Showing 78001 words to 81000 words out of 271643 words
Chapter 27 - Wani Gari Book 1 Complete Hausa Novel
ciwon ne?”
“Aa bana jin komai lafiyata kalau”
Ya sauke ajiyar zuciya domin ciwonta ne abun da ya fi damunsa a yanzu.
“Ummi har yanzu baki fada min yaushe ciwon nan ya sake ki ba, kuma me likitoci suka ce akai?”
Ta dubeshi.
“Ba nace wannan sirrinmu ba ne?”
“Ban fadawa kowa ba”
“Amman ka so ka yi maganar a gaban Namra ai, bana son kowa ya sani”
“Na ji, amman kina zuwa asibiti?”
“Na dade ban tafi ba, shakara biyu kenan da na gane cutar tana tare da ni”
“Amman Ummi kina shan magani? Kin san illar wannan cutar kuwa? Har kike cewa baki son kowa ya sani? Kin san abun da take janyowa”
“Likita ya min bayani, kuma yanzu zan duka da shan magani. Ina Waira?”
“Sun bata gado hoton ma daker ta yarda aka yi mata sai ihu take yarinyar bata da hankali”
Ummi ta mike tsaye tana tunanin mafarkin da ta yi wanda yayi kamanceceniya da abun da Waira ta yi a lokacin da ta so shiga dakin Maleek, suna tafiya Ummi ta juyo ta kalleshi.
“Kar dai ace aljana ta auri dan'uwanka Mahmood”
Mahmood ya girgiza kai.
“Haba Ummi wane irin aljana kuma? Yadda Maleek ya tsani mata har wata aljana ta samu damar aurensa?”
“Maybe ita ta saka mishi tsanar matan ai, wani mafarki na yi da ya ba ni tsoro...”
Jerawa suka yi suna tafiya tana labarta masa yadda ta yi mafarkin.
“Mafarki ba gaskiya ba ne, kawai dai dan kin saka abun a ranki ne ya saka kike yi mafarki, Ummi damuwata yanzu ciwonki ne yaushe zaki ga likitan? Kuma wane likitan ne yake dubaki, ba a wasa da ciwon nan”
“Sai na gama da matsalar Waira”
“And Ummi miye reason dinki na boye wannan sirrin ciwo ne fa”
“Bana son na tashi hankalin Babanku, kuma bana son hankalin Nimra da Namra ya tashi har da kai, dan dai Maleek na san ko ya rasa ni ba zai yi bakinciki ba”
Ta karasa a lokacin da Mahmood ya kai hannu ya tura kofar dakin da Waira take ciki.
“Maleek yana sonki Ummi, kawai dai wannan ciwon ne na kyamar mata ya saka shi nesantarki amman abun na masa ciwo, ya fada min haka kuma yace baya iya ayyana rayuwarsa idan babu ke, addu'a kawai ya kamata mu yi masa komai zai wuce”
“Kuma dole mu tashi masa tsaye, domin mafarkin nan da na yi jikina na bani kamar gaskiya ne in ba haka ba miyasa na ga Waira a mafarki har tana fadar wai kasheta za'ayi ban san ko suwa za su kashe ta ba”
Ummi ta zauna bakin gadon tana kallon fuskar Waira dake bachi.
“Akwai abun da yarinyar nan ta gani dazun tun da har gashi ta nuna”
Mahmood yayi shiru saboda baya son musawa Ummi. Ba shi kadai ba Abiey ma da ta labarta masa mafarkin a waya ta fada masa abun da ya faru be yarda ba.
“Mafarki ba gaskiya ba ne, kowa da yadda Allah yake halittarsa ku mata komai sai ku rika cewa aljannu ne, mun bincika abun nan a likitance an fada mana cewar halittace da Allah yake halittarsa kowa da irinsa”
Ta sauke ajiyar zuciya daman ta san ba lallai ne ya yarda ba.
“Hiayatee ki kwantar da hankalinki dan Allah komai zai wuce”
“Haka zamu saka masa ido ba tare da komai ba? Kullum sai dai ka ce min komai zai wuce when?”
Ta fashe masa da kuka kasancewar dakin babu kowa sai ita kadai da Waira dake bachi har lokacin, Mahmood tuni ya fice daga asibitin zuwa gurin aikinsa.
“Bari ki dawo sai mu zauna mu yi maganar abun da ya kamata, zamu saka ayi addu'a kuma muma zamu dage da yi har da sadaka idan ta kama har gurin dakin Allah sai aje ayi masa addu'a shikenan?”
“Eh amman da kullum baka yarda da zancena sai ka rika cewa komai zai wuce”
Daga can cikin wayar yayi dariyar manya, wadanda ke nishadi da matansu ya san halin sahibarsa tun kurciya na dawainiya da ita har zuwa yanzu da girma ya kama.
“Haba Madam yanzu ai na zubar da makaman yaki na ce za'ayi duk abun da kike so, kina asibitin har yanzu?”
“Eh ina son na tafi gida yanzu sai Hanne ta zo ta zauna da ita”
“Ya jikin nata? Likita ya fadi wani abu?”
“Sun duba komai a game da jinin idonta ba su ba mu sakamakon ba har yanzu, amman cizon dake hannunta sun ce da sauri tana da kyau jini, kuma likitan da ya duba da farko ya iya aiki shiyasa abun ya zo da sauki, sai dai yace duk da haka za su bata gado ta zauna har sai ta samu sauki gaba daya”
“Toh Allah ya biyaki, ita kuma ya bayyana mana iyayenta kuma ya shirya mana na mu yayan, ya nuna mana aurensu da yayansu a tare”
“Ameen... Abiey Ameen... Allah ya amsa....”
Ta amsa tana jin wani iri a zuciyarta, gani take kamar ba zata ga lokacin ba.
“Amman dan Allah ki saka ido akan yaran nan, bana son a samu wata matsala kuma ke ma ki kula min da kanki yawam tunani da damuwa ki ciresu kin fi kowa sanin yadda nake son farincikinki”
“Allah ya ba ni iko”
“Ameen, to sai na dawo?”
“A dawo lafiya Habibi”
“Allah ya sa”
Ya aje wayar, ita ma ta sauke wayar idonta na cika da kwalla, number Maleek ta lalubo ta danna kira ta saka hands-free. Ringing ďaya ya daga kamar yana jiran kiranta.
“Hello Ummi...”
Ya fada muryarsa har rawa take, sai da ta rumtse ido ta bude sanin uwa bata fushi da ďanta ta amsa masa.
“Na'am”
“I'm sorry ki yi hakuri da abun da ya faru bana nufin bata miki rai, ban san mi ya zo kaina ba kawai na samu kaina da bacin rai ne marar misaltuwa”
“Ba komai kana gida?”
“Aa na fita”
Ta yi shiru tana saurarensa sannan ta ce.
“Maleek ina son na tambaye ka, akwai mafarkin da kake ko kana ganin wani abun?”
Ta san it's not the right place ta yi masa tambayar, sai dai bata da zabin da ya wuce haka saboda baya zama da ita idan kuma ya dawo gida ba zai amsa mata tambayar ba.
“Ban fahimta ba”
“Baka mafarkin komai?”
“Ina mafarki kamar yadda kowa yake idan ya kwanta”
“Okay idan ka dawo za ku yi magana da Abiey”
“Okay amman kin hakura Ummi?”
“Ya zan yi Maleek uwa ai bata fushi da ƴaƴana na yi hakuri tun kana karami har ka girma, mi zai haka na ki hakuri akan abun da ka yi min? Ni dai ina son ka dage da azkar na safe da yamma, kuma idan zaka kwanta ma ka yi addu'a sannan ka roki Allah ya yaye maka wannan abun saboda yana damuna, bana son na mutu ban ga ka warke daga wannan damuwar ba Maleek, ciwon zai min yawa, idan zaka kwanta ka rika alwala kuma ka yi addu'a, sannan ka tsare karatun Qur'ane fiye da yadda kake yi, sannan ka rika daurewa ko da baka so kana zauna cikin kanenka da ni dan Allah duk abun da kake ji ka daure ka yaye abun a ranka idan ka ji abun ya taso maka ka nemi tsarin Allah”
“In Shaa Allah Ummi”
“Ka yi alkawari?”
“Na yi, ni ma abun yana damuna fiye da yadda yake damunki”
“Allah ya maka albarka, ya yaye maka ko minene?”
“Ameen na gode”
Ya amsa yana jin sanyi a ransa, ita ma sanyin ta ji domin daukar lokaci tana hira da ďanta Maleek ko da a waya ne zata iya kirgashi. Dawood ya dafa kafadarshi.
“This too shall pass Maleek In Shaa Allah, mu kan mu abun yana damun mu balle kuma mahaifiyarka da kai kanka dole ku damu, sai ka dage da addu'a nima kuma zan taya ka In Shaa Allah”
Maleek ya gyada masa kai, ya sauka daga kan motar da yake zaune ya saka hannunsa aljihu ya ciro kudi ya nufi wata almajira ya saka mata a robar baranta sannan ya dawo gurin motar suka yi sallama da Dawood....
*AFTER ONE YEAR.....*
*BAYAN SHEKARA ƊAYA....*
_Ku yi guessed abubuwa da da yawa🥰🙌_
©Khadeeja Candy
©®Copyright
2023
*W_G -it's not free, pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith Bank, then send the evidence to 08036126660*
26
Tsaye take ta jingina da karfen dake gabanta tana kallon harabar gidan, Mahmood na tsaye kusa da ita shi ma nasa hannayen suna jingine kamar nata. Daga ita har shi Maleek dake wasa da kallo suke kallo, farar singlet ce jikinsa sai short jean, da dukan kuzarinsa yake buga ball ya hada gumi sosai kamar mai yi tare da wasu team.
Kusan lokaci daya suka kalli Gate din gidan da aka bude manyan motor alfarma ta kunno kai harabar gidan.
Maleek ya tsayar da ball din da yake yana kallon motar data faka gabansa fuskarsa da murmushi. Wani kyakkyawan bakin saurayi ne ya fito gaban motar dayan kuma ya fito a gurin zaman driver, Maleek ya nufi wanda ya fito a driver seat da sauri ya mika masa hannu suka gaisa, Mahmood dake tsaye kusa da Waira kuma ya zagaya ta dayan side din ya koma dakin, ya sauka kasa gaba daya. Ummi dake falon tana gyara dankwalinta ta kalleshi tana murmushi.
“Sun iso ne?”
“Eah”
Da sauri ta bi bayansa fitowar Ummi falon ta yi daidai da fitowar Dr Zainab a motar dake bayan ta su yayanta. Ummi ta nufe ta da sauri Dr Zainab ma ta nufo Ummi da saurinta abun ka da an dade ba a hadu ba, sai suka rumgume juna cikin farinciki.
“Sannu da zuwa Aunty Zainab”
Ummi ta fada idonta na cika da hawaye rabon data saka ta a ido yau shekara biyu kenan da watani, domin Abuja ba gurin zuwan Dr Zainab ba ne tun bayan da suka bar kasar.
“Zahra... Ya kike ya gida ya rayuwa bayan rabuwa”
Dr Zainab ta dago Ummi daga jikinta tana kallonta tare da aika mata tambayoyi a jere.
“Lafiya Kalau Aunty Zainab mun yi marmarinki sosai ku shigo ciki mana”
Ta riko hannunta suka nufi cikin gidan tana share hawayen dake zubo mata, rayuwar baya take tuna ita da Dr duka sun manyanta a yanzu, sai dai ita da sauki ba kamar Dr Zainab da tsufan ya bayyana karar a fuskarta ba. Kusan gaba daya suka shigo falon, Ummi da Sister in-law dinta agaba, Mahmood da Maleek na binsu sai yayan Dr biyu yan mata dake binsu kamin mazan su shigo daga karshe. Kamshin turaren wutar da Ummi ta kamsashe falonta da shi ya fara yi musu maraba, suka zauna a falon Ummi ta kira Hanne ta zo ta dauke kayansu da ďaya daga cikin yaran dake aiki gidan Rilwanu yake shigowa da su falon.
“Mommy Sannu”
Maleek ya gaisheta da sunan da yake kiranta kamar yadda yayanta ma suke fada, fuskarsa da murmushi kadan yana dan shafa kansa, ya ji yadda suka tararda shi yayi haje haje da gumi kamar wani mai aikin sharar gida.
“Maleek ya aiki? Kai ma Babanka ya koya maka zaman gida da son kwallo ko? Ko kai zaka gado Abiey ne”
“Come on Mommy na girma yanzu, idan za a fara ai da kananan shekaru ake farawa, ni yanzu aikin da nake na kai shi ina?”
“Hmmm 'Uhmm Mai Martaba ma ba zai bari ba, ko a wacan karon da ya bar Abiey saboda yana hannun Ammy ne, kasan jinin sarauta ba komai suke aikatawa a nan arewa sai ya zama abun magana ko abun kunya, musamman a gurin tsufin sarakuna irin Mai Martaba da suka rike al'adar iyaye da kankani”.
“Yana da gaskiya ai, yana da kyau mu rike al'adunmu da addinin mu a duk inda muka samu kan mu, Juwairiya ya karatu ko an gama”
Ummi ta karasa da dariya tana kallon yar autar Dr Zainab dake kokari cire dankwalin dake kanta tana murmushi. Namra ta kai mata rankwashi a kai.
“Yauwa ko shekaranjiya sai da Ummi ta yi zancen ki, muma yanzu muna da yar'uwarki a gidan nan da bata son dankwali”
Ta wara ido tana sosa kan kana.
“Asss Yaya Namra da zafi fa sabon kitso ne kaina, zuwan da zamu yi Mommy ta cilasta ni yinsa”
Kallo daya Maleek yayi mata ya nufi upstairs yana rike da ball dinsa a hannu. Hakan yayi daidai da saukowa Waira dake sanye da gown din data tsaya iya ƙwabrinta, kanta babu ďankwali sai dai ta faka gashinta a guri daya ta sake a bayanta. A hankali take saukowa domin har yanzu tana tsoron sulbin da tile din yake da shi, Maleek kuma na hawa da sassafar, kallonta yayi ya daga sama har kasa sannan ya dauke idonsa, ita kam tuni nata idon sun yi nisa gurin tantance bakin da suka shigo gidan. Ta fi kurawa Dr Zainab ido ganin Ummi ta zauna kusa da ita tana rike da hannunta. Bata sauko gaba daya ba sai ta tsaya jikin Stairs din har sai da Jabir ya tambaye wacece ita.
“Oh Waira... Yata ce come here baby”
Ummi ta mika mata hannu, sai ta karasa saukowa a hankali ta tako zuwa gurin Ummi ta zauna a gefenta tana leken bakin Juwairiya da yar'uwarta Yesmin.
“Ko ita ce wanda Abiey ya fada min kuna riko yanzu”
“Definitely”
“Maa Shaa Allah kyakkyawa da ita tubarkalla, kuma har yanzu ba a samu iyayenta ba?”
Ummi ta dan juya ta kalli Waira sannan ta kalli Dr Zainab ta mike tsaye.
“Bari na hada miki ruwan wanka da kain Aunty Zainab, ku kuma sai ku shiga dakin Waira ko Namra ku watsa ruwa ga abincin can na dade da gamawa”
“Ina Nimra?”
Dr Zainab tambaya tana kallon tawainiyarta.
“Ta tafi gurin saloon”
“Okay, Namra aure har yanzu shiru? Ba ke ba ba yar'uwarki ba, ga Juwairiya ma da take karamar ku ana zancen yi mata baiko”
Namra ta rufe fuska tana dariya.
“Mommy muma soon za'ayi da yardar Allah”
“Haka kuke ta cewa saboda kun samu Abiey ya daure muku, da a gurina kuke ai da yanzu kun sha matsin lamba, shiyasa ya ki ya ba ni ko daya, idan na yi magana yace shi ma yaran ba su ishe shi ba idan sun min yawa na karo masa daya”
Duk suka saka dariya ban da Waira dake wasa da zara zaran yatsun hannunta. Dr Zainab ta nufi upstairs tana yaye mayafinta, Waira ta tashi ta koma kusa da Mahmood ta zauna, haka take idan ta ga bakuwar fuska bata da sakewa ko fita aka yi da ita ta tsawalla kenan har sai an dawo gida.
“What's her name again”
Jabir ya tambaya yana kallon idonta dake yawo a kasa. Sai Mahmood ya amsa masa.
“Waira”
“Waira.... What's that mean?”
Ya maimaita sunan tare da tambayar ma'anarsa, Mahmood ya daga kafadunsa.
“Just, but Ummi tace tana tunanin Nuwaira su kuma suke kiransa da Waira kawai”
“Oh okay har yanzu bata jin hausa?”
“Tana ji, and she can speak some, as well as English ana mata Evening lesson and tana zuwa makaranta”
Mahmood ya juya ya kalleta.
“Waira ki cewa Jabir barka da zuwa”
Sai ta dago ta kalli mutumen da Mahmood ya nuna mata, ta maida kanta kasa ba tare da ce masa komai ba.
“Yana ďaya daga cikin dalilin da ya saka na tsani yarinyar nan, sai ta rika abu kamar munafuka, ko kuma bata yarda da mutane ba Mtscheeeeee”
Waira ta kalli Namra wacce ta yi maganar ta sake maida kanta kasa. Mahmood yayi murmushi.
“Bata ga damar magana ba”
“Tau saboda ta ga baki ne ko? Kasan bata taba ganinmu ba sai yau”
Yesmin ta fada tana mika hannu ta karbi ruwan da Hanne take mika mata. Umar ya mike tsaye rike da wayarsa.
“Bari na fara ba cikina hakkinsa tukunna”
Namra suka saka masa dariya daman duk wanda ya san Umar ya san baya wasa da cikinsa ko kadan idan kuma zai ci ba kadan yake ci ba, wannan ya saka ya banbanta da yan'uwansa domin shi yana da jiki sosai kana ganinsa ka ga ďan lukuti ba kamar sauran yan'uwansa dake da kirar zaratan jarumai ba. Kusan lokaci daya Namra da cousin's dinta suka haura sama zuwa dakinta suna hira, Jabir kuma ya tashi tare da Mahmood sai ya rage falon babu kowa sai Waira dake zauna a cushion, da kuma Umar dake bawa cikinsa babban aiki, sai da yayi rabin plate sannan ya juyo ya kalli Waira dake zaune tana taba sarkar zoben dake wuyanta.
“Hey young lady zaki iya sama min wani lemun a fridge bana shan lemu mai kwakwa”
Ta dago sai dai bata juyo ta kalleshi, ta san da ita yake domin babu kowa a falon sai ita, Hanne ta fice tun bayan data mikawa Yesmin ruwa, sai dai hakan be saka ta motsa daga inda take ba balle ta yi alamar dauko masa abun da ya bukata.
“Bata san inda yake ba”
Ya sake juyowa jin wata kalar hausar bambarakwai.
“Ita wa?”
Sai a lokacin ta juya ta kalleshi ta idanuwanta masu matukar kyau da daukar hankali, sai ta nuna kanta.
“Waira... Bata sani ba”
Murmushi yayi mai kama da dariya ya juya ya cigaba da cin abincinsa. Ita kuma ya juyo da kanta tana cigaba da wasa da sarkarta, kusan ita da shi duk baki ne a gidan wata kila ma shi ya fita sakewa ya shiga yayi abun da yake so ita bata yi ba, har yanzu bata taba abu idan ba a Ummi ko wani ya bata umarnin yin haka ba, ta kayyadewa kanta abubuwan da take iya ci ko sha, wannan ya saka idan ka ganta kofar kitchen to Ummi ta kirata ta bata abun da ta sabawa kanta da ci ne, ko kuma ta shiga ta gada ma kanta kamar yadda Ummi ta nuna mata idan bata nan zata iya hadawa kanta tea ko zuba ruwa ta sha, ko kuma ta bude warmer ta zuba dankali ko dafaffen kwai domin bata cin soyayya, sai fruit da zallar madara, ko nama da aka dafa da gishi kawai ba tare da an sanka magi ko yaji ba, sai kuma cake da biscuits ko cookies da ake yi da kayan zaki wannan kan duk tana iya ci ko ta sha. Bayan shi bata da wani abinci da take ci. Wannan ya saka bata katsalanta a harkokin gidan duk kuwa da irin yadda Ummi take son ta saki jikinta da su ba komai ta san muhallinsa a gidan ba, kuma bata taba kokarin cilastawa kanta sani ba, domin komai yi mata ake idan Ummi bata yi mata