Showing 219001 words to 222000 words out of 271643 words
Chapter 74 - Wani Gari Book 1 Complete Hausa Novel
mata tambayoyi sai ta fadi iya inda zata iya ganewa a kofar garinsu, daga inda ta fito zuwa gurin da ta hadu da Ameer, domin nan kadai gurin da ta sani, sauran abubuwan da suka faru bata iya labarta ko daya, kasancewar bata cikin hayyacinta aka kawo ta asibiti, daga Katsina zuwa Abuja ma bata san komai akai ba domin ko da aka iso tana bachi. Police biyu aka basu daga Abuja bayan an sanar musu wasu police biyu za su tare su daga Katsina tare da wanda ya san hanyar garin har zuwa inda Nuwaira zata gane.
Tun cikin dare Ummi ta shiryawa Nuwaira komai nata, ta zaunar da ita ta yi mata nasiha ta karfafa mata guiwar cigaba da rike addininta konda kuwa danginta za su nuna basa son addinin nata. Namra na tsaye jikin kofar dakin rumgume da hannayenta tana kallon Nuwaira dake ta rutsar kuka kamar an mata mota, shigowar Ameer ne ya saka Namra ta hanye daga jikin kofar ta karasa cikin dakin kusa da Ummi ta tsaya daga tsaye yayin da Ummi take zaune Nuwaira na jikinta sai kuka take, bata son rabuwa da Ummi kuma bata san me zata je ta tararda a garin ba, zancen sarautar yana nan ko kuma kasheta za'ayi? Ya za su karbeta idan suka ji ta canja addini da al'ada? Yana daga cikin abubuwan da suke matukar daga mata hankali.
“Ummi Daddy ya ce na zo da ita, yana son su yi bankwana”
Maganar Ameer yake yana kallon sahibarsa yadda take kuka abun ba dadi yake masa ba, shi ma tafiyarta domin kawai ta zame masa dole ne amman baya son rabuwa da ita ko na minti daya, idan kuma ya tuna da Maleek zata tafi sai ya ji hankalinsa ya tashi domin ganin yake kamar shakuwa ce zata kara shiga tsakaninsu. Nuwaira ta dago daga jikin Ummi ta kalleshi da jajayen idonta, hakan ya bashi karfin guiwar karasowa ya risina inda take zaune yana kallon fuskarta.
“Daddy na yake son ganinki, na fada masa gobe zaki tafi shi ne ya ce na zo da ke yanzu”
Ta mike tsaye sai ya ja baya domin bata dama ta taka, bandaki ta shiga ta wanke fuskarta sannan ta fito ta dauki daya daga cikin hijab din da Ummi ta bata ta saka daya, sannan ta kalli Ummi alamar tana neman izinin fita, Ummi ta daga mata kai
“Tafi”
Ta juya ta wuce gaba Ameer ya bita baya, Namra da Ummi suka bi Ameer da kallo ganin ya zama kamar wani jela.
“Ameer ya ba ni mamaki Ummi, kamar ba shi ba”
“Ciwon So kenan Namra, mai haukatar da mutum mai tsutsuta bawa ya firgita kwakwalwarsa, mai rufe idon mai yinsa ya saka yin abubuwan da ba su dace ba, i was in his shoes before shi ya saka na aikata duk abun da na aikata a yanzu, Abiey ma hauka ne kawai be yi ba a lokacin da ya rasa ni, amman Ciwon So ciwo ne mai wahalar magani”
Ummi was talking from experience tana kallon kofar dakin har lokacin. Wani bangare na yarenta kawai Namra ke iya ganewa domin ita ma ta ga zahiri a abun da ya faru da yar'uwarta, kuma ita tana cikin dakin so.
AMEER POV.
“Zaki yi ta yin kuka ne har hawayenki su kare Nuwaira?”
Ta dago ta kalleshi.
“Baka san yadda nake ji ba, bana son rabuwa da kowa”
Yayi murmushi domin shi kan ya fita sani da jin duk wani abu da take ji na kewa da zata yi da mutane.
“Duk yadda kike ji, na fiki jin haka ke kewa ce kawai kike ji a ranki, ni kuma wata kalar azaba da radadi nake ji, saboda zaki tafi ne da ruhina na zuciyata, ban san ya zan kasance ba idan kika tafi, hauka zan yi? Ko kuma zan iya jurewa na yi hakuri na cigaba da rayuwa da tabon da kika min a zuciya, duk yadda zan misalta ba zaki taba ganewa ba, amman dai Daddy ya dora ni akan shawara, ta addu'a da neman zabin Allah kuma na dage da haka, wata kila babu alheri a tarayya ta dake shiyasa ma kika dage sai kin tafi, sannu sannu komai zai yaye har na manta da ke”
Yana maganar tana kallonsa har ya gama be kalleta ba, ita kuma bata fasa kallonsa ba har suka isa gidan, sai a sannan ya cire tissue ya mika mata. Ta karba ta share hawayenta ya fita motar ya zagaya ya bude mata ta fito ya rufe motar suka jekara suna tafiya har suka shiga cikin falon Mummy ta fara yi musu lale marbabun fuska a sake baki har kunne.
“Sannu da zuwa Marhabun lale”
Mummy da yayanta suka tarbi Nuwaira da farinciki da jindadi, Ameer da kansa ya shiga ya sanar da Daddy zuwan Nuwaira suka jero a tare suka fito daga bangaren, Daddy kamar ya hade Nuwaira ba saboda Ameer yana sonta kawai ba, sai dan addinin musulunci da ta shiga ya kara mata kwarjini da farinciki a gurin kowa. Liyafa Mummy ta shirya mata, sai dai ita kasa cin komai ta yi saboda tunanin gaba da take. Bayan sun gama cin abincin Daddy ya aika yarsa ta dauko masa ajiyar da yayi a dakinsa, ya gabatarwa da Nuwaira, sarka zinari ce mai matukar ktau da tsada irin mai cika wuya wadda ke hade da abun hannu da agogo.
“Wannan duka na ki ne, ina fatar idan kin tafi ba zaki manta da mu ba, musamman ma ďana Ameer, yana yawan maganarki kusan ya zama kamar wani soko akanki, ki rika tunawa da shi kina masa addu'a ko dan silar shigar da yayi miki a addinin Allah mai tsabta da natsuwa”
Ta saka hannu biyu ta karba, ba lallai ta fahimci minene ba saboda a garensu ba haka ake sarrafa zinariya a yi ado da shi a garinsu ba. Amman ta san abu ne mai kyau da tsada ganin yadda yake daukar ido.
“Zinari ne wannan, yana da kyau sosai”
Ta girgiza kai da sauri.
“Ba zan iya karbar wannan ba yayi yawa”
“No ba a maida kyauta karki ce haka ki karba mana”
Mummy ta fada tana kallonsu da murmushi. Godiya sosai Nuwaira ta yi ma Daddy har ta rasa kalaman hadawa ta nuna masa farincikinta. Mummy ma ta yi mata kyautar turaruka da earring masu kyau na GL da lace mai kyau. Suka rakota har gurin mota ta shiga suna daga mata hannu.
A tunaninta gida Ameer zai nufa da ita kai tsaye bayan ya bar gidan Daddy. Sai ganin ganin ya faka a gaban wani gate ya fita ta bude gate din ya shiga da motar ya sauya tuninaninta.
“Ina ne?”
Ta tambaya a lokacin da ya bude mata motar take kokarin fitowa.
“Kakata yau suka tare, na fada mata zan kawo ki, ki musu bankwana”
Kamin ya rufe motar Humaira ta fito rike da waya a kunnenta amman hakan be hanata yin welcoming din Nuwaira ba, cikin kyakkyawar tarba fuska a sake. Ameer ya wuce gaba Nuwaira ta bi bayansa har suka shiga cikin falon da ba a gama sakawa kaya ba, shi ya fara yi mata nuni da inda zata zauna sannan ya shiga dakin farko dake cikin falon. Humaira ta shigo after minutes da zaman Nuwaira a falon tana sake mata maraba da zuwa.
“Sannu da zuwa, Ameer yana yawan ba mu labarinki, kusan kowa ya san ki tun farko fara haduwarku ya fada kin yadda ya rikice akanki, bari na baki abun sha kar na cika ci da surutu”
Ta tashi ta shiga dakin da ke nuna madafa ce ta dauko mata ruwa da taliyar da ta girka, domin su ne kadai abubuwan da zata iya samu for now a gidan, kasancewar tarewar ta wuri ce kuma hankali Ameer ba kwance ba, be gabatar musu da komai ba, arzikinsu daya Daddy be manta da su ba, shi yayi musu komai a gidan. Nuwaira ta kai hannu ta dauki ruwan ta rike kamar wadda bata san abun da zata yi da shi ba. Can kuma ta daga kai tana kallon Ameer davya fito dakin Hajiya na bayansa tana takawa a hankali da sandar guragu, Bahijja na bayanta sai leken Nuwaira take kamar ba zata karaso kusa da ita ta kalleta ba.
“Sannu da zuwa yau bakuwar Ameer ce a gidan mu”
Nuwaira ta mike tsaye tana kallonsu, sai wani irin take ji, ta bakuncin mutanen da suka san da labarinta ita kuma bata san su ba. Hajiya ta karaso ta zauna tana kallon Nuwaira ita dai zuciyarta bata gamsu da yarinyar ba, ba dan tarbiyarta ko wani abun ba, sai dan ganin take ta fito daga bangaren Ummi ne, ganin take idan ya aureta Ummi zata sake dauke mata shi ne bayan duk abun da ta yi da farko, hakan na nufin ta ci nasara kenan. Cikin rashin natsuwa da sakin jiki Nuwaira ta gaisa da su, sannan ta yi musu sallama suka fito ita da Humaira ganin kamar Ameer ba zai fito yanzu ba.
“Da alama kin matsu ki bar gidan nan”
Ta kalli Humairah bata san me zata ce mata ba, domin ta san gaskiyar Hunairah ta fada, tabbas ta matsu ta fita saboda rashin sabon da bata yi da su ba.
“Karki damu, zamu taba da juna babu jimawa, domin na san Ameer yana sonki sosai irin son da ya wuce kwatance balle a kwatanta, ya wuce zane haka ma ya fi karfi fada, balle kuma ace alkalami ya rubuta, fatana dai ki share masa hawayensa ko san wahalar da ya sha”
Kallon Humaira kawai Nuwaira take kamar wadda bata fahimci abun da take fada ba. Fitowar Ameer ne ya saka Humairah ta dan matsa baya domin ba shi guri.
“How kika ji sabon gidan na ku?”
“Na ji dabam saboda ban saba ba”
“Zaki saba sannu, ki yi list din duk abubuwan da babu, idan ba zo sai ki ba ni a siyo, kuma ki gyara min daki daya zai zama ina da gida uku kenan gidan Daddy, Ummi, sai kuma nan”
Humairah ta yi dariya.
“Ka zauna a nan kuma? Kai da zaka yi aure?”
“Aure?”
“Yeah..”
Ta furta tana kallon Nuwaira, sai yayi murmushi ya girgiza mata kai, a take murmushin dake fuskarta ya gushe.
“How?”
Ta tambaya without saying it with sound. Sai ya daga mata kafadunsa.
“Ba kin min baki ba? Addu'ar da kika yi ma dan'uwanki ce Allah ya karba so get ready for your annoying brother”
Ya kalli Nuwaira.
“Let's go”
A tare suka sauka ya bude mata mota ta shiga ya rufe sannan ya zagaya ya bude bangarensa ya shiga, suka bar Humairah da mamaki da kuma tunani kala kala. Tun da suka hau hanya Nuwaira take kallon Ameer har suka kusa isa, shi kam ko da wasa be kalli inda take ba.
“Ameer ya kake ji a yanzu da kake da iyaye har uku?”
Sai ya amsa mata ba tare da ya kalleta ba.
“Ba dadi, ina ji mn rayuwa ta juye min upside down amman zan saba, kowa da kaddararsa”
Ta dan ji babu dadi ganin yanayinsa ya sauya sakamakon tambayar da ta yi masa, ta kai hannu ta taba shi.
“I'm sorry”
Ya kalli hannunta sannan ya kalli fuskarta sai kuma yayi murmushi.
“Yanzu ba kin musulunta ba, kin san halal da haram dole ki kiyaye wannan idan kin koma garinku”
Ta yi saurin dauke hannunta domin gaba daya ta manta da wannan haramcin. Bata sake cewa komai ba har suka isa, ya fara a daidai balcony din kofar Ummi. All her thoughts is zai kashe motar ya fita ya zagayo ya bude mata, sai ta ga ya kalleta yana murmushin da ya zame masa dole ne kawai.
“Finally kin ga Daddy daman kin taba ganinsa ai, amman dai yau kun gaisa kun san juna sani na musamman, kuma kin ga third parents din na, na san baki bukatar komai a yanzu right?”
Ta daga masa kai sai kallonsa take kamar yau dai jin kallonsa ya fi mata dadi.
“Ba zan shiga ciki ba, a nan zan sauke ki kuma ina miki addu'ar Allah ya sauke ki lafiya, ya tabbatar da ke akan addinin nan kuma ya kareki ya saukar miki da natsuwa da kwanciyar hankali a duk halin da zaki samu kanki, na gode sosai da kika ba ni danar saninki, kasancewa da ke ya janyo hankali zuwa ga alakata da Ummi, ido ya bude na fahimci rayuwa a daidai fiye da baya da nayi mata fahimta baibai, na kasance da ke a yanayi na nishadi da jindadi, sanadinki na san kishi, sanadinki na san so kuma sanadinki na san zafin rabuwa thank you so much for the experience, ina miki fatan nasara a duk rayuwar da zaki samu kanki a gaba, and i hope zaki bar kyautar da na baki saboda kin rika tunawa cewa kin taba kasancewa da wani Ameer”
Shi yake magana ita take hawaye har ya gama, ya dauke idonsa daga barin kallonta.
“Idan kin fita ki bude baya ki dauki kayanki”
Ta bude motar ta fita tana jin zuciyarta na narkewa, cikin rashin kuzari ta rufe masa motar ta bude baya ta shiga ta kwaso kayan da Daddy ya bata da Mommy tana kallonsa ko zai juyo ya kalleta amman yaki ya kalleta har ta kwashe ta fita ta rufe masa motar. Sai da ta fara tafiya sannan ya juyo da fuskarsa ya kalleta shi ma dan ya san ba zata iya ganinsa ba kasancewar bakin gilashi ne kallonta kawai yake tana tafiya hawaye ya sauko masa, kamar ta san son ganin fuskarta yake sai ta juyo tana kallon motar hawaye na sauko mata har wani jan numfashi take kamar zata shide, jin take kamar ya bude motar ya fito yace mata da shi za a tafi har garinsu. Amman har ta gaji da tsayuwa ta juya ta shiga ciki be fito daga motar ba, sai da ta yi minti biyar da shiga ciki sannan ya bude motar ya fito ya jingina da motar yana kallon kofar falon, ya shafa kansa ya sauke ajiyar zuciya, can kuma ya daga kansa sama yana kallon saman, kamin ya juyo ya bugu motarsa da karfi, ya sake shurinta motar. Ya dauki lokaci a haka sannan ya bude motar ya shiga ya dauki hanyar gidansu, da hannu daya yake tuki hannu daya ya shafa kansa gaba daya zafi yake ji a jikinsa ya rasa me ke masa dadi, kamar ya haukace haka yake ji sanin cewar bankwana ne yayi da Nuwaira bankwana na har abada, domin ya san ba zata taba dawowa ba.
MALEEK POV.
A hankali ya saki curtains din dakinsa ya sauke ajiyar zuciya, slowly ya fito daga dakin ya sauko kasa sai ya ci karo da abun da be yi zato ba. Nuwaira ce kwance akan kujera sai rusar kuka take kamar wadda aka yi ma mutuwa. Sai da ya waiga ya kalli stairs sannan ya zauna a hannun kujerar yana kallon kayan da ta watsar.
“Me kike yi ma kuka?”
Kamar jira take sai ta dago tana fada masa abun da ke cikinta.
“Ameer ne, wai bankwana yayi min tun a yanzu ba zai bari sai gobe ba, kuma ba zai raka ni ba...”
Kallonta yake yana kokarin fahimtarta, tunanin sai ya zame masa biyu, bayan ganin da yayi ma Ameer yana kallon Nuwaira da kuma bugun motar da yayi and now ita tama kuka take.
“Do you miss him?”
“I don't know”
Ta fada cikin kuka sannan ta mike tsaye ta nufi stairs still tana kuka, bin ta yayi da kallo har ta shige sannan ya mike tsaye ya nufi dinning, Coffee ya hada ya zauna a gurin yana sipping Coffee a hankali his mind is somewhere else sai tunani yake yi.
The following Day da wuri kowa ya shirya, Ummi ta cika ma Nuwaira bayan motar da zasu tafi da kaya bayan kayanta da suke gidan, ta bata wasu ga kuma wasu da ta samu a gurin Daddyn da Namra, chocolate da biscuits ma kala kala Ummi ta yi mata bag dinsu dabam kuma ta girka mata abun da zata iya ci, ta hada mata tea a madaidaicin flask ta dafa mata eggs. Bayan an saka komai police din da za su zakasu suka iso, Nuwaira ta fito tana kuka domin bata son barin gidan saboda sabon da ta yi, kusan kowa na gidan ya zame mata kamar dan'uwa, su suka cike mata gurbin abubuwan da ta rasa suka dandana mata dadin duniya suka cireta daga kuncin da kazanta da cutar da take ciki. Jerawa suka yi a balcony din har Abiey da Namra Mahmood da Ummi, Abiey da Mahmood ne kawai ba su yi kuka ba, Ummi kam ba a magana daman ita gwanar kuka ce, Namra ma da ba komai ke saka ta kuka ba sai da ta yi hawaye, saboda kukan da Nuwaira take, one after the other ta bisu da kallo dukansu sun jera babu Ameer, a lokacin ne ta gane cewar shi ma ya zama wani bangare na rayuwarta domin rashin ganinsa a cikin mutanen da take kallo a matsayin danginta. Ta takowa ta rika hannun Ummi ta saka a fuskarta
“Ummi na gode, kin zama uwata ban san dadi uwa ba sai akanki ban san miye dangi da yan'uwa ba sai da na hadu da ke, kin haska zuciyata kin zama sanadiyar yayewar kuncina, sanadinki nake iya magana da yaren da ba nawa ba, na san abubuwa da yawa ta dalilinki kin min gata da ban isa na biyaki ba kuma ba zan iya biyanki ba”
Ummi tana son ta yi mata magana ta fada mata abubuwa kuma ta yi mata godiyar da ta zama silar samun kan Ameer amman ta saka saboda kuka.
“Allah ya baki lafiya, Abiey na gode, Anty Namra Thank you”
Ta kalli Mahmood sai yayi mata dariya ita ma dariyar ta yi cikin kuka, kamin ta kalli Abiey dake tambayar ina Ameer.
“Ina Ameer?”
“Tun jiya yayi mata bankwana maybe ba zai iya ganin tafiyarta ba ne”
Maleek ya bashi amsa, yana bude motar ya shiga baya. Ummi ta ji tausayin ďanta Ameer, Abiey ya daga masu hannu sannan ya juya ya shige ciki. Maleek yaja motar police daya yana bayan motar, Nuwaira kuma tana can seat din baya na karshe zaune ita kadai. Maleek na ja motar