Showing 270001 words to 271643 words out of 271643 words

Chapter 91 - Wani Gari Book 1 Complete Hausa Novel

ba kuma kin sani”

“Zaka ba ni abincin na ci ko bata min rai zaka yi?”

Ya sumbanci hancinta da tsakiyar girarta.

“Lemme feed you Babyn baby”

Kujera yaja mata sai da ta fara zaunawa sannan ya zauna ya fara zuba musu abinci yana dariya, domin ya lura da gaske ta dauki zancen da zafi...



One year later......

Katon Event Center ne dake dauke da manyan mutane, decoration din kawai zaka kalla kasan biki na yayan naira. Manyan mata na sanye da ash lace yan mata kuma na sanye wani material mai kyalli maroon color, wasu kuma sun saka choice dinsu domin ba kowa yake son anko ba, musamman manyan mutane, a tsakiyar kuma Amarya da ango ne sanye da farare kaya, ango farar shadda amaryar kuma na sanye da farin yadi ta sha makeup ta rufe kanta da wani mayafin fari mai kyalle wanda ya sauko mata har kasa. Humairah ce tsaye tsakanin Amarya da ango sai watsa musu kudi tana tana dariya tana takawa. Kamin Ameer ya isa gurin rike da dansa Bashir da aka yi ma alkunya da Areef na tsakanin hannunsa da kafadarsa, ya ciro nasa kudin ya fara zubawa Mahmood da Amaryar Fiyya, fiyya ta karkata ta koma gefen Ameer ita da shi suka yi ta rawa jama'a na taba musu shi kansa Mahmood din sai da ya koma yana musu karin kudi, MC sai wasa yayan Amarya yake, Ummi ma tasowa ta yi ta watsa musu kudi tana murmushi, kusan kowa sai da ya taba musu a gurin.
Duk abun da ake Nuwaira na zaune a table dinsu ita da Maleek sai wasa hakora take. Can kuma ta kalleshi ta dago masa hannunta.

“Dan Allah ka cire min robar nan dan Allah Ya Maleek”

“Na cire miki roba ki shiga ki yi rawa?”

“Kadan zan yi?”

“Au ashe ma zaki yi din da gaske, ana kallonki da ciki dako dako ki shiga ki yi rawa saboda idonki ya zare ko?”

“To ina ruwanka cikin naka ne ko nawa?”

“Toh da naki ne? Cikinki ne?”

Ya mike tsaye sai shi na ya mike domin robar da ya saka mata a hannu ita da shi basa iya yin tazara.

“Wai ina ka siyo wannan shegen roban ne?”

“Saboda bikin nan na siyota daman na san cewa zaki yi sai kin yi rawa ai”

“Wallahi yau sai na maka kuka kala kala, idan mun koma gida”

“Ki fara tun a nan ma”

“Ko har nan da shekara biyu ba zan manta ba sai na ta yi maka kuka”

“Lokacin ai kin kara hankali ba zaki yi ba”

“Ya Maleek dan Allah ka bari na yi rawa”

“Ko baki da ciki ni bana sha'awar wannan rayuwar da mata suke zuwa cikin mutane suna rawa da sunan biki, balle kuma kina da cikin nan”

Ta fara masa kukan tun anan domin ta san kukanta a abun da ya fi tsana a yanzu.

“To ina son na musu liki ai”

“Okay cry cry baby mu tafi”

A tare suka jera suna tafiya ya rike hannunta mai robar ya saka yatsansa a cikin nata amman hakan be hana ta tana tafiya tana dan takawa ba, domin kidan dake tashi ko malam sai dai yace babu kyau ba dai ya ce babu dadi ba. Suna iss gurin ya ciro kudi ya mika mata sannan ya saka hannayensa ya zagaye ta zama tsakanin kirjinsa da hannunsa haka take likin har sai da ta gama, sannan ya ciro nasa ya lika musu, Nuwaira sai taka take ba damar ta zake ta yi rawa Maleek ya hanata wali, dukawa ta yi zata fita tsakankanin hanayensa sai ya riko hannunta, ya kai bakinsa kunnenta ya ce.

“Zaki ji ma kanki ciwo ne wannan robar ba zata bari ki tafi ko'ina ba”

Ta kalli robar baka ce mai kamar abun hannu sai wata yar danja ja dake jikinta, ta saka dayan hannun ta murza ta murza.

“Ba zan sake zuwa da kai biki ba Ya Maleek ko na gidanku ne sai dai ka zauna a gida”

Mahmood yayi dariya domin cikin masifa ta yi maganar kuma a bakin gaskiyarta take ba zata sake zuwa da shi biki ba. A yanzu ta gano dalilin da ya saka yace kar ta tafi tare da sauran yan biki ta bari su tafi tare, kuma tun a mota yayi mata wayo ya saka mata robar da sunan ta masoya ce ashe ba haka ba ne. Tana hango Ummi ta nuna masa ita

“Mu tafi gurin Ummi zan yi magana da ita”

“Mu tafi”

Tare suka isa tana isa ta kai bakinta saitin kunnen Ummi ta kai karar Maleek. Ummi ta kalli robar ta kalleshi.

“Cire mata mana haka kawai ka hanata walwala?”

Namra dake tsaye bayan Ummi tana kokarin gogewa yaronta bakin ta saka dariya.

“Gaskiya Ya Maleek kana da matsala, yau din ma da ake bikin dangi ba zaka barta ta wala ba?”

Shi dai be ce komai ba saboda Ummi take kusa.

“Ka cire mata shi Maleek yanzu nan?”

“Toh Ummi abun cirewa yana mota ai ta zo muje a cire”

“Ummi wayo yake miki Allah kuwa”

Ta fada a shagwabe kamin ta dago ta kalli gurin da Kanenen Ameer suke zaune wato yayayun Fiyya da aka yi aurensu a tare ta daga musu hannu, suma suka dago mata.

“Ba wasa nake ba key din yana mota”

“Bishi ku tafi ya dauko ya cire miki, haka kawai zai takurawa yata a cikin mutane”

“Ni ma ai shi na gani”

Nuwaira ta fada, Maleek ya girgiza kai yana murmushi ya ja suka fita daga gurin, yana tafe tana masa mita har suka isa gurin motar, jinginar da ita yayi jikin motar ya fara mata chakulkuli a wuya.

“Ni zaki yi kara gurin Ummi”

Ta saka dariya da kuka a lokaci daya.

“Give me a kiss”

Ta mika masa bakinta ya sumbanta sannan ya bude mata motar ta shiga ya zagaya ya shiga dayan side din ya rufe ya saka motar a lock.

“Kin ga yanzu sai mu zauna ni da ke a nan har a gama, idan kika gaji sai mu tafi gida”

Sai kawai ta fashe masa da kuka, dariya yayi ya kwanto dakanta jikinsa inda rigimarta ce ya saba da ita, tun da suka yi aure ta zame masa kamar wata yarinyar goye, indai tana kusa da shi shagwaba babu kalar wadda bata masa, rigima ma babu kalar wadda be sani ba tata, har ta kai yanzu idan be ga ta masa ba baya jin dadi. Fir Maleek ya murje ido ya hanata fita motar har aka tashi bikin, aikuwa suna komawa gida ta ce babu shi babu zaman lafiya, abinci ma sai yayi da gaske sannan ta ci ta kwanta kuma ba dan bata jin yunwa ba sai dan ta wahalar da shi. Tun da ta samu cikin ba zama lafiya kullum da kalar fitinar da take masa, daman can da take ita kadai ta yi masa haka balle kuma yanzu da ta suka zama su biyu. Haka dai yayi ta juriya tana biyewa hallayarta har Allah ya sa ta sauka. Ranar da ta haihu kamar ya hadeta murna kamar ya zuba ruwa kasa ya sha, ita kuma rarrashinta yake ta yi kamar ya lashe. Ranar sunan Baby ta ci sunan Ummi aka saka mata sunan Ummi wato Fadimatul Zahra, aka yi mata alkunya da Teema, duk wanda ya kalli yarinyar ya san yar Nuwaira domin fuskarta ta dauko gaba daya kadan ta tsakuro a fuskar Maleek. Idan aka yi magana sai Maleek yace saboda tana mace ne idan suka sake haihuwa shi zata biyo.




*** *** *** *** *** ***

Rayuwa ta zamewa Ummi a yadda kowa be zata ba, girma ya kama ita da Abiey jikoki sai kewayesu suke iyalai ta ko'ina sai hamdala. Abubuwa da yawa sun zowa iyalin ta inda ba su zata ba, a. Rayuwata koma cikin jindadi da farinciki, idan wannan ya sauke wannan ya dauka ranar da aka so week gida ko aka yi hutu Ummi bata da zaman lafiya saboda yawan magana da bari bari, hakan ya saka kullum gidanta baya rabo da sweet da kayan kwalama. Domin bayan Abiey yanzu tana da wasu mazajen kuma sojiji ciki har da masu sunan Abiey da ake kira da Aliyu Haydar wato dan Namra yarta ta biyu kuma ana kiranta da Little Nimra. Rayuwa cike take da kalubale wani lokacin dadi wani lokacin wahala, wani lokacin kuma a hada maka duka, wani sa'in kuma sai wahalar ta wuce dadi ya zo wani dadin kuma baya zuwa sai bayan wahala. So many blessings sun sauka ga iyalan wadda ya wanke duk wani kalubale da kunci da aka shiga, komai ya zama labari sai idan ya tuna.



Alhamdulillah Thumma Alhamdulillah

Yabo da godiya su tabbata ga Allah tsira da amincin Allah su tabbata ga Annabinmu Annabi Muhammad Rasulullahi Sallalahu Alaihi Wassalam. Alhamdulillah na gode Allah da ya bani ikon rubuta wannan labarin ina addu'ar Allah ya sa mu amfana da shi.

Kuma ina son na yi amfani da wannan damar na bawa wadanda na batawa rai akan rashin sani, kuskuren ko ganganci, a gafarce ni a yafe min 🥺🙏

Haka kuma ina sanar da wadanda suka karanta ba su biya ba, cewa ba free ba ne domin sauki nauyin hakkin karatu pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith Bank.

Littafin sadaukarwa ce ga Asma'u Badamasi (Asmee yar gagara) Safiyya Dan jumma (Ummul Falsak mai kan kwakwa) Salma Gidado (Salwees ƴar yarinya) Allah ya shiryaku.


Godiya ga duk wadanda suka siya littafin nan suka karanta shi ta hanyar halak, Allah ya bar kauna duka Fan's dina ina gaisheku a duk inda kuke, sai mun hadu a littafina na gaba mai suna HURIYYA labari mai ban tausayi da taba zuba, kuma mai dauke da rikita rikita.


Best Regards 🥰🙌
Khadeeja Candy ❤
080361266660


Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login