Showing 75001 words to 78000 words out of 271643 words

Chapter 26 - Wani Gari Book 1 Complete Hausa Novel

fito da shirinta suka wuce tare Mahmood da be samu tsayawa ya karya ba a ranar, daman Abiey tuni ya fice daga gidan bayan sun yi sallama da Maleek da ya dawo bangaren Ummi a dazun da abubuwa marar dadi suka faru. Sai ya rage Nimra ce kadai a gidan, hakan ya bata damar shiga bangaren Abiey ta shiga har dakinsa tana bincike inda yaks aje abubuwansa ta har ta samu sa'ar gano inda keys din motar ta yake ta dauko ta fito waje ta bude motar tana duba ko'ina. Har da addu'a take Allah ya sa ta sarewar saboda ta farantawa Ameer rai, can kasan kujera ta hango abu mai kamar akwaiti da sauri ta dauka tana budewa sai ta yi arba da abun da ba dan ta ganta a hannunsa yana busa ba da ba zata iya kiransa da sarewa kai tsaye ba, saboda ya sabon samfur ne. Da sauri ta fito motar ta rufe ta maida key din inda ta dauko shi ta dawo dakinta ta dauki hoton sarewar ta turawa Ameer sannan ta boye box din a karkashin gadonta.



AMEER POV.

Ya aje wayar yana murmushi ya cigaba da saka maballan rigarsa.

“Good Girl yanzu sai zancen haduwa zan yi wannan wasan da kyau”

After ya gama sakawa ya sake daukar wayar ya mayar mata da amsa.

‘Idan ba zaki iya zuwa can ba, then mu hadu a Galadimawa inda muka taba zuwa it's a safe place babu wanda zai gan ki kuma yanzu nan zan tafi sai kin iso’

Tana gama rubuta mata amsar ya kashe data shi ya saka wayar aljihu ya dauki abubuwa da ya san zai bukata ya fice daga dakin. Sai da ya zabi motar da ta yi masa sannan ya saka kanwarsa ta dauko nasa key motar a bangaren mahaifinsa ya karba ya hau ya kama hanyar Galadimawa. Ya isa in time saboda yayi abun da ya saba wato gudu da mota, ya ki ya kunna data shi balle ya ga abun da Nimra zata fada masa so yake ya cilasta ta baro gidansu zuwa inda yake bukatar ganinta so that ya san idan ya fara tasiri a zuciyarta ko akasin haka, yadda ta nuna masa ba zata iya zuwa gurin da suka saba haduwa da farko ba ya nuna tana tsoron yan'gidansu sun ganta kenan kamar yadda ta fada masa cewar idan mahaifinta ko wani ya gani bata san iya hukunci da za'ayi mata. Yana zaune cikin motarsa ya hango yarinyar da suka yi fada a gurin aikin mahaifinsa an sauke ta a wata motar da bata gurin aikin ba, 206 Saurayi a ciki yana sanye da kananan kaya kamar yadda Ameer ma ya saka kananan kayan, ita kuma tana sanye da rigar gurin aikin sai skirt ta dora after dress sai mayafin rigar da ta yafa tana rataye da jakarta daya hannunta na rike da bakar farar ledar dake dauke da rubutun kamfanin. Bude motar yayi ya fito ya nufi inda take tana tafiyarta a hankali.

“Miye a cikin ledar nan?”

Ta tsaya sai ta juyo ta kalleshi kamar ba zata ce komai ganin shi ne, sai kuma ta daure ta ce.

“Abinci ne?”

“Hmmm-uhmm wato kin yi sa'a ba a koreki ba bayan fadan da kika yi da ni, and now sata kike mana a gurin ko?”

Kalmar sata ta bata mata rai, sai dai mai nema baya fushi kamar yadda Kakarta ta fada mata dole ta hakurewa wani abun.

“Aa ni ban taba sata ba, mai gurin ya amince mana mu rika diba idan ya rage ko kuma idan mun san babu shi a gida”

“Oh Really i will ake him then, but before that bari na fada miki wani abu karki sake saka rigar kamfaninmu kina yawo da ita samari na dauki kala kala kuna iskancinku idan an gani sai ace a karkashin mahaifina kike aiki, and consider yourself a matsayin korrriya a gurin nan”

Ta daka masa tsawa domin kalmar iskanci da ya jefeta da shi ya bata mata rai.

“Sai me? Idan ka koreni rai ka acire min? Kuma ni ba yar iska ba ce ban san miye iskanci ban hada hanya da shi ba, amman kai ka sanshi saboda aikinka ne abun da kake yi ne, kuma ka bakar shegiyar shinkafar ku nan ka dauka ka tafi da ita”

Ta jefa masa shimkafar, har ta juya ta fara tafiya sai kuma ta dawo ta iso har inda yake ta kama hannunsa yaja kamar wani yaro haka ya rika binta har cikin unguwar ta shiga da shi har cikin gidan ta tsaya da shi kofar dakin ta bude kofar dakin.

“Ga gidan mu nan ka ga dakin da nake rayuwa nan, idan ka iya ka kore ni a nan din ma, sannan ka raba ni da duniyar gaba daya, sai na san ka kai tsohon shege, idan baka gode ni'imar Allah ba zaka godewa zabarsa, ba dai ka zabi wulakanta bayinsa ba saboda ya daukaka ya baka abun da bayinsa suke nema a karkashinka? Ka ji tsoron karshenka”

Wadanda suke cikin gidan suka fito suna kallonta da shi, Mamanta ma ta fito da sauri tare da kakarta dake lullube da zane zata fita bara.

“Miya faru Humaira?”

Mamarta ta tambaya sai Humaira ta fashe da kuka ta shige falon ta bar shi a gurin tsaye. Kakarta ta taso ka iso inda yake tana kallon fuskarsa da wani irin kallo kamar zata cinye shi.

“Jika na, ka yi hakuri idan wani abun Humaira ta yi maka, kai namiji ne, karfi da zuciya da fushi ba daya ba, a inda ta nuna maka a nan muke rayu, bata da kowa sai Allah marainiya ce ubanta ya rasu kuma da aikinku da dogara da shi take biyan makaranta tana mana hidima har ta yi ma kanta wani lokacin, mahaifiyarta bata sana'ar komai ni kuma kakarta bara kawai na iya, dan Allah karka koreta karka mata wani abun ka yi jinkan na kasa da kai, duk wanda ya nema a gurinka lallai dan ya san kana da shi ne, ka fi karfinmu nesa ba kusa ba, amman karka bari sherin shaida da zuciya su rinjaye ka, ka yi hakuri dan Allah...”

Ta duka har kasa tana bashi hakuri idonta dake cike da hawaye suna kallon fuskarsa, ba shi kadai take gani ba zubun fuskar da tsarin hallitar da tsayin take ganin kamar na ďanta ďa ďaya tilo da ya rasu, Kamar har ta so ta yi yayi sai dai wannan ya fi ďanta manyan ido da kyau da fadin kirji. Baya baya yayi ba tare da yace komai ba ya juya ya fice daga gidan cikin rashin kuzari, yana jin wani abu marar dadi a ransa.



©Khadeeja Candy
©®Copyright
2023

*W_G -it's not free, pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith Bank, then send the evidence to 08036126660*

25


Cikin motarsa ya dawo ya zauna yana ta kallon mutanen dake wucewa, ya duba duba hannunsa daidai saitin inda ta rika wutsiyar hannun ta ja zuwa cikin gidansu. Isowar Nimra ya saka shi sauke gilashin motarsa yayi mata horn, sai ta fito motar Ummi ta nufo inda yake rike da Box din ta saka mask a fuskarta tare da katon bakin gilashi, bude motar ta yi ta shiga ta zauna ta cire mask din da glass.

“Na karya dokar da Abiey ya saka min, kuma na karya alkawarin da na yi ma Ummi”

Ya kalleta a lokacin da hankalinsa da kuma tunaninsa suka dawo kanta.

“Wace doka?”

“Na yi ma Ummi alkawarin ba zan sake haduwa da kai ba, ita ta bukaci haka kuma na yi mata, Abiey kuma yace ko sunanka kar ya sake jin a gurin mu, yanzu kuma na fito ba tare da sanin kowa ba na zo nan”

Ya taba baki.

“Just”

Ta kalleshi.

“Just ne kawai?”

“Yeah don't tell me this is the first time da kika yi breaking rules din gidanku, yanzu fa an waye ba komai zaka aikata ka bar iyayenka su sani ba like this”

Ya kwanta jikin kujerar da take ya sumbanci gefen bakinta.

“You can't tell them same one kissed you”

Ya rika hannunta ya murza a hankali.

“And you can't tell them someone hold your hand, akwai abubuwa da yawa ba zamu fadawa iyayeba amman muna aikatawa, an waye yanzu Nimra muna wani zamani ne da muka fi iyayenmu wayo da iya sirranta abu”

Rawa jikinta yake, ba rawa ta tsoro ko fargaba ba, rawa irin da macen da namiji be taba rika hannunta ba ya fara a yanzu, wani abun take jin mai kamar faduwar gaba tana ji tana gani numfashinta na son sarkewa, so take ya janye hannunta daga rikon da yayi mata domin har yanzu murza mata yatsun yake amman ta kasa. Kiss din da yayi mata ma ta aje shi a wani ma'auni na dabam. Ta kasa kallonsa sai yawo take da idonta a titi.

“Ga... Ga.. Sarew... War...”

Ta samu kuzarin mika mishi bayan ta yaki zuciyarta. Be saki hanninta ba sai ya saka dayan hannunsa ya karba yana hadawa da hannunta ya rike, sai kuma ya daga hannunta ya sumbanta.

“Na gode sosai sarewar tana da muhimmanci a gareni”

Wannan karon ka ta samu kuzarin fisge duka hannayenta.

“Wannan be dace ba Ameer haramun be”

Dariya ya saka mata yana mata kallon mamaki.

“Karki ce min baki taba yin saurayi ba, or baki taba rike hannun namiji ba ko kissed even slept with him?”

“Subhanallahi Wallahi ban taba ko daya ba, ban taba saurayi ba balle har na kai ga aikata abun da kake tunani”

“So you're still Virgin? ”

Ta dauke idonta tana kallon wani gurin.

“You miss alot, babbar yarinya kamar ke? Baki da kawaye ne? Ina kika yi rayuwa?”

Ta bude motar.

“Ya kamata na tafi kar wani ya dawo be same ni a gidan ba”

Hannunsa ya mika ya juyo fuskarta ya matso da ta shi yana kallon bakinta sai ta juya ya sake juyawa da ita wannan karon gaf da ita yake, har tana shakar numfashinsa.

“Taya zan yarda baki taba kissed wani namiji ba?”

“Saboda ban taba yi ba, kuma ba zan yi karya ba”

“Can you swear?”

“Wallahi ban taba yi ba Ameer”

“Idan kuma kin taba yi kika min karya Allah ya halakaki kamin ki isa gida kin yarda?”

“Na yarda”

Tana rufe baki ya saka bakinsa cikin nata, abun ka da wanda be saba ba sai ta kasa komai har ya gama yawo da halshensa a bakinta ya cire, a nan kam tsoro ya bayyana a idonta sosai kamar yadda ya bayyana a jikinta take rawa har yana iya gani, wannan kadai ya isa ya yarda cewar bata taba tarayya da wani ba.

“Ki aje mana wannan sirrin, saka min number wayarki zan kira ki anjima amman zaki min wani alkawari a duk lokacin da na bukaci ganinki zan ganki?”

Ya dauko wayarsa ya mika mata, ta karba ta saka mashi number, sannan ta juya zata sauka ya sake riko hannunta.

“Baki min alkawari ba”

“Zan duba”

“Ba zan ce dubawa ba ne, zance ake na rayuwata i can not breathe when you're not near idan kuma kin fison na rika zuwa gidan ku kai tsaye then fine zan dauki ko wane risk just to see you Nimra...”

Kallonsa take, da gaske so take ta gane idan kalaman da suke fitowa a bakinsa har a zuciyarsa suke, miyasa zai sauya mata a iya yau kadai? Ya sumbace ya fada nata ba zai iya numfashi idan bata kusa ba, ya rika hannunta kuma yayi mata godiya da kawo masa sarewar da ta yi. Ganin irin kallon da take masa ya saka shi cewa.

“Na san fada muke, amman dukan abun da kika ba ni na karba na karba ne saboda na yarda dake, and now na bukaci ganinki kawai ba dan ina son sarewar ba, na san hakan kadai zan miki ki yarda mu hadu, zuciyata taan samawa kanta abun da take so ne Nimra ba tare da duba matsayi ko gaba ba”

Mutumen da ke ta rigima da ita ya ki yarda ba da hadin bakinta aka shirya masa komai ba, mutumen da girma kai kadai ya isa ya hana shi yin godiya a gareta. Da gaske abun da yake fada haka ne har zuciyarsa? Ta janye hannunta ta sauka a motar.

“Zamu rika haduwa wani gurin ba gidan mu ba”

“Okay take care of yourself”

Ta juyo ta kalleshi sai yayi mata murmushi, wata kalmar bata sake fitowa bakinta ya nufi motar da ta zo da ita ta bude ta shiga. Har ta yi ma motar key ta hau titi be bar gurin ba kuma be fasa kallonta ba har sai da ya daina hangota. Tana tukin tana tunanin yadda zuciyarsa ta karaya da wuri haka, ya yarda da ita kenan? Ta kai hannu ta taba bakinta amaimakon ta ji haushin abun da yayi mata domin bata taba aikatawa sai ta yi murmushi tana jin wani irin kimarsa na karuwa a idonta.

“Is this the sight of love?”

Ta tambaye kanta, domin wani irin yanayi take ji na dabam tun farkon haduwarta da shi har zuwa yau da wani abun ya shiga tsakaninsu? So ne ya saka take ganin abun da ba daidai ba a daidai har take iya karya dokar gidansu data mahaifinta? Take iya kyale wanda ba muharraminta ba ya rika hannunta har ya sumbance ta? Wata kila shi ma son ne ya saka shi saurin yarda da ita, daman ance wanda be taba yi ba idan ya fara masa baya masa da sauki. Kamar wanda aka yi ma albishir da yafiya haka Nimra ta wuni da farinciki da annashuwa a ranta ba ma kamar lokacin da ya kirata yana ta kashe ta da kalamai duk kuwa da be furta mata cewar yana sonta ba, gaba daya sai ta manta da wata damuwa ta tattara rayuwarta da duk wani tunani nata ta maida a gurin Ameer cikin wuni daya ta canja kamar ba ita ba. Tunanin yadda zata yi da iyayenta idan ta kulla alakar soyayya da Ameer sam be zo mata a rai ba a lokacin saboda farinciki ya dauke mata hankali.



AMEER POV.

Yana isa gida wanka ne abun da ya fara yi, ya wanke sarewar tas sannan ya zo gaban madubi yana kallon yadda Allah ya tsara halittarsa da mazantaka aka jera masa six pack kamar shi yayi kansa.

“Yaushe na yi arha haka, i kiss Nimra i hold her hands”

Shi kansa ba zai iya fadan yadda kyamarsa ta boye kanta har ya iya Sumbanta Nimra kai tsaye ba, duk kuwa da yanayinta da jikinta be nuna bata kula da kanta ba and the most abun da ya ja hankalinsa fada masa cewar bata taba yin kiss ba, ya kuma yarda domin ya lura da yanayinta macen da bata taba kebewa da namiji ba tana da banbanci da wacce ta saba yi ko ta taba, ita ce mace ta biyu da yawun bakinsa ya taba kaiwa a bakin wata bayan Angel, ita ma kuma Angel ribantarsa ta yi da tsabtarta da kuma aske gashin kanta da tayi kamar yadda ya bukata bayan ta daukar masa alkawarin tsare kanta, shi kuma shaidan ya rinjaye shi har ya saka rike kansa, a duk lokacin da bukatar hakan ga taso masa baya cilastawa kansa hakura da abun da yake ganin yana da iko da halin yinsa akan me zai cutar da kansa then?

Ya tsuke baki, tunanin daukar fansa da son lalata rayuwar kanwar makiyinsa ya mantar da shi wani abu kyama, wata kila kuma ita din bata da kazanta shiyasa be ji hakan a lokacin da yayi unkurin karya tarbiyar da iyayenta suka bata. And this fitinanniyar yarinyar ta ja hannunsa har cikin kazamin gidansu be mata komai ba. Ya tuna irin kalaman da kakarta ta yi masa cewar ita marainiya ce kuma ta dogara da abun da take samu a gurin aikin ne. Ya dan tabe baki zai kyale ta ne kawai saboda Kakarta da ta durkusa har kasa tana rokonsa ba dan haka ba sai ya koreta saboda ta masa tsiwa shi kuma baya son haka ya lura tana da zafin zuciya kamar shi. Tawul ya nufa ya dauka ya daura ya fada kan gado ya ya dauki wayarsa ya kira Nimra sai da ya fara tambayar ya ta isa gida da lafiyarta, sannan ya dora da wasu kalaman da zasu kashe mata jiki kuma ta yarda son ta yake ko da be furta ba.



UMMI POV.

Tana tsaye da mamaki take kallon matar dake goye da yaro a bayanta tana ta fada da Waira.

“Idan kika raba wannan auren ki yi yaya da ni? Ga yaya? Akan min zaki zo ki ce zaki shiga tsakanin masoya, a wace hujjar?”

Ganin Waira na kuka ta kasa cewa komai ya saka Ummi ta nufi matar ta fara bata hakuri.

“Dan Allah ki yi hakuri baiwar Allah bata sani ba ne”

Sai ta juyo ta yi kan Ummi da masifar.

“Ta sani mana, idan ta gani sai ta nuna? Haka kawai zan kyale ta? Hauka ake yi? Auren shekara da shekaru zata ce a rusa a rana daya? To ba zan dauki wannan ba, ni ina son mijina, yayanmu hudu da shi, ke ba auren kike ba da kike son shiga tsakanina da shi na aureshi tun da dadewa dan haka babu wanda ya isa ya raba wannan auren, ke da ake son a kashe ma komai ta dade sai sun kashe ki”

Jin matsifar ta yi yawa ya saka Ummi ta sake kallon babbar macen da zata yi sa'arta ta ce.

“Wai wayen wannan mijin na ki Baiwar Allah da kike ta wannan masifar?”

“Gashi can...”

Ta nuna bayan Ummi a tsawace tana zaro ido tsabar masifa, Ummi ta juya ta ga waye mijin kenan ta farka a firgice sakamakon taba ta da Mahmood yayi.

“Innalillahi wa'inna Ilaihiraji'un”

Ta fada tana mika sannan ta kalli Mahmood dake kallonta.

“Magana kike kina bachi lafiya?”

Juyawa ta yi ta karewa inda suke zaune kallo sai a yanzu ta yarda ba mafarki take ba, domin dan zaunawar da ta yi jiran a fito da Waira daga dakin hoto bachi mai nauyi ya dauke ta, kuma mafarki ya zo mata kamar a zahiri. Wacece wannan matar? Kuma waye mijin nata? Miyasa kuma take masifa da Waira shi ne abun da ya zo mata a rai.

“Are you okay ko kina jin wani

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login