Showing 234001 words to 237000 words out of 271643 words

Chapter 79 - Wani Gari Book 1 Complete Hausa Novel

tambaye shi, me yake bukata daga garemu? Idan rakiya yayi toh zai iya komawa mun gode da zuwansa, amman ba zamu zauna da butulu irinki ba, idan muka yi kora ba ma bukatar dawowarta a cikin danginmu, a da mun yanke shawarar kasheki, sai dai Eid ya bauta miki ya jure duk wata kalar azabar mu saboda mu barki ki rayu, ta karkashin kasa mun yi ta aika miki da mutuwa har a daren jiya, abun mamaki kin aje al'adarmu da addininmu saboda kin ga na wadanda suka fi mu karfi. Tabbas yaro baka shigo garin mu ba sai da ka shirya, domin wani be taba gwada karya mana dokoki haka ya kwashe lafiya ba, ba mu tana tsarrafa tsafi irin wanda muka yi a daren jiya ba, amman komai ya kasa samunka a kusa da dakin ma aljannunmu ba su kusanta ba, a tare da kai mun ga aljanna mai irin tsafinka mun saka wadanda suka fita karfi da iko sub rabata da kai a tunaninmu ita take baka kariya, da muka sake aika tsafi sai ya dawo mana, tun farkon shigowar muke ta jefarka amman jifar ta kasa isa a inda kake, madubin tsafinmu ya kasa ganin fuskarka, jama'ar da ake turawa su kiraka kana saka musu fargaba da tsoro, a yanzu ba ma jayya da kai mu dai ba ma shiga gonar kowa kuma ba ma son a shiga gonar mu, Eid ya fada min tun jiya ka dage sai ka ga Sarki zaka tafi, fadi bukatarka Sarki zai sallame ka ka yi tafiyarka”

Sarkin ne da kansa yake fada Eid na fassara masa dan dolensa, mamaki da jindadi da kauna ya hana Nuwaira cewa komai sai kallon Maleek dake cike da burgewa.

“Alhamdulillah, hakika duk wanda ya dogara ga Allah shi kadai Allah ya isar masa, ni bana tsafi van tana tsafi ba, kuma ban taba sanin yadda ake yinsa ba kuma bana fatar yinsa, ni dai na san ina bautar Allah ba tare da shirka ba, sannan ina karanta ayoyi da addu'o'in kariya, a jiya ma na kwana ina karanta suratul Bakara, kuma duk wanda yake karanta iya da ayatul kursiyu Allah ya turo mala'ikunsa su yi gadin Mutum ne, a inda mala'ika yake kuma aljani be isa ya raba gurin ba, muka karanta ta a gidanmu shiyasa kuka aika tsafinku be isa a garemu, domin idan aka karanta sau daya a wata tana tsare gida ta hana duk wani abu mai cutarwa rabar gidan har wani wata, saboda wannan ni ba tsafi nake ba da za ku surfafa bincike da za ku fahimci wannan addini ne ba tsafi ba, kuma ina fatar wata rana za su aje na mu addinin da al'adar ku karbi cigaban da duniya ta zo da shi haka ma ku rumgumi musulunci ku watsar da tsafinku”

Cikin alfaharin da jindadi Maleek yake fada ana fassarawa Sarkin da yarensa, har sai da ya kai karshe sannan Eid ya ce.

“Ba mu bukaci ka tallata mana addininka ko al'adarka ba, ka bar mu da na mu, kai ma ka rike naka, Sarki yana tambayar dalilin ganinsa da kake son yi, kuma ina ganin ka samu abun da kake bukata zaka iya tafiya”

“Aa ban fadi bukatata ba tukuna, dan haka ba zan bar garin ba sai na isar da abun da ya kawo ni”

Eid yaja numfashi da karfi da bakinciki sannan ya fadawa Sarki abun da Maleek ya fada.

“Tuk rid jaur bhakar suuf hutk garfha ifftuk galink galink ket”

Eid ya juya ya fassarawa Maleek.

“Ya fadi bukatarsa ba ma son zamansa a cikin garinmu”

“Ina neman auren yarku Nuwaira ne, saboda a yanzu irin addini take yi, ta saba da irin al'adata da kuma dangina, ina tunanin bata da bukatar zama a cikin garin nan, domin ba zata canja addini ba ba zata sake komawa addininku ba, kuma ba zata karfi kujerar tsafin da kuke son bata ba, idan har kuka yarda kuka ba ni aurenta zan dauke ta mu bar garin nan da ita yau din nan ba sai gobe ba, kuma ba za su sake ganinmu ba, ina tunani bata da amfani a gareku a yanzu saboda ta karya dokokinku kuma kun yafe ta kamar yadda ka fada”

Eid ya mike tsaye ya bar kujerar da yake zaune ya nufo inda Maleek yake cikin zafin nama, kamin ya karasa Sarkin ya daka masa tsawa.

“Karka kuskura kai kanka ga halaka, kana ganin wannan matashin ka san sai da ya shirya sannan ya shigo garin nan, neman yake a taba shi ya janyo mana fitina, fassara min me yake da bukata”

Sai da Eid yayi da gaske ya yaki zuciyarsa sannan ya iya fadawa Sarki abun da Maleek yake da bukata, daga baya ya jadadda masa da cewar ba za su aminta da haka ba, domin wannan ya zama cin fuska, kuma saboda ta karya dokokinsu har sun yi fushi da ita sun yafe ta ba shi yake nufin a barta ta aure wani bare ba. Sarki ya daga masa hannu.

“Yanke hukunci ba a hannunka yake ba Eid karka zafafa, kuma kar bacin rai ko soyayya ta saka ka manta da ka'idodi da dokikin garin nan, idan muka yafe mutum muna nufin cire hannayenmu daga duk wani lamari nasa, ko da kuwa zai mutu ne, kuma ba zamu tarbe shi ba ko da zai bukaci dawowa a garemu, ba kuma zai aura daga garemu ba.
Kaka ya taba fada min cewar kamin a haife ni, wasu mutane biyu sun taba karya mana doka, ya saka aka koresu daga garin nan, har yanzu babu ruwanmu da iyalansu, ta farko daga cikin gari take, lokacin da dadin tsafi yayi mata yawa sai ta zurfafa ta dauki maita, mu kuma ba mu yarda da maita ba, duk wani tsafi bayan wanda muka gada gurin iyayenmu ba mu yarda da shi ba, sanadin hakan muka kora Iya ta bi duniya, har yau babu ruwanmu da zuri'arta, bayan ita kuma Wasim ɗa daga masarautar nan, soyayya ta dibeshi kamar yadda take son dibarka a yanzu, ya karya mana dokoki ya shigo mana da bare, kuma ya fitar da ita ba tare da izinin kakanmu ba, daga karshe ya zabi addininsu da al'adarsa ya watsar da ta mu, hakan ya saka shi ma muka yafe shi, shi ma babu ruwanmu da shi da zuri'arsa, dan haka karka yi kuskure biyewa son zuciya ta kai ka ta baro”

“Duk wata azabtarwa da wahala da na jurewa sha a gurinku, tsawon lokacin da Waira ta dauka bata kusa, na jure ne saboda ina sonta ban taba fadawa kowa wannan maganar ba amman zan fade ta a cikin fadar nan, na san kowa ya lura da hakan, na raine ta tun tana karama har ta fara wayo, rana daya kuma sai wani ya dauke min ita?”

Wani daga cikin manyan masarauta da suke gurin ya mike tsaye ya isa gurin da Eid yake tsaye ya dafa shi.

“Kwantar da hankalinka Jarumi na, akwai mata da yawa a cikin garinmu da suke sonka, akwai matan da suka fi Waira kyau da komai ciki da wajen masarautar nan, ka rufe idonka daga ganin Waira ka bude idonka a garesu cikin kankanen lokaci za a gama da su, karka yarda zuciya ta deba ka gujewa umarnin masarautar nan, domin wannan matashin ba zai yarda ya barka maka Waira ba, ko da kuwa ka yarda ka koma cikin kalar tsafinsa ne, idan kuma muka hana masa ita zai iya gwada jayayya da mu”

“Toh a bar mu mu kara mana, sai a gane waye jarumi”

Ya fada da kakkausar murya yana tabe baki kamar zai yagashi.

“Ba mu taba gwada yaki ba, kuma ba zamu gwada saboda wata korariya a garinmu ba, ban yi tunanin karfin tsafi zai yi tasiri a gareshi ba, ko da ya ce ba zai aureta ba, ba samu yarda ta aura daga garemu ba wannan shine magana ta karshe”

Eid da duk sauran mutanen da suke fadar suka risnar da kai domin nuna biyayya ga Umarnin Sarkin da ba a musawa. Eid ya dago yana kallon Maleek fuska kamar an aiko masa da mutuwa, zuciya kamar bakin maciji dake cike da dafi, ya fice daga fadar yana hararar Maleek yana huci kamar zai fitar da hayaki. Duk wani abun da ake fada Maleek be ji ba, domin da yarensu suke maganar, Waira kuma jinta da ganinta tunaninta mamakinta zuciyarta da ruhinta gaba daya sun tafi gurin mutumen da take kira da yayanta wato Ya Maleek. Furucinsa na cewa yana son aurenta da jarumtar da ya nuna akanta sadaukarwa neman kareta sassauta ra'ayinsa da nema mata farinciki da yanci wani abu da ya kai ta rubuta a dutsen da ba goge zane da alkalamin zinari. Hawaye take irin hawayen da ba zata iya fadar na minene ba a yanzu, na farincikin abun da Maleek yayi mata ne ko kuma na samun yancinta ko kuma na komawa da zata yi gurin matar da ta zame mata uwa? Ko kuma dai na fasa kasheta da aka yi ne? Wata kila kuma na tsafin da suka ce sun yi ta aikawa Maleek ne be same shi ba.

“Nuwaira...”

Kamar wadda aka jefowa numfashi daga sama haka ta zabura ta dawo hayyacinta, sai ta lumshe ido tana jin ba a taba kiran sunanta da dadi kamar yadda Maleek ya kirata a yau ba. Rufe idon da ta yi sai ya saka shi tunanin ko bata ra'ayi ne musamman ma da yayi arba da hawayen dake zuba a idonta gashi tun da ya furta maganar take kallonsa ta kasa cewa komai kuma ta kasa dauke idonta daga gareshi.

“Ko baki so ne? Karki damu, na yi hakan ne saboda na sama miki hanyar fita daga garin nan, idan sun amince sun ba ni aurenki da zarar mun fita ba aurenki zan yi ba, za a miki aure ne best on zabinki”

Rashin Eid a fadar da zai iya fassara musu abun da Maleek yake fada, ya saka Sarkin amfanin da nasa baiwar ta tsafi ya yi communicating da aljannunsa suka fassara masa abun da Maleek ya fada, hakan kuma ba karamin dadi yayi masa, domin ya fahimci Maleek ba gaske yake son Waira ba, hakan na nufin zai fara mata yi mata butulci da zarar sun bar garin kenan, kuma hakan ya nuna Waira bata son shi, a kokarin Sarki na bakanta musu ya kalli na hannun damansa ya ce.

“A fadawa Dardu ya tada busa ya hura wuta, mata su fara nika ganyen za a daura aurensu a yanzu”

Nuwaira ta bude ido da sauri ta kalli Sarki domin daga ita sai jama'ar garin suka iya jin abun da Sarki yake fada ban da Maleek. Sarki ya kalleta yana tana tauna hakora ya ce.

“Zamu aura miki shi, kuma zamu cire duk wani tsafi da kariya ta mu da take jikinki yanzu nan, kuma duk wani abun da zai faru ko ya biyo baya karki neme mu, babu mu babu ke da zuri'arki”

Kasa cewa komai ta yi sai har lokacin hawayen ba su daina sauko mata ba.
Duk wata al'ada da ake gudanarwa kamin bikin auren sai da sarkin ya saka ka yi ta, ba a daura auren ba sai da suka hanka hannun Nuwaira suka cire layar dake cikin hannun nata, suka shafe jikinta da maganin da ke karya duk wani kalar tsafi na mutum, sannan aka daura musu auren har aka yi aka gama kuka take na azabar cire mata layar da aka yi a hannu. Maleek ya nemi izini ya koma masaukinsu ya dauki wayarsa sannan suka rakosu har bakin kofar garin suna tafiya ana wasa farar kasa a duk inda suka taka da haka har suka fita daga cikin garin. Kamin su isa gurin da motar Maleek take Nuwaira kamar zata fadi taka take taka kasar kafarta babu talkami ga jikinta sai rawa yake tana jin wata kalar azaba kamar an tsaga mata duka jikin. Maleek ya rigata karasa gurin motar ya bude mata back seat ta shiga ta kwanta domin bata iya zaman kirki ma, tun da ta rufe ido bata bude ba har ya kama hanyar Abuja. Sai da yayi tafiya mai nisa kiran Ameer ya shigo wayarsa shi har ya manta da waya a jikinsa ma sai a lokacin ya tuna. Hannu daya ya saka ya ciro wayar aljihunsa dayan hannun kuma yana driving da shi all his thoughts is Ummi ko Abiey ne ya kira but ga mamakinsa sai yayi arba da Number Ameer, haka nan kawai ya ji baya bukatar amsa kiran dan haka ya aje wayar a gefen seat ya cigaba da tukinsa a haka Ameer yayi masa kusan miss calls 30 da ya gaji da jin ringing din ne ya dauki wayar sai ya kiran Abiey ne ke shigowa wannan karon and ba zai ki amsa kiran mahaifinsa haka nan kawai ba.

“Hello”

“Maleek kana ina? How are you? Are you okay?”

“Ina lafiya kalau Abiey babu abun da ya same ni Nuwaira ce kawai bata da lafiya ina hanyar Abuja yanzu haka tare da ita”

“Alhamdulillah, amman me kake nufi tare da ita?”

“Labari ne mai tsawo Abiey but at the end dai sun ki karbarta sun yafe ta, and sun aura min ita bayan sun rabata da duk wani tsafi da yake jikinta”

“What? Okay Allah ya kawo ka lafiya”

“Ameen ina Ummi?”

“Tana saurenka muna tare da kowa a nan ka kula da hanya, mun yi magana da police akan cewar za su tafi yau su taho da kai bari na kira na fada musu kana hanya”

“I will”

Ya aje wayar ya maida hankalinsa gurin tukin yana yi yana dan juyawa ya kalli Nuwaira da idonta suke rufe.

“Nuwaira Nuwaira”

Ta bude idonta daker ta kalleshi.

“Sannu”

Bata amsa masa ba ta sake maida idon ta rufe. Haka yayi ta da ita har suka fara jiyo kamshin garin Abuja, ba shi tsayawa komai sai Allah ko ruwa be sha ba tun da suka bar Katsina har suka kusa isa Abuja. A lokacin da ya isa da ita cikin garin Abuja be sauka a ko'ina ba sai asibiti, domin ya lura da Nuwaira ta galabaita har bata iya bude idon ma idan ya kirata sai nishi take kamar mai nakuda.



AMEER POV.

Cikin wani yanayi na rashin lafiya ya isa gidansu Humairah ba dan ta kira a waya ya kasa amsa ba kuma yayi mata alkawarin zuwa ba da ba zai tafi a wannan yanayin da duniyar bata mishi dadi ba. Yana fakawa harabar gidan ta fito ta tarbe shi da far'ar irin na zumudin ganinsa sai dai yanayinsa da ta ganin bayan fitowa daga motar ya saka jikinta yayi sanyi daukin ganinsa da take sai ya ragu.

“Are you okay?”

“I don't know ina jin dai kamar ba ni da lafiya”

“Akan Waira ne?”

Yayi kamar be jita ba ya cigaba da tafiyarsa har ya shiga cikin falon, sai da ya zauna sannan ya gaishesu. Hajiya da kanwar mahaifinsa suka amsa suna karantar yanayinsa da ya canja.

“Allah yasa ba Ummi ce ta bato maka rai ba kuma Ameer”

Ya dago ya kalli Hajiya cikin yanayin damuwa.

“Hajiya idan kina son na so ki kuma na kaunace ki na girmamaki ki daina maganar Ummi marar dadi a gabana, duk wani abun da ta yi min ko zata yi min ita din uwata ce babu wanda ya isa ya canja wannan, kuma wannan damuwar tawa ba akanta ba ne akanta ba ne akan yarinyar da nake so ne”

Humairah ta zauna tana kallonsa.

“Wani abun ya same ta?”

“Ina fatar dai tana cikin aminci, domin Maleek ya bita sun shiga garin kuma police din sun ce mutanen sun fara dauka da zafi tun kamin su shiga da ita ma, ina ta kiran wayarsa kiran be shiga ba Abiey ma ya kira wayar bata shiga, and jiki na bani wani iri like kamar ba kalau ba akwai dai abun da yake faruwa”

“Da alama dai kana son yarinyar sosai Ameer”

Ameer ya kalli Bahijja ya daga mata kai yana kiranta da sunan da Humairah take kiranta.

“Sosai Mama ina son fiye da tunanin duk wani mai tunani”

“Allah ya zaba maka abun da ya fi zama alheri”

“Ameen thank you”

Ya kalli Humairah

“Ina list din?”

“Ko mu bari sai next time na ga kamar baka cikin yanayi mai dadi”

Sai ya mike tsaye ya saka hannunsa aljihu ya ciro kudi mai kauri ya duka gaban Hajiya ya aje mata.

“Ga wannan ko da zaku yi hidimar gida, zamu je da Humairah mu siyo wasu abubuwa sauran kuma ina tunanin sai dai na bada kudi a siyo dabam”

Hajiya ta mika hannu ta dauki kudin tana dubawa, farincikin ganin kudin ya kawar da damuwar maganar da ya fada mata akan Ummi a take ta washe da kau har ta fara hade fuska, ganin kamar baya son ana ganin laifin Ummi bayan kuma ita din a gurinsu babbar mai laifi ce.

“Ameer wannan duk hidimar gida? Maa Shaa Allah, Allah dai ya saka maka da alheri, ina ma ace mahaifinka yana raye ya ga wannan hidimar ace dansa ne yayi, Allah dai yayi masa rahma”

Ta karasa tana fashewa da kuka domin har ga Allah tana jin kewar danta, abubuwa da yawa tana yawan fata ina ma yana raye yayi mata, yau gashi kuma daga jininsa anyi mata amman bashi a raye balle ya gani. Maganar mahaifinsa da ta yi da kuma kukan ya saka Ameer kara shiga damuwa, sai ya ji abun ya ninka masa. Ajiyar zuciya kawai ya sauke ya fice daga falon. A mota Humairah ta same shi bayan ta saka hijabinta ta dauko takardar da suka yi list din. Be ce mata komai ba ya fara tuka motar, ita ma bata ce masa komai ba, kuma ta yi iya kokarinta ta dauke idonta daga gareshi har suka isa super market din. Ya faka ya ciro wayarsa yana gwada dialing number Maleek yana fadin

“Me zamu fara siya?”

A lokacin da ya kira wayar Maleek kiran ya shiga sai ya ji wani irin sanyi a ransa, har wani gyara zama yake yana kallon Humaira murmushi na bayyana a fuskarsa.

“Wayar Maleek ta shiga”

“Allah yasa ya daga”

Humairah ta masa addu'ar tana masa fatan samun jin muryar Waira domin bata son ganin damuwa a tare da shi, hakan ya saka take masa fatan samun Waira a yanzu

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login