Showing 252001 words to 255000 words out of 271643 words

Chapter 85 - Wani Gari Book 1 Complete Hausa Novel

ba, damuwarka na jefani a matsala sosai”

Ya kalleta da kyau.

“Why?”

“Saboda kana da muhimmanci a gareni, ina matukar tausayinka a yanzu”

Ya gwada yin murmushi.

“Da can baki tausayina kenan?”

“Ba karya a da kam bana tausayinka sai da ina jin haushin abun da kake yi duk kuwa da kasancewar bana da alaka da kai a wacan lokacin, a yanzu kuma ina tausayin halin da ka samu kanka a ciki”

Be sake ce mata komai ba ya ja motar suka hanyar gida. Yana yi yana satar kallonta har suka isa gidan.




NUWAIRA POV.

Tana jin takowar Namra ta dago kai. Cikin yanayi na damuwar da take ciki ta tambaye ta.

“Yau kuma a stairs kike son zama? Dakin ya miki wani abu ne ko kuma tsoro kike ji?”

“A'a dazun da Ya Maleek zai fita na tambaye shi jikin Ummi be fada min ba, ina jiran ya dawo ya fada min ne”

Ta fadi hakan ne kawai dan ta kare kanta amman ba dan son jin ciwon Ummi kadai take jiran dawowarsa ba har da daukin ganinss da take yi. Namra ta sauke ajiyar zuciya ta zauna kusa da ita.

“Baya son ya fada miki ne saboda fadin ba shi da dadi Nuwaira, ni ma da ace akwai yadda zan ji na hana kaina jin abun da na ji akan ciwonta a dazun da na yi, amman ban isa na yi hakan ba”

“Bata ji sauki ba?”

A take idon Namra ya cika da hawaye.

“Saukin dai muke fata a yanzu...”

Tana bata labarin tana kuka Nuwaira ma kukan take daman abun da ta dade tana tsoron faruwarsa kenan bayan ta gano ciwon Ummi. Kuka sosai take na tashin hankali har ta fi Namra daga murya daga karshe ma Namra ce ta koma tana bata hakuri ta kwantar da ita a kafadarta. Suna a wannan halin Abiey ya shigo bangaren yana sanye da nasa tufafin bachin, kallo daya zaka masa ka san akwai damuwa sosai a tare da shi domin damuwar ta kasa boyuwa a fukarsa.

“Me ya faru?”

Ya tambaya ganin Nuwaira na kuka sosai Namra na rarrashinta ita ma tana kukan.

“Na fada mata abin da ka fada min ne a dazun”

Abiey ya sauke numfashi a hankali.

“Toh ya za'ayi, dole sai hakuri, Nuwaira zan iya magana da ke a yanzu?”

Jin haka ya saka ta dago ta dube shi, sai ta mike tsaye ta fara saukowa, Abiey yayi ma Namra alama da ta ba su guri da ido, sai ta tashi ta haye stairs din ta shige dakinta. Abiey ya samu guri ya zauna ya zubawa Nuwaira dake kokarin ganin ta saita kanta ido, ita ma sai tausayinta ya kama shi domin ita ta rasa duka uwa da uba a age dinta, kuma matar da ta zame mata uwa tana kokarin tafiya ya barta.
“Babu abun da zamu yi sai hakuri, ki cigaba da yi mata addu'a In Shaa Allah zata samu sauki”

Ta amsa masa da kai tana share hawayenta.

“And dalilin zuwa a nan saboda ke ne, dazun Alhaji Bashir mahaifin Ameer ya same ni da maganar aurenku da Ameer ya son idan kun daidaita kanku mu kuma sai mu shiga ciki, domin ina son na hade aurenku da Namra da kuma Maleek da Mahmood saboda kawai na faranta ran Ummi, likitoci sun ce idan akwai wani abun da ya muke da buri ko kuma ita take da buri to mu aiwatar mata da shi a yanzu, domin ciwon nata kara tsanani yake”

A take tashin hankalin ya rufe Namra, wani irin faduwar gaba da fargaba da bata taba samun kanta a ciki ba ya rufeta, bata san wani abu gumin tashin hankali da sarkewar numfashi ba sai a lokacin, kamar ta bude baki ta cewa Abiey bata son Ameer kuma ba zata iya ba, domin yana da girma a idonta kuma baya wata magana mai girma bata taba hadasu haka ba, gani take kamar idan ta musa masa zai ce bata kyauta masa ba ne.

“Nuwaira”

Ta kasa amsawa kuma ta kasa dagowa ta kalleshi sai hawaye suke mata zuba kanta na sarawa a take zazzabi da tsanyi suka rufe ta.

“Nuwaira ina son ki bude bakin ki amsa min abun da zan tambaye ki, karki ji kunya ko nauyi na, karki cuci kanki kuma karki cutar da kowa, ki fada min abun da yake ranki, Shim kina son Ameer?”

Ta dago jajayen idanuwanta ta kalleshi hawaye na mata zuba ta girgiza kai alamar aa bakinta har rawa yake saboda kukan dake cikinta.

“So na aure nake magana kina son Ameer zaki iya aurensa ki zauna da shi? Idan baki sonki ki amsa babu wanda zai miki dole domin ke ma amanace a gurinmu”

Abiey ya fada mata a kokarinsa na fahimtar da ita, sai ta girgiza kai.

“Toh shikenan, amman kin tabbatar baki son shi? Kuma ba wani ya cilasta fadar hakan ba?”

Ta daga masa kai da sauri.

“Akwai wanda kike so a yanzu? Wanda zaki iya gabatar mana? Domin a al'ada da addininmu wanda kika kai a yanzu, kin kai munzalin aure, kuma addinin musulunci ya bawa mace zabar wanda take so, ba a yarda a aurawa mace wanda bata so ba, akwai wanda kike so?”

A al'adarsu bata sun kunya a yayin zaben miji ba, amman sai ta samu kanta da kasa amsawa Abiey wannan tambayar, wata kila tana jin tsoron yadda zai kalli abin ne ko kuma tana tsoron reply din da Maleek zai mata ne.

“Bude baki ki min magana idan akwai wanda kike so idan kuma lokaci zan baki ki yi tunani zan iya miki haka, amman dai ina son ki sani ina son cika burin Ummi ne”

Jin haka ya bata gwarin guiwar amsa masa ba tare da ta dago kan ta kalleshi ba.

“Tun a can garinmu an daura mana aure da Ya Maleek amman shi da Ameer sun ce ba auren gaskiya ba ne sai an sake daurawa”

Abiey na jin haka ya fahimci inda ta doso, domin ta yi masa magana ne da halshen damo, bata fito fili ta fada masa abun da take nufi ba, wata kila tana tsoro ne ko kuma tana jin kunya.

“Eh haka ne, dole ne sai an sake daura muku aure na musulunci, yanzu dai idan na fahimta Maleek kike so kenan?”

Abun ka da wanda ba bahaushen mutum ba sai ta daga kai tsaye tana kuka.

“Eh amman zai iya min fada, shi baya so na nindai ba zan auri Ameer ba, Ya Maleek nake so”

“Ta kwana gidan sauki, daina kuka yarinya zan yi magana da shi idan ya amince shikenan idan kuma be amince ba shi ma ba zan masa dole ba kamar yadda ke ma ban miki dole ba”

Ta amsa da kai sannan Abiey ya mike tsaye ya nufi bangarensa, tsoron kar Maleek ya dawo ya same ta a falon ma ya saka ta shige dakin Namra ta kwanta kwanan dole, amman bachi ya ki daukarta sai ta da dare ya raba. Washe garin Abiey ya labartawa Maleek abun da ya faru tsakaninsa da Nuwaira bayan na gama fadawa Daddy yadda suka yi a waya, Maleek sai ya rasa me zai yi farinciki ta fadi shi take so, ko bakincikin dan'uwansa Ameer ya rasa? Domin ya lura Ameer yana son Nuwaira sosai sai dai ba su isa su yi mata dole ta so abun da bata ra'ayi ba.

“Amman Ameer zai ji wani iri idan ya ji, zai shiga damuwa”

“Ina kyautata zaton zai fahimta, kuma idan har ya sauya a yadda ni da kai muke gani zai yarda ya karbi wannan kaddarar ne”

“Amman Abiey abun is some how ta ya zai kalleta a matsayin matata?”

“Ta yadda zaka kalleta a matsayin matarsa da ace abun da yake nema ya samu, idan baka ra'ayinta kai ma ba zan maka dole ba kamar yadda ban mata dole ba, zaka iya gabatar da wadda kake so sai mu bincka iyayenta da tarbiyarta kamin lokaci ya kure mana”

“Zan yi tunani akai Abiey, a bani kwana biyu”

Daga haka ya mike tsaye ya fice daga falon, ji yayi baya bukatar ganin kowa sai Nuwaira a lokacin dan haka ya nufi bangaren Ummi, yana shigowa ta ganshi sai ta saki kular hannunta ta juya zata bar falon da gudu, cikin hanzari da jarumtaka ya sha gabanta sai ta duke ta rufe kanta, tunanin take zai mata fada ne ko ya fada mata magana marar dadi akan abun da ta yi, domin bata da masaniyar yana sonta ko akasin haka all what she knows is ita dai tana sonsa. Dukawa yayi gabanta ya kalleta gabansa na bugawa da mugun karfi, har lokacin kuma ya kasa faricikin ya kasa bakinciki kuma ya kasa ganin laifinta haka ma yana ganin babu hujjar da zata saka ya zargeta da kin Ameer.

“Me ye na rufe idon?”

“Fada zaka min?”

“Saboda kin san abun da kika yi baki kyauta ba ko?”

“Ni dai kawai na fadi abun da yake zuciyata ne”

Ta amsa da muryar dake nuna alamar tana daf da fashewa da kuka, har lokacin kuma bata yarda ta dago ta kalleshi ba. And now murmushi ne a fuskarsa sometimes tana abu kamar wata yar 6 years.

“Me yasa baki son Ameer?”

“Ni dai kawai bana son shi da aure?”

“Sai wa?”

Ta ki yarda ta amsa masa, har ya gaji da jira ya mike tsaye ya rumgume hannayensa yana kallonta.

“Ba fada zan miki ba tashi tsaye”

Ta ki ta mike tsayen kuma ta ki ta dago kan, har sai da ya gaji da tsayuwa ya fice daga falon, yana maida kofar ya rufe sai ya jingina da kofar ya lumshe ido yana murmushi...






AMEER POV.

Zagaye zagaye Daddy yayi ta masa sannan ya fada masa gaskiyar abun da Abiey ya fada masa na irin amsar da suka samu daga gurin Nuwaira. Ameer yayi murmushin da hausawa ke cewa ya fi kuka ciwo ya hade wani abu da ya tsaya masa a makoshi.

“Daman na saka ran haka, domin na lura da yadda take mu'alama da ni babu so a ciki”

“Wata kila lokaci take bukatar a bata...”

“Aa Daddy, da ace kudi yana siye rago kyau na san zaka iya siya min, idan har bata son aurena bana son na aureta a dole kuma iyakar son gaskiya da zan nuna mata a yanzu shi ne na barta ta auri wanda take so, ko da kuwa bera ne, indai hakan zai saka ta farinciki ni ba ni da matsala zan jur har na saba, sometimes dole ne mu karbi kaddara, Humairah tana yawan fada min haka, kuma ni ma ya zamin ishara wata ma rai ta rasa saboda ni, ni me yasa ba zan iya hakuri ba? I have to accept this Daddy”

Duk kokarin da yayi na danne zuciyarsa sai da hawayen bakinciki suka zubo a idonsa.

“Haka ne, wani lokacin kana ganin abu sai kuma ya zama ba alheri ba ne a gareka, Allah ya saussauta maka Ameer, zan yi magana da Abiey ya daga maka kafa har ka warke daga wannan ciwon kamin ka samu sukunin son wata a ranka”

“Ba zan taba warkewa ba daddy har a bada, kuma ba zan bari hakan yayi tasiri gurin hana ni cika burin Ummi ba, wannan ne lokacin da zan amsa sunana na cikeken musulmi mai yarda da kaddara”

Daddy ya sauke ajiyar zuciya yana kallon Ameer cike da tausayi.

“Allah zai maka mafita soon Ameer”


“In Shaa Allah”

Ya tashi ya fice daga falon. Dakinsa ya shiga ya kwanta sai ya ji gadon baya masa dadi, ya tashi zaune zaman ma babu dadi, a take ya fara safa da marwa yana son yayi kuka ya kasa domin abun ya fi karfin kuka a gunsa, sai dai mamaki kawai yake da dariya wani gefen kuma yayi murmushi. Da ya ji kamar ba zai iya da zaman gidan ba ne ya saka ya fice daga gidan ya nufin gidan kakarsa, a nan kam ya samu sukunin yin kuka bayan ya budewa Humairah zuciyarsa. Dole ce kawai ta saka ya shiga gidan Abiey da daren ranar domin ya gama shirinsa na tafiya ziyarar Ummi, kuma yana son tafiya yayi ma Abiey Namra Mahmood da Maleek sallama har ma da Nuwaira. Daya bayan daya ya biyu yana sallama da kowa, Abiey ya dade yana masa nasiha kuma ya nuna masa babu hannu ko laifin kowa a ciki, bayan ya gama karanta masa muhimmanci yarda da kaddara, hakan da Abiey yayi masa ya saka shi jin sanyi domin be saka tsammanin Abiey zai zaunar da shi ya masa nasiha mai ratsa zuciya haka ba, bayan duk abun da ya faru a tsakaninsu sai a yanzu yake tsantsar nadama da bakinciki abun da ya aikatawa Nimra, a yanzu ya fi gane yayi kuskure fiye da baya. Bayan ya fito ya shiga dakin Mahmood ya gaisa da shi kuma yayi masa bankwana tafiyar da zai yi ya shiga dakin Namra a nan ne hankalinsa ya tashi a lokacin da yayi arba da Nuwaira abun ka da mai karfin hali kuma sai kallonsa take, sai yayi mata murmushi ya ce.

“Zan tafi gurin Ummi gobe kina da sakon da za a kai mata?”

Ta kalli Namra sai ta kasa cewa komai.

“I'm sorry for loving you Nuwaira, i was afraid of leave you, amman yanzu na fahimci we are not mean for each other, ina miki fatan alheri kuma ina miki addu'ar Allah yasa wanda kike so ya rike ki amana ya so ki fiye da ni, ban cancanki ba Nuwaira a gane hakan a yanzu, kin cancanci auren tsabtatacen mutum wanda kika so saboda samun farincikinki, baki cancani mutum mai son kai da rufe ido ga bukatun wasu ba irina, duk haka kuma zan miki godiya domin zuwanki a rayuwata ya canja rayuwata ya koya min darasi da karatun da ban san da shi ba a baya”

Hawaye ya sauko idonta maganarsa na taba ta, sai dai ita dai ta san har ga Allah bata jin son Ameer da aure, ko da kuwa zata rasa Maleek ne, ba Ameer ba har Eid da yake dan'uwanta bata jin zata iya aurensa, haka ma bata jin tana yi ma Sulem dinta irin wannan son, Maleek kawai wanda yayi nasarar cike wannan ramen a zuciyarta.

“Bana nufin cutarwa dan Allah ka fahimta”

Sai ya mata murmushi ya girgiza mata kai.

“Noo please don't cry idan ban fahimce ba waye zai fahimce ki? I know what you mean”

Ya kalli Namra dake rike da system.

“Zan wuce gurin Ummi gobe ayi mana gafara ban san ta rai ba”

“Ameer dan Allah karka hukunta kanka karka dorawa kanka laifi akan abun da ya faru, dukan mu muna kuskure, please don't feel bad akan abun da ya faru, i wish i could do something”

“You're such a wonderful Sister, thank you sai na dawo”

Ya juya ya fice daga dakin, sosai tausayinsa ya kama Namra. Ta juya ta kalli Nuwaira dake kuka.

“Ina ma ban dawo ba, na bata ran mutane a nan na saka wasu a damuwa Ummi ma ba zata ji dadin haka ba, me yasa zan zaba a tsakanin yan'uwa?”

Namra ta aje system din hannunta ta nufi inda Nuwaira take tsaye ta rumgumeta.

“Baki da laifi ke ma, Ameer ba shi da laifi haka ma Maleek, so baya duba kusanci ko tazara, haka baya duba alaka da yan'uwanta baya duba arziki da talauci, na tabbatar da ace Ya Maleek ne ya rasa ki zai iya rasa ransa ma”

Nuwaira ta dago ta kalleta.

“Ya Maleek din?”

“Kwarai Nuwaira yana sonki fiye da yadda kike tunani, sai dai yana da wani irin kawaici da karfin hali, yana da halin girma da kokarin na danna abun da yake ji a ransa”

“Amman be taba fada min yana so ba”

“Yana duba alakarki da Ameer ne, amman a yanzu komai ya zo karshe dole ne kowa ya karbi kaddarasa kuma ya yarda da gaskiya”

Nuwaira ta maida kanta a kirjin Namra ta kwantar tana tunanin Maleek din. Gaba da rikicewa Maleek yayi a lokacin da Ameer ya sauko kasa, sai ya dan juya baya yana taba kayan dake dinning din, kunyar kallon Ameer yake kuma yana jin kamar be kyautawa Ameer din ba. Ameer na ganin haka ya isa gurinsa ya saka hannu biyu ya dafa shi yana murmushi.

“You got lucky, babu wanda ya fada min amman a yanzu na fahimci kai ta ce tana so kenan”

Maleek ya juyo ya kalleshi cikin karfin hali, zai yi magana Ameer ya tari numfashinsa.

“Please don't say anything, Wallahi ban ga laifinka ba, yarinyar nan ta cancanceka, kuma kai sadaukarwa ka yi da zuciya daya, sai Allah ya saka maka, na san zaka rike amana fiye da ni kuma ina mai tabbatar maka hakan ba zai taba alakarmu ba blood is thicker than water”

Maleek ya rugume shi yana jin babu dadi, if ba dan neman ya faranta ran Nuwairar ba da shi ma zai iya hakura da ita, domin ba ya jin zai iya samun farinciki ga bakinciki dan'uwansa. Ameer ya sake shi suka yi sallama sannan ya fice. Gidan Hajiya ya nufo a falo ya same ta bayan ya gama yi mata sallama ta sanar masa Humairah tana dakinta fever ya rufeta, cikin sauri ya shiga dakin sai ya same ta kwance a kan gadonta idonta a rufe ta lulluba da blanket. Gefen gadon ya zauna ya kira sunansa sai ta bude idonta a hankali.

“Me ya same ki?”

Hawaye ne ya sauko idonta.

“Ina ta tunanin abun da zan maka na dauke damuwar nan dake tare da kai a yanzu Ameer, gashi gobe zaka tafi zan yi kewarka sosai”

Yayi murmushi.

“Ki yi min addu'a kawai kuma tafiya ai zamu yi waya, zamu yi video call ma”

Ta tashi zaune.

“Zan je na yi magana da Nuwaira kamin ka dawo maybe ni zata fahimce ni”

“No na rufe babinta a yanzu Humairah, ba mu iya cilasta wasu su so mu, ya kamata mu koyi haka? Ba ma iya juya zuciyar wani garemu”

“Haka ne, da zamu iya da mun juyo da zuciyar wasu izuwa garemu, dole ne mu karbi kaddara”

“Yeah, kuma daman can kin yi min baki idan an rasa mai so na ba zai na dawo ki san yadda zaki yi da ni ba”

Cikin zolaya yayi mata maganar amman a take ta ji an zare mata duk wani ciwo da take ji, sai ta sauko da kafafuwanta ta sauke idonta kasa tana murmushi. Shi kuma ya

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login