Showing 63001 words to 66000 words out of 271643 words

Chapter 22 - Wani Gari Book 1 Complete Hausa Novel

a nan ya kamata a ajeta ko kuma dakin su Nimra”

“Aa daga zuwan yarinya ba san wace iri ba ce sai a hade ta da yayana?”

“To zan iya kaita dakina saboda ba zai yiyu a aje ta BQ ba duba da yanayinta da kuma ciwonta, ya kamata ace ta samu kulawa kuma ta haka ne zata sake jiki da mu”

“Ban yarda da kwanta dakin yayana ba zan yarda ta kwanta dakinki? You're more important to me”

Juyowa ta yi ta kalleshi sai ta yi murmushi.

“Yau kuma?”

“Kullum ma, ke kika jamyo duk abun da nake furtawa ko yake faruwa ai, kamin na ga yayana wa na fara gani ba ke ba?”

Da murmushi yayi furucin kamar yadda ita ma murmushin yake shimfide a fuskarta. Duk abun da ake Mahmood na tsaye jikin Stairs ya kasa karasa saukowa kuma shi be hau sama ba, idonsa na kan mahaifinyarsa duk wani motsi nata yana idonsa.

“Mahmood zo ka shiga da ita dakin dake kusa da na Maleek”

Sai a lokacin ya sauko ya saka hannu ya dauke ta cak ya haura da ita sama. Abiey ya mike tsaye yana fadin.

“Ki saka mai aikinki ta kai musu abinci, CP yace su zo nan kai tsaye ba sai sun shiga office dinsa ba, nima kuma yunwa nake ji”

“Yanzu zan saka ta kai musu, daman tun dazun muka gama shirya komai, ni kuma i will serving my King”

Girgiza kai yayi ya fice yana dariya, sun saba irin wannan wasan amman faruwa abubuwa ya saka sun rufe babin wadandasu abubuwa da dama. Sai da ya fice sannan Nimra ta dago ta kalli Ummi.

“Har yanzu Abiey fushi yake da ni”

“Zai sauko yata, dole zai daina fushi da yarsa, ki bashi lokaci Abieynku yana daukar zafi akan abubuwa amman yana da kyakkyawar zuciyar mantawa kuma ya yafe, sai dai ba a nan take ba”

Ummi data karaso kusa da ita ta kai hannu ta taba ta.

“Yar autar mata, ta so ki fadawa Hanne ta kai baki abinci da abun sha”

“Toh”

Ta amsa sannan ta tashi tare da wayarta ta fice daga falon, Ummi kuma ta nufi dinning...



©Khadeeja Candy
©®Copyright
2023
*W_G -it's not free, pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith Bank, then send the evidence to 08036126660*

21

After ya nuna musu BQ sai ya samu guri a cikin set din cushion din da aka jera a Balcony ya zauna, yana tsala wayarsa. Har Hanne ta gama ziyar kaiwa bakin abincin da abun sha Maleek ba dago ya kalli gurin ba, Mahmood ne ya fito daga falon yana kallon harabar gidan zuciyarsa cike da tunani kala kala kamin ya kalli gurin da dan'uwansa yake zaune ya nufi gurin. Ajiyar zuciya ya sauke hakannya sakan Maleek dubansa domin ba kasafai Mahmood yake barin wani abun ya dame shi, kusan shi da Namra a gidan babu wanda zai ce ga damuwarsu, Namra saboda bata sake jiki da kowa ciki har da Ummi da yar'uwarta Nimra, komai yake cinta sai dai ta barshi a cikinta, shi kuma baya barin damuwa ta kusance shi ma balle har ya damu da ita, idan ma akwai damuwar kenan, babu abun da suka nema suka rasa a duniyar nan hakan ya saka damuwa nesanta inda suke.

“Are you okay?”

“I hope so”

Ya amsa yana kallon harabar gidan, Maleek ya cigaba da danna wayarsa.

“Tunani nake yadda rayuwa zata zama idan babu Ummi”

Mahmood ya fada ba tare da ya kalli inda Maleek yake zaune ba. Cak Maleek ya tsayar da taba wayar ya dago kalli Mahmood.

“Baka da hankali? How could you say that? Kasan abun da ake nufi da babu Mahmood? Rasa ta fa kenan mutuwa, ta ya zaka fadin irin wannan maganar?”

Mahmoud yayi murmushi yana kallon Maleek, da ya mike tsaye rai a bace.

“Wannan ranar ba zata zo ba Mahmood idan kuma ta zo to ba zata same ni da rayuwa ba, ban taba mafarkin rana zata zo da zan saka kafata a cikin gidan nan ace Ummi bata nan ba, ban san me ya zo kanka ba ya kamata ka yake shi ka nemi tsarin shaidan daga wannan mummunan tunani naka i hate nonsense”

Ta zazzaga masa magana sannan ya saka kafarsa sai fice daga gurin sai kuma ya juyo ya kalleshi.

“Ko wani abu kanji Mahmood?”

“No ban ji wani abu ba, kawai zuwan yarinyar nan ne ya ba ni tausayi ta rabu da iyayenta, ya saka ni tunanin mu idan muka rasa Ummi ya zamu ji irin yadda muka saba da ita?”

“Ku da kuka saba da ita kenan, ya kake tunanin ni da ka kasa kebewa da ita ko da tsawon awa daya ne? Balle har na raba jikinta na rumgume ta a matsayin uwata? Baka tunanin ina jin zafin haka Mahmood? Mi yasa zaka min irin wannan maganar? Why?”

Ya karshe maganar muryarsa na karkarwa irin na wanda rauni da bakinciki ya dade a zuciyarsa.

“Bana nufin bata maka rai...”

Fuuu ya fice daga gurin be tsaya sauraren abun da Mahmood zai fada ba, baya jin komawa ya cikin gidan hakan ya saka shi nufar Katon Garden din dake gidan, Garden da aka kawata da itatuwa da fulawoyi ta ko'ina ta bangare daya kuma an yi Swimming Pool, an jera kujeru a kusa da gurin, ta dayan gefen dama kuma kebantattun tsuntsaye ne da aka yi musu muhalli na dabam, sai barewar dake ta kiwonta a gurin wani decoration na busashen itace. A hankali yake takawa har ya isa gurin da tsuntsayen suke ya bude yar wayar da aka kewasu da ita ya shiga cikin garden din, guri ya samu a gurin kujerun nan da ake na siminti ya zauna yana kallon yadda wasu suke tashi wasu na sauka. Wayarsa dake hannunsa ya bude Gallary ya shiga can wani gurin ajiyar sirrin ya kamo hoton mahaifiyarsa inda take zaune tare da Abiey aka yi musu hoto Tan murmushi har koranta sun bayyana. Yatsansa yakai ya shafa saitin inda take a jikin hoto yana jin wani launi marar dadi na masa yawo a zuciya. Shi ne kadai abun da yake iya, ya kalli hotonta ko ya shafa amman a fili ba zai iya zama yayi shawara ko hira da ita ba, ba zai iya kai hannu ya taba taba jikinta a matsayinta na mahaifinyarsa ba, ba zai iya kebewa daga ita sai shi na tsawon awa daya ba, tun da yayi wayo ya mallaki hankalin kansa be san wata rana da haka ta taba faruwa a tsakaninsu ba, sai dai duk da haka Ummi bata taba juya masa baya ba, bata taba jin ta tsana shi ba, tana kokarin ganin ta ja shi a jikin sai ta ga hakan ya gagara sannan ya saka masa ido ta daina kokarin kebewa da shi a cilas ko taba shi, sai ma taimaka masa da take na yadda zai rayu ba tare da yan'uwansa sun shiga rayuwarsa sun bata masa rai kamar yadda baya bukata ba.

Shi dai ya san ba tsanar mahaifiyarsa yayi ba, domin bata yi masa abun da zai saka ya tsane ta ba, idan ma ta yi masa dole ya so ta saboda ita din uwa ce, balle kuma bata yi ba, sai dai ya tsabarsa da mata ne ya saka ita din yake kaurace mata saboda ita ma tana daya daga cikin jinsin matan. To miyasa ya tsani matan? Why? Shi kasan ba zai iya fada ba, be yi soyayya ba balle yace yaudararsa akai yi, be zauna da matar uba ba balle yace ta cucheshi. Sai da aka kira Sallah magariba sannan fito daga gurin, a harabar gidan ya hadu da Ummi ta nufo Garden tana kallonsa.

“Mahmood yace min kana Garden tun dazu gashi Magariba ta yi baka san iya abin da zai sauko ba”

Cike da kulawa irin ta uwa take masa magana, lafiyarsa ce abar damuwarta a yanzu. Ya dan dauke kai daga barin kallonta ya kalli kasa.

“Ina taba waya ne ban ankaro lokaci yayi ba sai da na ji kira, bari na je na yi alwala”

Ya amsata yana tafiya sai ta juyo ta biyo bayansa domin inda sabo ta saba da halinsa. Yana gaba tana bayansa har suka shiga falon kai tsaye ya nufi Upstairs ita ma stairs din ta nufa domin gabatar da nata alwalan, daf da zai wuce dakin da Waira take ciki ya shiga nasa dakin sai gata ta fito da gudu daga dakin da yake bude kicibis suka yi da Maleek bata tsaya komai ba ta rumgume shi ta rike da mugun karfi.....

Duk wani abu mai rai da motsi a cikin jikinsa sai da ya tsaya cak, ciki har da bugun zuciyarsa da numfashinsa.
Ummi ta rufe baki daga bayansa da take tsaye domin ta ga abun da ya faru, Nimra da ta biyo bayanta da gudu ma ta tsaya cak ta zaro ido. Shisshikar kuka kawai Waira take tana kara rike shi ba dan ta san waye shi ba ita dai gurin boya da cuto kawai take nema. Ganin ya rumtse ido ya ya cige baki ya saka Ummi ta nufo inda yake da sauri ta banbare hannun Waira har da mai ciwon taja ta baya, a lokacin ne wani abu mai kamar ba suma ya ziyarce shi sai ya ji wani uban jiri da rawar jiki na neman kamashi ya bude ido zuciyarsa har gargada take numfashinsa na sarkewa. Waira sai kuche kushen ta subuce a hannun Ummi take ta sake rikeshi ganin take kamar maza sun fi mata yi mata kirki da kyautata. Tasss ya wanke mata fuska da mugun mari har sai da ta ji wata kara a kunnenta ganinta yayi batan wucin gadi, kwatankwacin tsayin da yayi a dazun da ta rumgume shi irinsa ta yi jini ya cika bakinta idonta ya cika da hawaye ya sauko mata...




AMEER POV.

10:24pm O'clock

Abincin ya masa dadi fiye da na kullum har cikin kwakwalwa kansa yake jin yadda abincin yake kai masa. Ba karyar Step Mother dinsa ta iya girki musamman na yau da ya zama na dabam.

“Da alama dai yau gaba daya zaka cinye jalof”

Ameer ya tsayar da cin abincin da yake yayi murmushi tare da daukar cup din ruwa ya sha.

“Sis don't fake it ke ma fa kin ji dadin abincin nan”

Sister ta yi  murmushi tana cigaba da cin abincin. Wayar dake kam teburin ya dauka ya shiga Instagram dinsa ya the first thing da ya fara dubawa shi ne account din Nimra, sai kuma yayi sa'a ta amsa masa bukatarsa ta son following dinta.

“Good Girl, i like you”

Ya furta yana jin kamar wani target dinsa ya kama hanya.

“Is she the one?”

Ta tambaya duk kuwa da bata san abun da yake kallo a wayar ba, sai ya dago ya kalleta.

“Who?”

“Girlfriend”

Yayi wani miskilin murmushi

“Tun da kike a rayuwarki kin taba jin na yi maganar budurwa?”

“Noo amman na san kana da ita”

“No Fiyya ni bana boye komai ai, idan akwai ta definitely zaku sani, more especially you, kin san you're my favorite, so ni bana da budurwa?”

Ya maida hankalinsa gurin wayar yana tunanin irin sakon da zai tura mata.

“Amman miyasa? Ni Wallahi ban taba maka magana ba ne kawai amman na dauka kana da girlfriend”

“Idan har zan yi budurwa zan zabo mai tsada ce, kuma har yanzu ban taba cin karo da wanda ta yi daidai da ra'ayi na ba, idan har zan so mace dole sai mai matukar tsabta wanda bata taba sanin miye kazanta ba a rayuwarta, wacce ke wanka da tsabta kamar yadda nake, who can cook delicious food, mai yawan kamshi wacce idan an rabe ta babu abun da zan ji sai Kamshi, mai matukar kyau fara sosai yar gidan masu kudi, mai ji da kanta, kuma wacce idan na ce ta aske gashin kanta zata aske yi kamar dai Angel, sannan kuma Virgin”

“Wacece kuma Angel”

“Wata Ahlil Kitab ce, kin san su babu ruwansu da barin gashi, kuma tana da tsabta irin yadda nake so a jikin mace”

“Tab za a samu duk mai abun da ka lisaffa amman ban da yawan tsabtarka da kuma aske gashin kai, sai idan ka samu wacce bata ta gashin daman”

“Za a samu wata rana, duk da na san dukan abun da na lissafa abu ne mai wahala a yanzu ba musamman ma virgin din, domin yan mata yanzu tun a waje suke siyar da mutuncinsu da kudi ko da sunan soyayya, ke kanki bana iya shaidarki a yanzu”

Ta zaro ido tana kallonsa da mugun mamaki har tana nuna kanta.

“Ni.... Na yarda na bada mutuncin ne ai sai Momy ta ci Ubana”

“Lokacin da za ku yi ai babu wanda zai sani, ita kanta Momyn ba zaki bari ta gane ba, ku yaran zamani ne kun fi iyayenku wayo”

Ya fada kamar ba da shi ba, ya mike tsaye yaja kujerar baya.

“Good Night”

Ya fice daga gurin yana taba wayar, fiyya ta bishi da kallon mamaki har fice daga falon gaba daya.

“Kasan yan matan da ka lalata kenan shiyasa kake fadar haka”

Ta fada bayan ya fice.

Motarsa ya nufa ya sai jingina yana jin nan ne safe place da zai samu damar aikata abun da yake son yi.

“After all abun da kika Hada kai da dan'uwanki kika min be wadatar ba sai kin sake cutar da ni da cewar na dauko wata yarinya a motar? Why Nimra? Me na tare muku ne? Miyasa ba ku son ganin farincikina?. Ban tsammanci kalar wannan rayuwar daga gareki ba, a farkon ganin da na yi miki na aminta da ke shiyasa zuviyata ta natsu da ke, ashe akwai abun da kike shirya min, kin kyauta Nimra kuma na gode”

Ya tura mata bayan ya gama rubutawa, so yake ya kalailaye zuciyarta ya siye da kalaman dauraya ya yaudare ya karye mata guiwa kamar yadda ta yi masa.

“By the way, akwai sarewata a cikin motar, ki aiko min da ita a inda muka saba haduwa dake”

Ya sake aikawa, daman sarewar na daga dalilin da ya saka ya nemi handling dinta a IG. after ya gama tura mata ya dago jikin motar ya dawo cikin gidan, yana tunanin yadda sakon zai riske ta, yana misalta irin amsar da zata ba shi Idan har yayi nasarar karya mata zuciyar.
Yana shiga dakinsa amsar sakon da ya tura ya fara dawo masa tun yana karantawa a tsaye har ya kai ga zaunawa.

“Dukan abun da kake zargin na aikata saboda na cutar da kai ban aikata ba Ameer Allah shi ne shaidata, Maleek ma ba shi da wani buri ko kudiri na cutar da kai, sai dai kuskuren fahimta da kuka samu, kuma ni ban san ka bar motar a can ba balle har na saka a aikata maka abun da kake zargina da shi, mi zai saka na saka wata a motar dan kawai na cutar da kai, miye ribata idan na yi haka? Ka fada min garin da ka tafi? Balle na aika wani yayi maka haka? Ka aminta da ni Ameer, ina cikin damuwar abubuwan da suka faru, mahaifina baya magana da ni saboda abun da na aikata na baka mota da kudi da wayata da na yi, har aka samu wata yarinya a motar ka”

Yana yi yana tsayawa har ya gama karantawa, yanayin yadda ta turo masa sakon zube a lokaci daya ya tabbatar masa da cewar ya fara yin nasarar karya lagonta, duk kuwa ba be san abun da take shirya masa a boye ba. Har yanzu be ji ya yarda da ita cewar ba da hadin bakin yayanta ta bashi motar ba.

“Sarewar kuma ban duba motar ba, balle na san abun da yake ciki saboda yau aka kawo motar tare da yarinyar a gidanmu, amman bayan komai ya lafa zan duba motar na dauko maka sarewar idan tana ciki, kuma ba zamu hadu a inda muka saba haduwa ba sai dai a gurin da muka taba zuwa da kai wajen Abuja, shi ma kuma idan har na samu sarewar domin ban san iya abun da zai faru idan mahaifina ko Maleek ya gan ni tare da kai ba”

“Really”

Ya fada bayan ya gama karanta sakon na biyu, sannan ya jefar da wayar saman gado ya cire rigarsa yana tunanin wata kila kuma ita ce take shirya masa wani zagon kasa kamin ya gama saka tasa gadar saren.....



DR SHURAIM POV.

“Wato ana yi ma mutun kallon mai hankali sai ka tarar babu hankali a tare da shi, ko kuma tunani zan ce?”

Hajiya Hajara ta fada tana masa kallon bacin rai.

“Yanzu ina yarinyar take?”

Cewar Mahaifinsa. Shuraim ya kalli mahaifiyarsa domin damuwarta ce ta fi daga masa hankali ya san mahaifinsa mai fahimta ne zai iya fahimtarsa amman Hajiya kam sai yayi da gaske.

“Ita yarinyar tana hannun Police na kai musu ita, ni kuma ina lafiya”

“Ina kwana? Kuma na kira wayarka baka daga ba daga baya kuma ka kashe wayar”

“Hajiya yarinyar bata yarda ta bar ni ba, a dole a can muka kwana ni da ita CID din, sai da safen nan da suka kama hanya sannan ta hakura, kuma kin san mace ce be kamata na barta ta kwana a can ba saboda mace ce, kuma na san idan idan na fada miki ba zaki bari na kwana a can ba ko dan yanayin jinin dake zuba a idonta ya kamata ace na tsaya a gurin gudun kar sai na dawo wani abun ya faru su ce ni na cutar da ita, shiyasa ban amsa kiranki”

“Aifa duk yadda zaka yi ka kare kanka ka sani, ku kullum ana nuna muku yadda za ku tsira sai son jefa kai a halaka kuke”

Fada ta yi masa sosai a washen garin ranar da ya koma gida, sa'arsa daya mahaifinsa ya masa uzuri har ma ya tare masa fada a gurin mahaifiyata. Sai da ta gama masa fadan tsab sannan ya fita daga falon ya shiga domin bangarensa yana wajen falon ne, ya shiga dakinsa cikin rashin jindadin rayuwa da Waira, har lokacin ya kasa natsuwa da inda za aje da ita, tunawa da yadda ta tsaya tana kallonsa ba ta yi kuka ba ya kara tausayinta a cikin ransa.

“Allah sarki Allah yasa tsare ki Waira Waira”

Ya maimaita sunan a karo na farko bayan

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login