Showing 84001 words to 87000 words out of 271643 words

Chapter 29 - Wani Gari Book 1 Complete Hausa Novel

kawai yayi after that be fada mata wani abun dariya ba. Ummi ta juya ta koma ciki tare da Hanne suna ta mamaki, Nimra kuma ta kashe masa ido irin na zolaya.

“Yaya dai Jabir ko dai taku ta zo daya?”

“Da wa? Ai ba zaki yarda ba”

“Saboda me? Indai ruwan zai maka wanka ai sai dai mu nama maka na dauraya”

“Hmmm -Nhmmm Nimra kenan ke zaki yarda ki barwa wata ni?”

Ta saka dariya domin ta san halinsa da barkwanci musamman idan baya son abu yanzu ne zai juye ya mayar akan wani.

“Ni na mashinshini na kai ne baka da kowa, shiyasa nake maka kamu ka samu wannan yarinyar ta taimaka maka”

Ya girgiza kai yana cije baki.

“Ko waye mashinshinin nan na ki ki fada masa you're taken kuma ina da kishi bana son wani na rabar iyalina”

Dariya ta saka gudun kar Maleek dake zaune can gefe ya gwatsaleta ya saka ta juya ta koma falon tana gyara dankalin kanta. Shi kuma ya sake juyowa ya fuskanci Waira.

“Fada min ina iyayenki suke?”

“Waira zata fada, amman ba wayo ka yi ba”

Fada masa take zata fada masa, amman ba dan yayi mata wayo ba, shi kuma sam be gane salon karin halshen nata ba, shiyasa be yi kokarin cewa komai ba har ta cinye biscuits din dake kan plate din gaba daya ta kalleshi idonta na cika da hawaye ta ce.

“Waira bata da yaya, bata da Baba, bata da Mama amman tana da Eid”

“Waye Eid?”

“Dan'uwanta ne, yana sonta, Eid yana mata komai amman yanzu be neme ta ba, Waira ba zata koma garinsu ba, idan ta koma Sarki zai kasheta”

Mamaki ya kama Jabir.

“Saboda me? Me kika aikata? Wani kika kashe”

Sai ta girgiza kai hawaye na sauko mata.

“Bata kashe kowa ba, amman Sarki yace idan Waira ta gudu ba zata iya dawowa ba, kuma wani ya mutu saboda ita, za a kasheta”

“Miyasa kika gudu? Baki da yan'uwa a can? Ke baiwa ce ko kuma me?”

Ta girgiza kai hawaye na sauko mata kamar ba gobe.

“Waira bata san kowa ba, ita kadai take zaune tana da....”

So take tace bera da zakara kuma ba zata iya fadar hakan da hausa ba, ta suna sunan da aka fada mata na zaka da bera.

“Waira tana da Hens, Waira tana da Rat, Waira Waira zata mutu kusa Sarki ba zai kyale ba, zai kasheta”

Ta girgiza hancinta na zubar da majina kamar yadda idonta ke zubar da ruwan hawaye.

“Waira bata son ta mutu, Waira tana son ta ga Eid Waira bata son ta koma, ba zata gane hanya ba”

Da gaske take fada domin tana yawan tuna mutanen garin da rayuwar da take a garin amman ko kadan ta kasa tuna sunan garin ma balle kuma ta san hanyar da zata bi ta tafi, ita dai ta san ta rayu a wata duniyar kamin ta samu kanta a nan, kusan kullum sai ta kwanta da tunanin Eid da berayen da suke rage mata kewa. Ta kalli Jabir tana kuka sosai.

“Waira bata son ta mutu, Waira tana son Eid, Eid ba zai zo ba, Sulem ba zai zo ba... Waira tana Son Sulem....”

Ya matso kusa da ita ta jingina kanta jikinsa yana jin tausayinta na kama shi. Har suka ci suka sude Maleek be dago ya kalleta ba tun bayan kallon da yayi mata da farko, sai dai kunnuwansa suna sauraren komai take fada and one by one ya fahimci ko wace kalma dake fita bakinta.

“Waira bata son makaranta, suna mata dariya idan ta yi magana, Waira bata da kawa a makaranta”

Kusan duk wani abu dake cinta a rai sai da ta fadawa Jabir, the way da yan makaranta suke tsokanarta yana mata ciwo sosai, idan aka tambayeta ta kasa bada amsa ko kuma ta yi bayani ba a yadda suke yi ba, suna mata dariya ita kuma tana jin zafin haka, idan an tashi cin abinci bata da abokin zama ta ci abinci, she's not that child da za a ce tana tsoron mutane domin ba small girl ba ce, but yanayin rayuwarta ya saka tana shakkar kusantar mutane, ga yanayin mu'amalarta da shigarta ya ya banbanta da na sauran yan makaranta domin bata son taka talkami har yanzu, tana isa makaranta sai take cirewa ta rike a hannu, ta inda Allah ta taimake ta rashin rufe kai ba ita kadai ce bata yi ba, domin akwai yara da yawa a makaranta da basa rufe kansu wasu ma ristoci ne wasu kuma musulmai ne da suka ari rayuwar turawa suka yafa.
Ko baya ga wannan ma ita dai gani take an cilasta mata na cewa dole sai ta koyi rubutu da karatu, abun da bata iya ba tun farko, sai dai hakan ya taimaki rayuwarta domin tana jin yaren hausa da English a yanzu, sai idan an yi mata mai sarkakiya ne kawai ba zata gane ba. Rike hannunta ďaya a ciki ďayan.

“Waira tana son Ummi.. Tana son Nimra.. Waira tana Son Mahmood... ”

Ya nuna kansa.

“Waira tana son Jabir?”

Ta dago ta kalleshi idonta har sun sauya kala saboda kuka. Sai ta girgiza masa kai alamar aa.

“To Waira tana son Maleek?”

Nan ma ta girgiza kai.

“Waira tana Son Namra? Da Abiey?”

Ta girgiza kai a karo na uku cewar bata son su.

“Mun shiga uku har da Mai Gidan gaba daya? To shi mi yayi?”

Bata son Abiey da ďansa Maleek saboda basa sakar mata fuska yadda Ummi da Nimra suke, kuma basa janta a jiki yadda ya kamata, Jabir kuma yau ta fara ganinshi taya zata san halinshi har tace tana son shi. Maleek ya mike tsaye ba tare da ya dauke plate din da ya ci abinci ba ya fice daga gurin ya koma cikin falo. Ita kuma sai ta saka gefen rigarta ta share fuskarta, Jabir ya yamutsa fuska alamar kazanta.

“Noooo bari na dauko miki tissue”

Ya tashi shi ma ya bi sahun dan'uwansa Maleek, sai ita ma ta tashi ta nufi hanyar Garden tana tunani kala kala, a cikin abubuwan da take tunanin babu mao mata ciwo kamar rashi ganin Eid tana son ta sake saka shi a idonta kamin ta mutu, domin ta san mutuwarta zata iya zuwa mata a ko wane lokaci, Sarki be taba alkawari ya saba ba, kuma ba zai fasa akanta ba.

Abun ka da gwani, daga shiga dauko tissue Jabir ya shantake da bawa Ummi labarin abun da Waira ta fada masa, da kuma fahimtar manufarta da yayi. Tausayinta da kaunarta sai ta karu a zuciyar Ummi.

“Shiyasa bata da sakewa yarinyar nan kullum tana zaune kusa da ni, komai ake hira ba zata saka baki ba, shekararta ďaya a gidan nan amman taki ta sake jiki da kowa, wata kila shiyasa ta ki ta fada mana inda garinsu yake saboda bata son a maida ta garin, Allah kadai ya san abun da ta yi going through”

“Tace bata son Abiey da Maleek amman tana son da Nimra da Mahmood”

Ummi ta yi murmushi tare da mikewa tsaye tare da mika hannu ta karbi tissue dake hannun Jabir.

“Ba ni tissue”

Jabir ya mika mata ta zara ta share hawayenta daman abu kadan yana saka ta kuka a yanzu saboda zuciyarta a raunace take. Jabir har ya mike tsaye zai bita sai mahaifiyarshi sai dakatar da shi.

“Yanzu kuma ai sai ka ba ta damar magana da ita tun da ka yi mai yuyuwar, sanadinka ta fadi abun da ta boye kar kaje yanzu zata ce ka tona mata asiri wata kila yardar da kai ta yi shiyasa ta fada maka”

“Gaskiya yarda ce kam tun da bata fadawa kowa ba sai ni”

Nimra ta kwantar da kanta jikin Dr zainab.

“Ta ba ni tausayi”

“Darasi ne agareku ku da kuke da iyayen a raye, kuma suka dage suka ba ku gata da tarbiya daidai gwargwado, sai ku bisu da addu'a kuma ku cigaba da yi ma Allah godiya kuna musu biyayya”

Maganar da Dr Zainab ta yi ta soki Nimra, sai ta yi shiru kamar ruwa ya ci tana kallon wani gurin na dabam har sai da Jabir ya fice sannan ta tashi zaune tace.

“Mommy akwai maganar da nake son na yi da ke, amman ba yanzu ba sai mum kebe saboda magana ce mai girma, but ke kadai zaki iya taimako a nan saboda Abiey yana jin maganarki kuma zaki iya tankwara Ummi ta aminta ma”

Dr Zainab ta kalleta da duba da babu wasa a cikinsa.

“Wace magana ce?”

“Akan wani ne, kusan dai zan iya cewa maganar aurena ne, amman dai sai kin kara hutawa zuwa gobe ko jibi zai mu yi maganar, amman for now karki fadawa kowa mun yi maganar wannan sirrinmu ne”

Dr Zainab ta gyada mata kai cike da jindadi daman kullum burinta ta ga sukana dan'uwanta, kusan ta fi kowa damuwa da rashin auren da kowa be yi ba a cikinsu tun daga kan Maleek da be son zancen aure har zuwa Nimra da Namra da suke mata, a take ta ji duk ta matsu goben ta yi fada mata ko minene.


*** *** ***

Waira na tsaye tana kallon barewar dake ta kiwo ita kadai Ummi ta iso gurin rike da tissue ta dafa Waira, sai Waira ta juyo ta kalleta.

“Kin ce kina so na, amman baki taba hira da ni kin fada min damuwarki ba miyasa? Ina yawan tambayar ina iyayenki suke baki fada min ba”

Waira ta sauke ido kasa.

“Waira bata da kowa, Waira bata san Iyayenta ba, Waira bata san waya haife ta ba, Waira bata ga Babanta ba, bata ga Mamanta ba”

Ta fashe da kuka, sai Ummi ta riketa.

“Wani lokacin barin damuwa a cikin rai ba ya maganin komai, ko da yake fitarwa ma bashi magani, sai dai idan ka fada kana jin sanyi, we all have story to tell, kowa yana da damuwa da burin da yake boyewa a zuciyarsa, Waira na miki alkawari, matukar abun da kika fada gaskiya ne, zan rike ki kamar ƴata wata kila saboda haka Allah ya dubi zuciyata ya yafe min son zuciyar da na aikata a baya, ni ma na rasa farinciki kamar dai, ina da damuwa wacce na boyeta a raina na kasa fadawa kowa, sai dai na san hakki ba zai daina bibiyata ba, tarin dukiya da kayan more rayuwa sun yi kadan su manta da ni kuskuren da na aikata a baya, farinciki a zuci yake na rasa nawa”

Hawaye take sosai tana jin kamar ta samu damar fashe ƙurjin da ya nuna yayi mata tuwa a zuciya.

“Wata kila shaidan ne yake ribantata, amman ina jin son ďana a raina, fiye da sauran ina kewarsa sai kace na taba rayuwa mai tsawo da shi, ina son na hada su guri ďaya matsayin yan'uwa, gabar dake tsakaninsa da Maleek ina son ta wuce na rumgume su biyu a lokaci ďaya, ina son kamin na mutu na roki yafiyarsa kamin ranar da Allah zai tsayar da ni ya tambaye miyasa na aikata son zuciya da abun da nake ganin kamar hanya ce mai bullewa, na manta shi ke kashewa ya raya, soyayya ta rufe min ido a wacan lokaci, ni kawai yarinya ce mai wauta da sakarci a wacan lokacin, hakkin Deen da na iyayensa yana kaina, hakkin Ameer yana kai na, ina son na gyara komai kamin ďan lokacin da ya rage min ya kare, ina son na kyautatawa ďana na fada masa irin kaunar da uwarsa take masa, na roki yafiyarsa, so nake na yi masa gata kamin na mutu amman taya.....?”

Ta rumgume Waira tana kuka, Waira ma kukan take duk kuwa da kasancewar bata fahimta takamaiman dalilin daya saka Ummi take kuka sosai haka ba, kuma take kalaman da bata gane manufarsu ba. Rumtse ido ta yi ta dafa hannun Ummi a kokarinta na fahimta abun da Ummi take fada. Duk abun da suke Maleek na tsaye jikin gilashin windows din ďakinsa yana hangesu, sai dai ko za'a kashe shi ba zai iya fadar abun da suke cewa ba, ko kadam be jidadin hango mahaifiyarsa tana kuka sosai ba, wata kila labarin Waira ne ya taba ta, daman ya san ta da rauni, shi ma da yake dakakken ya ji tausayinta balle kuma ita. Ya cire hannunsa ďaya dake cikin aljihu ya saki curtains din.




©Khadeeja Candy
©®Copyright
2023
28


Ta saki Ummi da sauri ta daga kai ta kalleta, a take ta mance da kalar nata damuwar, tausayin Ummi ya kamata, tsoro da mamaki suka bayyana a fuskarta. Ummi ta yi kasa ta zauna tana kukan data kasa controlling din kanta, Waira ta bita suka zauna a gurin sai dai ita ba kuka take a yanzu ba, mamaki ne ya kusan kasheta da kuma tausayi. Ganin dukansu jiran mutuwa suke yi. Ummi da ta zo da tissue da sunan ta sharewa Waira shawaye sai gashi  Waira ta dauko tissue tana sharewa Ummi hawayenta. Cikin karfin hali Ummi ta yi murmushi ta karbi tissue ta share hawayenta, sannan ta mike tsaye Waira ma ta tashi tana kallon Ummi da wani irin kallo da take jin kamar ace yana iko da damar yaye mata damuwarta ta kawar mata da komai, domin ta rike ta kamar yarta bata taba nuna mata kyama ko hantara a iya zamanta a gidan ba, tana ganinta a ciki yanayi na damuwa sai dai ba ko yaushe ba, domin tana kokarin boyewa saboda yayanta da mijinta, hakan ya saka bata taba kokarin netso ta shiga duniyar tunaninta ta hango rayuwar da take boyewa a cikin ranta ba.

“Ummi... Waira tana tana son Ummi”

Ta fada tana kallonta, wani sabon babin kallon tausayi ta budewa Ummi da zarar ta kalleta sai ta hango abun da ta gani daga rayuwarta. Ummi ta rike fuskarta tana dariya.

“Ummi ma tana son Waira, amman ba haka ake cewa ba, kin kasa iya hausa daidai har yanzu, saboda baki bude baki ki yi magana idan ana hira, cewa zaki yi Ummi ina sonki fadi na ji”

“Ummi ina sonki...”

“Yauwa Yata yar albarka”

Ummi ta rumgume ta tana murmushin da kusan ya zame mata a dole a kowa ne wuni da dare, domin mutane suna ganin zahirinta ne baďininta kuma ita kadai ta san abun da take ciki. Sun dade a haka sannan ta riko hannunta suka dawo cikin falon. Yammaci ranar har dare Waira kusa da Ummi ta rayu kamar yadda ta saba wai dai wannan ya kusanci ya fi na baya, ko ina Ummi ta motsa idon Waira na kanta. Dr Zainab suka tattauna maganar yadda Ummi take ganin ya dace da Waira sai dai bata yanke hukunci ba har sai ta ji daga bakin mijinta. Bayan Sallah Isha'i aka sake gabatar musu da abincin da Hanne ta girka, Ummi kuma ta damawa Waira madara da kankara kamar yadda ta saba mata a kowane dare. Tana gama sha ta kwanta akan doguwar kujerar tare da yin matashin kai da cinyar Ummi, Dr Zainab ce ta sauko sanye da gown marar nauyi sai hula a kanta tana rike da wayarta, Juwairiyyya da Yesmin suna dakin Nimra tare da yar'uwarta suna ta hira, Mahmood kuma ya fita tare da Jabir da dan lukuti wato Umar, Maleek ne kawai a Falon sai Ummi da suke kallon wani documentary da ake a Al Jazeera, Hanne ma ta shige BQ bayan gama aikinta a bangaren Ummi domin babu abun da ta rasa a sashenta sai dai kadaici da take fama da shi wani lokaci, kasancewar bata tare da kowa sai ita kadai kanta, da kuma karamin tv da Abiey ya saka mata da startime ta kama channel din da take so a ko wane lokaci. Ummi da Maleek ne kawai ke kallon sai kuma Gwaggon su Maleek wacce ta sauko a yanzu ta zauna tana latsa waya, Waira kam Ummi ce tv ta, daman can kallo ba burgeta yake ba, farkon fara ganin mutane a tv ya tsorata daga baya ta saba sai dai hakan ba saka ta saki jiki ta dauke shi da muhimmanci ba ko wani abun burgewa ba, har yanzu tana kallon wani abun na rayuwarsu dabam da ya sha banban da nata, akwai abubuwa da yawa da bata waye da su ba a tsawon zamanta a gidan, wasu abubuwan kuma basa burge ta, har gobe tana marmarin rayuwarta ta baya kamar yadda bahaushe ya ce sabo turken wawa. Lokuta da dama Ummi zata shigo falon ta tarar kowa yana zaune yana kallo ko taba waya ita kuma hankalinta yana can wani gurin dabam, ko kuma ta boya a bayan kujera ta kwanta idan bata son zama a cikin mutane, shi ma kuma sai idan Ummi bata kusa kamar idan ta leka bangaren Abiey ko kuma wata fitar ta kama ta, ko kuma tana kitchen tana girki.

Time to time Maleek yake jefar Waira da kallo a sace, yana mamakin me Ummi ta fada mata take ta mata wannan kallon a yau, ya san ta saba da kallon mutane har sai mutum ya sargu, ba ma kamar Ummi sai dai wannan karon kallon da take yi mata ya so yayi yawa ko ma yayi. Suna a wannan halin ne Dr ta dauko labarin rayuwar waje wacce ta sha banban da Nigeria kasancewar gidan jaridar suna tattauna abun da ya shafi Africa ne, yadda ake bin doka da order da kuma yadda komai yake a tsare can take ta ba su labari, can jefi Maleek yake sako bakinsa yana fadar wani abun da ya sani a lokacin da Karatu ya kai shi kasar. Shigowa Abiey ne ya tsinke musu hirar waje da suke, annashuwar dake fuskarsa na farincikin ganin yar'uwarsa kuma macen da yake mata kallon uwa abokiyar shawara wacce ke share kukansa tun a wacan lokaci ya saka Ummi jindadi, domin bata da farinciki a yanzu sai an mijinta Abiey. Tsokanarta ya fara yi yana dariya sosai kamar ba shi ba, har buga kafa yake kasa tsabar nishadin da yake ji a yau. Sai da suka yi rabin hira sannan Juwairiyyya da Yesmin suka sauko suka gaishe shi domin ba su san shigowarsa har sai da Ummi ta kwalawa Namra kira. A bangaren ya cire babbar rigarsa

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login