka be taba gwada yi da ba haushiya ba, sai ita da yake bata ko wane kalar umarni ta bi ciki har da aske gashin kanta da tayi saboda shi, domin tsabtarsa bata tsaya iya ga tufafi ba har da gashi baya so more Especially na wasu matan da yake ganin attachment ne ba ainahin na su ba.
Rasa gurin zuwa ya saka shi zuwa gurinsa ba a time da ya saba zuwa ba, ba dan ya saba lati ba, sam baya lati a zuwa aiki kuma no matter how yana shiga office yayi duk abun da yake aikinsa ne, sai dai ya wulakanta mutane yadda yake so ko ya kori wasu, wannan halinsa ne da kowa ya sani. Shiyasa suke taka tsantsan da bin dokokisa gudun kar ya jefa su a matsala yayi musu sallamar dole. Ba halinsa bane yin Sallama balle kuma amsa gaisuwa, hakan ya saka be kula masu aikin tsabtacen muhallin dake ta gaisheshi ba, har ya isa gurin kofarsa Office dinsa ya saka code bude kofar ta bude masa ya shiga ciki ya zauna, nan kadai gurin da be yi marmarin zuwa ba, musamman a yanzu da ya shigo cikin damuwa. kujerarsa ya nufa ya zauna ya runtse ido kujerar ta fara juyawa da shi tana tunanin yadda abubuwa suke masa zafi a yan kwanakin nan. Zaman baya masa dadi haka ya saka shi mikewa tsaye ya nufi fridge ya dauko gorar ruwa ya kai bakinsa, sai da ya sha rabinta sannan ya aje saman fridge din ya nufi Window ya bude fararen Curtains din da suke gurin ya tsaya gaban glass din yana hango kasan begen da mutanen dake kokarin shigowa masu aikin gyara harabar kuma na ta yi. Hannunsa daya ya saka aljihu sannan ya juyo ya nufi gurin Telephone din dake gefen teburinsa kira yayi sannan ya kara a kunne.
“Idan Faruk ya zo ina nemansa”
Shine abun da ya fada ya aje telephone din, ya sake zaunawa wannan karon kofar shigowar yake kallon. Faruk be shigo office din ba sai takwas da rabi, ciki tsoro da fargaba ya shigo sanin waye Ameer zai iya cewa ya masa laifi, domin tun kamin ya shigo office dina ka fada masa Ameer na nemansa kuma shigowar safiya yayi. Da katinsa yayi amfani ya bude kofar sannan ya shigo Office din dake dauke da kyamarorin tsaro, kamar yadda ko wane Office yake. Da ido Ameer ya fara tsare shi sannan ya mike tsaye ya dauki pen din dake gurin ya yagi diary ya rubuta masa numbers