Showing 141001 words to 144000 words out of 271643 words

Chapter 48 - Wani Gari Book 1 Complete Hausa Novel

amman ya ki baki kulawa saboda baya kaunarki, sai daga wasu kike samu kulawa da kauna, kuma saboda ya rusa farincikinki sai ya fito da rana tsaka ya rusa mafarkinki...”

Humairah ta yi fuskar mamaki jin wani abun banbara gwai, tana kokarin fahimtar hanyar da yake dorata, kamin ta zaro ido ta rufe baki da sauri tana kallonsa...




UMMI's POV.

Cikin rauni da fargabar zai dauko ko ba zai dauka ba ta zabura a lokacin da yanke kiran nata. Sai ta hade yawu da karfi ta zauna bakin gadonta, daman dai she wanted to know halin da yake ciki domin ta fahimci yana da saurin fushi da zuciya, kar ya jefa kansa a wani hali. Sakon kar ta kwana ta aika masa sannan ta aje wayar ta mike tsaye sai ga kira ya shigo, da sauri ta dawo ta dauki wayar a zatonta Ameer din ne ya kirata sai ta ga Namra. Lumshe ido ta yi ta sauke ajiyar zuciya sannan ta amsa kiran.

“Assalamu Alaikum Namra....”

“Innalillahi Wa'inna Ilaihiraji'un”

Shi ne ya biyo bayan sallamar da Ummi ta yi wayar dake kunneta ta subuce ta fadi kasa...
Labarin da Mahmood ya bashi ya zama masa wani sabon lamari a cikin kai da be taba mafarkin faruwarsa ba. A tunaninsa Mahmood zai fada masa cewar Ummi tana dauke da cutar cancer su tattauna akan cutar, amman sai ya fada masa wani labarin na dabam da fi karfin tunaninsa ya firgita kwakwalwarsa.

“Ya za'ayi na yarda da wannan? Ummi bata taba auren wani kamin Abiey ba, da ma Abiey ka ce sai na ce yes saboda Mahaifiyarsu Namra, amman Ummi bata taba aure ba, kuma bana tunanin zata samu ďan ta hanyar da be dace ba, idan ma gaskiya ba ne me zai saka ta ta boye tsawon shekarun nan bata bayyana ma kowa ba? Kuma ko sau daya bata taba nuna cewar Ameer ďanta ba ne? Maybe dai Ameer ya shirya duk wannan ne?”

Mahmood ya kalleshi.

“Da wa zai shirya? Ummi zai hada kai da ita ta fadi karya saboda me? Kuma ba shi ya fada ba ita ta fada in her own mouth, babu wanda ya matse ta, shi kasan a yanayin yadda ya bar gidan bana tsammanin zai yarda domin daukar yake ma bata cikin hayyacinta”

“Taya wai Ameer zai zama ďan'uwan mu? Not just dan'uwa ma ace dan Ummi ne wai ita ta haife shi da kanta? Ai kai ma kasan ba zai yiyu ba, wannan ba abun da hankali zai kama ba ne”

“Then ask her”

“Baka ganin halin da take ciki? Ba ta a halin da ya kamata ayi mata wannan maganar, amman ai dole gaskiya zai fito saboda Abiey ba zai dauka ba”

“Yanzu baka fahimci labarin da na gama baka ba, kenan? Abiey ma ya san da wannan, shi da kansa ya zo yayi mata fada akan me yasa ta fadi wannan abun sai gashi na gabatar masa da ciwonta a dole ya bar zancen”

“Amman taya Ummi zata haifi da ace bata bashi kulawa ba kuma be girma a tare da mu ba, ko sau daya bata taba fada mana labarinsa ba? Kuma shi Ameer mutanen da yake kallon a matsayin iyayensa ya alakarsu take da su kenan? Taya ma duk haka ta faru idan ma da gaske ne? Kuma shi Ameer ya san da haka ko kuma yaya? Kuma ďan ma na waye? Na mahaifinmu ne ko na wani”

“Nima ina son na sani sosai, sai dai bana son mu zurfafa tunani kar mu tunanin abun da be kamata ba, mu jira kawai mu ji ta bakinta zai fi, for now dai dole zata fada mana tun da gaskiyar ta bayyana”

Maleek ya gyada kai mamakin ya cika kansa har ya rasa ta ina zai fara tunani, abun sam be kama kanshi ba.

“If ma da gaske ne miyasa Ummi bata fada ba lokacin da muka samu matsala da shi? Karka manta fa har fada ta rika yi saboda ba a kama wanda yayi min aika aikar ba”

Maleek ya fada yana ciro wayar dake aljihunsa ya duba kiran Namra, he pick up the call ya kara a kunnensa kukan da ya ji tana rerawa har ya hana maganarta fita shi ya fara daga masa hankali.

“Namra are you alright?”

“Ciw...ciwo... Ciwon... Nimra ya tashi and.... She... Couldn't survive.... ”

“What do you mean?”

Ya tambaya da karfi. Sai ta amsa masa da ihu tana fashe da wani kalar kuka mai karfin gaske

“We lost her...”

“Innalillahi
Innalillahi
Innalillahi.... Innalillahi wa'inna Ilaihiraji'un”

Haka ya rika furtawa sai a karshen ya samu hada kalmomin gaban dayansu, ya mike tsaye rike da wayar try to control himself.

“Lafiya?”

Mahmood ya tambaya shi ma yana mikewa tsaye ganin hankalin ďan'uwansa a tashe.

“Nimra ce we lost her...”

Maleek ya fada hawaye na zubo masa. Mahmood ya duke da sauri a gurin yana buga hannayensa a teburin dake gabansu har sai da hankalin mutane ya dawo kansu. Maleek ya yi following call din Namra amman bata daga ba ya sake kira bata daga ba sai ya nufi Waiters ya biya kudin ruwan da aka kawo musu ya fice da gudu, ya saka key din motarsa kusa da sau uku sannan ya shiga daidai ya shiga motar ya murza key da irin sifar da be taba tashin mota a haka ba. Kamar ya sato motar haka yake tukin yana ratsa motoci har ya iso gida, be tsaya danna horn asan da zuwansa har a bude masa gate ba a wajem gate din ya bar motar ya fito da gudu ya bar motar a kunne ya tura karamar kofar gate din da karfi, jin ta a rufe ya buga mai gadin ya bude masa, kamar an korasho haka ya shigo cikin gidan da gudu su kansu ma'aikatan gidan sai da suka tsorata, ta gudu ya shiga falon kitchen ya fara nufa ya leka sai ya tararda Hanne a ciki da Yesmin suna hira suna aiki, ya fito da gudu ya haura stairs din kamar zai zame, ta tura kofar dakin Ummi da sauri ya shiga.

“Ina wayarki Ummi ara min zan kira wani?”

Ummi ta juyo ta kalleshi hawaye na kwaranya a idonta.

“Mun rasa Nimra ko ba haka ba?”

Tsaye yayi cak ya rasa me zai ce mata eh haka ne, ko kuma aa ba haka ba ne? Tausayinta ya zame masa biyu. Daker ya cira kafarsa ya isa gurin da take tsaye ya rumgume mahaifiyarsa abun da be sani ba shi ma hawayen yake kamar ita, sai dai shi yana kokarin ya fita karfin hali ne saboda ta samu kwarin guiwa kar ita ma su rasa ta daman ba lafiya ce ya wadece ba.

“Ki yi hakuri Ummi mutuwa bata da magani”

Sai ta dago kamar jira take ta bashi amsa tana hakki tana kuka

“Haka ne Maleek, mutuwa bata da magani, na rasa mijina na farko a lokacin da nake da kurciya, na rasa mahaifina tun kamin girmana na rasa mahaifiyata a lokacin da girma ya fara kamani, yanzu kuma na rasa yata, bana fatar na sake rasa kowa kuma.. Bana fatar na sake ganin gawar kowa”

Ya saka hannayensa ya rike fuska yana kuka naman fuskarsa na rawa.

“Mu kuma ba ma fatar ganin gawarki Ummi, ba ku fata kar Allah ya nuna mana wannan ranar”

Ya maida ita kirjinsa ya rumgume ita kuka shi kuka aka rasa mai rarrashin wani....

“Ummi...”

Muryar Waira ta saka suka juyo gaba dayansu suka kalleta tana tsaye bakin kofa kanta ba dankwali kamar kullum sai kallonsa take idonta a waje daman can sarki tsoro ce balle ta ga suna kuka. Maleek ya saki Ummi ya saka gefen rigarsa ya share hawayensa ya nufo kofar da Waira take tsaye da niyar ficewa sai suka jiyo karar Yesmin dake kitchen hakan yayi daidai da tsayawar motar Jabir, Umar daki daki ma ya fito da gudu domin Namra ta rike kowa kira take tana fada masa yar'uwarta ta mutu har da wadanda be kamata ta kira ba. Kan kace kwabo gidan ya karade da kuka kana ji kasan an rasa rayuwa mai tsada, Waira ta gudu a inda ta saba boya ta boye tana kuka sosai kamar ranta zai fita, domin tana matukar son Nimra, Ummi da Nimra su ne mutane da ta fi kauna bayan Shuraim da Eid..

Wani tashin hankali be bayyana ba sai da aka iso da gawarta a falon Ummi, gata kwance cikin karaga an daure babban dan yatsan kafarta da dan'uwansa, an daure hannunta ba ta motsi an lullube da babban zane. Kowa kuka yake a gidan domin ba su taba dandana zafin rasa rai ba sai a yau, ba ma kamar Namra dake ta kara tana fisge-fisge ji take kamar ace tana da ikon bada kyautar rai da sai ta bawa yar'uwarta.

“Ni kam na yi bakar tafiya, tun da na iso gidan nan bakaken abubuwa kawai suke faruwa, da nasani ban zo ba”

Shi ne abun da Dr Zainab ta fada tana kuka. Maleek ya kalleta yana istijara.

“A'uzubillahi minal shaidanin rajin, Mommy ki daina fadar haka be dace ba, mu fa musulmai ne ko kuka da kuka duk be dace na ba a son ana tsare gawa ana mata kuka”

“Allahu Akbar, yau yata ta canja suna daga Nimra zuwa gawa kaico mai rai”

Ummi ta fada tana kara fashewa da kuka sosai. Maleek da Jabir da Umar ne suka rika gawar aka maida ita a wani empty daki dake kasa saboda idan an haura da ita stairs zai zama aiki, idan kuma aka barta a falon za su tsareta da kuka ne duk da kasancewar falon babba ne mai kamar wata karamar fada. Tun da aka shigo da gawar Nimra a gidan Abiey be fito daga dakinsa ba, kuma ba kuka yake ba sai dai yayi shiru wani abu ya tsaya masa a kahon zuciya... Hoton gawarta da ya gani a asibitin bayan Namra ta kira shi ta fada masa ya rasa yarsa ya doshi asibitin ya ganta a lokacin da aka fito da ita daga dakin da aka shiga da ita domin bata taimakon gaggawa, sai dai ina mai ajiya ya karbi abarsa, mai kira yayi kira babu tsaya, tarin kwararin likotoci ko kayan aikin basa hana mutuwa ko karin wa'adi.

The death of Nimra hit every one of them, domin ba su saka mata ran mutuwa, even though likitan yace za su iya rasa ta, kuma numfashinta ya gagara sauka normal kamar yadda yake. Sai just like yadda mafi yawa mutane suna daukar bugun zuciya kamar baya saurin kisa, but ana haduwa da ajali kuma kowa da silar mutuwarsa. Waya kan waya aka rika kiran Abiey tun daga familynsa na bangaren Ammy har zuwa na Mai Martaba, da na Yesmin amman ya kasa amsa kiran kowa sai na amininsa Sauban. A lokacin da Abiey ya amsa wayar, Sauban ya fara shimfida masa kalaman hakuri da juriya da kuma yadda da kaddara, Sauban ya tunatar da shi abubuwa da dama daga rayuwarsu da baya yayi masa kalamai na kwantar da hankali da saukar da natsuwa. Duk da haka idon Abiey ko kwalla be yi ba balle hawaye. Bayan ya tabbatar masa da gobe zai yi sammakon biyo jirgin safe daga Dubai to Nigeria sannan suka yi sallama. Abiey ya aje wayar ya mike tsaye ya taka yana jin kafarsa kamar ba tashi ba gaba daya jikinsa ma ya sauya as well as zuciyarsa. Ya fito daga bangaren yana jin yadda yanayin gidan ya canja gaba daya saboda rashin yarsa, Nimra ce ta biyu da yafi kauna a cikin yayansa bayan Maleek, domin ita ba kamar Namra take ba da girman kai ko ji da kai, she's very friendly tana zama ta yi hira da shi kamar yadda Maleek ya dauke shi aboki ko ma fiye da haka. Ta kofar baya ya shigo bangaren Ummi ya daga kai yana kallon yan'uwa da suke kusa na garin Abuja da suka cika falon duk kuwa da kasancewar dare ne. Dr Zainab ta fi kowa fahimtar ďan'uwanta tana ganinsa ta san abun da ya kawo shi sai ta fada masa inda gawar yarsa take. Ya taka da kafarsa ya murda kofar dakin ya shiga, sai yayi arba da ita tana kwance a cikin karaga slowly ya karasa kusa da gawar ya sunkuya ya saka hannu ya yaye zanen da aka rufa mata, fuskarta ta bayyana gata kwance kamar ta yi magana amman ba dama, hannu ya saka ya shafa fuskarta yana tuna maganarsa ta karshe da ita a asibiti, ya risina ya sumbance ta sai a lokacin hawaye suka cika idonsa har suka diga a jikin gawar. Yana kokarin mikewa tsaye sai ga Maleek ya shigo da sauri daman baya falon a lokacin da Abiey ya shigo da ba zai bar shi ba.

“Abiey haba me zaka yi a nan kuma?”

Abiey ya juyo ya kalleshi hawaye na masa zuba idonsa yayi ja sosai kamar wan watsa masa yaji a ciki.

“I'm here to tell na yafe mata duk wani hakki nawa da yake kanta kuma na nema mata gafara”

“Ganinta a haka zai haifar maka da damuwa, damuwarka kai da Ummi matsala ce a garemu”

Abiey ya daga dansa ya mike tsaye, Maleek ya rufe gawar hannunsa na rawa idonsa na kuka ya rika mahaifinsa suka fice daga dakin.



A Daren babu wanda yayi bachi, daga Ummi har Abiey da sauran yan'uwan da suke shakikanta, domin sauran familyns Abiey komawa suka yi gida saboda an fadi cewar sai gobe da 10am za'ayi jana'izarta. Kusan kowa kwana yayi yana nema mata gafara ban da Waira da bata san kalar addu'ar da zata yi mata ba, sai kuka kawai take jikinta na rawa. Babu wanda ya bi ta kanta daman Ummi ce da Nimra masu kulata Nimra ta tafiyarta tafiyar da babu dawowa, Ummi kuma imani da yarda da kaddara ne kadai ya hana ta fita hayyacinta, amman ta yi kukan da ya canja kamaninta ya kusan tashin rashin lafiyarta sai dai bata fadawa kowa ciwon da take ji. Misalin 3am Maleek ya fito waje ya daga dakin da gawar Nimra take saboda ance ba a barin gawa ita kadai, and shi ne mai karfin zuciyar da zai iya zama da ita. Shesshekar kuka ya ji a bayan kujerar da ta saba boya, definitely ya san ita ce a gurin mamakin yadda take ta kuka har yanzu ba ta yi bachi ba. Lekawa yayi sai ya same ta a takure idonta har ya fara duk sanyin ac dakin be hana ta tara gumi ba. Dagowa ta yi ta kalleshi idonta yayi ja sosai fatar idonta ta kumbura, farar fatar fuskarta ta yi ja sosai saboda farar bata bata son wahala, hancinta ma yayi ja. Da hannu yayi mata alama da ta taso, sai ta girgiza masa kai ta kwantar da kanta.

“Taso ki kwanta”

Ta taso tana kuka ta bi bayansa ya san bata son mutane, kuma gidansu yanzu akwai mutane dan haka ya nufi dakinsa da kanshi ya tura kofar dakin ya bude mata. Da kai yayi mata alama da ta shiga ta kwanta, sai da ta daga kanta sama ta kalleshi sannan ta shiga, sai ta kwanta a kasa jikinta na taba gadonsa. Blanket ya dauko ya shimfida mata kan doguwar kujerar dake dakin yayi mata alama da ta koma can, sai ta tashi ta nufi gun ta kwanta ya dauko karamin bargo ya rufa mata.

“Da gaske Nimra ta mutu?”

Kallonta kawai yake ya rasa kalar amsa da zai bata, ya san ita ma tana jin kamar ba gaske ba ne, abun it's so hard to accept. Be ce mata komai ba ya nufi kofar dakin ya fice yaja mata kofar. Downstairs ya sauko yana kallon gurin da Nimra ta gi yawan zama, kitchen ya zarce kai tsaye ya kunna tap ya tara cup ya sha ruwa, sai ya ji su da daci. Ya aje cup din yana kallon harabar gidan da komai yayi tsit, da cije bakinsa ya girgiza kai idonsa suka sake cika da hawaye. Immediately ya baro kitchen ya dawo dakin ya zauna yana da Nafilar dare.

Washe gari aka yi mata sutura, aka yi mata Sallah kamar yadda addinin musulunci ya shar'anta, sannan aka dauketa zuwa gidanta na gaskiya wato final destination. Hauka ce kawai Namra da Ummi ba su ba, amman sun yi kuka har hawayen suka kafe musu. Duk dauriyar Abiey sai da ya fashe da kuka a lokacin da aka zo sakata kabarinta. Har sai da aka rike shi Maleek kuka Mahmood kuka duk wani na kusa sai da yayi kuka a lokacin da suka rufe Nimra...








______________

Allah ka jikan Mahaifin, shi ne first gawan da na fara arba da ita a rayuwata. Please include him in your prayers Allah ya lullube kabarinsa da Rahma ya yafe masa. Tabbas mutuwa akwai ciwo💔😭
*Littafin WANI GARI na kudi ne biya ki karanta cikin aminci pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith Bank, then send the evidence to 08036126660*



“Abun is some how, amman taya aka dauki tsawon lokaci haka babu wanda ya fada maka?”

Ya juyar da fuskarsa dayan gefen yana kallon wani bangare na dabam.

“I think Daddy yana kokarin kare ni, domin ta ba shi ni kyauta, kuma ya rika ya rike ni ya so ni fiye da yadda yake son kansa, idan kuma yana son kwanciyar hankali dole ya bar magana ta kasance a rufe”

“Wata kila ita ma tana da dalili na aikata haka fa farko, kuma a yanzu ba ba zata rasa dalili da ya saka ta bayyana maka ba”

“Bata da wani dalili Humaira, kawai ina tunanin mijinta da take aure a yanzu ya nuna cewar baya so na, shiyasa ta aikata hakan ko kuma tana tsoron talauci, a yanzu kuma ban san dalilinta na bayyanawa”

“Ameer...”

Ta kirashi sai ya juyo ya kalleta.

“Ban taba ji, kuma ban taba ganin uwar da ta dauki cikin ďa wata tara ta haife shi kuma tace bata sonsa ba, ko da kuwa ďan nan ta hanyar zina aka same shi balle kai da aka haifa da hanyar sunna, kuma irin ku da suke nisa da iyayen kun fi komai shiga rai, dole akwai wani abu mai karfi da zai saka ta aikata haka, saboda ka aje duk wani abu da kake ji a zuciyarka ka fuskance ta ka tambaye dalilinta na aikata maka haka, wata

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login