Showing 105001 words to 108000 words out of 271643 words

Chapter 36 - Wani Gari Book 1 Complete Hausa Novel

waya taba zomo?”

“Kuma ka rika?”

Ta kalli Waira ya kalli zomon ya daga kafadunsa he can't tell why ya rike mata zomon.

“Ummin ai baya ciwo”

So take tace cizo. Ummi ta yi murmushi dake tare da hawaye daman kukanta a kusa yake.

“Wow...”

Mikewa yayi tsaye ya taku daya ya kara matasawa inda Waira take zaune tana facing dinsa, ya dora mata zomon saman jiki ya kabe jikinsa ya nufi hnayar fita falon. Ummi ta duka a gurin tana kallon Waira.

“You're so special Waira, zuwanki gidan nan ya taimaka min sosai kin canja rayuwar ďana, sanadinki na fahimci abun da ban fahimta ba akan Maleek, komai yana da sanadi, ke ce sanadin canjawa Maleek”

Bata kula da zancen da Ummi take ba saboda hankalinta yana kan sabon abokinta.

“Ummin ki rike Zilll zan yanka abinci”

“Ki bashi wanda kika yanka idan na dawo sai na rike miki, zan duba bangaren Abiey ne”

“Tohm okay”

Ta amsa har sau biyu sannan ta shiga bashi abincin. Ummi ta ja kumatunta tana kara jin kaunarta ta mike tsaye tana murmushi ta nufi hanyar da zata sadata da bangaren Abiey. Tana tafe tana tunanin abubuwa biyu da suka zo mata a lokaci daya, wato ganin Ameer da kuma abun da Maleek yayi a yau, da ane ko taba zomon ba zai yi ba saboda Waira ta taba shi, amman a yau wai shi ne ya rikewa Waira zomo ta zauna a kusa da shi tana kusantarshi tana yanka abu, kuma idonsa na kanta.

“Kamar yadda Zahra ta wanke shawara na yanke shawarar zan aurar da su duka a watan da zai kama, idan basa da wadanda suke so, akwai yayan yan'uwa da abokai za a hada su”

Shi ne abun da Ummi ta ji daga bakin Abiey kamin ta tura kofar falonsa ta shiga, Dr Zainab ta dago tana kallon Ummi da tausayi a fuskarta har tana zubar da hawaye.

“Zahra kin ga da inda yayi ikonsa? Ashe haka abu ya kasance, wani hukunci sai Ubangiji”

Ummi ta nemi guri ta zauna tana kallon Abiey.

“Ina ganin zamu daga musu kafa zuwa wani lokacin da Nimra zata samu natsuwa, ba mu sani ba ko Namra ma bata da wanda take so kamin lokacin na san ta samu idan kuma akwai sai ya fito, ita kuma Nimra zata samu sakewar zuciya da natsuwa kamin lokaci, domin ba abu ne mai sauki ka rabaka da wani kuma a aura maka wanda baka so ba”

“Ba zan daga musu kafa ba, daman ai sun kai munzalin aure, duk su fito da mazaje ayi musu aure”

“Amman dole a fahimtar da ita dalilin da ya saka ba za a barta ta auri Ameer ba?”

“Ta ina kenan? Shiyasa nake na ce da laifinki a lamarin nan, idan ba haka ba ta ina za a ce Nimra ta kulla alakar soyayya da wani har ta kai ga haka baki sani ba?”

“Saboda ba ni kadai Allah ya bawa ikon kula da ita ba, ni da ita duk a karkashin kiwonka muke Abiey”

Ummi ta amsa masa a gautsine.

“Abun da kike kokarin ki aikata na fahimtar da Nimra ba ni kadai zai shafa ba, ke da Ameer din za ku fi kowa cutuwa saboda rayuwarsa ce zaki rusa, ki haddasa masa bakinciki da ke kanki kuma ki butulcewa wanda yake dawainiya da shi tun yana karami har ya girma”

“Ban ce dole sai ta hanyar fada mata ina da alaka da Ameer ne kadai za a fahimtarda ita ba, amman kai me kake tsoro ne Abiey? Ban ce ka dauki dawainiyarsa ba ban bukaci komai daga gareka ba ni dai kawai ina son ďana a kusa da ni....!”

“That's it, daman na sani ai, amman babu yadda ban yi da ke ba a wacan lokacin akan ki aje yaron nan a hannunki kika ki, sai yanzu yaro ya girma yana rayuwarsa dabam zaki ce ki rusa rayuwarsa kuma ki rusa rayuwar mutanen da suke rike shi a matsayin ďa? Damuwata ba akan Ameer ne kawai ba har da matsalar da zaki jefa kanki a ciki ina jin tausayinki Zahra da abun da zai biyo baya”

Dr Zainab ta kalli Abiey ta kalli Zahra ta dafe kanta.

“Innalillahi wa'inna Ilaihiraji'un, yau Abiey da Zahra ne suke sa'insa? Abun da ban taba gani ba? Subhanallahi wannan abun yayi muni, Zahra ki yi shiru dan Allah karki sake magana”

“Har zuwa yaushe zan yi ta yin shiru Aunty Zainab? Shekara nawa a tare da Abiey? Ina da mafarkai da buri amman na rufe su saboda na samu zaman lafiya da mijina, shim ba ku taba tunanin kewa da kaunar uwa ga ďanta ba? Kai da ya aikatawa yarka haka ka ji zafi balle ni da ya kwanta a cikina wata tara da kwanaki na rike ka shi a hannuna na shayar da shi? Ko ka so Ameer ko karka so shi idan aka tsaga jinin Ameer sai an ga nawa a ciki”

Abiey ya girgiza kai yana murmushi takaici.

“Ba zaki gane ba ne Zahra, yaron da kike ta kokarin ki dawo da shi kusa da ke, ba shi da kirki ba ta inda zai girmamamu ko ya tsaya ya fahimce, ina gudun kar bakincikin ya zama mana biyu, domin ba ke kadai zai shafa ba har da ni, duk abun da ya same ki a tare za mu raba either na dadi ne ko akasin haka, sannan yanzu ba abun kunya ba ne ki zaunar da shi ki fada masa yadda aka yi kika rabu da shi? Bayan kin katse masa jindadin da yake a can?”

Ummi ta mike tsaye.

“Ba abun kunya ba ne, kuskuren da na aikata nake kokarin na gyara, amman kai abun kunya ne a gareka yanyanka su ji cewar ka ki ka taimaka min a lokacin da naje neman taimakonka, da ban aikata abun da zan kwanta a gado ya hana ni bachi ba...!”

Abiey ya hade fuska kamar be taba dariya ba, Dr Zainab ta yi saurin runtse ido tana girgiza kai.




WAIRA POV.

A cikin abubuwan da ta yanka ta bawa zomon karas ne kawai ya ci, sauran idan ta ba shi baya karba tana ganin haka ta mike tsaye tana shafa shi, can kuma ta dorashi saman kanta jin sonsa take kamar ranta, kawo mata zomon da malamin yayi ya tuna da yawa daga rayuwarta na baya, hannu ta saka ta cire ribon din dake kanta ta birjita gashin kanta ta dora zoman a saman kanta tana dariya, sai ta fara zagaya falon tana tafiya, har ta isa gurin kofa ta bude ta fito Maleek dake tsaye jingine da kofar ya juyo ya kalli zomon dake saman kanta yana mamakin yadda take rikonsa ko tsoro bata ji.

“Waira zata tafi daji”

Kallonta yake without asking ina ne dajin? Fita zata yi a gidan gaba daya or me take nufi? Bata damu da saka talkami ba ta nufi entrance din ta fara sauka, idonsa ya koma gurin kafafuwanta karamin guddugenta da take takawa tana sauka gurin gwanin sha'awar kafafuwanta ma sun fito sala sala kamar tsokar kaza, kallonta kawai yake har ta sauka ta nufi Garden a nan ya gane Garden take nufi da daji, samun kansa yayi ta saka wayar aljihu ya sauka gurin a hankali ya bi bayanta. Ko da ya shiga gurin har ta kusan raye icen kwakwa dake gurin, kansa ya daga yana mamakin yadda take iya hawan ice ba tare da taka komai ba, sai kafafuwanta da take tsalle da su da hannayenta da ta saka tana rike icen. Abun da ya fara zuwa masa a rai is saboda icen be gama girma ba ne saboda haka ne ba mata wuyar hawa ba, be gama raba dayan biyu ba ta haye sama riko dayan dake kusa da shi ta dira akai, can kuma ta samu sa'ar mika hannu ta riko icen mangoro ta koma kansa, yana tsaye a gurin kusan sai da ta hau duk wani icen dake kusa da kusa da juna. Masu yayan itatuwa ta tsinko ta jefo kasa sannan ta biyo ta sauko ta saka hannu ta dauka ta fara ci, sai da yayi kamar ya ce mata ta wanka kamin ta ci sai kuma wata zuciyar tace ina ruwanka? Cikinka ko nata? Yana kallonta har ta gama ci sannan ta nufi fanfon dake gurin ta kunan ta wanke hannunta ta tara hannayenta ta sha ruwan sai da ta koshi, kana ta nufi gurin da ta rufe zomon ta dauko tana masa magana da yarenta, gaba daya hankalinta be kai kan Maleek dake tsaye can gurin kofar Garden din yana kallonta ba domin ba a gurinsa hankalin nata yake ba. Ta tako ta fito cikin itatuwan ta nufo kofar fita a nanta tsaya tana kallon Maleek da tunanin ko ya ganta lokacin da ta hau itatuwan, dan tsoro da fargabar kar yayi mata fada ko ya fadawa Ummi ta yi mata ya saka ta kasa karaso gurin sai kallonsa take tana shafa zomon dake hannunta.

‘Waya koya miki, hawa itace? For how long kike hawan itace’

Wani salon iskanci da rainin wayo na kin son magana irin na Maleek, duk a cikin ransa yake mata wadannan tambayoyin kamar ance masa zata iya karanta abun da yake ransa ne. Ganin wannan ba zata fitar da shi ba ya saka shi tambayarta abun da ya saka ya biyota a gurin, domin tun a dazun da ta yi maganar abun yake cinsa.

“Waya fada miki Ummi zata mutu?”

Ta yi kasa da kanta kamar ba ita yake magana ba.

“Uh.. Hmm”

“Waira na sani, ta gani”

Cikin yanayin na jinin sarauta ya taka ta karasa inda take tsaye, sai ta yi baya ta jingina da wayar dake gurin.

“Waya fada miki? Ta ya kika san Ummi zata mutu?”

A take idonta ya cika da hawaye.

“Ummin tana da ciwo ciwon mai kashe Ummin ne, ciwon na mutuwa ne”

“Wane lalar ciwo ne?”

“Ban sani ba, amman bata fadawa kowa ba Ummin tana jiran mutuwa, Waira ma tana jiran mutuwa”

“Waye zai kashe ku? What kind of nonsense is this?”

“Ba karya ba ce, na gani da gaske Ummin tana da ciwo, kuma Ummin tana son ta ga Ameer”

Ta share hawayenta, maganarta ta masa wani iri ya kasa yarda gaskiya take fada ko akasin haka, amman da karya take ba zata fadi haka a gaban Ummin ba dazun har tana kuka. Sai da yayi kamar ya tambaya waya bata zomon dake hannunta sai kuma ya juya ya fice daga gurin, da kuzarinsa ya dawo part din Ummi yana kokarin hawa Stairs din Jabir da Mahmood suka sauko, kai tsaye dakin Ummi ya nufa, sai da ya suke ajiyar zuciya sannan ya kai hannu ta tura kofar ďakin ya saka kafarsa sai duk ya ji wani iri domin ba zai iya tuna lokacin da yake da kurciya ya shiga ďakin mahaifiyarsa ba, ko ciwo take sai dai ya gaisheta a falo ko bangaren mahaifinsa idan sun hadu. kamshin turaren jikina kamshin dakinta, jimke hannayensa ya fara yi thinking of ta ina zai fara, kamar wanda aka kama yana sata haka jikinsa ya fara rawa tun kamin yayi abun da be saba ba wato bincike...

35

THREE DAYS LATER...

Nimra ce kwance a cinyar Dr Zainab, kallo daya zaka yi mata ka san damuwa da kuncin zuciya sun saka ta a gaba, domin ta rame sosai kamar ba ita ba, kwana biyu bata iya cin komai sai ruwa su ma kuma idan Ummi ta matsa mata ne, gaba daya ta dauki damuwa ta saka a ranta, bata fita daga dakin kullum tana ciki idan an kawo mata abinci yadda aka aje shi haka za a dauko shi. Duk wani kokari da yar'uwarta Namra ta yi na ganin ta dauke mata hankali daga damuwa abun sai ya ci tura domin ba kadan soyayyar Ameer ya kama ta, tana taba jin som namiji kamar yadda take son Ameer ba, bata san yadda zata cire soyayyarsa a ranta ba ko da kau shekaru dari aka raba mata nan gaba, wani irin sonshi take irin son da take jin zata iya kai karar Abiey da Ummin a gurin wadanda za su barsu su ji maganarsu abarta ta auri Ameer.

“Nimra rayuwa ta yi haka? Dubi yadda kika maida kanki? Ni dai wannan zuwan be min dadi ba sam na ji abubuwa kuma na ga abubuwan da ban jidadinsu ba”

“Mommy yanzu babu yadda zaki yi ki lallaba Abiey ya bar ni na auri Ameer? Wallahi ina son Ameer, daman na san haka zata faru shiyasa na ce zan fada miki wata magana tun a farkon zuwanki na so na fada miki abun a sirrance saboda ki san yadda zaki shawo kan Abiey sai gashi komai ya lalace ya zo ta inda ba mu zato ba”

“Nimra abun da iyeye basa so hakuri ake yi, karka zafafa kace kana so, abubuwa da yawa ba alheri ba ne a garemu, ki yi wannan nazarin kuma ki yarda da hukuncin Allah”

“Mommy ba zaki gane abun da nake nufi ba, Mommy Soyayya akwai ciwo idan kana son mutum zaka ji zaka iya aikata komai saboda ka same shi, idan kuma aka ce mutumen ya barka ko an raba ku sai ka ji kamar ka kashe kanka ka saboda bakinciki”

Dr Zainab ta yi dariya.

“Nimra kenan, ku da kuke yaya kuka san soyayya balle kuma mu da muke iyayenku? Babu alakar soyayyar da ban gani ba tsakanin Mahaifinki da Zahra, idan an bude miki sirrin yadda aka yi sanadin samuwarki zaki sha mamaki, amman da iyayenki suka yi hakuri daga baya sai komai ya zo musu da sauki fiye da yadda suka sha wahala a baya, Mahaifinki ya zo Zahra irin son na tabbatar ace be aureta abu ne mai wahala yayi aure, abu ne mai wahala alaka mai karfi ta sake shiga tsakanina da shi, saboda yana ganin ni na hana shi samun Zahra wacan lokacin, babu kalar haukar da Abiey be yi ba akan Zahra, shiyasa shekaranjiya da na gansu suna sa'insa sai abun ya bani kuma kuma yayi min ciwo, domin tun da ya aureta be taba kirana ko ita ta kawo min kararsa ba, ban ce basa samun sabani ba, amman basa bari a gane balle har ace wani ya shigo yana musu sasanci, Abiey baya son fushin Zahra ko kadan, idan tana son abu yakan fita kaunarsa amman wannan karon abun da na ji kuma na gani ya bani mamaki, sai dai ta wani bangaren yana da gaskiya domin ina hango abun da zai biyo baya, idan na yi tunani ta wani bangare ina ganin cewar gaskiya yake fada, kuma dole a daga masa kafa idan ya nunawa ďan makiyinsa kiyayya, musamman ma ta yadda abun ya bayyana, da ace ba ta wannan hanyar abubuwan suka biyo ba wata kila da an samu sauki, sai dai yadda abubuwan suka zo ne dole su fusata shi”

Nimra ta daga daga jikin Dr Zainab ta kalleta.

“Ban gane abun da kike nufi ba Mommy wani abun nw ya faru?”

Gudun kar aji mutuwar sarki a bakinta ya saka ta kawar da maganar gefe ta hanyar yin murmushi.

“Bari na tashi na duba aikin da ake kar abar Namra ita kadai da aiki, ko zaki zo muje?”

“Aa, Namra ta jidadi zata auri wanda take so an barta zata yi soyayya ta wanda take kauna ba kamar ni ba”

Ta fada tana jin wani sabon kuka na sakata gaba. Dr Zainab ta ce.

“Shi ma sai an bincike halinsa da zuri'arsa idan ya cancanta sai a aura mata idan kuma be cancanta ba sai a bata damar kawo wani kamar yadda aka baki ke ma a yanzu”

“Ni zan kawo ba Mommy, bani da kowa sai Ameer idan ba shi ba sai dai na mutu ban yi aure ba”

“Aa Allah dai ya saukewa”

Shi ne kadai abun da ta fada ta fice daga dakin. Kasa ta sauko tana jin yadda falon ya dauki kamshi ana ga shiryawa bakon Namra abubuwan dadin, ita ma ta zage dantse ana ta aikin da ita saboda bakon nata ne kuma wanda take matukar jin da shi, ko ba komai kokarin zuwan da yake cikin kwana uku abun a yaba ne, kuma hakan ya nuna da gaske sonta yake da aure ba iya chat da waya abun ya tsaya ba, domin tun haduwarsu a Instagram sau biyu kawai suka taba ganin juna a fili, shi ma kuma zuwan gaggawa yake a Abuja sai ta fita su hadu a wani gurin su gaisa, sai da ta sada shi da Ummi sun gaisa sau biyu, ita ma ta gaisa da yan'uwansa sosai har live video yayi ta gaisa da iyayensa, sun santa ta san su. Yanzu kuma ta sanar masa iyayenta suna son ganinsa sai ya zabi ya yanke duk wani abun da yake ya gabatar da kansa a matsayin mai son yarsu. Sati ta bashi shi kuma ya rage ya zabi kwana biyu, saboda damar da yake ta jira kenan na neman aurenta.

  Ummi ta fara sanar ma ranar da zai zo, ita kuma ta sanar da Abiey duk da kasancewar basa cikin yanayi na fahimtar juna a yanzu, sai dai babu wanda ya sani sai Dr Zainab ita ma saboda an yi a gabanta ne. Falon Dr ta zauna tana ta tsokanar Namra kamar ba yarta wai bata shiga kitchen ta taya Ummi aiki amman yau da yake saurayi zai zo har da ita ake komai, Juwairiyyya da Yesmin sai dariyar suke.
Dr Zainab na fita Nimra ta tashi ta nufaci kofa a hankali ta bude ta leka ganin babu kowa saman ya bata damar fitowa tana sanda kamar wacce zata yi sata ta tura dakin Ummi ta shiga ta duba ko'ina bata ga waya ba sai ta fito ta shiga dakin Namra nan ma bata samu abun da take so ba, ta fada dakin Mahmood, shi ma baya nan wayarsa ma bata nan sai Umar dake zaune a kan kujera yana kallon wasi series a laptop.

“Umar dan Allah wayarka zaka ara min”

“Okay”

Ba tare da tunanin komai ba ya cire key ya mika mata wayar sai ta karba ta fita ta koma dakinta da sauri, number Ameer ta saka ta kira wayarsa sai ta ki shiga, saboda ba shi da number ba, ya saka only wadanda yake da number su za su iya

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login