Showing 93001 words to 96000 words out of 271643 words

Chapter 32 - Wani Gari Book 1 Complete Hausa Novel

ta mike tsaye da sauri tana yi ma Ummi sannu da zuwa hankalinta a tashe ganin hawaye a fuskar uwar ďakinta.

“Sannu da zuwa Hajiya, lafiya?”

Ummi bata iya amsa mata ba ta haura sama tana tafiya daker sai ka ce mai ciwon kafa, saman bed dinta ta fadi zaune. A yau kam sai ta ji tana kewar mahaifiyarta fiye da kullum, wasu kalamai da tarbiyar da mahaifiyar ta dage akansu take tunawa, ashe haka iyeyenta suka ji? Musamman ma mahaifiya domin ita ko da ta tashi bata san natan mahaifin ba, sai dai mahaifiyarta ta sha wahala akanta saboda ta yi rashin jin magana a lokacin da take da kurciya, kuma mahaifiyar na yawan fada mata cewar idan ta fita bata da kwanciyar hankali har sai ta dawo, ita kiriniya ce kawai take yi sai jan magana, wani abun ma ba ita take aikatawa ba faruwa yake yi saboda wautarta da shiririta, a wacan lokacin na su tashin akwai matukar kurciya da rashin wayo, kamar na yaran yanzu ba, da wasu suke fin iyayen ma wayo. Ita ba ďakin wani take zuwa ba, amman hankalin mahaifiyarta yana tashi ina ga ita data kama Nimra a gidan wani.

“Ashe haka kike ji Mama? Allah ya miki lullube kabarinki da rahma ya yafe miki”

Ta mike tsaye ta cire hijabinta ta nufi inda wayarta take ta dauka ta kira Abiey, ringing biyu ya yanke kiranta ya kira da kansa.

“Hiayatee....”

Sai ta yi shiru kamar ba zata amsa ba.

“Are you there?”

“Abiey... Wallahi a yau ina jin kewar mahaifiyata fiye ko yaushe, na san na girma amman ina jin kamar ace tana kusa da ni na raba jikinta na ji sanyi kuma na fada mata damuwata, duk girman mace tana bukatar uwa ko uba a kusa da ita, ko dan ta kallesu kawai ta ji sanyi a ranta, kuma ta kara kyautata musu”

“Hiayatee, yanzu aka kira ni daga makarantar su Waira wai ta yi fada da wata suna neman mahaifinta, amman zan kira Maleek ko Mahmood su tafi, gani nan zuwa gida yanzu nan”

Ya yanke wayar, kusan shi ne abokin shawararta a duk abun da ya shafe ta, idan bata fada masa damuwarta ba waye zata fadawa? Shi ne kadai mutumen da ya ke gane abun da take so tun kamin ta furta. Wayar dake hannunta ta fara ringing tana dubawa sai ta yi arba da number Yaya Maryam, yayarta the one and only sister she has, wacce suke uwa ďaya uba ďaya, yar'uwar da suka sha wahalarta a tare da Mama lokacin da kurciyata take cinta.

“Assalamu Alaikum”

“Wa'alaikissalam, Zahra Lafiya kike?”

“Ba kalau ba Yaya Maryam ina kewarku”

“Miya faru? Abiey ya kira ni yace na kira ki ko hankalinki zai kwanta kin kira kina masa maganar Mama, hankalinshi duk ya tashi”

“Yaya Maryam, yau na ďanďana wani ďaci da uwa take ji idan Yayanta suka mata karya, ina cikin wani irin bakin ciki na uwar da ta bawa yayanta tarbiya aka rusa, sai dai kuma a yanzu yanke shawara nake”

“Fada min abun da ya faru?”

Ummi na cikin labarta mata abun da ya faru ta ji an yi knocked a kofar dakinta Nimra na kiran sunanta..

“Ina zuwa”

Ta yanke wayar tana kallon Nimra data turo kofar ďakin ta shigo idonta a kasa domin tana jin kunyar hada ido da Ummi, ba dan fuskarta dake nuna alamar kuka ta yi ba, da ta rantsewa Ummi akan karya cewa gurin Saloon ta tafi albashi daga baya sai ta bayyanar mata da Ameer a matsayin wanda take so.

“Da ace kina da kunya kamar yadda nake gani a idonki, da Ubangijinki ya kamata ki fara kunya, kamin ki aikata abun da kika aikata, da kin ji kunyar yin karya da kuma shiga gidan wanda ba mijinki ba ki taba jikinsa ki sumbance shi ki cire tufafinki a gabansa ki bar shi ya aikata abun da yake so da ke”

A lokacin ďaya ta saki jakar hannunta da mayafinta da wayarta ta fadi kasa ta kama kafar Ummi.

“Aa Ummi na yarda na ina zuwa gidan, ina rika hannunsa ko taba jikinsa ko sumbantarsa amman Wallahi na rantse miki da sarkin da babu abun bautawa da gaskiya sai shi ban taba aikata zina ba, ban taba yarda wani namijin ya san yi a matsayin ƴa mace ba, Wallahi ban aikata ba Ummi”

A tsakanin yarda da yar'uwarta Ummi ta samu kanta, ba zata yi saurin yarda da maganar data fada mata a yanzu cewar bata aikata zina ba, domin a baya ta yarda da ita kuma ta same da wannan halin, kuma ba zata karyatata kai tsaye ba, domin ta yi mata rantsuwa da Allah.

“For how long kike tare da shi? Waye shi? Miya fada miki ya yaudare ki kika watsar da tarbiyarki? Miyasa ba zaki fito ki fada mana kina son aure ba? Akwai abun da muka rage ki da shi da kika tafi gurin wani ya baki?”

Ta girgiza kai tana kuka sosai.

“Ba ku rage ni da komai ba Ummi, idan na fadi haka na yi karya kuma na ci amanarku”

“A yanzu ma kin ci amanarmu Nimra miye rage? Kin yi komai kin daka kin tankade kin shanye”

“Ummi ki dubi girman Allah ki yafe min”

“Ki fada min wanene?”

Ummi ta daka mata tsawa sai ta jikinta ya dauki rawa domin bata taba mata fada haka ba.

“Idan baki fada min ba, shi Abiey idan ya zo sai ki fada masa”

Nimra ta matsa baya da sauri tana girgiza kai.

“Aa Ummi ba zaki fadawa Abiey wannan maganar ba, ba zaki fada masa abun da na aikata kai tsaye ba, wannan a tsakaninmu ne, ba zaki fadawa Abiey haka ba dan Allah Ummi”

“Toh wanda ya koya miki karya ya yaudara yace ki zo ki koya min ko?”

“Ummi dan Allah ki rufa min asiri, karki fadawa Abiey wannan maganar”

“Idan kika ga ban fada masa ba, to na mutu kamin ya iso ne”

Tana jin hakan ta tashi da sauri ta dauki wayarta ta jakarta ta fice daga dakin. Dakinta ta shige ta maida kofa ta rufe ta saka key. Cikin hanzari irin na magidanci mai damuwa da iyali Abiey ya shigo gidan, kamin na isa ďakin da matarsa take har ya matsu. Ko sallama be yi ba ya tura kofar ďakin ya shiga.

“Madam Lafiya”

Ya tambaya yana zaunawa a kusa da ita cike da kulawa. A yanzu ba hawaye take ba bacin rai ne a tare da iya daya maye kukan da take a na bakinciki a dazun.

“Ba lafiya ba Abiey, wani nauyin ne ya fado wanda ba zan iya dauka ni kadai ba”

“Fito fili ki fada min abun da yake faruwa”

“Shawara ce na yanke, daga Nimra har Namra za su fito da miji cikin satin nan kuma aurensu ba zai wuce kasa da wata ďaya ba”

Yanzu ma kallonta yake, sai dai kallon mamaki ne yake mata wannan karon.

“Hiayatee ba zaki yanke wannan hukuncin mai zafi a cikin kankanen lokaci haka nan kawai ba, dole akwai abun da kika gani fada min meya ke faruwa ne?”

“Jiya.. Dare bayan na fito daga bangarenka na leka ďakin kowa har na kai ga na Nimra, sai na samu wayarta a kasa bachi ya sace ta, na duka na dauki wayar sai na yi arba da wani sabo daya daga min hankali, number bata da suna sai heart emoji, ya turo mata sako cewar ta san irin karyar da zata sake yi su hadu, yayi missing dinta, and he can't wait for her hug and kiss...”

Wani dim dim dim gaban Abiey yayi ba, ya kara tattara hankalinsa ya maida gurin Ummi.

“Ban mata magana ba, sai na kyaleta daman ta fada min cewar jiya ta tararda taro da yawa a gurin saloon din da taje bata samu ba, dan haka yau tana son ta koma, na bata dama saboda na gane da gaske can zata tafi ko wani gurin, bayan ta fita na bibiyi motarta ina cikin tawa motar har ta isa wani gida aka bude mata gate ta shiga...”

Ummi ta bashi labarin komai har zuwa yanzu da ya shigo cikin gidan. Abiey ya mike tsaye ya cire babbar rigarsa ya aje har sai da Ummi ta ji tsoro ta tashi ta bi bayansa da sauri. Dakin Nimra ya nufa yana tabawa ya ji kofar a rufe sai ya banki kofar dakin da wani irin karfin zuciya da jiki.

“Nimra ki bude dakin nan, idan ba haka ba zan saka a balle kofar nan kuma idan aka balleta sai na rabaki biyu sai dai a buga ni a Jarida ki bude dakin nan na ce”

“Abiey calm down bari na yi magana da ita”

Ya dakawa Ummi tsawa.

“Ya zaki ce na kwantar da hankalina? Kamar baki san girman abun da ta aikata ba? Dole na yi magana da ita”

“Zata bude amman ka matsa jiki kofar zan mata magana zata bude”

Ya matsa gefe yana sauke numfashi da karfi, rabon da ya samu kansa a bacin rai irin haka tun a lokacin da Deen yake raye. Ummi ta matsa kusa da kofar ta ce.

“Nimra...”

“Na'am”

Sai ta amsa cikin kuka muryarta na rawa gwanin tausayi.

“Bude kofar nan, zamu yi magana da ke”

“Aa Ummi aa dan Allah”

“Ki bude na ce, so kike ki sake bata mana rai? Tambayarki zamu yi kuma dole ne ki amsa mana zamu yi magana ta fahimta ne ki bude kofar”

Ummi ma da kamar fada take mata maganar domin ita ma nata ran a bace yake. Sanin Abiey zai fi yi mata sassauci idan Ummi tana kusa ya aaka ta nufi kofar ta bude tana kuka sai ta matsa baya da sauri. Ummi ce ta fara shigowa sannan Abiey da sauri Nimra ta yi gefen Ummi sai Abiey ya daka mata tsawa.

“Karki kuskura taba min mata, dawo nan ki tsaya...!”

Wani irin dauke numfashi ta yi kamar zata shide, saboda tsawar ta ratsata kanta shiga har cikin jikinta, sai ta dawo ta tsaya a inda ya nuna mata jikinta na rawa.

“Tun yaushe kike aikata fasadin nan? Me ya saka baki bashi damar zuwa gidanku ba kika zabi kebewa da shi?”

“Saboda ba za su yarda ba Abiey, kuma ba mu aikata fasadi ba Abiey, Wallahi ban aikata zina ba”

“For how long kike tare da shi?”

Ummi ta tambaya.

“Anfi shekara.....”

“Innalillahi wa'inna Ilaihiraji'un, waye ubansa a garin nan dan gidan uban waye? Akan wani dalili kike haduwa da shi a wajen gidanku?”

Abiey ya tambaya yana matsawa kusa da ita, muryarsa kuwa kamar zata tashi ďakin. Matsawa ta yi baya tana kallon Ummi kamar tace Ummi zo ki cece ni ba dama. Bata ankaro ba Abiey ya kai mata mugun naushi a fuska sai da hokoranta ďaya ta dago bakinta ya cika da jini, wani tsalle ta ta yi, ta yi baya da sauri ta rike bakin ta haura saman gadonta.

“Wayyo Allah na na shiga uku, Ummi ki taimake ni Abiey ka yi hakuri dan Allah”

“Waye shi na ce?”

Ya sake daka nata tsawa, a rike ce ta fara zazzago masa bayani.

“Ameer ne, Ameer dan gidan Alhaji Bashir, wanda suka yi faďa da Ya Maleek, Ameer din da na bawa Motata ta tafi da ita Katsina Ameer ďin...”

Bata karewa ba Abiey ya daga mata hannu ya rumtse ido, Ummi kuma ta fadi zaune tana kallon Nimra cikin matukar tashin hankalin da ba a saka masa rana.

“Bakar zuri'a, bakin jini, ubansa ya gama shi kuma yanzu na shuka min nashi, so yake ya lalata min zuri'a so yake ya ɗasa min bakincikin da ubanaa ya bari...”

Abiey ya fada cikin wani irin fusata da be san ma iya abun da zai fito daga bakinsa ba. Kamin ya juyo gurin Ummi.

“Duk laifinki ne, babu gargadin da ban miki ba akan yaron nan, ta ya za'ace yarinya tana fita waje ta hadu da wani sama da shekara ďaya baki sani ba a matsayinki na uwa sai bayan da ya gama lalata min ƴa?”

Ummi ta mike tsaye tana kallon mijinta cikin wani irin bacin rai ta amsa masa.

“Kwarai laifina ne Alhaji Aliyu sai ka hada ni da ita Nimra ka binne...!”

Ta daki kofar ďakin da karfi ta fice fuuu kamar zata tashi sama.....






MALEEK POV.

“Ohhhh”

Ya fada yana buga teburin dake gabansa, bayan Abiey ya fada masa ya tafi makarantar su Waira ya ji abun da yake faruwa saboda sun buga masa waya kan cewar ta yi fada, kuma ya kira wayar Mahmood be samu ba, ga Ummi ya ji yanayinta da matsala zai tafi gida. A dole dolensa ya tashi tare da wayarsa da key din motar ya fice daga office din, yana gwada kiran Mahmooda ya ji ko zai same shi ya fada masa Abiey yace ya tafi saboda shi ya fasa zuwan, be samu ba har ya shiga motarsa ya murza key ya dauki hanyar makarantar. Har ya isa cikin makarantar be daina karan Mahmood ba kuma be samu wayar ba.
Cikin makarantar ya shiga gurin principal din ya gabatar da kansa, sai suka isa da shi gurin vice principal, a nan ya samu Waira zaune rumgume da jakarta, tana ganinsa ta mike tsaye da sauri ta nufo inda yake wai ita ta ga wanda ta sani sai kuma ta ja ta tsaya tunawa da basa shan inuwa ďaya. Gurin ya samu a one of visitors chairs ya zauna yana kallon mutumen da ya mika masa hannu suka gaisa.

“Sunana Maleek na zo ne akan maganar wannan yarinyar”

Ya nuna Waira.

“Eh mahaifinka ya kira ai ya fada cewar ba zaka samu zuwa ba, amman ďansa zai zo”

“Lafiya me ya faru?”

“Fada suka yi da wata yarinyar, ita dai yarinyar tace Waira ta fara tsokanarta, sai suka fara fada shi ne ita Waira ta dauki dutse ta buga nata akai kanta har da jini yanzu haka ita ma mahaifinta yana hanya”

Maleek ya juya ya kalli Waira da ta rumgume jaka, sannan ya juyo ya kalli mutumen.

“Waira bata da fada gaskiya, sai dai ko idan ita yarinyar ta fara taba ta”

“Ba a gane gaskiyar kowa, ita ta kasa magana daidai yadda za a fahimce ta”

Maleek ya dauki takadar dake gaban teburin mutumen ta pen ya mika mata.

“Rubuta abun da ya faru”

Ta karba ta soma rubutawa tana hawaye.

“Kullum tana tsokanata tace min ni ban iya hausa ba, kuma bana magana da daidai, tana ce min kuma kafira ban san me hakan ke nufi ba, ko ta rika min dariya, shi ne yau da aka kai mu park ta tsokane ni kuma na buga mata dutse saboda ta fi ni girma ba zan iya fada da ita ba”

Ta mika masa sai ya karanta ya mikawa mutumen, mutumen ya karba yana tsaka da karantawa mahaifin yarinyar ya shigo tare da ita, har wani hakilo yake yana an taba masa ya.

“Wannan ne mahaifin yarinyar?”

“Aa yayanta ne bismillah zauna mana”

“Ba zan zauna ba, kuma sai na dauki mataki akan abun da aka yi ma yata matukar ba ku hukunta yarinyar nan ba sai kun ga abun da zai biyo baya domin ďa be fi ďa ba”

“Ka yi hakuri ka zauna muna tattauna ne a akan maganar?”

“Tattaunawar me? Ga ciwo kuna kallo ta ji wa yata kuma ku ce kuna tattaunawa karshenta a ba ni hakuri bayan an cucu yata”

“Toh me kake so ayi maka Malam? A fashe mata kan ita ma? Bayan kuma yar ka ce take tsokanarta?”

A take fada ya kaure a tsakaninsu, domin Maleek ya kasa jurewa da abun da mutumen yake yi ne, suka yi ta fadawa juna magana daker aka shigo tsakaninsu, Maleek ya saka Waira a gaba suka fito daga cikin makarantar zuwa gurin motarsa. A nan Waira ta nade hannayenta ba zata shiga mota ba, daman can bata kebewa daga ita sai shi a mota ba, fadan da ta ga yayi da wacan mutumen ya saka ta tsorata tana ganin kamar itama fadan zai mata idan ta shiga motar. Ya bude mata motar da kansa.

“Shiga mu tafi”

Ta lake kafada.

“Shiga ko na mareki yanzu nan”

Ya daka mata tsawa, sai ta shiga motar da sauri ya rufe ya zagaya dayan side din ya shiga ya saka key, wani yanayi ya samu kansa a ciki na dabam, domin be taba kusanci da mace a mota kamar haka ba, be ma taba daukar mace a motarsa ba, sai wannan karon wanda ya tabbatar da acan da ne ba zai ma iya ba, ko da kallonta ne balle har ya dauketa.

“Waira bata son Abiey, Abiey ya kira waya yayi mata fada, Waira bata son Maleek, Maleek ya zo da mota yayi mata fada ta shiga Mota”

Ta fada tana takurewa gurin daya sai hawayen da suka fi kama da na shagwaba take. Ya kalli gefenta ya dauke ido.

“Baki son uba, baki son ďansa sai ki kashe su toh”

Tana jin hakan ta san bakar magana yayi mata sai kawai ta fashe da kuka, ta kama zoben dake wuyanta ta rike. For the first time ya ji kukan mace ya sauka a kunnensa daidai wa daida ya cika kwakwalwarsa.

“Ohhhhhhhhh miye wannan kuma? Zaji min kuka for sake i hate this crying, Abiey why zaka aiko nan? Kai”

Ya bude wani guri a motarsa ya dauko airpod ya saka a kunnesa ya kunna Bluetooth din wayarsa yayo connected ya kure karatun Qur'ane dan ya daina jin kukanta. Har aka isa gida bata daina kuka ba, shi kuma be bata hakuri ba ko kallon inda take be yi ba. Tana ganin ya cire abun kunne ya kashe motar sai ta bude muryarta mai kara ta kwala ihu just to annoy him tun da ta lura baya son kukan.

“Louder please”

Ta kara karawa tun da ya bukaci haka.

“Very good well done, to fitar min a mota please...”

Bata fita ba sai cigaba ta yi da kukan, shi kuma ya bude motar ya fita ya barta a ciki. Yana shiga cikin falon ya san ya lafiya ba, domin tun a downstairs yake jin kukan Nimra bama kamar da ya haura sama. Dakin mahaifiyarsa ya fara shiga sai ya same ta tsaye gaban madubi tana hawaye, kamar jiran take ya shigo sai kawai ta juyo ta fara bashi labarin abun da ya faru tana ta maimaita gurin da Abiey yake dora mata laifi, tun fara bashi labarin har ta gama hawaye take.

“Ba zai bar ni da abun da ya ishe ni ba, sai

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login