Showing 87001 words to 90000 words out of 271643 words

Chapter 30 - Wani Gari Book 1 Complete Hausa Novel

ya aje domin yau ko marmarin part dinsa haya yi tsabar murna da farincikin ganin yar'uwarsa, Ummi ta daga kan Waira da ta yi bachi ta aje a kan kujerar a hankali sannan ta tashi ta dauko masa abincinsa ta jera masa komai a inda yake zaune. Abun ka da ďan'uwa cin abincin da Dr Zainab ta yi a dazun be hanata karawa a yanzu da ďan'uwanta yake cin nasa ba, hira suka sha sosai har kusan sha ďaya na dare Ummi tun tana saka baki ana yi da ita har ta fara jin bachi, sai hamma take tana murza ido.

“Toh Sarkin bachi ya fara kawo ziyara ko? Har yanzu baki daina bachi da wuri ba, na dauka duk kin watsar da ragancin nan ai”

Karaf Abiey yayi tare numfashin yar'uwarsa yana shigarwa matarsa.

“Doctor yadda Zahra take da juriya ko ke zaki iya ba a yanzu, duk fa yawancin aikin gidan nan ita take yi, ko bata ti girkin kowa ba sai ta yi nawa saboda ban son abincin kowa sai na matata da uwata kin kuma sani, ai tana kokari ma, da ke ce da yanzu kin yi bachi, ko kin dauka na manta yadda kike ne?”

Dariya ta saka ta girgiza kai, yadda yake tsokanarta sai ka rantse ita ce kanwa shi ne yaya, ko kuma ka yi zaton yan yaya da kanwa ne ba yaya uwa ďaya ba. Maleek ya tashi ya fice daga falon yana murmushi daman ya san halin Abbansa idan yar'uwarsa na kusa baya raga mata kamar yadda ita ma take masa idan ta tashi ramawa. Ummi bata bar falon ba sai da ta kira Mahmood ganin shiru shiru be dawo ba gashi har dare ya fara lulawa.

“Ga mu a hanya, Jabir ne ya debe mu nesa kin san ya kwana biyu be shigo garin ba, amman dai mun kusa isowa gida”

“Toh Allah ya kawo ku lafiya”

Ya ake wayar kusa da inda Waira take kwance ta dauki babbar rigar da Abiey ya cire tare da jakarsa ta nufi bangarensa, ko minti uku bata yi da shiga ba, ya shigo yana cire agogon hannunsa tare da kiranta da sunan da ya saba kiranta tun kurciya har yanzu da girma ya zo, soyayya bata canja ba balle ya sake mata sunan da har gaban yayansa idan ya kama yana kiranta da shi.

“Hiayatee ya gidan?”

Ya aje komai a muhallinsa sannan ta juyo tana taya shi cire rigar dake jikinsa ta dauko masa bathrobe ya saka, sannan ta shiga ta hada masa ruwan wanka.

“Yau ka yi latti dawowa, na yi zaton zaka dawo da rana ma saboda zuwan Aunty Zainab”

“Na so na dawo, amman aiki ya rike ni Wallahi”

“Ya dai kamata ka huta Abiey, yaranka sun kawo yanzu wani abun za su iya maka shi, by the time ka kawo tsufa hutu ya kamata ka samu, muma iyalinka mu samu time dinka”

“Wani abun dole ne sai ka yi da kanka, ko da na so na cire hannuna abokam kasuwancin ba za su bari ba, amman dai komai lokaci ne”

“Kullum haka kake fada, kuma lokacin tafiya yake yi baya jiran kowa Abiey, lokuta da yawa ina jin son kasancewa da kai amman baka da time sai dare ko kuma da safe kamin ka fita, akwai abubuwan da ya kamata ace kana saka ido akansu a gidan amman rashin zamanka baya bari, nima kuma ba kullum nake son kasancewa da yara ba”

“To zamu duba, abun da Hajiya take so shi za'ayi dole, zamu aje abun da zai aju wanda ya kamata a rage kuma za mu rage, har ma da wanda za a bari In Shaa Allah”

“Toh Allah ya bada iko”

“Ameen Allah ya miki albarka”

Ta yi murmushi ta bude wardrobe ta fara ciro masa pajamas, shi kuma ya shiga bathroom din, kamin ya fito ta feshe su da turare ta dauko masa maganinsa na ciwon kafafuwa da yake sha ta aje masa tare da ruwa. Sai da ya shirya ya sha maganin sannan ta fita ta koma bangarenta ta hado masa coffee, a lokacin babu kowa falon sai Waira dake bachi da kuma Plasma dake kunne. Bangaren mijinta ta dawo ta kawo masa coffee da ya saba sha tun can baya ta mika masa kana ta zauna kusa da shi tana labarta masa labarin Waira. Tunanin namijj ba ďaya da na mace ba, haka zuciya ma ta mace ta fi tausayi da saurin yarda. Hakan ya saka Abiey be yi saurin amincewa da labarin da Ummi ta ba shi ba, ba Ummi yake karyatawa ba, Waira ce lamarinta ya ďan daure masa kai.

“Amman ta ya aka yi kika tabbatar gaskiya ta fada miki?”

“Kasan ba tun yau ba, na sha yi mata magana akan garinsu da abun da ya shafi rayuwarta bata fada min komai, idan ka lura bata da sakewa irin yadda ya kamata, kusan kullum a tsorace take bata da walwala, kuma yanayinta sai ya rika min kamar mai tunanin wani abu, wata kila tana tsoron fadar garinsu ne, kar ace za a maida ita”

“Maida ta kam dole ne”

“Tace kasheta fa za'ayi”

“To ya kike son ayi mata?”

“A barta ta zauna a nan tare da mu kawai, gudun kar mu maida ita mu jefata a matsala”

“Hajjaju ai ko zata zauna tare da mu, dole ne sai mun san inda yan'uwanta suke, dole ne mu san garinta da kuma dalilin da ya saka suke son kasheta, ko kuma kina tunanin haka nan kawai za su kasheta ba tare da wani abun ba,? Ko da tana da gaskiya ya kamata mu ji gaskiyarta, kuma idan har zata yarda ta fada mana garinsu ai ba mu kadai ko kuma ita kadai zata tafi ba sai tare da jami'an tsaro, bayan haka kuma za mu sake kafa shaida a gurin jami'an tsaron saboda su san duk abun da yake faruwa ko da wani abun ya taso”

“Ba zan hana a fadawa police ba, amman dai zuwa garinsu ai kamar tona mata asirine idan ma yan garin ba su san inda take ba, ka ga mun bude musu hanya sai su aikata mata abun da suke so, kuma fa ta fada ma Jabir iyayenta sun rasu bata san iyayenta”

Ya kai hannunsa ya dafa kafadar matarsa a kokarinta na saitata a hanyar da yake ganin za au bulle musu.

“Madam, ki zauna da ita ki yi hira da ita cikin hikima ki yi mata tambayoyi ki saurari labarinta ko iya ta nan zamu gane gaskiyarta kuma mu fahimci halin data fito, sannan na sha miki magan akan nunawa yarinyar addini amman baki kula da wannan”

Ya aje cup din dake hannunsa.

“Na kan nuna mata tallar addini ne kawai ban fara mata ba, kuma ka san ba ayi ma mutum dole a addinin musulunci”

“Na sani, amman yanayin mu'amalarki da ita da kuma yadda kika nuna kyaun addinin shi zai saka ta ji tana sha'awar shiga, ya kamata ki rika nuna mata wasu abubuwan”

“Zan yi kokarin yin haka”

“Toh Allah yayi miki albarka, ya bada iko Hajiyata”

“Ameen”

Ta amsa da murmushi, sannan ta mike tsaye tare da daukar cup din tana fadin.

“Bari naje na duba Aunty Zainab”

“Duk ke kadai wai aikin gidan nan be miki yawa ba? Ya kamata dai a kawo miki mai taya ki gaskiya”

Domin kawai ya tsokane ta yayi maganar, sai ya yi sara akan gaɓa ya sosa mata inda yake mata kaikayi.

“Kamar kasan abun da yake raina kenan Wallahi, kawai na rasa ta ina zan fara maka maganar ne”

Dariya yayi

“Kamar gaske, mata ai basa son abokiyar zama balle ke da na san ki da kishi”

“Kishi ai na yara ne ranka ya dade, yanzu mun wuce wannan kuma har ga Allah ina son ka karo wata saboda ka samu mai maka wasu abubuwan ko da bana nan, kara ka saba tun yanzu abun zai fi maka sauki”

Ba fahimci yarenta, hakan ya saka shi nitsawa a duniyar zoyalarta da yake.

“Kuma idan na tashi kawarki zan auro”

“Ai ba ni kawar da bata da aure a yanzu, a dai duba mai mutunci wacce zata son yayanka”

“Hauka kenan ban yi aure da kurciya ba zan yi shi yanzu da furfurata a gemu, yayanki ma ai ba za su bari ta zauna lafiya ba, ke din dai ke ce Allah ya bar min abata har mutuwa ya sa ke za ki min wanka”

Ummi ta yi murmushin da ita kadai ta san abun da take sakawa a ranta sai kuma Allah.

After like 30 minutes da barin Ummi da Abiey bangaren, Mahmood ya dawo gidan tare da Jabir da Umar, ba su shiga bangaren Ummi ba sai suka tsaya a dayan side din da mostly idan aka yi baki a nan suke sauka saboda wadatar gurun kuma an samar da komai a ko wanw ďaki. A waje suka ci na su abincin na dare dan haka ba su damu da leka bangare ba Ummi ba. Maleek kuma be fito daga dakinsa ba sai karfe ďaya saura, ya sauko sanye da nasa pajamas din, Plasma dake kunne ya fara nufa ya kashe, yana juyowa Waira na farkawa sai ta tashi zaune tana kallonsa da idonta masu kamar na mage. Tashi tayi ta dauki wayar Ummi dake kusa da ita ta haura sama, bata dade ba ta sauko har lokacin yana tsaye gurin Plasma doing nothing thinking nothing, zuwa ta yi ta boya bayan cushion din da ta kwanta. Sai da ya fara kallon gurin for like 15 to 20 seconds sannan ta taka a hankali ya leka, sai ya same ta ta kwanta a kasa ta takure guri daya take rike da wayar Ummi, ba tabawa take ba ta dai rike wayar kawai. Upstarts ya nufa yana hawa ya tura kofar ďakinta a hankali sai ya hango Yesmin kwance a kan gadonta, slowly ya rufe kofar ya nufo downstairs, saukowa tai daidai ta fitowar Ummi daga bangaren Abiey rike da cup a hannunta.

“Aljanin dare baka kwanta ba?”

Ya ďan yi murmushi kaďan kamar na amsa mugun dole.

“Abinci nake son ci”

“Okay”

“Yarinyar nan bata kwanta ba”

Ummi ta juyo tana kallonsa domin ta yi rabin falon, jin muryar Ummi ya saka Waira ta fito daga inda take ta nufo Ummi.

“Waira Baby kin tashi?”

Ta daga mata kai.

“Kina jin yunwa”

Ta daga kai.

“Zaki sha tea? Ko madara?”

“Tea”

Ta amsa, sai Ummi ta kama hannunta.

“To zo muje mu hada tea”

A tare suka shiga kitchen din Ummi ta hada tea a cup biyu ta bata ďaya ďayan kuma ta ce ta dauka ta kaiwa Maleek, sai ta girgiza mata kai.

“Aa”

“Dauki ki kai masa ba ni na saka ki”

Ta aje nata cup din ta dauki na Maleek ta fito kitchen din tana tafiya a hankali ta nufi inda yake zaune a dinning yana cin nasa abincin daren, kusa da plate din da yake cin abinci ta aje masa tea a hankali. Sai ya dago ya kalleta.

“Tea Ummi ta ce Waira ta kawo Tea..”

Ta fada sannan ta juya ta nufi hanyar komawa Ktchen din yana binta da kallo.




©Khadeeja Candy
©®Copyright
2023
29

“Kin kai masa Tea”

Ta daga sai Ummi. Ta girgiza mata kai.

“Bude baki yi min magana”

“Waira ta kai ma Ya Maleek Tea”

Ta saka Yaya ne saboda haka Nimra ke kiransa.

“Ba haka ake cewa ba, cewa zaki yi Na kai ma Ya Maleek Tea din”

“Na kai ma Ya Maleek tea din”

Ta maimaita kamar yadda Ummi ta bukata, sai Ummi ta yi murmushi.

“Good daga yanzu idan na yi miki magana ki rika bude baki kina amsa min, kin ga dazun na ji haushi duk zamana da ke a gidan nan baki taba bani labarinki ba, amman wani yana zuwa kin fada masa komai har dariya kike masa sosai ana jin muryarki ko'ina”

Ummi ta yi sad face tana bayyana damuwarta a fili, sai Waira ta kama kunnenta ta ce.

“I'm sorry Ummin”

A karo na biyu Ummi ta sake yin murmushi.

“Good na yi hakuri amman karki sake kin ji ko?”

Har ta daga kai sai ta tuna da Ummi tace ta rika bude baki tana mata magana, a take ta ce.

“Tohm”

“Minene Good ma?”

Ta mata thumps up tana dariya.

“Yayi kyau”

Ummi ma dariyar ta yi ta dauki tea ta mika mata, muje falo ki zauna ki sha idan kika gama sai ki kwanta. Kamar mai jiran umarni sai ta karba ta juyo ta fito kitchen, gurin da set din kujerun falon suke zata nufa sai Ummi ta dakatar da ita.

“Zo ki zauna a dinning”

Ta juyo sai ta kalli Maleek dake zaune yana ci abinci ta kalli Ummi, Ummi taja mata kujerar dinning dake kusa da Maleek, ta mata haka ne saboda ta sake jiki da shi, domin shi ne kadai mutumen da bata shan inuwarsu sai kuma Namra. Bata son musu hakan ya saka ta taka a hankali ta isa gurin ta zauna a kujerar da Ummi taja mata, ta rike tea da hannu biyu marikin cup din ta yi sama da shi, haka take idan tana shan tea ko a abu a cup sai ta rike da hannu biyu. Bayan ta zauna Ummi ta bar dinning din zuwa duba bakinta, jikinta ya bata Maleek kallonta yake hakan ya saka ta juyo ta kalleshi sai ta ga idonsa yana kan zoben dake wuyanta, ta kalli zoben sannan ta dago sai suka hada ido.

“Ummi tace Waira ta zauna nan”

Ta fada da sauri gudun kar yace ta masa laifi. Shi kuma sai ya amsa mata a ransa.

“Kin ji nace miki wani abu ne?”

A zahiri kuma sai ya dauke idonsa daga barin kallonta ya cigaba da cin doyarsa, juyawar da yayi sai ya bata damar rama kallon sarkar wuyanta da yayi, sai dai ita a yanzu a fuska take kallonsa kamar wani hoto ko kyaftawa bata yi, ta gefen ido ya ga tana kallonsa kuma kallon ya kasa barinsa ya samu natsuwa har sai da ya dago ya kalleta, abun ka da wanda be iya munafurci ba sai ta kasa dauke idonta taga barin kallon nasa, idonta suka fara blinking babu tsayawa kamar marar gaskiya, can dabara ta zo mata sai ta rumtse idon gaba daya. Samun kansa yayi da murmushi a cikin zuciyarsa ya dauki ruwan dake gabansa ya sha ya ja kujerar baya ya tashi ya bar mata dinning din.

Ummi dakinta ta fara dubawa sai ta tarar har Dr Zainab ta yi bachi, gudun kar ta yi motsi mai karfi ta tasheta ya saka ta shiga a hankali ta bude bathroom ta yi wanka tare da wanke baki sannan ta fito ta dauko kayan bachinta ta saka ta fito tana ta kamshin turare. Dakin Namra ta fara budewa ta leka saita same ta ita kadai tana bachi, daman can ta san Namra ba zata kwana da kowa a dakinta ba, idan har wani zai kwana akan gado daya da ita kara ta kwana akan kujera, ita dai bata son ta motsa ta ji wani a kusa da ita. She has so many rules and regulations na banza da take sakawa kanta just to be unique. Ac dakin Ummi ta rage ta ya janyo mata kofar ta maida ita a yadda take. Sannan ta nufi dakin Nimra abun ka da mai son jama'a sai ta same ta ita da Juwairiyyya suna kwance a gado daya, sai dai da alama Nimra bata shiryawa bachi ba, domin wayarta ta fado kasa hannunta kuma yana lilo a gefen gadon ga wutar dakin a kunne ba kamar Nimra da ta kashe nata ba. Ummi ta karasa ta duka ta dauki wayar sai ta ga missed calls biyu daga heart emoji guda uku, ga kuma wani sako a saman screen din wayar.

(𝑫𝒐𝒏'𝒕 𝒕𝒆𝒍𝒍 𝒎𝒆 𝒌𝒊𝒏 𝒚𝒊 𝒃𝒂𝒄𝒉𝒊 𝒕𝒖𝒏 𝒚𝒂𝒏𝒛𝒖 𝒌𝒊𝒏 𝒃𝒂𝒓 𝒏𝒊 𝒅𝒂 𝒌𝒆𝒘𝒂𝒓𝒌𝒊, 𝒈𝒂𝒏𝒊 𝒂 𝒏𝒂𝒏 𝒔𝒂𝒊 𝒋𝒖𝒚𝒊 𝒏𝒂𝒌𝒆 𝒂 𝒃𝒆𝒅 𝒊𝒏𝒂 𝒔𝒉𝒂𝒌𝒂𝒓 𝒌𝒂𝒎𝒔𝒉𝒊𝒏 𝒕𝒖𝒓𝒂𝒓𝒆𝒏𝒌𝒊, 𝒃𝒚 𝒕𝒉𝒆 𝒘𝒂𝒚 𝒌𝒊 𝒔𝒂𝒏 𝒊𝒓𝒊𝒏 𝒌𝒂𝒓𝒚𝒂𝒓 𝒅𝒂 𝒛𝒂𝒌𝒊 𝒚𝒊 𝒈𝒐𝒃𝒆 𝒎𝒖 𝒉𝒂𝒅𝒖 𝒊 𝒂𝒍𝒓𝒆𝒂𝒅𝒚 𝒎𝒊𝒔𝒔 𝒚𝒐𝒖, 𝒊 𝒄𝒂𝒏'𝒕 𝒘𝒂𝒊𝒕 𝒇𝒐𝒓 𝒚𝒐𝒖𝒓 𝒉𝒖𝒈 𝒂𝒏𝒅 𝒌𝒊𝒔𝒔 𝒌𝒊𝒏 𝒔𝒂𝒏 𝒃𝒂𝒏𝒂 𝒈𝒂𝒋𝒊𝒚𝒂 𝒅𝒂 𝒌𝒆 𝒊 𝒍𝒐𝒗𝒆 𝒚𝒐𝒖 𝒔𝒘𝒆𝒆𝒕 𝒅𝒓𝒆𝒂𝒎)

Wani irin tashin hankali da fargaba irin na uwa mai ƴaƴa mata ne ya bayyana a fuskar Ummi, jikinta ya dauki rawa as well as zuciyarta dake bugawa, she can't believe ta ga sakon nan a wayar ƴarta ƴar ma Nimra wacce zata rantse idan aka saka mata yatsa a baki ba zata ciza ba, a cikin sakon babu abun da ya fi daga mata hankali kamar inda yake cewa ta san kalar karyar da zata yi su hadu? Su hadu a ina? Ina suke haduwa? Why not ya zo gidansu idan sonta yake? Wani ta hadu da shi yake mata wayo haka? The hug and kiss part ma abun tashin hankaline, Nimra zata iya rumgumar wanda ba mijinta ba har ta sumbance shi? Bayan wannan sai kuma me? Ummi ta kalli Nimra dake sharar bachinta hankalin kwance bata san abun da ke faruwa ba. A hankali Ummi ta aje wayar a gefen gadon ta juya ta nufi switch din dakin ta kashe sannan taja kofar a hankali ta fice, gaba daya jikinta yayi sanyi, tunani kala kala ya fara zuwa mata har da wanda be kamata ta yi ba a lokacin, tafiya kawai take tana saukowa basa not knowing downstairs take saukowa har sai da ta ji Waira kira sunanta.

“Ummi ta shanye tea”

Ta kalli saitin inda take ta sauke wani uban ajiyar zuciyata ta kai hannu ta dafa zuciyarta, tunanin mai kokarin gurbata mata tarbiya ƴa take, kawa ta hadu ita marar tarbiya ko kuma saurayi? Amman idan kawace ya akayi bata san da ita ba a matsayinta na uwarta? Sai a yanzu take gane maganar da hawasa suke cewa mai ƴaƴa mata hannunsa a kirji yake har sai ya aurar da su, idan kuma ya aurar ba ya rufe ƙofa. Ta bawa Yayanta yarda 100% saboda tarbiyar da take ganin ta yi musu hakan ya saka wanin abun bata damuwa ta zafafa bincike kwakwaf akansu ba.

“Waira zo muje ki kwanta dare yayi sosai”

Waira ta taso ta nufo inda Ummi take sai Ummi ta rike hannunta suka haura sama, ta shiga da ita dakinta ta bude wardrobe ta dauko mata kayan bachi ta aje mata akan gado.

“Shiga ki yi wanka ki yi brush zan jira ki a

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login