Showing 126001 words to 129000 words out of 271643 words
Chapter 43 - Wani Gari Book 1 Complete Hausa Novel
da gorar ruwa sai ta tsaya jikin kofar. Da ido ya tambaye ta lafiya sai ta turo baki a shagwabe ta fara magana idonta har wani ruwa ruwan kwalla suke yana ce mata tak zata fara amayar masa da hawayenta
“Zan sha tea, ko cake ko a soya min arish ina jin yunwa”
Be ce mata komai ba, ya aje gorar ruwan ya nufi inda mug suke ya dauka ya hada mata tea iya yadda ya fahimci Ummi na hada mata, ya aje ba tare da yace mata ta zo ta dauka ba. Ita ma kuma kamar ta san ba zai ce ta zo ta dauka din ba sai ta nufi inda mug din yake ta saka hannu biyu ta dauka, ta fito Kitchen din ta dawo falo ta zauna tana son tea din zafi da tiririn da yake ba zai bari ba haka ta rumgume mug din tana kallon tea. Maleek ya fito daga kitchen din yana amsa wayar Abokinsa Abdull, yanayin yadda yake amsawar sai yayi mata kamar da Shuraim yake waya da sauri ta aje tea hannunta ta nufi inda yake tsaye rike da kujerar dinning ta tsaya tana kallonsa.
“Sulem? Sulem?”
Ya girgiza mata kaiwa, sai zuciyata ta raya mata me zata yi idan ba kuka ba, a sake ta fara aikin hawaye.
“Ba Suleem ba ne”
Ya fada bayan ya gama amsa wayar.
“Kirashi, ki kara shi”
“Ya za'ayi na kira shi? Ni ban da number shi, miye hadi da shi ma?”
“Akwai”
“Babu”
Ya juyo ta dawo hau kan kujera ta kwanta ya takure kanta. He just don't know why ya kasa dauke idonsa daga barin kallonta, and yana jin wani abu kamar ba dadi a takurawa kanta da kwantawa kan kujerar da ta yi, sai dai ba zai yi magana ba ko da kuwa zata shekara a haka. Bata dago ba sai da Jabir ya shigo shigo falon tana ganinsa ta tashi zaune da sauri kamar daman shigowarsa take jira.
“Waira bachi kike yi?”
Ta girgiza kai, sai ya sakar mata murmushi.
“Miye na sad face? Ko fada ka yi mata?”
Ya karasa yana kallon Maleek, Maleek be ji zai iya amsa masa dan haka ya maida kansa kan wayarsa dake hannunsa.
“Ta so muje ki raka ni gari”
Ta mike tsaye da sauri ta nufi inda yake.
“Ba a fita da ita, idan ka ga ta fita sai idan makaranta zata je, Ummi bata son a fita da ita”
“Idan ta zo ka ce mata ni na fita da ita ba wani bako ba”
Jabir ya kama hannunta ya juya da ita zata fice, har Maleek ya unkuro kamar ya yace baki sha tea ba Waira sai kuma wata zuciyar ta hana shi, but he don't know why kawai baya jin natsuwa da fitar da Jabir zai yi da ita.
41
MALEEK POV.
Gaban windows din falon ya isa ya faga curtains din yana kallon Jabir da ya budewa Waira gabam gaba ya shiga ya zauna tana share hawaye, ya rufe mata sannan ya zagaya ya shiga mazaunin tuki ya murza key din motar. Sai da Maleek ya ga fitarsu sannan ya saki curtains din ya nufi hanyar dakinsa. Ya san karya ya fada cewar Ummi bata bari a fita da Waira kuma ba zai iya fadar dalilinsa na yin karyar ba, shi dai be tana gwada fita da ita ba, haka ma Mahmood da Namra, Ummi kuma ba fita take irin haka nan ba, wani lokacin ko da zata fita Waira tana makaranta ko ana mata lessons, ko tana bachi, sai dai a yadda ya lura Ummi bata damuwa da rashin fitarta dan haka ya fahimci cewar bata son a fita da ita ba dan ta fada masa ba. Ya tura kofar dakinsa ya shiga, abu daya ya fado masa a rai wato bude jakar da ya dauko a dakin Ummi domin sanin me ke ciki, daman irin wannan lokacin yake so, da babu kowa a gidan babu mai takura masa.
Sai dai be natsu da hakan ba har sai da sakawa kofar key, sannan ya nufi closet dinsa ya dauko jakar. Be takurawa kansa sai ya bude key din ba sai ya saka reza ya yanka saman jakar, ya san he most explain idan yaje maida mata jakarta, but for now yana son sanin me ke cikin jakar da har Ummi ta saka shi a cikin akwai ta dora masa kaya kuma ta rufe a wardrobe dinta. Ya bi duk takardunta ya duba be ga abun da yake nema ba, domin be ga wani abu daya shafi ciwonta ba, shi kuma zuciyarsa ta kasa natsuwa da zancen da Waira ta yi musu cewar tana da ciwo da zai kasheta. Saman jakar ya yanka ya bude saboda zip din yayi tauri, takardar ya tarar ya fara cin karo da su as he expected daman ya san Ummi ba zata yi ma kudin wannan mugun boyon ba, domin ba su barawo a gidan. Cikin wani yanayi na kamar nadamar ya saka hannu ya dauko takardun ya fara dubawa, each and every paper da file da ya ci karo da su na rashin lafiyartar ne, stage din da ciwonta yake da kuma dokokin da likitoci suka bata. Tashin hankali ba a sa maka rana inji bahaushe, Maleek ya mike tsaye da sauri yana duba takardar cikin matukar tashin hankali da rudani.
“Ummi.... How.... How....”
Ya furta murzar na karkarwa har hakoransa na son haduwa da juna, taya Ummi zata boye babba abu kamar wannan? Abiey ya sani? Kowa ya sani? Maybe shi saboda ba shi da kusanci da ita ne ya saka be sani ba.
“Innalillahi wa'inna Ilaihiraji'un”
Zuciyarsa ta kusanto masa da abun da bakinsa zai furta kwakwalwarsa ta samu natsuwa. And now ya fahimci gaskiya Waira take fada cewar ita da Ummi duk suna jiran mutuwa ne, babu abun da ya fi ba shi mamaki kamar boye ciwon da Ummi ta yi miye manufar yin haka? Ya sake daukar wata takardar yana dubawa, sai da yayi gaske sannan zuciyarsa ta raya masa gaskiya yake gani ba karya ba, and the most painful part is ya sa there is currently no cure for multiple myeloma, but treatment is available, ga wanda cancer dinsa ta kai stage 3. Ya lumshe idonsa da suka ki bashi hadin kai, hakan kuma be hana hawayensa saukowa ba duk kuwa da irin kokarin da yayi na hana kansa kuka.
“Me zai saka ki boye wannan babban almari Ummi? Why?”
Damuwarsa a yanzu is tana shan maganin? Tana ganin likita akai akai? Karar wayarsa ne ya katse masa tunanin da yake, sai da ya share hawayensa sannan ya bude idon ya saka hannunsa aljihu ya ciro wayar. Kanensa ne Mahmood mai kira, and yes he need someone to talk to, hakan ya saka shi picking calls din.
“Maleek na ga motarka a waje, please come out ina Garden akwai abun da nake son mu yi magana da kai”
“Okay”
Ya maida wayar aljihunsa ya riko takardar da yake son nunawa dan'uwansa ya nufi kofar dakin ya bude, fitowarsa ta yi daidai da hawan Ummi stairs din, kallonta yayi ita ma ta kalleshi sai ta dauke kai ta nufi dakinta ta bude ta shiga. Be yi kasa a guiwa ba ya bi abun da zuciyarsa ta raya masa na bin bayan Ummi ta tura kofar dakin ya shiga sai ta jiyo rike da mayafinta ta kalleshi. Rauni, tausayi, da losing hope su ta gani shimfide a fuskar danta a lokacin da ya tunkaro inda take rike da takardun da bata gama tantance na miye ba domin fararen takardu ne da bakin rubutu a jiki ba file ba balle ta yi saurin ganewa.
Wani yanayi da ta dade tana sakashi a mafarkinta, ta dade tana jira zuwansa, take ta fatan ganin zuwan ajalinta. Shi ya sameta a lokaci da ranar da bata yi tsammani ba, wata hug daga ďanta Maleek, a lokacin da ya karasa kusa da ita sai ya rumgumeta ya lumshe ido jikinsa na rawa, irin na wanda be taba rumgumar mace ba, duk gurin da wata kofa ta gashi take a jikinsa sai da ya ji ana tsikara masa allura, hawaye ne masu tsananin zafi suke sauko masa. Zuwan abun da baka yi tsammani a lokacin ba, da kuma tunanin dalili shi ya hana Ummi yin wani kwarran motsi, sai ta tsaya a gurin kamar ice.
“Ummi dan me zaki boye mai muhimmanci haka?”
Ta lumshe sai hawaye suka kwankwaso mata kofa, ta daga hannayenta ta rumgume danta, a tunaninta yana magana ne akan Maleek.
“Miye hujjarki na boyewa? Mu kika boyewa ko har da Abiey? Ko kuma ni ne kawai ban sani ba saboda ba ni da kusanci da ke?”
Ya dago daga jikinta sai ta zauna gefen gado tana hawaye, shi kuma ya zube kasan guiwowyinsa rike da takardun, cikin fargaba da wani yanayi mai kama da firgici ta mika hannu ta karbi takardun tana dubawa sai gabanta ya fadi, tashin hankalinta da damuwa suka karu, abubuwa biyu za su zo ma iyalinta a lokaci daya.
“Ina ka samu wannan Maleek”
“A cikin jakarki, zuciyata ta kasa samun natsuwa tun daga lokacin da Waira ta furta cewar kina ciwo kuma zaki mutu, tun a ranar babu ranar da bana bincike a dakinki, kawai so nake na samu natsuwa ashe wani karin tashin hankalin ne zan tarar, for how long zaki yi ta boye mana wannan Ummi?”
Ta saka hannunta biyu ta rika fuskarsa kuka yake sosai kamar wani karamin yaro.
“Ko wane bawa da irin yadda Allah yake halittarsa da kuma kalar kabubalen da ake aiko masa, i face alot of challenges tun kurciyata har zuwa girma, bana so yayana ko mijina ya fuskanci ko daya, akwai abubuwa da yawa da za su rushe sanadiyar sanin cewar ina dauke da wannan cutar, ina da burika da yawa da nake son cikawa kamin cikar wa'adin da Allah ya dibar min, za ku hana ni yin abubuwa da yawa idan kuka sani, zaku saka ni yin abubuwa da ban yi niya ba, zan cilasta muku yin abubuwan da ba su kuke sha'awa ba, bana son damuwata ta saks shafar wani, bana son na sake saka kowa a damuwa, Maleek kai Musulmi ne, da ciwo ko ba ciwo idan ajali yayi kira dole aje, sanin wannan zai daga muku hankali har nima ku hana ni kwanciyar hankalin”
Ya saka hanayensa duka biyu ya dafe na mahaifiyarsa da suke kuncinsa ya runtse, tun da yake a rayuwarsa be taba shiga tashin hankalin da ya kasa rike kukansa ba irin wannan, ba taba fuskarta bakinciki kai tsaye irin yau ba, kamar zuciyarsa zata tsage gida biyu haka yake ji.
“Da ace na san da zuwan irin wannan ranar, da na roki Allah ya dauki rayuwata kamin yau. Ina kaunarki Ummi fiye da yadda kike tunani, ina son ki fiye da yadda nake son kaina, ki yafe min bakinciki da na yi ta saka ki Ummi”
Ya karasa yana kama hannayenta yayi ta sumbanta kamar marar hankali. Ganin kamar ya rikece ya saka ta kama kanshi ta dora a cinyarta ta sauke yataunta a saman kumatunshi.
“Na ji babu dadi a lokacin, amman zuwan Waira ya saka na fahimci ba a ra'ayin kanka kake min abun da kake yi ba, shiyasa na cilastawa mahaifinka kuma na jaddawa kaina neman maka magani a gurin Allah, na fadada addu'ar da nake har zuwa kasa mai tsarki, kuma na yi da magiya a gurin Ubangijina kalli yadda rayuwa ta zama a yanzu, ka canja Maleek, kana mu'alantarmu kamar ba kai ba, kasan tsawon lokacin da na dauka ina jiran ranar da zaka rumgume ni a matsayin uwa? Ina da burin ganin rayuwarka ta canja Maleek, da ace zan samu aron lokaci zan so samun ganin rayuwarka da iyalinka, kuma na ga hadinkanka ga yan'uwanka”
Ya dago ya kalleta bakinsa na rawa.
“Zaki gani Ummi, duk wani buri da kike da shi a duniya sai na cika miki shi Ummi i promise you, Innalillahi wa'inna Ilaihiraji'un”
Ya furta ya runtse ido yana girgiza kai, be tana jin tsoro irin na yanzu ba, domin abun biyu ya zame masa tsoron rasa uwa, da kuma tsoron rayuwar da zai yi da ita a yanzu a matsayin marar lafiya, ya san abun da zai yi da cinsa ne...
Wayarta dake jaka ta fara ringing, amman ta kasa motsawa daga inda take balle ta amsa, kusan sau uku ana kiran wayar bata amsa ba, hannunta hana kan danta tana shafa kansa hankalinma yana gurinsa. Suna a wannan halin Mahmood yayi knocking sannan ya turo kofar dakin ya shigo rike da wayarsa a hannu, jimm yayi jikin kofar kamar mai tsoron karasawa inda suke, tunaninsa be bashi komai ba sai abun da ya faru a dazun a game da Ameer. After taking deep breaths the ya motsa jiki ya shiga cikin dakin, hi pick up some papers da suke gurin, his mind ia tell him maybe evidence ne da za su tabbatar masa da abun da Ummi ta fadawa Ameer a dazun, domin shi ma dai yana jin kamar be gamsu ba, sai dai be mata maganar miyasa ta fadi hakan, da gaske ne ko kuma tana bawa Ameer din tsoro ne? Duk ba bukaci sani ba, abun da yayi shi ne shiru ya bude mata mota ta shigo ya kawota gida.
Sai dai abun da ya ci karo da shi sai ya kawar da wacan damuwar da tunanin gaskiya ne ko kishiyarta, hausawa suka ce sawun giwa ya take na rakumi, hankalinsa be tashi kamar na Maleek ba, domin shi ya san da matsalar, sai dai ganin matakin da take a yanzu ne. Juyawa yayi ya fice daga dakin rike da takardun ba tare ya fada mata abun fa ya kawo shi dakin ba. Kai tsaye bangaren mahaifinsa ya nufa a sitting room ya samu Abiey zaune cikin yanayi dake nuna ransa a bace yake.
“Ina take?”
“Abiey me yasa kake nemanta?”
“Idan zan ga matata sai ka ba ni izini ne?”
“No tun da naji ka ce ka kira sau uku bata daga ba...”
Be karasa ba Abiey ya tari numfashinsa.
“Kuma sai na kira ka na ca ka sanar da ita ina son ganinta ba”
“Ban fada mata ba saboda na tararda da ita a yanayin marar dadi, ban sani ba ko zaka yi mata magana akan abun ya faru ba ne?”
“Ta fada maka ne? Ko kuma an yi a gabanka?”
“An yi a gabana, and think this is more important da kiran da kake mata”
Ya mika masa papers din da suke hannunsa. Kallonsu Abiey yake kamin ya mika hannu ya karba... Kasa duba sauran yayi sai ya dago da sauri ya kalli Mahmood.
“What is this? Na waye?”
“Na Ummi ne, wannan ne abun da take boye mana na tsawon lokaci”
Ya amsa yana kawarda fuskarsa saboda hawayen dake cikin idonsa. A take zuba ya karyowa Abiey.
“Is this a joke?”
“Wa zai yi wasa da irin wannan ciwon mai tsada? Gaskiya ne Abiey”
Abiey ya shiga kansa daga goshi zuwa keya kamar mai alwala, ya mike tsaye ya nufi kofar fita sai kuma ya juyo ya dawo ya zauna jin kamar kafafuwanshi ba za su kai shi ba.
“A ina ka ga wannan?”
“A dakinta, she's with Maleek”
“Lahaula wala'kuwwati illa billah, Ya Ilahi”
“It so hard, why do we have to face this at this age?”
Mahmood ya fada cikin muryar kuka. Abiey ya kalleshi.
“Amman ka tabbatar ta kardunta ne?”
“Ga suna a jiki Abiey? Kuma ko bayan takardu ni na dade da sanin wannan ciwon saboda na tana tararda da ita a daki gashin kanta na cirewa, amman ta hanani fadawa kowa, ina ta ajiyar wannan abun a raina kuma yana ci na, ko wane duba idan na yi mata da ciwon nake mata shi”
Abiey yayi shiru yana tunawa lokutan da yake yawan ganin gashinta a gadonsa sai tace maskin dare ne yayi mata aski, the ciwo da take da yanayinta, da yawan bashi results din cewar Likitoci ba sun ce hawan jini ne sai Ulcer, sai a yanzu yake fahimtar he make a big mistake da ya fifita aikinsa da wasu abubuwa be tsaya ya kula da yadda matarsa take gudanar da rayuwarta, how comes yana mijinta ace be san ciwonta? Ta ya be fahimci halin da matarsa abar kauna take ciki ba tuntuni.
“Amman da ka sani ko a boye ne sai ka sanar min, akan me za a boye irin wannan ciwon? Ko hiv take dauke da shi ya kamata na sani balle leukemia kasan hadarin wannan cutar?”
“Ita ta bukaci kar na fadawa kowa, ni ma kuma sanin da na yi be wuce shekara da wani abu ba”
Abiey ya dafe kansa ya runtse ido yana jin duniyar na juya mishi. Can ya dago yayi ma Mahmood alamar ya fita da hannu.
AMEER POV.
Barin gidan yayi gaba daya bayan ya fito bangaren mahaifinsa, tunani kala kala akan maganar karshe da ya tarar Daddy na yi a waya, be gamsu da abun da ya ji yana fada ba. Ta dayan bangaren kuma zuciyarsa na ta son ya tattauna akan kalaman Ummi. Tuki yake yana tunanin kiran Hajiya Jamila duk kuwa da mahaifinsa ya ce kar ya kirata, but he need to ask her few questions, wata kila ita da Ummi sun san juna if not Ummi ba zata ambaci sunanta ba. Be ankara ba ya ji an bugu bayan motarsa da karfi a lokacin da ya karyo kwana, a take ya faka burki, daman mai nema a duhu balle an haska masa, da dai shi ya bugu motar wani ba zai tsaya ba, amman tun da tasa motar aka daka dole zai duba. A fusace ya bude motar ya fito wanda hakan yayi daidai da fitowar Jabir a tasa motar dake bayan ta Ameer.
“Sorry please amman kai ne mai laifi domin baka duba ba kawai ka hau babban titi”
“Oh Really saboda titin na Ubanka ne? Ni da motata zaka fada min ban duba titi ba? Baka tukin hankali ka yi shaye shayenka sannan ka fada min maganar banza....”
“Amman dai daga ganinka baka da tarbiya, daga magana sai ka fara zagin mutane...”
Jabir ya mayar masa a fusace yana nunashi. Ameer zai yi magana idonsa ya sauka akan Waira dake zaune gaban motar ta runtse ido sosai ta dafe kunnuwanta tun a lokacin da motarsu ta bugu da