Showing 144001 words to 147000 words out of 271643 words

Chapter 49 - Wani Gari Book 1 Complete Hausa Novel

kila zata baka gamsasshiyar amsa”

“Bana ma som ganin fuskarta a yanzu, bana son komawa gida, gaba daya na rasa me ke min dadi”

“I hope alakarka da Daddynka ba zata canja ba”

Ya girgiza.

“Ba zaki fahimci abun da nake ji ba Humairah, i wish bayan na mutu hakan ya faru”

“Mahaifiyarka bata kyautar da kai a gidan marayu ba, bata jefar da kai a hanya kamar yadda wasu iyayen suke ba, bata bada kai inda za ka sha wahala ba sai a inda aka nuna maka gatan da ko mahaifinka na gaske iyakar abun da zai yi kenan, please Ameer ka dubi wannan abun da idon Rahma”

“You take her side saboda mace ce yar'uwarki”

“No ina fada maka gaskiya ne, kuma ita ta fika zama abun tausayi, wata kila da zaka tambayi labarinta da zaka ji bata da laifi abun da ta aikata”

“Kalli yadda alaka ta kullu tsakanina da Nimra da ace ta kai na biye a yadda ta so na mun gudu mun yi aure yaya kenan? Ashe ma kanwata ce it hurt so bad, all this while Maleek yana kallona wani sakare saboda ya san komai”

Ya daki sitiyarin motar da karfi har sai da Humaira ta zabura.

“Calm down please ba lallai ace ya sani ba, maybe su ma ta boye musu”

“Amman Humaira ya zan kalli duniya da wannan?”

“I think zaka cigaba da zama a matsayin dan Daddy ita dai ta yi subutar baki ta fada maka gaskiya, kuma ina son ka kalli abun da budaddiyar zuciya please”

“Okay na kalli abun a yadda kike son na kalla, then what zai canja abun da ta yi? I don't even know my real father, sunansa ban sani ba ya rayuwarsa take ina yan'uwansa suke duk ban sani ba, wannan kadai ba abun bakinciki ba ne? Yanzu ne duniya zaka min dariya ashe duk abun da nake takama ba na ubana ba ne”

Ya dafe kansa.

“Na mahaifinka ne mana, shiyasa na ce ka kalli abun da budaddiyar zuciya, saboda ka fuskance ta tattauna da ita ka yi mata tambayoyi, kuma ka san yadda za ku bullowa abun saboda samun mafita, bayyana wannan abun wani abu ne na sirri da be kamata kowa ya ji ba, kuma za ku iya rufe wannan abun a tsakaninku”

Ta kunna wayar hannunta ta duba agogo.

“It getting dark ya kamata na shiga gida kar a fara nemana”

Ya gyada mata kai.

“Please keep reciting Hasbunallahu Wani'imal Wakil, aka samu sauki In Shaa Allah”

Nan ma dai kan ya gyada mata yana ta kallonta har ta fice daga motar da ke bude. Duk wani tsana da ta yi masa da kiyayyarsa da take ji a ranta sai ta ji abun ya tafi, tausayinsa ya cika mata zuciya, yadda yake rayuwa yana alfaharin da cewar Mr Bashir mahaifinsa ne ace a yanzu ba shi ne ya haife shi ba, abun dai kamar a shirin film ko littafi, domin abu ne da be cika faruwa a zahiri ba. Tsaye ta yi tana kallon motarsa har sai da ta daina hangoshi sannan ta juya ta koma cikin. Ba shi da wani gurin zuwa da ya wuce gidansu, daman idan bashi a office yana a gida ko kuma yana tare da abokansa, sai dai a yau jin yake baya kaunar kwana a gidan. Saboda haka ya nufi gidansa, fakawarsa ke da wuya a harabar gidan kiran Daddy ya shigo wayarsa, sai da yayi kamar ba zai daga ba sai kuma wata zuciyar ta hana shi kin amsa kiran Daddy.

“Hello”

“Kana ina?”

With serious voice Daddy yake tambayarsa.

“Ina gidana”

“Gidanka? Yaushe ka fara zama a gidanka?”

“Na kan zo sometimes da rana, yau kuma ina jin zan kwana a nan ne”

“Saboda makiyanka suna cikin gidan daka saba kwana?”

“No Daddy no har abada, kawai dai ina jin gidan kamar ya matse ne, ina jin wani yanayi marar dadi idan na tunkari gidan”

“Shiyasa na ce ka bar abun nan ya zauna a sirri, domin har yanzu baka mallaki hankalin da zaka iya controlling kanka da zuciyarka, me zai saka ma na yarda a gidanka kake? Kuma idan a gidan kake waya san iya abun da zai biyo baya? Zaka iya illata kanka ko ka illata wani, ko kuma a zo a yi maka wani abun”

“I can controlling myself, Daddy ni ba karamin yaro ba ne zan iya kula da kaina, sanin gaskiya ba zai kara min komai ba sai kwarin guiwa da sanin waye ni, bani da halin wulakanta kowa a yanzu, mutanen da nake ganin kamar na fi, wata kila sun fi ni komai, i need to know su waye familyn mahaifina, waye shi, wata kila ni din ba dan kowa ba ne, na ci mutuncin mutane da dama, saboda ina jin cewar na fi su, ashe ba haka ba ne”

“Ko a yanzu ka fisu Ameer, fada maka gaskiya ba zai canja matsayinka da duniya take kallonka da shi ba, ba kuma zai saka na tashi daga mahaifinka ba, babu abin da zai canja, sai dai idan butulce min zaka yi, ina son zan samu Zahra mu tattauna wannan maganar a barta ta zauna a sirri, kuma har yanzu Ameer shi kadai ne ďa namiji da Mr Bashir ya taba haihuwa, babu wanda zai fika gata da jindadin rayuwa i promise you this”

“Mahaifin Maleek ya fada min, saboda rashin kudin aiki aka siyar da cikina, kuma bayan siyar da cikin Ammy ta fada min Zahra ta kyauta da ni a gareka, wata kila saboda tsoron talauci ne ko Daddy? Akwai abun da ya fi wannan zafi? Kana ganin zan iya aje wannan abun na manta da shi?”

“Ameer ka dawo gida ka kwana, bana son ka je ko'ina”

Daddy na fadar hakan ya yanke kiran be tsaya jiran abin da Ameer din zai fada ba, domin ya fahimci Ameer din yana son jan maganar ta yi tsawo kuma ba lallai ya fahimci abun da yake kokarin lurar da shi a yanzu ba. Aje wayarsa ta yi daidai da sauwa hawaye a babban mutum kamar Mr Bashir ba tare da ya kalli Mommy dake gabansa ba ya ce.

“Jamila ta lalata min duk wani abu da shirya, ko da yake ba laifinta ba ne ita kadai har da Zahra, yanzu sun kirkiri tazara tsakanina da wanda na fi kauna a duniyar nan, kuma sun yi nasara shiyasa bahaushe yace tsintacciyar mage bata mage, da na san wannan ranar zata zo da ban karbi wannan kyautar da Zahra ta yi min ba tun farko”

Cikin yanayi mai ban tausayi Mommy take kallon jagoranta nata idon na kwarar da kwalla ta ce.

“Ka yi hakuri, haka Allah yake ikonsa idan ya zo, da ace ya so da dauke Ameer zai yi gaba daya ya mutu, ba ku san abun da zai faru gaba ba, dan Allah ku bar jayayyarsa, masu iya magana sukan ce ba a jayyyar ďa da miji, idan aka yi jayayyarsu tafi suke su bar masu jayayyar”


Mommy bata taba sanin cewar ba shi ya haifi Ameer ba sai a yanzu da komai ya lalace. shakuwarsu da yadda kaunar Ameer take a zuciyar mijinta take tunawa sai tausayinsa ya kamata. Tun da ya aureta be taba zancen mahaifiyar Ameer da ita ba idan ma ta dauko masa sai yace mata baya son maganar a dole take kawar da zancen domin ita macece mai matukar son farincikin mijinta yana ďaya daga cikin dalilin da ya saka take nunawa Ameer kauna, domin ta lura yana matukar kaunar Ameer ya kuma tabbatar mata da hakan tun kamin ya aureta.

“Baka taba kuskuren aikata wani abu da zai nuna Ameer ba ďanka ba ne, ko da wasa baka son bacin ran Ameer, Wallahi a rayuwata ban ga wani uba da ya nunawa ďansa gata fiye da yadda ka nunawa Ameer ba, lallai duniya zata girgiza idan labarin nan ya fita”

Tana fada tana kuka, ita ma tausayin Ameer din take jin cewar be sani ba sai a yanzu, kara ma Daddy ya san da sirri amman ya boye saboda farinciki ďansa, amman Ameer fa? Dare daya da wuni aka ruguza masa komai.

“Wata kila da Jamila bata aikata abun da ta aikata tun farko ba, da ba mu jefa yaron nan da kanmu a matsala kamar haka ba, ina tsoron kar ya shiga wani hali”

“Jamila ai dole ta fada masa gaskiya, saboda ta bata alakarku, na yi imani ba zata tado maganar kai tsaye ta fada ba, amman idan har ya bukata zata fada masa domin tana kallonka a matsayin wani wanda ya samu farinciki da kyautar ďa silarta amman ya kasa zama da ita, ya ki yarda ta bawa wannan yaron kulawa a karkashinsa, kai ma baka yi mata adalci ba, domin saboda kai ta aikata haka sai gashi kuma ka rabu da ita.... ”

Mommy na aje ayar zancen Daddy ya rufe da fada, domin ji yake a yanzu ba shi makiyiya a rayuwarsa kamar Zahra da Jamila, ba ma kamar Jamilar da ita ce silar komai.

“Toh zama zan yi da ita? Bayan ta yaudare ni? Ta jefa a matsala ta aikata kuskure da addinin musulunci ma be yarda da shi ba, sannan yanzu ki kalli idona ki ce wai na kyale ta? Haukace ne ni da zan zauna da ita? Ko kuma neman haihuwa hauka ne? An isa ayi ma Allah wayo ne? Yanzu da ya tashi ba ni yayan ba ya ba ni ba? Taya za zauna da macen da bata da tawallaki da imani a zuciyarta? Idan har zata iya aikata hakan me kike tunanin gaba? Da ace ban gane gaskiya ba haka zamu yi ta zama ina kallonta a matar kirki? Ashe ke ma dai baki da hankali, ina ganinki mai ilmin ashe na banza ne”

“Allah ya huci zuciyarka, ban ce ka zauna da ita ba, kawai ina fadar abun da na fahimta ne”

“Fahimtar banza fahimtar wofi, mai daki ai shi ya san inda yake masa yoyo, karki fada min maganar banza, ina neman abun da zai zame min mafita ni da ďana sai kuma ki fara fada min wata maganar banza akan Jamila Malama tashi ki fice daga daki”

“Ka yi hakuri dan Allah... ”

“Ki tashi ki fice na ce”

Ta mike tsaye cike da nadamar maganar da ta yi ta fice daga dakin ta bar shi sai huci yake, abun da ba halinsa ba domin mawuyacin abu ne ta ga bacin rai a fuskarsa idan ma ransa ya bace yakan yi kokarin boye abun ya barshi a ransa.




AMEER POV.

Ji yake kamar shi kadai ya rage a duniyar nan he's feeling so lonely. Wani irin tarin bakinciki da damuwa ne a cikin ransa, ya dade a cikin motar kwance idonsa a rufe sannan ya bude motar ya fito ya shiga ciki, sai da ya fara bude fridge ya dauki gorar ruwa ya sha sannan ya dawo falonsa ya zauna yana sauke ajiyar zuciya. Be yi bachi ba kuma be tashi daga falon ba har kusan 11pm, tunani yake wani abun yana zuwa masa baibaiwa wani a daidai, wani tunanin kuma idan ya fadada sai ya ji kamar ya fashe da kuka. Sha daya na dare da yan mintuna kiran Abdull ya shigo wayarsa, yana ganin sunan mai kiran gabansa ya fadi zuciyarsa ta raya masa cewar Maleek ya labarta abokansa abun da yake faruwa shiyasa Abdull ya kira shi by this time. Amsa kiran yayi ya saka wayar a speaker yana tunanin kalar amsar da zai bawa Abdull idan ya tambaye shi.

“Hello”

Ameer ya fada cikin rashin kuzari murya can kasa. Kai tsaye Abdull ya fada masa dalilin kiran.

“Ameer ka ji kanwar Maleek ta rasu”

Jin an fada masa abun da ya sha gaba komai wato mutuwa ya saka shi zabura ya gyara zama da sauri.

“W-w-w what? Wace wace wace please wace?”


“Nimra, ta rasu da daren nan asibiti”

Ameer ya aje wayar akan center table dake kusa da shi ya dora hannunsa saman kai ya gurfana a kasa kamar mai neman gafara.

“Innalillahi Wa'inna Ilaihiraji'un Allah ya Abdull how? Why?”

“Why? Mutuwa ai bata da magani, ba kai ka fada min an kaita asibiti ba? Maybe ciwon be barta ba”

Ya girgiza kai ya rufe bakinsa yana kuka.

“Na kasheta Abdull ni ne... Ni ne silar mutuwarta.. Na rabata da duniya... Oh my God yanzu ya zan yi da hakkinta?”

“Ameer lafiya kake kasan me kake fada?”

“I break her heart, na yi ne kawai saboda na bakantawa Maleek, and ba son gaskiya nake mata ba, kuma na fada mata and.... Shi ne silar sumanta har aka kaita asibiti now you're telling me ta mutu, Me yasa abubuwan nan za su zo min a yanzu Abdull I'm such bad person i didn't deserve anything good at all, ina zan roki yafiyarta? Yanzu ya zan yi da hakkinta”

Dauke wuta Abdull domin shi dai ya kira ne kawai ya sanar masa kamar yadda abokinsu Dawood ya sanar musu so that su taru su tafi gurin abokinsu domin jajanta masa kuma ayi komai da su, kamar yadda suna gudanar da al'amurransu a can da, duk kuwa da kasancewar babu wanda ya taba rasa rai a cikinsu sai a yanzu da Maleek ya rasa, sai dai duk abun da ya samu suna taruwa su jajanta ma juna, ba dan ma matsalar da Ameer ya samu da Maleek ba da a kullum tare suke rayuwa.

“Ameer... Kasan me kake fada kuwa? Amman Ameer ya sani? All this fadan da kuka yi har abun ya kai su gurin police iyaye suka shiga abun be tsaya iya nan sai da zuciyarka ta raya maka ka aikata ma yarinyar nan wani abu? Yanzu miye amfanin aikatawar da ka yi? Gashi ka zama silar mutuwarta, innocent live, da ma ace kana sonta da gaske sai abun ya zo da sauki amman kasan baka sonta ka aikata hakan saboda kawai ka cutar da ita? Kana da matsalar rayuwa Ameer, idan ka dauki gaba da mutum kai ala dole sai ka ga bayansa, burinka ka wulakanta kowa cikin har da mu da muke abokanka, kuma babu wanda zai fada maka ta ji wannan ba rayuwa ba ce mun sha nuna maka amman baka ji ba, yanzu kana tunanin hakkin yarinyar nan zai barka? Idan iyayenta suka yi kararka ma za a iya kwatar musu hakkin yarsu, bayan haka kuma ka karawa kanka kiyayyar kanka a gurin Maleek da iyayensa.. Sannan.... ”

Yanke wayar yayi fahimtar Abdull ba zai gaba zuba masa kalaman da suke kona masa rai ba.

“Nimra...”

Ya furta yana hawaye, wayarsa ta sake ringing wannan karon Dawoo ne ya kira shi, wata kila shi ma zai sanar masa an yi mutuwar ne, sai ya ki daga wayar sai hawaye kawai yake, wani rauni da nadama suka mamayeshi. Sai a yanzu yake ganin be kyauta ba, be aikata daidai ba, be dace yayi haka ba, me yasa ya cutar da Nimra? Son zuciya ne ya kai shi ga aikata hakan ko kuma rauninta? Wa gari ya waya yanzu? Gashi Ummi ta fada masa kanwarsa ce, that's mean Ummi ta haife ta kenan? If wani ya aikata wa kanwarsa haka ya zai ji balle kuma ace shi da kanss ya aikata? Ya mike tsaye ya fara safa da marwa a falon, dariyarta ce ta fara fado masa a rai yana tuna yadda take nishadi idan ta zo gidan, saboda tana tunanin son gaskiya ya nuna mata, yadda ta rike hannunsa tana rokon ya rike ta amana ya tsaya mata a duk lokacin da za su tsinci kansu a cikin mawuyacin hali, yadda take yawan fada masa tana kaunarsa ga kuma irin marin da Abiey yayi mata a lokacin da suka zo daukarta restaurant ya tsaya masa a rai, kiran da ta yi masa a waya na karshe har ya fada mata cewar shi baya kaunarta ya hana shi sukuni. Sai da ya kai tsakiyar falon ya fadi durkushe ya fashe da wani irin kuka mai taba zuciya, sosai yake kukan da ace gidan ba babban gida ba ne da makota ma za su iya jiyo muryarsa.

“Nimra ki yafe min.... Ki yafe min Nimra.... Na shiga uku, i hurt this innocent girl, i hurt her hakkinki ba zai bar ni ba, me yasa na aikata? Akan me zan dauki dansa akanta? Meyasa na zama wawa? Why ido zai rufe na kasa ganin abun da zai biyo baya?”

Fada yake da kansa kamin ya daga hannunsa ya dauke fuskarsa mari, ya daga hannayensa ya buga kasa, be taba jin ya cutar da wani cutar da ta kai makura ba irin wannan, sam be dorawa Nimra mutuwa a yanzu ba, shi be ma zaton son da take masa ya kai har haka ba.

“I'm such a bad person”

Ya fada yana jin kamar akwai abun da zai iya yi ya dawo da rayuwar Nimra ya roki gafararta. Tunanin yadda take rayuwa da shi a gidan ya dawo masa komai nata gani yake kamar lokacin yake faruwa, dariyarta ta cika kunnensa. Da sauri ya dauki key din motarsa da wayarsa ya fice daga gidan, sai da yayi kamar ya tafi gida kuma ya ji ba gidan yake bukata ba, kai tsaye gidansu Nimra ya nufa sai ya faka nesa da gidan yana kallon gidan, yadda motoci suke shiga da fita ya tabbatar masa da yarinyar da ya cutar ta bar duniya. Sai da dare yayi sosai ya juyo ya dawo gidan, ban da Mommy babu wanda ya san dawowarsa domin ya dawo a wani yanayi kamar ba shi ba. Dakinsa ya kulle ya rasa abun da zai yi, yadda gidansu Nimra ba a runtsa ba shi ma be yi bachin ba har garin Allah ya waye, washe gari yayi wanka ya shirya tun da wuri ya saka mask da bakin tabarau ya fice daga gidan. Gidansu Nimra ya sake komawa ya tsaya nesa da gidan yana kallon motocin dake shiga da fita, yana a gurin har aka fito da gawarta aka wuce da ita zuwa makabarta domin a cikin gidan aka yi mata Sallah sai da motocin suka yi nisa sannan ya bi bayansu har makabarta ya shiga ya tsaya can wani gefe domin ya san be isa ya taka karasa gurin, gawar Nimra ce first gawar da ya taba rakiya zuwa kabari, shi tun da yake a rayuwarsa be taba zuwa makabarta ba, sai dai ya gani

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login