Showing 102001 words to 105000 words out of 271643 words

Chapter 35 - Wani Gari Book 1 Complete Hausa Novel

ta Innalillahi Wa'inna Ilaihiraji'un, ki yi sallah ki fadawa Allah damuwarki ki roki sasauci da zabi na alheri, Abiey zai sauko amman dole ne a yanzu sai yayi fushi sosai kin ji”

A hankali ta daga kai tana jin kaunar Ummi a ranta da kuma tausayin kanta.

“Kalli yadda kika saka ni kuka ni da yar'uwarki, karki sake yin haka kin ji? Ke musulma mai tarbiya, na yardar ba ki watsar da tarbiyar da na baki ba, tun da har baki bashi mutuncin ba, yadda kika oya yakar zuciyarki ta hana ki aikata zina, ya kamata ki yake ta ta hana ki batawa iyayenki rai, domin bacin ran iyaye yana tare da fushin Allah, idan kika bata mana rai ko da kin gudu kin tafi wani gurin ke da ahi ba zaku taba ganin haske ba, amman idan kika bi komai a hankali sai a samu maslaha”

Ummi tana fadar tana shafa kanta, kamin ta kalli Namra ta ce.

“Je ki kira Maleek ya zo ya bata magani”

Namra ta share hawayenta ta mike tsaye ta fice daga falon zuwa gurin nemansa a wajen bangaren Ummi. Ummi ta kalli gefen kujerar da Waira ta boya ta ce.

“Baby Waira Yata fito mana me kike yi ma buya? Wa kike tsoro”

“Abiey...”

Ta fada daga can inda take boye.

“Abiey ya tafi bangarensa Umminki ce kadai a nan sai yar'uwarki Nimra fito”

Ta fara lekowa ta karewa falon kallo ta ga babu kowa sai Ummi da Nimra sannan ta fito da sauri ta nufi gurin Ummi ta zauna a kasa dayan side din da Nimra take zaune tana kallon Nimra da idonta yake rufe tana zubar da hawaye.

“Kalli wacce ta rasa iyaye da yan'uwa da abokai da gari, ta rasa abinci da masu jin kalar yarenta ta bata mutu ba ta rayu tare da mu, sai ke ce zaki mutu dan kin rasa saurayi? Karki bari shaidan ya sharin zuciya su rinjaye ki Nimra”

Nimra ta bude ido ta kalli Waira take leken fuskarta, murmushi karfin hali Nimra ta yi mata sai Waira ta saka hannu ta fara share mata hawayenta, ta mika hannunta ta kama hannun Nimra ta rike ba dan komai ba sai dan ta san abun da yake faruwa, ta kwanatar da kanta a jikin Ummi kamar yadda na Nimra yake kwance. Ummi ta girgiza kai tunanin Ameer da kalamansa sun hanata sukuni, furucinsa na cewar saboda be san dadin uwa ba shi ke nuna be san muhimmancinta ba ya matukar tsaya mata a rai. Me aka fada masa? Uwarsa ta mutu? Shigowar Maleek ya saka ta share hawayenta ta kalleshi sa'insar da sukayi a dazun da Ameer take ta gani a idonta.

“Treatment zaka mata ka bata maganin da ya kamata”

“Ban taba mata treatment ba”

“Ka fara daga yau, kuma ban ce ka fada mata ko da kalma matar dadi ba balle har hannunka ya sake kaiwa a jikinta, Namra rikata ku tafi dakinta ki hada mata ruwa ta gasa jikinta zan hada mata wani abun ci a yanzu”

Ummi ta karasa tana kallon Namra wacce ta amsa mata da kai ta rika yar'uwarta suka mike tsaye. Waira ta bude ido da sauri tana kallon Nimra.

“Ta sanshi i know him... Waira ta san shi ta gane shi ta san shi”

Haka take ta fada da sauri tana nuna Nimra, daga Ummi har Maleek dake tsaye ba su fahimci abun da take nufi ba, Ummi kuma bata da lokacin tsayawa ta fahimceta a yanzu balle har ta gyara mata abun da take furtawa. Da ido Maleek ya harare a tunaninsa zata fara ba bada labarin abun da ya faru a school dinsu ne a yau, sai ta yi tsit kamar bata gurin.

“Bari na je na siyo magani”

Maleek ya fada sannan ya juya ya koma ta kofar falon da ya shigo. Waira ta bi Nimra da kallo har sai da suka haye sama gaba daya sannan ta dauke idonta ta dawo da su gurin Ummi.

“Ummi...”

Ummi ta kalleta wasu hawayen suna tarar mata a ido.

“Ummi miyasa Ummi ba zata bari Nimra ta aure shi ba”

“Saboda wani abubuwa da yawa tashi ki je ki cire uniform dinki”

Ta tashi ta nufi upstarts, sai kuma ta juyo.

“Ummi... Meyasa Ummi ba zata fadawa Abiey tana son mijin Nimra ba?”

Ummi bata bi ta kan maganar ba, domin tana cikin damuwa a yanzu.

“Na ce ki tafi ki canja uniform dinki”

Waira ta juya ta karasa hayewa sama, Ummi kuma ta cire hijabinta ta kwanta akan kujera tana ta addu'ar samun saukin zuciya. Waira na shiga dakinta wanka ne abun da ta fara yi sannan ta fito ta saka wando da riga ta sauko kasa bata samu kowa a falon ba sai motsin da take ji a kitchen, hakan ya saka ta nufi kitchen kai tsaye ta leka sai ga ta samu Ummi a tsaye.

“Ummi ta canja”

Ta fada tana shafa tufafin jikinta, Ummi ta juyo ta kalleta tana jin kamar zuciyarta zata tsage.

“Ummi. Meyasa Ummi ba fada fadawa Abiey bata da lafiya?”

“Lafiyata kalau tafi falo ki zauna zan hada miki tea yanzu ke da Nimra”

A maimakon ta juya ta fita kamar yadda Ummi ta bukata sai ta rugo da gudu ta rumgume Ummi ta fashe da kuka.

“Waira tana son Ummi”

Ummi ta shafa bayanta..

“Ya isa, bana son jin kuka kowa a yanzu je ki zauna zan kawo miki tea kamin mai lessons dinki ya zo kin ji? Ni ma ina sonki”

Ba dan ta so ba ta bar jikin Ummi ta fito falo ta zauna ta takure guri daya kamar bakuwa, tana kallon Maleek ya shigo ya haura sama zuwa dakin Nimra, aka sake bude kofar Dr ta shigo tare da Jabir hankalinta a tashe.

“Ina Zahra take?”

Ummi na jin muryar Dr Zainab ta fito daga kitchen din ta nufota ta rumgume tana jin wani sanyi sanyi a ranta. Jabir kuma ya nufi Waira dake ta sharar kwalla.

“Waya taba ki?”

“Ummi zata mutu...”

Yayi saurin rufe mata baki, a zatonsa kuka da ta ga Ummi tana yi ne ya saka ta tsorata har take furta haka.

“Subhanallah, ki dina fadar hakan ba abubuwa ne akwai suka faru kuma komai zai wuce kinji?”

Ta girgiza kai ta fara magana da karfi cikin kuka.

“Ummi tana kuka, Ummi tana da ciwo Ummi zata mutu, Ummi ba zata fada ba, Ummi tana son mijin Nimra, Ummi ta haifi Mijin Nimra”

Ta ta saka dayan hannunta ta share hawayen fahimci abun da take nufi bata iya fadar da kyau ba hakan ya saka ta kalli Ummi dake kallonta ta ce

“Ummi talk, tell them ki fada musu”

Kusan kowa kallonta yake daga Maleek dake saukowa rike da syringe a hannunsa har Mahmood da ya turo kofar falon ya shigo da zimmar sanar mata mai lessons dinta ya zo, balle kuma Ummi data tsorota da abun da Waira take fada, Jabir kuma be fahimci zancen da kyau ba as well as Maleek sai dai kalmar Ummi zata mutu ta daga musu hankali, Dr Zainab ma bata fahimcin yaren nata ba.

“Me take fada ne? Ni ban fahimta ba”

Jabir ya tambaya yana kallon Ummi.

“Ummi tana da ciwo mai mutuwa Ummi zata mutu Waira tana son Ummi”

Ta sake fada tare da fashewa da wani irin kuka mai karfi, a wannan karon Mahmood ya fahimcin inda ta dosa, Maleek kuma ya shiga hudu sai idonsa suna akan mahaifiyarsa.

“Waira ki tafi dakinki yanzu nan?”

Ummi ta fada, sai Mahmood yayi karaf ya ce.

“Mai lessons dinta ya zo yanzu nan”

“Okay wuce ki dauko jakarki ki tafi gurin lessons dinki”

Ta sauka daga kan couch din ta nufi upstarts haka ta raba gefen Maleek da ya gagara saukowa ta wuce dakinta ta dauko jakarta ta sauko ta fice daga falon.

“Me yarinyar na yi take fada ne Zahra?”

Dr Zainab ta tambaya.

“Shirmenta ne mana, da ma kin tafi gurin Abiey kun tattauna zai fi”

Maleek ya sauko ya nufi kofa ya fice daga zuwa gurin motarsa ya bude ya dauko wata ledar sannan ya dawo ciki ya haura zuwa dakin Nimra zuciyarsa da tunani kala kala. Dr Zainab ta nufi hanyar da zata sadata da bangaren Abiey, Jabir da Mahmood kuma suka zauna a falon Mahmood na labarta masa abun da ya faru a game da Nimra da kuma rashin mutun Ameer da ya sani. Ummi kuma ta koma kitchen din ta cigaba da abun da take tana tunanin inda Waira ta samu wannan labarin, hausawa suka ce sawun giwa ya batar da na rakumi, gaba daya sai tunaninta ya koma gurin Waira.


WAIRA POV.

A inda suka saba zama su yi lessons ta zauna akan kujerar da aka siya mata da karamin tebur din da take dora littafan karatunta, dattijon da zai yi shekara 50 yana ta zuba mata karatu amman hankalinta baya guri, tunaninta ya tafi akan dalilin Ummi na boyewa kowa ciwonta da kuma burinta akan Ameer, a yanzu kuma ta rasa gane dalilinta na kin son auren Nimra da wanda take so, domin ta ga komai a madafar iliminta sai dai illar ce ta kasa gani har yanzu.

“Waira?”

Ta kalleshi da idanuwanta masu kamar na mage.

“Lafiya kike yau?”

Ta girgiza kai domin ya saba fahimtarta tun kamin ta fada masa komai, ita kuma bata boye masa damuwarta a duk zuwan da yake gidan, wannan ya saka take jindadin zuwansa fiye da zuwa makaranta da ake takura mata. Ya bar jikin allon ya dawo kusa da ita ta tsaya.

“Fada min meya faru yau kuma?”

“Ummi tana son Mijin Nimra, kuma Ummi tana da ciwo, kuma ciwon zai kasheta ta mutu kamar Waira, amman ba ta fada ba, Ya Maleek ya daki Nimra kuma Nimra tana son... ”

Ta kasa karawa domin bata rike sunansa ba saboda haka bata san yadda ta kwatanta shi ko ta kira shi ba, Dattijon yayi murmushi ya dauko kujerar ya dawo kusa da ita ta zauna.

“Ki daina damuwa da matsalar wasu, ke ma kina cikin taki matsalar ai, ki daina kuka haka nan kukanki yana saka ni jin babu dadi”

“Toh”

Ta amsa tana kallonsa idonta na sake cika da wasu hawayen. Ya saka hannunsa aljihu ya dauko apple ya mika mata sai ta karba ta rike, a can idan suna darasi take cin apple kullum idan ya bata yau kuma da take cikin kuka da bacin rai sai ta kasa ci ta rike Apple din kawai a hannu, mikewa yayi tsaye ya nufi jakarsa ya bude ya dauko farin zomo ya nufota da shi ya dora mata saman jiki sai ta saki apple din da sauri ta rike zomon.

“Neman wannan zomon ya saka ban zo jiya gurin darasinki ba, ina fatar kina son shi”

“Sosai sosai”

Ta rumgume shi a jikinta tana jin kamar beranta ne na baya data rasa.

“Thank You”

Murmushi da farincikin da ya gani a fuskarta wanda ya kawarda bakinciki da bacin ran da take ciki ne yafi komai faranta masa rai kuma daman abun da yake son gani kenan. Ta mike tsaye ta aje zomon zata rumgume shi sai yaja baya da sauri.

“Aa aa aa, dauki jakarki ki shiga ciki darasi ya kare sai gobe idan na dawo”

Ta juya ta dauki zomon da ya fara neman gurin boya tana dariya fararen hakoranta a waje kamar ba ita ba, ta dauki jakarta da dayan hannunta ta fito daga gurin ta nufi part din Ummi da gudunta, tsaye yayi yana kallonta da murmushi a fuskarsa har sai da ta fice sannan ya nufi jakarsa ya dauka ya fice daga gurin, har ya isa gate be daina waigen part din kamar ya san zata dawo ta daga masa hannu, sai gata ta fito daga part din tana masa waving hakoranta a waje. Daga inda yake ya daga mata hannu sannan ya fice yana tafiya kamar mai ciwon kafa.
34

Bayan ya wuce ta dawo cikin falon ta fara neman zomonta da ya bata daga inda ta aje shi.

“Uteee Teee Uteeee”

Kiransa take da yarenta kamar an fada mata yana jin abun da take fada, abun da bata taba yi a gidan ba wato magana da yarenta shiyasa har yanzu babu wanda ya san kalar yaren da take a gidan.

“Ukur tek fi, utee utee kat...”

Fada masa take idan ya fito zata ba shi abinci mai kyau mai dadi. Ta fara leken kasan kujerun dake falon sai ta hango inda yake boye jikin wata kafar kujera, rarrafe ta yi ta isa gurin ta kama shi ta fito tana dariya ranta fal da farincikin da ta manta when last ta yi murna na samuwar wani abu.

“Daga yau sunanka Zill”

Ta fada da yarenta sannan ta mike tsaye ta nufi hanyar Kitchen. Tana bada baya Maleek ya saukowa daga stairs din da yake tsaye ya nemi guri ya zauna da mamakin yaren da ya ji a bakin Waira.

Ita kan tana leka Kitchen din ta ga Hanne da Ummi a ciki sai ta ja ta tsaya ba tace komai ba.

“Me kike so Waira?”

“Barta ta dauki abun da take so, it's high time ace komai sai an yi mata, ita ma ya kamata ta fara mu'amalantarmu kar mar yan'uwanta”

Ummi ta fada tana juyowa ta kalleta, sai Waira ta lake kafada tana son yi kukan shagwaba.

“Waya baki zomo?”

Ummi na tambaya sai dariya ta biyo bayan kukan da Waira take son yi.

“Teacher....”

Ta amsa tana shafa shi.

“Ke kika ce masa kina so?”

Ta girgiza kai.

“No amman tana so”

“Ina so”

Ummi ta gyara mata.

“Ina so”

Ta sake fada.

“Ummin za ci abinci”

“To zo ki daukar masa”

Ta shiga cikin kitchen din ta nufi gurin da ake aje kayan marmari ta dauki kwatankwacin abin da ta san tana ci ta saka a plate. Hanne ta kalleta tana gyara tumatur ta ce.

“Zomo ya fi son giďa da salat ko karasss”

Waira ta kalli Ummi.

“Ummin zaki siya Karass, gida salak”

“Muna da karas a fridge ai sai dai a nemo giďa da salat, Hanne duba mana Fridge akwai karass ki dauko mata”

Hanne ta nufi inda Ummi ta fada ta bude ta dauko ledar karass biyu, domin Ummi tana sakawa a kullashi a leda kamar na siyarwa aje idan an antashi amfani sai dai a dauko kawai. Waira ta karba ta dora sannan ta fito falon hannunta rike da plate daya dayan kuma rike da zomo, wayo idonta ya fara yi tana kallon inda zata aje zomon be gudu ba, duk abun da take Maleek be kalli inda take ba. Takowa ta yi a hankali sautinsa ganin shi kadai ne a falon, kusan lokaci daya aka cire masa tsoronsa daman ta rage tsoronsa domin ya dan canja ba kamar da ba, dazun ma saboda ta ganshi da bulala ne ya saka ta tsorata.
Ta nufe shi ta aje plate din kasa ta kama zomon da hannu biyu ta dora masa saman jiki ba tare da tambayarsa zai rike mata ko akasin haka ba, da sauri ya dago yana kallonta irin lafiya kike?

“Kar ya gudu rike sosai da kyau”

Ganin zomon zai sauka jikinsa ya saka yayi saurin rikewa kamar yadda ta bukata.

“Good”

Ta masa thumb up, bata san baya son mace ta taba jikinsa ko ta rabe shi ba, domin bata taba rumgumarsa ko taba shi ta ga abun da yake damunsa ba, a iya tunaninta bashi da halin kirki ne a farkon zuwanta gidan, daga baya kuma ta ya sauko har yakan zauna ayi hira da shi sai ta fahimci ya jefar da wacan halin nasa ne marar kyau, yanzu ya shirya mu'amala da kowa.
Bata tare da tunanin komai ba ta juya ta koma kitchen ta dauko wuka da wani babban tray ta dawo inda yake zaune rike da zomon ta zauna a kasa ta fara yanka karass din tana yanka apple, shi dai kallonta kawai yake, he's feel something different about her, lokuta da dama tana masa abun da baya iya musa mata ko yi mata magana, not like other girls da zai iya kashewa ma idan suka masa haka, tun bayan marin da ya taba mata a karon farko da taba jikinsa be sake sha'awar kai hannunsa a jikinta da sunan duka ko hukuncin ba, a wacan karon ma da ta rika shi ya ji wani yanayi na dabam ba zai iya bayyana yadda yake ba, ba jindadi ba ne kuma ba na rashin dadin ba, wani abu ne da be taba jin irinsa ba a rayuwarsa yana ďaya daga cikin dalilin da ya haddasa masa daukewar numfashi na wucin gadi, wata kila saboda mace bata taba rumgumarsa ba ne, balle ya san ya dumin jikin mace yake idan ya gwaraya da na namiji duk da kasancewar a fusace ta hau stairs din a wacan lokacin bacin ran da be san na minene ba.

There is something special about her, her unique skin colar da gashinta da ya banbanta na kannensa, the way she talk idan ta kama dole iya zaman da ta yi a gidan na shekara daya ua fahimci tana da kiyaye doka, domin duk wani abun da ta san za a mata fada idan ta aikata tana kokarin kiyayewa musamman a abun da ya shafe shi, bata cika magana ba hakan na matukar burgeshi da ita domin baya son yawan surutu tana da natsuwar da idan ba a kusa da Ummi ta zauna ba zata nemi bayan kujera ta boya. Yana fara kallon kyakkyawar hallitar da Allah yayi a fuskarta na dagon hanci da blue eyes ga karamin pink lips sai zuciyarsa ta buga da mugun karfi kamar zata fisgo ta fado kasa. This is first time da yake kallonta da wani irin kallo da be taba yi ma ya mace ba, kowane motsin da hannunta yake da na abun da take yankawa har zuwa zaman da ta yi da kuma daukar abun da ta yanka ta ci, even taunawar da take kallon yadda bakinta yake motsi yake.

“Waira...”

Ummi wanda ta fito daga kitchen ta yi tsaye cak tana kallon ikon Allah. Maleek da Waira suka kalli inda take, Maleek mamakin tsayuwarta a gurin yake ya manta da abun da yayi a yau sabon abu ne da be taba yi ba, Waira kuma jiran take ta ji abun da Ummi zata fada bayan kiran sunanta da ta yi. Ummi ta karaso gurin ta nuna zomon dake hannun Maleek, sai Maleek ya kalli zomon.

“Oh ta ba ni rikonsa ne

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login