Showing 159001 words to 162000 words out of 271643 words

Chapter 54 - Wani Gari Book 1 Complete Hausa Novel

kuma yaji ba zai iya ba saboda gadarar ta tashi. Sun bashi littafi ya saka details dinsa, sannan aka kira Waira ta zo office din, ta shigo tana sanye da uniform, gashin kanta a fake a baya an sako shi ya sauko a bayanta, blue and black din uniform din ya mata kyau sosai. Tana ganin Ameer bata tsaya komai ta rumgume shi da murna.

“Da gaske zaka zo ashe”

“I said i will”

Ya amsa fuska ba yabo ba fallasa.

“Motana yana waje muje can mu yi magana”

“aa zaka jira mu tashi ne sai mu tafi tare, kai zaka kai ni gida zai mu yi magana a hanya”

“Let's talk first”

“Okay kaje ka jira ni a mota yanzu za a buga karaurawa”

Ya juya ya fice daga office din, sannan mutumen ya kalleta ya ce.

“Kin san shi?”

“Sosai”

“Okay ba wani matsala ko?”

Ta amsa masa babu da kai sannan ta juya ya fice. Ajinsu ta koma ta zauna a kujerar ta hada littafanta ta saka a jaka sannan ta kufa kanta a teburin da take karatun domin kowa da kujerarsa, haka take bata da sakewa a makaranta saboda suna mata kallon bare, gashi ita kuma ta kasa sakin jiki da saba da kowa, a kullum idan ta shigo makarantar tana maida hankali tayi abun da ya kawo ta ne, wannan ya saka take daga cikin students masu kwazo da saurin gane abu idan aka fada, ko aka yi musu bayani, secondly lessons din da ake mata a gida yana matukar taimaka mata sosai, sai dai sauran daliban da suka maida hankali kamar ita sun fita experience domin sun fara daga farko ne ita kuma ta hau abun ne daga sama.
Tana jin na kada ƙaraurawa ta goya jakarta da sauri ta dauko cake din da Ummi ta yi mata dake karkashin table dinta ta fice cikin zumudi ta nufi gate, a ka'ida idan za a fita daga makarantar sai anyi signed daga mai daukar har dalibai idan kuma School bus ce zata kai su gida zai sun yi shi ma mai tukin yayi da nufin shi ya kai su gida. Ita ta fara saka hannu a inda ta saba, sannan security ya nufi inda motar Ameer take ya kai masa littafi ya karba yayi sign din. Sannan ta bude front seat ta shiga yana kallonta sai ta sakar masa murmushi.

“Ya karatu?”

“Ba dadi”

Ya rage idonsa yana kallonta, he can't lie tana da kyau duk yadda zai misalta abun ya wuce tunaninsa, ba ma kamar yanzu da yake ganin nishadi da murna a fuskarta.

“Why?”

“Bana son karatun ni ai, Ummi forced to do so”

“If you don't want babu wanda zai saka ki dole, you can tell her”

“Ko na fada mata ba zata bari na zauna a gida, kuma Ya Maleek zai yi fada he hate me so much”

Ta dan bata fuska ta turo baki, irin batawar da ya kara mata kyau domin a shagwabe ta yi maganar. This is the second time da ya ji abubuwa suna burgeshi akanta, far'arta da kuma bata fuska ko wanne kyau yake kara mata. Ba dan ya tabbatar ita din ce yarinyar da ya gani a can duniyar ba mai matukar kazanta da datti da ko za a hade kur'ane a rantse masa ba zai yarda ita ce aka gyara ta zama kyakkyawa haka ba, har wani abu nata yake burgeshi, yarinyar fa ganin bera a kanta ya saka shi amai, gashi a yanzu ko yar minister ba zata gwada mata kyau gashi ba, domin an gyara mata shi ya kwanta lum ya kara baƙi sai sheki yake kamar ba nata ba.

Ta bude dan box din cake din ta saka hannunta ta gutsira cake cin ta ci. Yanzu kuma bakinta yake kallon yadda take motsa shi a hankali tana cin cake din, ta dago ta kalleshi sai ta dauki karamin spoon dake gefen box din ta saka ta dibi cake din ta kai masa saitin bakinsa. Ya kalli cake din sannan ya kalli fuskarta.

“Akwai dadi ka ci, na aje ban ci ba saboda kai, ban yi break ba”

Ya bude baki ta saka masa ya fara taunawa, ta aje spoon din ta saka hannunta ta fara ci.

“Akwai dadi?”

Ya daga mata wani irin kallonta yake kamar ya hadeta. Ta sake daukar spoon ta diba ta kai masa a baki ya karba ya ci, sai ta aje ta saka hannu tana ci.

“Ni bana ci abinci da wannan”

“Why?”

“A garin mu da hannu muke cin komai, ya fi dadi”

Ta saka saka dauka ta kai masa a baki, wannan karon da hannunta ta kai masa. Sai ya dan tsaya kallonta sannan ya bude bakin ta saka masa.

“Ummi ce ta yi min yayi dadi sosai”

Cak ya tsaya da taunawar da yake, fuskarsa ta canja daga ba yabo ba fallasa to ba yabo, hannu ya kai ya dauki tissue ya zuba ragowar a ciki ya sauke glass ya jefar. Wani iri yake ji ace mahaifiyarsa tana raye amman be taba cin abincinta ba ko sau daya, be san yadda girkinta yake ba.

“Tambaye ni abun da kike so, zan tafi”

“Kai zaka kai ni gida ai, na fadawa Ummi ba school bus zata maida ni ba”

Ya juyo ya kalleta kamar ya ce wani abu, sai kuma kwarjininta da ya cika masa ido ya hana shi kin cewa komai. Ya maida hankalinsa gaba ya jaya motar suka kama hanya, ko da wasa be sake kallon inda take ba.

“Ka yi fushi kuma? Saboda na baka cake din Ummi? Why do you hate her?”

“Why don't you ask her why she hate me from first place?”

“She didn't, tana sonka sosai Ameer”

“Kuma ta bar ni? Ita tace ki zo ki ba ni cake? Ki siye ni da kalamai?”

“Aa bana karya, bata ce tana son na baka cake ba, daman ni abincina daga cake sai biscuits ko fruits, tana yi min cake kullum”

Yayi shiru be ce mata komai ba, sai hawaye da suka cika idonsa.

“I'm sorry”

“You shouldn't”

“Ummi tana sonka sosai”

“Waira ke yarinya ba ki san komai ba”

Ta tari numfashinsa.

“Na san komai, na san komai tun kamin Ummi ta fada min na san komai”

Ya kalleta

“Taya? Wannan dan iskan Maleek ya fada min ko?”

“Ni bana hira da Maleek, he hate me shi ma kuma ni na fada masa, na sani ne ssboda ina iya sanin abun da ya faru da mutum”

This time around dariya yayi.

“Waira kina tunanin kin fini wayo? Kina iya sanin abun da zai faru miyasa kike tambaya waya koya min busa?”

“Be zama lallai ka sani ba, amman idan na rumgume ka zan iya sani”

“Then what are you waiting for?”

“Stop the car”

Ya samu guri ya faka gefen titi sai ta bude gefenta ta fita ta zagaya inda yake ta bude masa.

“Fito”

Samun kansa yayi da bin umarninta ya fito daga motar, sai ta rumgumeshi ta rufe ido, saman kanta yake kallo hannayensa na zube a muhallinsu, ta kai minti talatin tana rumgume da shi, shi be gaji ba kuma be saka hannu ya rumgume ta ba ko yace ta sake shi, duk kuwa da irin abun da yake ji. Ta dago ta kalleshi da kamar tsoro.

“Eid ya koya maka?”

Ta daga mata kai, ba dan yarda tana iya ganin past life din mutum ba.

“A garin da ka je karatu? Kana yawan busar sarewa amman baka iya mai kyau kamar nasa ba”

“Maybe kin san shi, shi ya fada miki cewar ya koya min”

“Be fada min ba, amman na san shi, shi ďan'uwa ne, na san da cewar shi kadai ya iya busar shiyasa nake mamakin yadda naji kana busawar”

“Na ji wannan sai kuma me?”

“Yau ka kade wata tsohuwar ka kaita asibiti”

“A motata akwai jini maybe kin ga jinin ne, cewa tsohuwa ce kuma wannan kin canka ne kawai, look Waira ke da Ummi ba za ku iya wasa da kwakwalwata ba”

Ya juya zai shiga sai ta ce.

“Ranar da Ummi ta fada maka ita ce mahaifiyarka, ka tafi gurin wata mata Humaira, ka fada mata damuwarka. Jiya kanwarka Fiyya ta shiga ďakinka ta yi magana da kai, kamin ka zo nan daga office kake. Kana shirya yadda zaka bar garin nan ka koma wata duniyar da babu wanda ya sanka ka zauna, ranar da Nimra ta mutu ka zo nan da dare, sa safe ma ka zo, da kai aka kaita makabarta, kuma shi ne zuwanka na farko, wannan shi ne karo na farko da wata ta yi hatsari ka tsaya ka dauketa ka kaita asibiti kuma har ka sakata a motarka, kamin ka zo nan kaje gurin wanki mota, sai ka yi tunanin za su yi zargin ka kashe wani sai ka fasa bada wanki ka zo da motar a haka, kana son ka tambaye ya aka yi na zama haka ya aka yi na iya hausa, ka taba ganina a school bus a lokacin da baka gane ni ce ba, ni kuma ban ganka ba..... ”

Haka ta rika zayyano masa abubuwan da suka faru da bata sani ba, da kuma wadanda ya san be yi maganarsu da kowa ba sai kansa. Tana fara maganar ya juyo yana kallonta da tsananin mamaki har ta kai aya.

“Ya aka yi kika san haka?”

“Wannan shi ne sirrina da ban taba fadawa kowa ba, ina ganin rayuwar da ta faru, ta haka ne na gane Ummi tana dauke da cutar leukemia, ba tare da ta fadawa kowa ba, ta haka na gano yadda take ta boye soyayyarka a zuciyarta, na gano damuwarta na son rayuwa da kai ni na fadawa Iyalanta tana dauke da cutar da take stage 3”

“Duba kike yi?”

“Bana duba, al'adar garinmu kowa yana irin baiwarsa ta tsafi ne, sai dai ni tawa ta sha banban da saura, saboda ana jiran na kai wasu shekaru ne a ba ni sarauta ta sarauniyar matsafa da garin, sai kuma gashi na gudu saboda an zarge ni da kashe kashe wani, alhalin ban aikata ba?”

“Me yasa ba ayi amfani da tsafin an gano ba ke kika aikata ba?”

“Ban tsaya jiran a gano ba, na gudu saboda bana son sarautar kuma a dokar da aka saka min idan na gudu kashe ni za'ayi”

Hawaye ya sauko idonta.

“Ina iyayenki suke?”

“ba ni da iyaye, duka sun mutu, ni kadai nake rayuwa a cikin wani daki, tare da beraye da zakaru, ban san wani abu dadi bachi ba sai da na zo nan, ban wani ya kira da ya ba sai da Ummi ta kira ni, ban san gatan da dadin dake cikin wanka kullum ba sai a wannan duniyar, ban san saka wani tufafin a kullum ba sai a nan, tun ana yi min da karfi, har na fara yi da kaina saboda na saba, a yanzu ko wane dare sai na yi wanka na wanke baki nake kwantawa, tsabanin can da ban san wani abu tsabta ba, ni da iyayena suka mutu sun tafi sun bar ni a cikin wata kazamar rayuwa, ni ce bana son tsabta bana son wanka saboda ina ganin hakan shi ya fi min, kuma ni zan iya mutuwa a kowane lokaci saboda na san ba za su kyale mu ba, ni da Ummi duk mutuwa muke jira, ita tana son ta gyara komai kamin ta tafi, tana son ta rabe ka ka kyautata maka, ni kuma bana son komai sai dai na san bana son mutuwa”

Be san lokacin da ya rumgume ta ba, ya lumashe ido hawaye suka zubo masa.

Sai ta fashe da kuka sosai.

“I can take you back, zan maida ke inda na dauko ki, zaki nuna min hanyar garinku, zamu tafi tare mu roki yafiyarsu”

“Ba zan gane hanya ba, sun bata da komai a kaina, wanda ba dan garin ba, ba zai shiga garin ba, ba za su yafe ba, ba za su saurari kowa ba, ba zaka iya ba”

“Zan iya Waira i will do this”

Ya sumbanci saman kanta.

“Ni dai ina son, kamin na mutu ka zauna lafiya da Ummi, ita tana sona sosai, ita ce ta zama min uwa, a gurinta na san abun da ƴa take ji idan uwarta tana raye, ta ba ni duk wani jindadi bata kyamata tun ina da kazanta, ina son ka yi rayuwa da ita lafiya, ina son na ga haka kamin na mutu ko kuma ita ta mutu, ina son farincikinta, Ameer ko wani dare na gani tana kuka saboda kai, tana kaunarka sosai tana son kasancewa da kai, kana da iyaye ai kai Ameer ba zaka taba sanin dadinsu ba har sai basu da rayuwa, na yi mamarin nawa, idan ina son ganinsu sai da na rumgume danginsu na ga hoton fuskarsu na ga rayuwarsu i miss them”

Ya dagota daga jikinsa ya sake hannunsa biyu ya share hawayenta.

“Ba zaki mutu ba, babu abun da zai same ki, na saka taimakonki a lokacin da ganki a daji, yanzu ba zan ki taimakonki ba”

Ta daga kanta tana kallonsa.

“I won't hurt anyone anymore, domin ban san ta inda zan fara neman gafara ba i regret what i did to Nimra i wash...”

“Then don't hurt your mother, karka dawo ita ma kana nadama a lokacin da bata nan, we're all making mistakes, kowa yana yin kuskure muna yin ba daidai ba to miyasa idan wasu sun yi ba daidai ba ba zamu yafe musu ba?”

Yayi murmushi yaja kumatunta.

“You're so brilliant”

Ta yi murmushi tana kallon cikin idonsa da blue eyes dinta.

“Zaka yafe mata?”

Yayi shiru.

“To zaka so ka zauna da mu?”

Wannan kam a take ya amsa mata.

“No no”

“Please bana son ka bar ni, ni bana da dangi a yanzu kai ku, mutumen da nake so rasa su nake, kuma ka ga ni ba dadewa zan yi ba idan na mutu sai ka tafiyarka”

“Wayo kike min Waira you're just building a room for Ummi”

“I'm building a room for all of us, ina son mu yi rayuwa a gida ďaya, kamar iyali daya a gidan nan Nimra ce kawai take so na sai Ummi da Mahmood, Ya Maleek baya so na, Abiey ma baya so na, na rasa Eid, da Sulem i don't want to lose you too”

“You wouldn't, idan kina so zaki iya magana da Ummi ki dawo gidanmu da zama”

“Me yasa kai ba zaka zauna a gidan Ummi ba? Why do you hate her”

“Saboda ba zan iya zama karkashin inuwa ďaya da Maleek ba, ba zan iya zama a gidan mahaifinsa ba”

Ta kama hannunsa.

“Please”

Ya rike hannun nata yana murzawa a hankali. Kamar daga sama suka ji muryar Maleek.

“Ke Waira”

Ta zabura ta juya da sauri tana kallon inda muryarsa ke fitowa, Ameer kam ko dago kai be yi ba balle ya kalleshi kuma ya ki ya saki hannunta duk kuwa da irin kokarin da take tana son kwace hannun. Ummi ta bude mota ta fito ta biyo bayan Maleek da ya nufo inda Ameer da Waira suke tsaye.

“Maleek Maleek bari na yi magana da shi”

Shi ne abun da take fada tana kokarin rikowa shi domin ta lura da yadda ransa yayi matukar baci.

“Daman na raya a zuciyata kai ka dauke ta, tun da muka je makarantar aka ce mana wani ya zo ya tafi da ita, na raya kai ne sai gashi ina duba details din abun kuma sai na ga kai din ne”

Ameer ya saki hannun Waira ya kalli Ameer fuska kamar bakin hadari.

“Me ye a abun kunya? Biyo yarinyar da ka tsana har makaranta da sunan daukarta, ko kuma tare abokinka a hanya kana fada masa maganar banza a lokacin da mahaifiyarka take kokarin hanaka?”

“Thank you ka ce Mahaifiyata ashe ka san bata cancanci zama uwar kazamin yaro irinka ba”

“Sai kuma gashi ta haife ni, ya ranka?”

“Fessss haihuwarka kawai ta yi bata amsa sunan mahaifiyarka ba”

Ummi ta dakawa Maleek tsawa.

“Maleek ina ganinka kamar mai hankali? How could you say those words to your own brother?”

Ameer yayi murmushi yana kalleta.

“Karki damu, Maleek be taba zama ďan'uwana ba and he wouldn't be, he is just a friend shi ma kuma a can da”

Ameer ya maida dubansa gurin Waira.

“Shiga mota na kai ki gida”

Ta girgiza kai da sauri hawaye na mata zuba, jikinta sai rawa yake ita dai daman can bata son ta ga ana tashin hankali balle kuma a yanzu da take ganin kamar saboda ita ne komai ya faru. Da ido Maleek yayi mata alama da ta wuce zuwa gurin motarsa. Ta fara takawa Ameer ya fisgota ya dawo da ita.

“You should know your limit kai ba ubanta ba ne da zaka rika juyata yadda kake so she's under no one control but me”

“Saboda kai ne ubanta kenan?”

“Saboda ni ne silar zuwanta nan”

Maleek yayi murmushi da ya fi kama da dariya.

“Yarinyar da ka ce baka sani ba? Yarinyar da ka bari a mota saboda kana tunanin ta mutu? Yarinyar da ka wulakanta? Ashe dai ka santa kenan Maleek what a shame”

“Okay that's enough, kuna kunyata kanku ne kawai a gaban idona, ku daina saka ta a cikin matsalarku you guys have no idea what she's going through”

Ummi ta kama hannun Waira dake ta kuka ta nufi motar da suka shigo da ita ta barsu a tsaye idan ma cinye junansu za su yi sun dade ba su yi ba. Ganin ran Ummi ya bace ya saka Maleek bin bayanta ya bar Ameer tsaye a gurin yana kallonsu. Ummi da Waira baya suka shiga shi kuma ya shiga gaba yaja motar suka kama hanya.

“I warned yarinyar nan, Ummi do you plan this?”

“Yanzu kuma ni ce bar zargi ka gama da da zaka dawo a gurin uwarsa?”

“Ummi ta ya aka yi ya san lokacin da suke tashi? How ma ya zan makarantarsu? Kuma ke kika ce kar school bus ta dawo da ita, secondly tun dazu nake cewa mu taho amman baki fito ba sai da kika tabbatar ya dauketa”

“Idan ma daukarta yayi me ye matsalarka? Shi ma yana da iko da ita kamar yadda kake da, babu ubanta a cikinku”

“Ba shi da iko da ita Ummi, be san cinta da shanta ba be san gurin bachinta da karantunta, be san damuwarta da kukanta ba, be san farincikinta ba dan haka ba shi da wata isa ko iko akanta, a gidanmu take Under my father control, ba zan taba bari yayi iko da ita ba he's late, yana son iko da

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login