Showing 48001 words to 51000 words out of 271643 words

Chapter 17 - Wani Gari Book 1 Complete Hausa Novel

kashi kashi kowa tufafinsa dabam, wani abun da ya bata tsoro kuma yadda suka tsareta wasu na kallonta wasu na damunta da magana wasu na rubutu, hankalinta be kara tashi ba sai da dayan likitan ya miko hannnunsa ya riko hannunta.

“Ahir hir Ahir verrr yat tour tour tor”

Ta fada da karfi ta fisge hannunta daga rikon da yayi mata, likitan nan ne dai na dazun da ya bata Apple, duk kirko kirko suka yi suna kallonta ba da farko kallon kurma suke mata ganin taki magana, a yanzu kuma da ta yi magana ta ba su mamaki, domin wani sabon yare suke ji a tare da ita.

“Kamar Fulatanci take Dr Shuraim”

Wanda aka kira da Dr ya juyo ya kalli dan'uwansa da mamaki.

“Ba fulatanci ne ba, fulatanci yarena ne da shi take yi da na ji”

“Kasan ance fulatancin ko wane gari ya banbanta da sauran”

“Yes, kalmomin suka banbanta amman muna gane yaren juna wannan ba fulatancin ba ne, wani yaren ne na dabam”

Ya sake juyawa ya kalleta da manyan idonsa masu matukar daukar hankali, cikin kwayar idonta yake kallo.

“Anene fulfulde?”

Ta rumgume kanta tana kara matsawa baya. Be sake ce mata komai ba sai ya dauki abincin ya matsar mata da shi hannu ta saka ta buge abincin ya zube kasa ta dauki Apple din kadai ta rike.

“Waya bata Apple”

Ya tambaya yana kallon Nurses din dake bayansa, suma kallon mamaki suke masa domin sun san shi ya bata apple din da kansa.

“Dazun kai ka bata da kanka”

With confused ya kalli wacce tayi maganar, baya son musu surutu ma bangarensa ba ne balle kuma musu, hakan ya saka be damu ya musa musu ba, all what he thought is wani likitan ne ya bata suka yi zaton shi ne. Matsawa yayi kusa da ita sai ta matsa baya kamar zata shige jikin ginin tana masa kallon tsoro, hannunsa ya kai ya rika kanta yana kokarin duba idonta dake kama da nashi tsabar farin idon, sai dai nata gwaiduwar ciki blue ce tsabanin tashi da take baka wulik, kallo daya zaka mata ka fahimcin kyaunta ya banbanta da na sauran mata sa'aninta duk kuwa da kasancewar dattin dake jikinta. Tana da masifar kyau ga kirjinta a cike daidai har ya fi na sa'arta domin rigar saƙin dake jikinta ta fata tana fito da ainahin zatin kyaunta ne. Be ankaro ba ta dantsara masa cizo a hannu da mugun karfi, abun ka da wanda ya dade be ci nama ba hausawa suka ce masa maye wai idan yayi cizo ba a warkewa da wuri, idan kuma yayi magana sai ta kama Mutun lol, tana dota hakoranta a hannunsa kamar reza haka hakoran suka yaga rigar hannunsa suka shiga har cikin naman hannunsa sai wani zafi yaji kamar an yanke shi da wuka a take jini ya fito sai dai ba mai yawa ba, cikin zafin nama ya fisge hannunsa yana zaro ido

“Easy Girl...”

Da sauri Police din da suka zo daukar report dinta suka jo kanta da gudu suka riketa dayan ya juyarda hannunta da karfi zan lankwasa sai Likitan yayi saurin dakatar da shi ganin yana kokarin yi mata illa kamar ya samu katon namiji.

“Nonono she's just a girl karka ji mata mana”

“Ai kara ayi mata haka, what is akwai dafi a bakinta fa? Ba mu san waye ita ba”

Ya fada yana kara matseta.

“Saketa dan Allah ta tsorata ne tana zaton zan mata wani abun ne”

Ya saketa kamar yadda Dr Shuraim ya bukata, sai ta rumgume hannayen nata m har da mai ciwon.

Dr Shuraim ya fice gurin rike da hannunsa har lokacin ciwo yake ji a  iz  sosai, kamin ya karasa Office dinsu na Likito ya cire safar hannun ya jafa a gurin da aka tana da domin zuba shara, bathroom 2(8 ya fara shiga ya wanke hannunsa sannan ya fito ya dauki audiga ya saka a gurin ya goge, sannan ya cire labcoat din dake jikinsa ya aje ya ciro wayarsa dake ringing ganin mai kiran ya saka shi murmushi.

“Hey Baby Girl”

“Ruhul Kal ya kake ya aiki?”

“Ina lafiya fatar ke ma haka kike?”

“Nima haka, ya Katsina”

“Katsina na nan sai zafin kamar za a kama da wuta”

“Mu kuwa ruwa ake mana yanzu, wani guri na samu na fake ma”

“Daman ku yan Abuja kun fi kowa zama yan gayu, fatar dai ruwan be taba min ke ba”

“Ya jika ni kadan”

“Da ace zan ga ruwan an kuwa da na masa duka”

Ta kyalkyale da dariya, shi kuma yayi murmushin da ya bayyana fararen hakoransa da suka haska bakar fatar jikinsa mai kyau da sheki.

“Take care of yourself zan kiraki idan na bar gurin aiki”

“Toh I love you”

“I love more and more and more Baby girl”

Ya sauke wayar, sannan ya fice daga gurin, dakin da ake aje majiyanta ya sake komawa sai ya samu har lokacin suna nan tsaye akan yarinyar yanzu ma har an samu karin wasu mutane dake kallonta a cikin masu jinya.

“Wannan ai zaku tsoratata ne, please kowa ya koma gurinsa”

Kowa ya wuce ban da police din da suke zon tirsasa ta tayi magana.

“Ba zata iya magana a yanzu ba, a yadda na fahimta ko tayi magana ba zai amfanar ku komai ba, domin ba ta jin yarenku inda ba ta yi hakan da gangan ba, kai kana duba jikinta da yanayin tufafinta kasan ba ta jin yarenmu”

“Amman Doctor zai dauke ta lokaci kamin ta warke?”

“Eh ya danganta da kalar majicin daya cije ta, zata iya sati ko sama da haka a ka'ida dai ana son ta samu kulawa mai kyau na wata daya idan abun yana da karfi wata shida shi ne zata warke gaba daya”

“Okay mun gode, dan sandanmu daya zai tsaya tare da ita saboda bada tsaro da kuma kula da ita, ni kuma zan je na sanar da halin da take ciki”

Da kai ya amsa masa, sannan ya mika masa hannun suka gaisa su biyu suka fice dayan ma da aka bari domin bata tsaro fita yayi saboda ganin Likitan ya zauna a saman gadon da take zaune. Kallonta Dr Shuraim yake yana son fahimtar wasu abubuwa a tattare da ita.

“Baby Girl...”

Ya kirata da irin sunan da yake kiran Babensa, domin be san sunanta balle ya kirata da shi.
Ya leka kasan fuskarta sai ta boye kanta.

“Akwai bukatar ki tsabtace jikinki ki ci abinci a baki magani”

Kamar wacce ta san abun da yake fada sai ta lake kafada daga boyen da take ta fashe da kuka. Da kamar mamaki ya ke kallonta.

“Kina jin yarena?”

Nan ma ta lake kafadar.

“Wane yare kike ji?”

Nan ma ta sake yin abun da ta yi dazu, sai ya fahimci bata son yayi mata magana ne.

“Okay Baby Girl zan barki ki huta”

Ya mike tsaye sai ta dago kanta ta kai apple din hannunta a baki ta fara ci, still tana kuka kamar wata shagwababbiya. Shi dai be sake ce mata komai ba ya fice.




AMEER POV.

Fitar Ameer da kamar minti biyar da fitar Ameer Daddy ya kira Momy sai a lokacin yake fada mata abun da ya faru, da kuma response din Ameer akan cewar shi be san da labarin yarinyar ba.

“Wata kila da gaske ne, kasan Ameer baya tsoron amsa laifi idan ya aikata kamar yadda ya amsa maka cewar ya karbi motar”

Ajiyar zuciya ya sauke mai dauke da damuwa.

“Ina fatar haka, sai dai ina jin kamar ba yarda da shi ba, kwana biyun nan abun da Ameer yake ya fi karfin na baya”

“Jarabawa ce, dole hakuri zamu yi muna masa addu'a har Allah ya shiryar da shi, kuma ni ina ganin kamar ayi masa aure a zai saka ya natsu”

“Tun da nake da Ameer be taba min zancen soyayyar ba, gaba daya mata basa gabansa shiyasa na sha mamaki lokacin da yake fadar akwai wata yarinyar shi har suka samu matsala da abokinsa”

“Kai mahaifine ai, zaka iya zaunar da shi ka nuna masa inda kuskurensa yake, idan ya manta karatun sai ka tusa masa, yaran yanzu sai da haka, kuma duk wata lalace da kake ganin Ameer yayi laifinka ne, sam baka yarda ayi masa magana idan yayi kuskure”

“Akwai yara da yawa da suka tashi a cikin gatan irin na Ameer, amman basa yin abun da yake yi, zai fi kyau mu dora abun a babin kaddara Allah ya hukunta kawai”

“Toh Allah ya shirya mana, amman gaskiya a maida hankali gurin yi masa aure kasan aure yana natsar da Mutum kuma idan an tashi kar a nema masa yar Babban Mutun domin ba ko wace mace ce zata iya zama da shi ba, sai dai a nema masa mai hakuri wanda zata iya bin halinsa”

“Idan kuma yana da wanda yake so fa?”

“Shikenan ta kwana gidan sauki, sai a aura masa daman ai ya kai munzalin auren kuma Allah ya hore komai”

“Nima kuma shekaru suna ja, ina da burin ganin haka kamin ta Allah ta kasance”

Furucin da Daddy yayi sam be yi mata dadi ba, hakan ya saka bata sake cewa komai ababin maganar ba.

“Zan aje waya, saboda ina shirya abincin rana”

Yayi murmushi ya sauke wayar, sannan ya sake kiran CP, duk wani abun da za ayi a kashe maganar Daddy yayi domin baya son damuwa a yanzu kamar yadda likitansa ya tabbatar masa.


Jikin Motar Momy ya jingina thinking of din yarinyar ta mutu yadda zai bata ma Maleek da kanwarsa suna, a yanzu din ma tunanin yadda zai yi amfani da wannan damar ya taba martabar gidansu Maleek yake, he just wants to take revenge shi dai zuciyarsa suna masa take Maleek yayi masa Zagon Kasa, ya bude motar ya shiga yayi mata key jin kamar yana marmarin gurin da suka saba zama da abokansa ya saka shi nufar wani gurin shakatarwar na dabam, domin baya son ya sake shiga safgarsu tun bayan wulakancin da suka masa na zabar Maleek su barshi.




MALEEK POV.

Babu wanda yace Uffan a cikinsu bayan Abiey ya gama labarta cewar Ameer yace shi be san yarinyar ba be san inda ta fito ba kuma ba shi da alaka da ita.

“Amman karyar yake yi yana son ya kulla mana wani abun ne kawai”

Namra ta fada cikin jin haushi domin ji take kamar ace yana gabanta ta kwada masa mari. Ummi ta kalleta a hankali jin yadda take magana da zafin rai sai dai bata ce komai ba ta mai da kanta kasa tana jin zuciyarta ba dadi. Maleek ya saka hanayensa aljihu

“Wata kila kuma gaskiya ya fada, domin na san waye Ameer baya shakar ya amsa laifi komai girmansa matukar ya aikata zai ce shi yayi, idan har be amsa ba to be aikata din ba ne”

Namra ta girgiza kai.

“To waya aikata? Waye zai yi hakan bayan shi? Ko da ma ace wani ne yayi ai shi ne sila, kai da Ummi kamar kuna son kare Ameer din nan makiyin mu ne fa”

Maleek ya nunata da yatsa.

“Don't you dare raise your voice on me, na ce be aikata ba and i meant it tun da ya amsa cewar ba shi ba ne ba shi din ne ba, beside ai yarinyar tana da baki sai ta fadi wanda ya dauko ta”

“CP yace yarinyar bata jin hausa, kuma bata iya turanci ayi communicate da ita ma ya zama aiki”

Cewar Abiey with curious face. Ummi ta kalli mijinta da fuskarta ta wadanda lafiya bata wadace su ba.

“Yarinyar tana Katsina ne?”

“Eh likitoci sun ce zata samu wata daya zuwa 6 kamin ta warke garau”

“We can stay with her a nan har ta samu sauki kuma ta iya fahimtar yarenmu ko kuma mu mu fahimcin nata, then sai a hadata da yan'uwanta”

Maleek ya karba mata.

“Shi ne akwai yafi daman police sun san da maganar in case of wani abun ya faru suna sane, tun da yarinyar bata da wanda zata zauna a gurin can KT din, maybe ma daga wata kasar aka satota aka samu motar a ajeye aka saka ta a ciki, mude Allah tana raye that's just it”

“Shi ne, tun da mace ce be kamata a barta a can ba, ba zata samu kula yadda ya kamata ba, kuma babu kowa a can tare da ita, ko ba komai mu muke da hakkin kula da ita saboda a motar Nimra aka ganta”

Ummi ta sake fada duk da ta san ba lallai ne Abiey ya yarda ya dauki shawarata a yanzu ba, Nimra kam bata ma falon domin ganin take kamar mahaifinta be bukatar ganinta a yanzu bayan duk abun da ta jefasu ciki, itama kanta tana kunyar hada ido da shi.

“Kar kuma mu aikata abun da zai zama mana na nadama daga baya! Kar ta zama mana cuta”

Abiey ya fada a nasa fahimtar kamar be kamata yarinyar ta zauna a gidan ba, domin mai son abin ka ya fika dabara.

“Ko da ta zo da wata muguwar manufa Allah ba zai barta ba, domin mu mun yi da niyar kwarai ne, kuma Allah yana kallon zuciyar kowa”

Wannan karon da gwarin guiwa Ummi take fadar haka, Mahmood ma be ce komai ba domin shi dai baya goyon bayan kawota a gidan kamar yadda yake a zuciyar Namra.

“Idan ma haka ne, ai shi Mahaifin yaron ya fi cancanta ya rika saboda dansa ya jefar da motar”

“Idan kuma be rikata ba, sai mu rika rayuwa ce be kamata a salwantar da ita saboda jayayya ta son zuciya ba, In Shaa Allah babu wata matsala da zata faru”

Ummi ta amsawa Abiey da yayi maganar with full confidence.






©Khadeeja Candy
©®Copyright
2023
©KHADEEJA CANDY 17


Tun a jiya da ya gama aikinsa ya bar asibitin be sake shigowa ba sai washe gari, yanayin aikin da ya tarar a office na duba patient ya saka be bi ta kan patient din suke kwance ba, sai abokin aikinsa ne yayi da zimmar shi zai duba su da rana idan zai fice. Misalin karfe daya da yan mintuna ya tashi aikin, sai dai be dauki komai nasa ba ya fita yayi Sallah a Masallacin, sannan ya dawo Office din ya bude akwatinsa ya dauki Stethoscope tare da wasu files ta saka Lab Coat ya fice, ya dade yana magana da wani abokinsa da ya tarar a ward din yana hira da nurse, tattauna suke akan zaben da za a gabatar na Nigeria da kuma wanda suke ganin idan aka zaba zai kawo canjin da sauyi a Nigeria. Safar hannu ya fara sakawa, Nurse din da suke duty suka rufa masa baya su biyu domin gabatar da na su aikin. Daya bayan daya ya rika bi yana duba mutane kamin ya kawo gurin yarinyar da ya duba jiya, gaba daya gadonta a zagaye yake an rufe shi da curtains din da ake rufe gadon marasa lafiya, yana daga curtains din Nurse din dake gefensa ta ce.

“Yarinyar fa ina tunanin kamar bata da hankali, tun jiya bata barin kowa ya taba ta kuma ta koma karkashin Bed din sai kuka take Halima tace min ko bachi bata yi sai ta leko sai ta koma ta boya”

Shiga yayi ya leka karkashin gadon sai ya hangota ta cunkushe guri daya ta rumgume hannunta mai ciwo. Hannunsa ya saka aljihu ya ciro wayarsa ya kunna flashlight dinsa ya haska ta sai ta yi saurin rufe idonta domin hasken yayi mata yawa, tun da take a rayuwarta bata taba ganin hasken gulub ko na fitilar hannu ba, iyakar su hasken aci balbal ko na wutar itace ko ta kara. Nurse din zata yi magana sai ya daga mata hannu ya kashe fitilar ya mika mata hannunsa.

“Baby girl zo nan”

Kin kallonsa ta yi balle ma ta mika masa hannun, mikewa yayi tsaye ya ciro kudi aljihunsa ya fita daga gurin ya aiki daya daga cikin masu sharar gurin ta siyo masa apple da ruwa.

“Tun jiya bata ci abinci ba, kuma aka rasa wanda zai kula da haka?”

“An kula fa masu jinya sun bata abinci ko dazun, amman ba ta ci ba ruwan kawai ta sha, kuma ta ki fitowa a kasan gadon”

“Police din jiya ba su dawo ba?”

“Bana jin sun dawo, shi ma wanda aka bari nan ba a nan ya kwana ba kuma be dawo ba, da sun dawo da mun samu labari kuma babu wanda ya zo dubata, ni ina ganin kamata yayi ace sun dauki hotonta sun saka a Internet ko Allah zai saka a dace da yan'uwanta”

Dr Shuraim dai be sake cewa komai ba, ya cigaba da duba masara lafiyar da suke gabanta, har sai ya gama sannan ya karbi aikan da yayi ma mai share sharen Asibitin, son ganin yadda zata kaya ya saka suka biyo bayansa har da wace ya aikan. Dukawa yayi ya lekata tana ganin fuskarsa sai ta yi saurin rufe ido. Sabuwar takardar ya karba ya dora mata apple din akai ya tura mata, sannan ya aje ruwa ya dauke kansa. Be yi zaton zata yi saurin aminta ta taba ba, sai gata ta miko hannu ta dauki Apple daya, ta fara ci da sauri, ko tsayawa bata yi ta tauna da shi da kyau take hadewa tsabar yunwar da take ji, ta sake miko hannu ta dauki na biyu ta cinye ta dauki na uku har ta cinye Apple din guda uku sannan ta miko hannu ta dauko gorar ruwan, murda ta yi sai ta ji mabudin da karfi ba kamar na dazun da aka bata ba, hakan ya saka ta turo gorar waje, Dr na ganin haka sai ya dauki gorar ya bude mata ya sake ajewa, sai gashi ta ziro hannu ta dauka ta sha ta turo masa rabi. A nan ya lekata sai ta sako masa ido tana jin sake jiki da shi ba kamar sauran da take ganinsu kamar dodo ba.

“Baby Girl zo nan”

Ya mika mata hannu, kalmar Baby Girl ya zauna a kanta, tun a jiya da ya furta mata ba kalmar kawai ba, har da wasu maganganu da aka yi ta dauki wadanda ake yawan furtawa duk kuwa da kasancewar bata san ma'anarsu ba. Kallon hannunsa dake sanye da safa take kamar mai tunanin zuwa, ganin hakan ya saka ya dawo ta hannu ya cire safa daman

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login