Showing 99001 words to 102000 words out of 271643 words

Chapter 34 - Wani Gari Book 1 Complete Hausa Novel

number ya kwashe ya saka a wayarsa da danna kira. Sai da ya kira kira har sau uku ba a daga ba ya sake gwadawa ana biyar aka yi picking.

“Assalamu Alaikum”

“Wa'alaikussalam...”

“Who's this?”

“Ameer saurayin Nimra”

Wani deep Ummi ta yi ta nemi guri ta zauna kunnuwanta na sake saka mata sautin muryarsa, wasu zafafan hawaye suka kwankwaso mata kofa.

“Na san be kamata na kira ba, amman ina son mu yi magana ne ta fahimta, ina son ki duba ďakin Nimra ki gani tana nan?”

Ummi ta tashi da sauri ta fita dakinta ta isa kofar dakin Nimra ta tura kofar sai da ga babu kowa a ciki, ta leka bandaki bata ganta ba, a take ta girgiza kai.

“Bata ciki”

“Tana nan tare da ni, ta gudo ta zo inda nake tana son mu gudu ni da ita, saboda tace ba za ku yarda na aureta ba, ita kuma zata iya mutuwa idan kuka rabata da ni, sai dai ba zan iya bari ta aikata hakan ba saboda kuskure ne da zai kara mata tsana a idonku, please ki zo ki tafi da ita zan aiko miki da address inda muke yanzu nan. Ke uwa ce Ummi ban san dadin uwa ba domin na tashi ba tare da na santa ba, tawa uwar ta rasu tun ina jarari saboda haka ban san dadinta ba sai rashinta, amman ke yanyanki sun san dadinki kuma ke ma kin san ďadin yaya, be kamata ki bari Maleek yayi mata wannan dukan ba, da nine mahaifiya ba zai yarda wani yayi min haka ba, balle kuma uwa ta da na tabbatar zata iya hada yakin duniya saboda ta kare ni daga wani ya yi min jina jina a jiki haka, balle kuma Nimra da take mace ce, idan ba ku san alakarta da ni, ku fahimtar da ita cikin hikima da soyayya ba ku yi mata horon da fadan da tunaninta zai gushe har ta bar gidansu ta zo gurina ba, and i want to clean this doubt to you ban taba aikata zina da yarki ba, tsawon lokacin da muka dauka a tare tana boye soyayyata a gareku ba mu aikata abun da kuke tunani ba, i know I'm a bad person but ban taba yarki ba. For now zaki iya zuwa ki tafi da ita kamin mu bar gurin”

Tun da ya fara maganar har ya kai aya Ummi bata ce masa komai ba, sai sauraren muryarsa take wani bakinciki na bude mata sabon feji, hannu ta mika ta taba ginin dake bayanta ta jingina a hankali ta lumshe ido. Can kuma ta bude idon tana ta kallon number da ta yi appearing a truecaller da sunan Ameer. A yau ďanta ya kirata, amman ba kira na sanin cewa ita mahaifiyarsa bace, ba kira nw irin an ďa da uwa ba.

Sakon address inda suke ne ya biyo bayan kiran da yayi mata, ta mike tsaye har lokacin hawaye take, ta kasa tsayar da kuka kuma ta kasa saka hannunta ta share, saukowa ta yi downstairs ta nufi gurin mijinta, tana shiga falon sai ta samu Maleek da Abiey zaune da alama wani abun suke tattaunawa, sai dai shigowarta ya saka sun maida hankalinsu a gurinta.

“Nimra bata gidan nan”

“Kuma..?”

Maleek ya fada da mamakin wani irin hali yar'uwarsa ta daukarwa kanta.

“Ta gudu ta tafi gurin Ameer, ya kira ni a yanzu ya fada min inda zan same ta”

Abiey ya hade wani kwalolon bakincikin da ya tsaya masa a makoshi.

“Ina daf da yafe yarinyar nan...”

“Ba zaka iya ba Abiey, ka fi kowa sanin yadda ake ji idan iyaye suka juya baya, ko ka manta abun da ya faru tsakaninka da Mai Martaba? Ba zaka aikata hakan ga marainiyar da uwarta ta tafi ta bar mana amanarta ba, da ace ta saba aikata maka hakan sai ka ce ka gaji amman bata saba ba, kuskure aka samu ya kamata ka duba mata Abiey, ni bazan iya juyawa yata baya ba”

Ta juya ta fice daga dakin, da gudu ta iso bangarenta tana kuka ta shiga ta dauki hijan dinta ta saka ta dauki makullin motarta ta fito da saurinta ta sauko kasa. Tana fitowa waje sai ta samu Abiey Maleek sun data mota ita kawai suke jira.


AMEER POV.

Ameer ya aje wayar yana matukar jin tausayin halin da ya jefa Nimra, be taba sanin abun da yake aikatawa be kyautu ba sai a yanzu da ya firgita yar mutane ta fita daga hayyacinta. Bama kamar data fito daga bandakin yana kallon fuskarta ya san samun damar kebe kanta ta yi kuka ne kawai ta yi amaimakon wanke fuskar da yace ta yi, yana ta kallonta har Humaira ta zaunar da ita a kujerar da take zaune a dazun, wannan karon tausayine a fuskar Humaira ba kamar dazun ba, bata san abun da ya faru ba, amman yadda ta ga jikin Nimra da kuma kukan da take ya saka jikinta yayi sanyi tana jin tausayinta.

“Zaki iya cin wani abu na kawo miki?”

Humaira ta tambaya, sai Nimra ta girgiza mata kai alamar aa. Humaira ta kalli Ameer dake kallon Nimra.

“Ban san miya faru ba, ban san damuwarta ba, amman ka sani idan kai ka cutar da ita Allah ba zai barka ba”

Ta fada idonta na cika da hawaye, kallonta Ameer yayi yadda take iya fada masa magana ba tare tsoro ko fargabar abun da zai mata ba abun har mamaki yake ba shi, shi kam a rayuwarsa be taba haduwa da tsagera ba irin wannan yarinyar, ba dan ta samu damarsa ba har yaushe zata kalli tsabar idonsa ta fada masa cewar idan shi ya cutar da yarinyar da bata da alaka da ita Allah ba zai barshi ba, sai dai ta ďayan bangaren kalaminta ya sanyaya masa jiki domin duk wani mai imani da tausayi idan ya ga yadda Nimra take zubar da hawaye dole ya tausaya mata, musamman ma shi da ya san silar kukanta da kuma halin da ya jefarta.

“To yar iya na gode sai ki koma gurin aikinki”

Ta watsa matsa harara kasa kasa, tana zaginsa a ranta dan dai ba zata iya fada a fili ba.

‘Bakin Azzalumi macuci, shaidane mai karyar arziki, Allah kadai ya san abun da ya kullawa yarinyar ya yaudare, ita kuma ta fi kyau da kudi ta cutar da kanka, waya sani ma ko ciki yayi mata, dan iska dan kasan wuta... Da wani shegen hanci na shi kamar tattasai, kai kamar ganwon albasa’

Tana tafiya tana zaginsa a ranta, tana ayyana da ace ita ya cuta sai ta karya masa kafa ya zama gurgu.

“Ameer mu tafi yanzu”

“Okay amman akwai wanda nake jiran ya kawo min sako zan dan jira shi minti kadan”

Sai a lokacin ta fara jin ta tsargu sboda babu mayafi a jikinta kuma babu talkami. A da idan zata shigo gurin sai ta saka mask da glass saboda kar wanda ya santa ya ganeta. Dan karamin veil Humairah ta kawo mata tare da gorar ruwa mai sanyi.

“Karbi wannan ki rufe kanki”

Ta kalli Humaira sannan ta mika hannu ta karba, ta lulluba, Humaira ta mika mata gorar ruwa.

“Ba zan iya sha ba, bakina ciwo yake”

Ta nuna mata bakinta dake kumbure.

“Wayyo sannu Allah ya isar miki”

Ameer ya kalli Humaira da sauri ganin tana zakalkalewa.

“Ga wa?”

“Ga wanda ya cuceta mana, daman mace rauni ne da ita wasu mazan suna amfani da haka su cutar da ita, kuma idan mutum ya san be yi cuta ba miye ruwansa da Allah ya isa”

Wata uwar harara Ameer ya watsa mata, ba dan yana a yanayin da baya son biye mata ba, da sai ya gaura mata mari a gurin ko ta shiga hankalinta, domin ya kura bata tsoronsa sam kuma bata kunyar fada masa magana, sai dai baya a cikin yanayin da zai biye mata su siyar da hali a gurin, dan haka ya dauke idonsa yana kai zuciyarsa nesa ya tattara hankalinsa ya maida gurin Nimra. Ganin hakan ya saka Humaira ta juya rike da gorar ruwanta ta koma a iyakar gaskiyarta take neman Allah y isarwa yarinyar da zuciyarta ke raya mata Ameer cutar da ita yayi, ko da yake ta ďayan bangaren tana ganin kamar har da laifinta taya za'ace duk wakar nan da take mata idan suka zo gurin bata dauki haske ta gane Ameer yaudararta zai yi ba, saboda yawan taba ta yake ta kyale shi yana shiga jikinta gashi yanzu har ta kai yayi mata duka kuma ya dauko sun ta zo gurin babu ko mayafi a jikinta babu talkami.

Ameer na ganin kiran number da ya kira ta Ummi dazun ya fahimci sun iso gurin, sai ya yanke kiran ya aika mata da sako daidai inda zata tsaya ta jira shi. Sannan ya kalleta ya ce.

“Tashi mu tafi”

Gudun kar ya rikata su fita tare mahaifiyarta ta gani ranta ya bace sai ya nemi Humaira ta rika masa ita suka fito yana gaba Nimra dake dafe da Humaira tana bayansa, sai da suka iso gurin motarsa da yayi parking sannan Ummi ta bude motar da facing din ta su ta fito tana kallonsa kamanin da ta gani a fuskarsa da jikinsa sun matukar daga mata hankali zuciyarta sai rawa, ita kadai take masa kallon tausayi da kauna, Abiey da Maleek kuma suna matsa kallon tsana daga cikin motar kamin su bude su fito. Nimra na ganin iyayenta sai hankalinta ya tashi ta fashe da kuka.

“Ameer kaika kira su?”

Ya juyo ya kalleta.

“Ba zan iya bari ki aikata kuskure nan ba Nimra”

“Ba kai ka fada min zaka iya mutuwa a kaina ba?”

“Hakan baya nufin na cutar da ke a yanzu, ba ki san abun da yake kasa ba”

“Innalillahi Wa'inna Ilaihiraji'un ”

Ta fada tana runtse ido. Maleek da Abiey suka iso gurin da suke tsaye Ummi kuma ta kasa karaso sao kallon Ameer take. Abiey ya kai hannu ya fisgo Nimra daga hannun Humaira ya tsinka mata mari sai da wutar kanta ta yi daukewar wucin gadi. Sannan ya kalli Ameer cikin bakar fuska ya ce.

“Babu kai babu jinina, babu kai babu zuri'ata, babu kai babu iyalina...”

Ya juya ya nufi motarsa yana jan hannun Nimra da karfi, ita kuma da yake bata da kunya sai kiran sunan Ameer take, har mutane suka fara lura da abun da ke faruwa. Allah ne kadai ya tsare Ameer be fadawa Abiey bakar magana ba, domin babu mai fada masa magana marar dadi be rama ba, sai dai tausayin Nimra da son nema mata sassauci ya saka be furta ma Abiey komai ba, sai kallon Ummi dake tsaye tana hawaye yayi daga inda yake yake fadar.

“Wata kila kin taba yin so a lokacin da kike da kurciya, ban sani ba ko kin san yadda yake da zafi da rikita zuciya, CIWON SO yana da wahala da dimauta mai yinsa, mutum kan fita hayyacinsa ya aikata abun da be dace ba, dan Allah ki dubi Nimra da idon rahma, wanda be taba so ba idan ya samu ba zai fita ďakin son da sauki ba, karki bari mijinki ya cutarta da ita dan Allah. Bata watsar da tarbiyar da kuka mata ba, duk abun da ya faru ba laifinta ba ne laifina ne...”

Each and every words da ya furtawa Ummi sai ta ji kamar magana yake jefa mata, gaba daya duniyar ta juye mata upside down. Maleek ya tabe baki yana kallon Ameer da tsarki.

“Nice one Ameer kai kake furtawa Ummi wannan maganar saboda da baka da kunya kuma baka da mutumci?”

Ameer ya matsa kusa da Maleek yana furzar masa da numfashi da karfi tare da saka hannayensa aljihu yana kallon cikin idonsa.

“Saboda bana da uwa a raye ba shi yake nufin van san darajar uwa ba, kai kuma baka san miye soyayya ba, baka san CIWON SO ba, saboda haka be kamata ka tsoma rubabben bakinka ba, baka san komai akan masoya ba dan haka karka sake karanbanin shiga a abun da ka zahilta, zan raga maka ne kawai saboda Uwa...”

Ameer ya daga hannunsa ya nuna Ummi dake tsaye, suna kallon kallo akuya kallon kura shi da Maleek. Maleek yayi kamar ya fada masa magana sai kuma wata zuciyar ta hana shi ya juya yana huci da jin ďacin maganar da Ameer ya fada masa ya nufi motarsu.

“Wayyo Allah zuciyata...”

Ummi ta fada tana kai hannu ta dafe zuciyarta, Maleek ya rikata da sauri ya saka a back seat inda Nimra take zaune ya rufe motar sannan ya bude front seat ya shiga domin Abiey ne yake tuka motar. Daga Humaira har Ameer tsaye suka yi suna kallon motar har ta fice daga gurin sannan Humaira ta cire hannayenta biyu da suke dafe a fuskarta tun a lokacin da Abiey ya mari Nimra ta ji kamar ita aka mara ta dafe kumatunta bata dauke ba sai da suka wuce. Sannan ta kalli Ameer tana hawaye ta ce.

“Baka kyauta ba, kalli yadda ka saka ƴa da uwa kuka saboda selfishness dinka, ka san yadda uwa take ji idan aka lalata tarbiyar ƴarta? Wallahi kana da hakki da yawa akanka”

Ya juya zata koma ciki, ya saka hannunsa ya rika dantsen hannunta ya fisgota ya dawo da ita daf da shi har tana iya iya jiyo numfashinsa ya kalli cikin kwayar idonta ita ma ta kalli tasa...





©Khadeeja Candy
©®Copyright
2023

𝐖𝐀𝐍𝐈 𝐆𝐀𝐑𝐈

33

Sun dauki tsawon lokaci a haka ya kasa ce mata komai.

“It hurt...”

Ta fada slowly, sai ya kalli hannun nata ya sake.

“Ban yafe ba”

Ta fada da muryar da zai iya ji bayan ta wuce shi, yawu kawai ya hade ya nufi motarsa, ya bude ya shiga sai a lokacin ya kalli wayar Nimra dake hannunsa, samun kasan yayi da rashin sukunin abun da ya aikata, ya daga kujerar ta daya kwantar a dazun yana kallon gurin kamar tana nan, kamin ya kwantar da tashi kujerar ya kwanta a gurin gaba daya ya rasa ta inda zai dafa ya wanke Nimra, halin da ya jefata a yanzu ya matukar daga masa hankali, yana kwance cikin motar har la'asar sannan yaja motar ya fita daga gurin ya faka a gurin wani masallaci dake bakin hanya yayi sallah la'asar nesa da mamu.


*** *** ***

Har suka isa gida Nimra bata daina kuka ba, Abiey na faka motar ya fita ya nufi gurin masu gadi yayi musu gargadin cewar kar wanda ya kuskura ya bar Nimra ta sake fita daga gidan. Sannan ya dawo ya bude gefen da Nimra take ya fito da ita ya jefar a kasa kamar wanda be san inda ta fito ba, Ummi ta juyo da sauri ta kalleta sai dai bata da kuzarin da zata iso gurin domin zuciyarta a rike take. Abiey ya sake rika hannunta ya nufi cikin gidan da ita kamin ya isa falon Namra da Mahmood sun fito Waira ma tana bayansu, sai kowa ya kasa bawa Abiey hakuri ganin yadda fuskarsa take a hade kamar bakin hadari, tun da suke a rayuwarsu Abiey be taba saka hannu ya dakesu ba kuma ba taba yardar wani ya taba masa yara ba domin yana matukar kaunar yayansa, sai dai a yau shi da kansa yake yi ma Nimra hukunci. Sama ya hau da ita ta saka ta cikin dakinta ya janyo kofar da karfi.

“Kar wanda ya bari ta sake fita a gidan nan”

Waira na ganin zai saukowa ta yi saurin guduwa ta boya bayan kujera jikinta na rawa gani take kamar ita aka yi ma jina jina a jiki, a zatonta Abiey ne yayi ma Nimra wannan dukan daya canja mata kammanin. Tsoron kar ya hukuntata da laifin data aikata a dazun ya saka ta fashe da kuka tana rufe bakinta, dazun ma ba karamin fada yayi mata ba balle kuma yanzu da ya doki yarsa ita ma zai iya dukanta. Namra ta rika Ummi ta karasa shigowa falon ta zaunar da ita saman kujera.

“Ummi are you okay? Please kar ki saka abun da Nimra ta aikata a ranki”

Ummi ta juyo ta kalli Mahmood dake maganar tana kallonta cike da kulawa. Ta lumshe ido ta bude so take ta cika rokon da ďanta yayi mata na ganin ta bawa Nimra kariya.

“Je ka fito min da Nimra”

“Amman Ummi ba zaki hakura har zuwa anjima ba?”

Ta girgiza masa kai. Sai ya mike tsaye ya nufi upstairs ya tura kofar dakin Nimra ya shiga, kwance ya same ta a kasa tana kuka kamar ranta zai fita.

“Ta so Ummi tana kiranki ita ma kin saka ta kuka idan haka shi ne burinki, sakamakon da zaki yi mata kenan”

Nimra ta dago ta kalli Mahmood ta koma ta kwanta ita kadai ta san abun da take ji a zuciyarta, ganin ba zata tashi ba ya saka ya iso gurin ya rika hannunta yana janta da karfi domin shi ma a yanzu haushinta yake ji, sanin zata wahala ya saka ta fara rarrafe tana bin bayansa daker da sauko downstairs din, sai dai wani abu mai kama da kunya da jin nauyi ya hanata karasa inda Ummi take zaune, Maleek ya gurin dinning tsaye ya rumgume hannayensa yana harararta kamar zai cire.

“ƴa ta taso mana”

Ummi ta fada kamar ba komai tana kallon Nimra, kalaman da Ameer yayi mata a dazun ya dawo mata da tunanin rayuwarta ta baya, a yanzu tana iya fahimtar halin da Nimra take ciki. Bacin rai ya saka Maleek da Mahmood bari falon, sai Namra ce ta tashi ta riko hannun yar'uwarta tana kuka ta kawo ta gurin Ummi, Ummi ta rika kanta ta kwantar a kan cinyarta.

“Ya isa haka, wannan kuka ya isa Nimra ki kwantar da hankalinki ki saka ranki a inuwa, komai zai wuce kin ji? Karki sake kokarin guduwa ki bar ni saboda wani, kina tunanin uwa zata rayu idan babu yayanta a kusa? Ke kika da saurayi kika kasa jurewa balle ni da na haife ki? Kamin ki aikata wani abu ki rika tunawa da Umminki, kuma kin ga da acw guduwa abun kirki ne da wannan saurayin na ki be barki kin dawo ba, bude baki ki yi

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login