Showing 135001 words to 138000 words out of 271643 words
Chapter 46 - Wani Gari Book 1 Complete Hausa Novel
𝐀𝐦𝐞𝐞𝐧🥰
*Littafin WANI GARI na kudi ne biya ki karanta cikin aminci pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith Bank, then send the evidence to 08036126660*
44
Kamar mashayi haka Ameer ya isa gaban motarsa sai budewar ya gagareshi, saboda rashin kuzari da kuma rawar da zuciyarsa take wadda ta haifar da jikinsa zazzabi. Jinginawa yayi jikin motar ya kife kansa wasu kalar hawayen sauko masa wadanda be san daga ina suke fitowa ba. Sai dai ya san a rayuwarsa be taba kuka da bakinciki da jin tashin hankali a lokaci daya kamar yau ba.
Meyasa ma ya zo duniya? Akan me rayuwarsa zata yi tsayin da zai ga wannan bakar ranar a yau? Da ace ya mutu kamin yau da yafi masa domin be sam komai ba. Matar nan kullum addu'a nake mata ina jin na rasa wani gurbi na uwa, ina jin abubuwa da yawa da ace tana raye ba zan aikata ba ko na rasa ba, ashe tana raye, ta kuma san ina raye amman ta kasa zuwa duba ni ta kasa nemana sai a yanzu da ta shirya tarwatsa rayuwata, me zai saka ya zubar da hawaye? Akan macen da bata cancanci zama uwa a gareshi ba? Wani bangare na zuciyarsa ya karanta masa, a take ya ji kukan ya yanke masa, kuzarin da ya rasa ya taho da gudu ta yarbe shi, fa sauri zazzabin ya bar jikinsa. Sai ya bude mota ya shiga yayi reverse, yanayin yadda yake tuka motar har ya fice be nuna yana cikin tashin hankali ba, duk kuwa da kasancewar hakan ya kasa boyuwa a fuskarsa.
Tafiya mai nisa yayi kamar zai fita garin Abuja, kawai be san inda zai tafi ba, ya tafi gidansa ya kebe shi kadai? Ya kama hotel ya zauna? Or yayi ta driving har ya gaji? Ya rasa na zaba atsakanin abu ukun da zuciyarsa ke lissafa masa. Sai dai definitely ya san baya bukatar zuwa gida a yanzu, ji yake kamar ba zai jure kallon Mr Bashir a matsayin wanda yayi adopted dinsa ba not his biological father, duk rayuwar da suka yi a tare duk wahalar da Mr Bashir ya sha a kansa ace ba mahaifinsa ba ne? Ya dauki nauyinsa ya rike shi tsakani da Allah all this ahi ba mahaifinshi na gaskiya ba ne? All this wealth da ya tashi a ciki ya ga Mr Bashir na juyawa har ta kai shi ma ya isa sarrafa wani abu daga ciki, ba mahaifinsa ba ne? Yadda yake sakar masa kudi da duk wani iko da gata still he's not his biological father? Even for once Mr Bashir be taba nuna masa cewar shi ba ďansa ba ne. Ya cire shi a kowace kalar rigima ya bashi damar aikata duk abun da yake so ya daure masa gindi still ba mahaifinsa ba ne? Zuciyarsa ce ta buga da mugun karfi abun da kwakwalwarsa take kalato masa ya fi karfin tunaninsa, wani hudu bakincikin mai zafi ne ya rufe masa kirji. A take ya ji babu wanda yake bukatar gani kamar a lokacin kamar Mr Bashir, kamar mahaukaci haka ya taka burki ya juya motarsa tsakiyar titi he just got lucky titi babu manya motoci a lokacin, ko da ma akwaisu ya shirya yin haka domin jin yake kamar rayuwarsa bata da amfani a yanzu. Sai da ya kusa isa gidan then ya sake jin bana bukatar shiga cikin gidan ba dan an masa laifi ba, rauni zuciya yake kusantoshi a duk lokacin da rai ya rasa masa ganin fuskar Mr Bashir. Faka yayi nesa da gidan ya fito waje ya tsaya yana kallon motar kamar mai tunanin abun yi? Jin kamar numfashi zai gagareshi ya saka shi bude motar ya dauko ruwan gora ya daga kansa sama ya kafa gorar a bakinsa ya fara shan ruwa kamar rakumi, ragowar kuma ya daga gorar sama suka zubar masa a fuska suka jika jikinsa musammansa ma kirjinsa dake masa zafi kar an watsa masa tafasasshen talge a ciki.
“As Simple as that you just look in to my eyes kika fada min cewar ke ce mahaifiyata? Akan me? Me yasa ba zata bar wannan ya cigaba da zama a sirrin ba?”
Ya tambaye kansa wasu hawayen ya cika idonsa?
“Ina take son na rayu? So take na tsani duniya? Me jindadin rayuwata ya tsare mata?”
Ya sake tambayar kansa a karo na biyu, yana jifa da empty gorar ruwan dake hannunsa.
‘Saboda ka taba Malee ne, kuma ka taba Nimra su ai yayanta ne da take matukar kauna’
Zuciyarsa ta amsa masa tambayarsa da amsar da zata fi gamsar da shi. A take ya girgiza kai yana kara gamsuwa da hakan, domin a lokacin da duk wannan be faru ba, bata nuna cewar shi danta ba ne, a yanzu ya yarda da maganar Hajiya Jamila cewar bata sonsa, kalli yadda wanda ba ubansa yake nuna masa kauna fiye da iyayensa, kalli Hajiya Jamila ma yadda take sonsa. Tabbas da ace Ummi ma tana sonsa ko da tabin haka ne da bata barshi ya tashi a hannun wani yana masa kallon ubansa ba. Yanzu ya duniya zata kalleshi? Taya zai fuskanci mutane? Alfarmar da yake samu ta mahaifinsa zai rasa a yanzu, korar wanda yake so da bawa wanda yake so aiko ko mukami ya fita a hannunsa a yanzu, mutanen da ya wulakanta saboda yana jin cewar shi dan Mr Bashir ne ya za su kalleshi idan suka ji? Mutuwa ce kawai be yi ba a lokacin amman komai na duniya ya taru ya tsaya masa cak a lokacin. Yana kallon wayarsa na kara ya kasa dagawa kuma ya kasa kashewa. Yana tsaye a gurim har aka kira sallah Magariba, that's what he can't afford to miss, sallah in time, wannan ne a abun da ya saka shi shiga motarsa duk kuwa da kasancewar ba kiran sallah ya ji ba, domin unguwarsu tafiya ce mai nisa tsakaninsu da massallaci that's why kowa yake yin masa masallacin a gida, for masu kula da addini kenan, wasu kuma babu ruwansu da gina Masallaci, though he's muslim App ya gane Magariba ta yi saboda kiran sallah da app da ya fara. Yana fara tukin wayarsa ta kara ringing sai ya kalli inda wayar take aje, number Hajiya Jamila ce take kiransa da sunan da yayi saving number ta wato Ammy with heart emojis. Ya amsa kiran and put the phone on speaker.
“Ameer kana ina? Ka daga min hankali, na kira mahaifinka yace min baka gida, shi ma yana ta kiranka baka daga wayarsa ba? Please Ameer ka san muna matukar kaunarka, mu ba kamar Zahra ba ne, idan ka shiga wani hali ko ka illata kanka zamu shiga uku ba, ba zamu iya bearing rashinka ko shiga damuwarka, dan Allah karka jefa kanka a matsala please we love you kuma ka sani, sanin gaskiya ba zan saka mu canja maka komai ba, ba zai canja cewar kai ďan mu ba ne, sai ma kaunarka da tausayinka da suka karu a zuciyarmu”
Cikin kuka take fada masa hakan, shi ma hawayen yake yana jin tausayinta da kuma na Mr Bashir da kansa a lokaci daya.
“I promise you ba zan jefa kaina a halin da hankalinku zai tashi ba, i will control my temper, i will take care of myself”
“Thank you, please pick up your phone call your dad ka yi magana da shi”
“Does he know kin fada min gaskiya?”
“No kawai na kira wayarsa a saboda na kiraka baka daga ba, sai ya fada min shi ma ya kira baka dauka ba kuma na san ya damu”
“I already reach home bye”
Ya yanke kiran ya jingina jikin motarsa, this is the first time da ya taba tsayawa haka a gate din gidansu peacefully ya danna horn yana jiran a bude masa. Yaja motar kamar marar lafiya ya shiga yana ta kallon bangaren da mahaifinsa yake. Calmly ya faka motar ya bude ya fito ya bar wayarsa da takardar da Zahra da bashi tare da hoton ya nufi Garden. Tun da yake a rayuwarsa be tana kunna fonfon Garden yayi alwala na sai yau, saboda yana matukar kyamar gurin, kasancewar ma'aikatan gidan suna yawan zuwa gurin diban ruwa idan babu a fanfon masallaci. Damuwa ta mantar da shi dokokinsa na ware kansa da yake a masallaci yana sallah a one place ba tare da hada kafada da sauran mamu ba, sai gashi a sahun gaba, wani direban Daddy yayi ikama, mai bawa fulawowayin gidan ruwa yaja Sallah, kamin su sallame mamaki ya cika kowa. Ya sallame kamar yadda ake sallame ko wace sallah magarib, ya karanta addu'o'in sallah as usual ya daga hannunsa zai yi ma mahaifiyarsa da be taba manta ta mutu ba addu'ar samun rahma a kabarinta, sai ya tuna she's alive and healthy, hawaye suka zubo masa, saurin rumtse ido yayi ya hade yawu, ya mike tsaye sannan ya bude idon ya fice daga masallacin. Fitowarsa ta yi daidai da shigowar Motar Daddy, saboda kauna irin ta uba da ďa sai Daddy ya kasa tuka motar ya wuce ďansa sai sauke gilashin motar yayi yana tukin daidai tafiyar Ameer da ya ki yarda ya kalleshi, but murmushi yake saboda ya boyewa Daddy damuwar da ta bayyana kanta a fuskarsa.
“Yau na yi latti ka riga ni samun jam'i”
“Mu ma yanzu muka gama sallah”
Yanayin yadda ya amsa masa da kuma muryarsa da kallonshi da Ameer ya kasa yi ya kuma damuwar da ya gani a fuskar dansa, ya saka yayi saurin isa inda yake aje mota ya faka, domin shi yake tuka kansa da alama fitar ba mai nisa ba ce, domin jallabiyar dake jikinsa ama ta nuna haka. Kamin Ameer ya iso Daddy ya fito motar yana kallonsa. Sai Ameer ya kasa karasawa inda yake ya yanki hanya ya shige bangaren Mommy. Daddy na ganin haka ya ciro wayarsa dake pocket ya kira Hajiya Jamila. Kamar tana jiran kiransa domin ringing daya ta fara ta yi picking.
“Kin kira ni dazun, kina tambaya ta Ameer na fada mikin nima na kira shi be daga ba, and now yarona ya dawo gida, baya son kallon idona, na ga damuwa da ban taba ganin irinta ba a fuskar ďana, ya kasa karasowa kusa da ni ya shige bangaren Mommy, fada min me kike fada masa?”
Hajiya Jamila dake sanye da hijabi tana zaune gaban TV ta yi shiru for a seconds sannan ta ce.
“Gaskiya na fada masa, saboda ya bukaci na fada masa, kuma ya yi min ikirarin cewar idan na masa karya zai tsane ni, ba kuma zai sake yarda da ni ba, ba zan iya rusa wannan alakar dake tsakanina da Ameer ba, domin na fika sonsa, na san komai daren dadewa gaskiya zata bayyana”
“Da gaske kike yi? Ba duk gargadi da na yi miki?”
“Me yasa baka gargadi Zahra ba? Sai ni? Kana tunanin har yanzu kana da iko da ni? Ko kana tunanin zan manta irin butulcin da ka yi min bayan duk abin da na aikata saboda ka samu farinciki mu jidadin rayuwar aure na aikata? Amman duk baka duba wannan ba, a tsame ni a gidanka, ka raba ni da ďan da nake kallo a matsayin nawa, ďanta ruwan nonona ya taba zauna cikinsa, ďa daya tilo da na taba rumguma a hannuna a matsayin jaririna, ďan da duniya take kallo a matsayin ni na haife shi, kana tunanin duk zan manta da wannan? Ai kaima ka cancanci ka ji dacin da na ji”
“Idan har zaki iya fadawa Ameer gaskiya, to ba son gaskiya kike masa ba, kuma a yanzu na gode Allah da ya raba ni da ke tun wuri, kuma fada masa gaskiya ba zai canja komai ba, Ameer is still my son, babu wanda ya isa ya kwace hakan daga hannuna, har ita mai ikirarin uwarsa, na yi ma mijinta gargadi saboda ya ja mata kunne, idan kuma ba su ba, na san yadda zan yi da su all, and from today babu ke babu Ameer”
Ya yanke kiran ya nufi bangarensa yana takawa da karfi, kana ganinsa kasan ransa a bace yake. Ameer sai da ya kwatanta Daddy ya shige cikin sannan ya shiga bathroom dinsa ya wanke fuskarsa ya fito rike da towel yana goge fuskar. Boutique dinsa ya shiga ya tsaya a dakin yana kallon yadda Daddy ya zuba masa tufafin sakawa kamar shi ya fi kowa gata a duniya.
*Littafin WANI GARI na kudi ne biya ki karanta cikin aminci pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith Bank, then send the evidence to 08036126660 ki huta karanta na hakki*
Juyawa yayi kadan ya kalli kansa a katon madubin dake nuna har talkamin kafarsa. Zafin yana kirjinsa da idanuwansa, kansa yake kallo amman a badini gobensa yake hangowa, this is the most painful truth he has ever know gaskiya mai mugun daci da dafi a zuciyarsa. Hoton fuskar mahaifinsa dake jikin moton da Ummi ta ba shi yana ta dawo masa a ido yana ganin kansa a matsayin mahaifinsa. Ya jefar da tawul din a tsakar dakin ya fito kamshi na tsara shi ta ko'ina the women he thought is his step mom tana sakawa a gyara masa dakin a saka masa kamshi kamar yadda yake so saboda tasan abun da yake so kenan, kuma Daddy ya fada mata zaman lafiyarta ta yi ďansa abun da yake so.
Ya fito waje ya sauko falon ba tare da ya bar kowa ya ga fuskarsa ba, one of his fav Sis tana masa magana ya ki kulata ya fice daga falon. Cikin motarsa ya koma ya zauna ya dauko takardar yarjejeniyar ya sake karantawa countless times ya dauki hoton Deen ya kura masa ido, sai a yanzu ya lura sam baya kama da Daddy ta ko'ina, but how come be taba lura da hakan ba? Bude motar yayi ya fice rike da takardun bayan ya dauki wayarsa ya nufi bangaren Daddyn feel dizziness.
NAMRA POV.
Ta yi murmushi tana daidaita tsayuwarta.
“Mai jiki da sauki sosai”
“Maa Shaa Allah, Allah ya kara mata lafiya, ke fa ya kike?”
Shuraim ya tambaya a dayan bangaren.
“Ina nan kalau, saboda kana kusa ni, yaushe zaka sake shigowa kasan dai ba zaka wuce ba tare da mun sake ganin juna ba ko?”
“Zan zo hakan, ko dan ma yarinyar nan Waira, saboda na kasa manta yadda na barta a gidanku, tana ta kuka ta shiga damuwa, kanwarki ma na so na zo an dubata, amman ina tsoron yanayin da yan'uwanki ko iyayenki za su kalleni”
Iyakar kokarin da ta yi na danne abun da ta ji ne a lokacin da ya ambaci cewar zai so zuwa ko dan Waira.
“Ban gane ba, me ka gani a gurin iyayena kuma?”
“Sai na ga kamar ba jindadin zuwa na ba, bayan na gama bayyana musu ko ni waye, especially your Dad yanayin yadda yake amsa min ya nuna cewar ya san mahaifina, kuma kamar be yi maraba da ni ba”
Alamar mamaki ne ya cika fuskarta domin bata jin wannan ba, saboda ba a gabanta ya gaisa da su ba, kuma tashin hankalin da suka samu kansu a ciki na ciwon Nimra ya saka ba ta yi maganarsa da kowa ba.
“Ka fada masa wanin abun da be dace ba ne? Ko kuma akwai wani abu a nasabarka da be dace kowa ya sani ba?”
“To ban sani ba a halin yanzu, har sai na samu mahaifin mun yi magana da shi, amman ni ma san babu wata illa a nasabata sai dai kamin na tafi ina bukatar sake ganin ki gaskiya, kuma ina son ganin yarinyar nan please”
“Kana dai son ganinta, ba da ni ba”
“Both ke da ina ina mamarin ganinku, ita saboda na kwantar mata da hankali ta natsu, ke kuma saboda nawa hankalin ya kwanta, so please ki saka mana meeting point kuma ki zo min da ita”
“When?”
“Yau if possible, idan kuma ba zai samu ba zan hakura har zuwa gobe, ba dan haka ba babu abun da zai saka na sake kwana garin Abuja”
“Zan kiraka idan abun da kake bukata zai samu”
“Ganinki mai samuwa ne na sani, sai dai fitowa da Waira ne ba ni da tabbaci, amman dai ki min kokari please”
“Okay”
“That's my Babe Girl i love you ”
Ta samu kansa ta kasa amsa masa da i love you too kamar yadda ta saba sai sakon godiya data aika masa ta kashe wayar, ta juyo yana kallon Nimra dake bachi. Me yasa Abiey yayi masa haka shi ne abun da ya fara zuwa a ranta kamin ta fara jin kamar ta tsani Waira saboda yawan maganarta da Shuraim yake dan zuwan nan da ya yi. Daf da zata zauna aka turo kofar dakin sai ta fasa zaman ta kalli Maleek da ya shigo fuska babu walwala ba kuma zata ce ransa ne a bace ba, domin ba ta ga alamun haka ba, ya kusa cin karfin damuwarsa dan haka bata bayyana a fuskarsa ba, yana a wani yanayi da abu ne mai wahala ka bayyana halin da yake ciki, damuwa ce ko bakinciki ko rashin lafiya da jindadi ba kuma zaka ce yana cikin farinciki ba, haka kuma baka isa ka ce yana nishadi ba.
“Sannu da zuwa”
Da kai ya amsa mata ya zauna a kujerar dake fuskantar Nimra, yana kallon kanwarsa ta rame sosai kamar ba ita ba, har yanzu oxygen ne a bakinta da hancinta numfashinta na tafiya wahala kamar dai wanda yake daf da bankwana da duniya.
“Ya jikinta?”
“Da sauki, gashi har ta samu bachi, da bata iya bachi kuma likitan yana tsoron yayi mata allurar bachi saboda yanayinta, amman ga dukan alamu yanzu sauki ya fara zuwa”
Hannu ya kai ya shafa kanta da babu dankwali yana jin tausayinta, domin ta fada tarkon mutumen da ya tabbatar ko sama da kasa za su hade ba zai aureta ba, gashi tana ta wahala akansa. Namra ma kallonta take har sai da wayar Maleek tayi ringing sannan hankalinta ya koma gurinsa.
“Ina asibiti gurin Nimra”
“Akwai maganar da nake son mu yi mai muhimmanci Maleek, akwai abun da ya kamata ka sani”
Mahmood ya fada a dayan bangaren.
“Akan ciwon Ummi?”
“No akan Ameer”
“Me ya kuma ya faru?”
“I can't tell you on the phone, sai dai