Showing 138001 words to 141000 words out of 271643 words
Chapter 47 - Wani Gari Book 1 Complete Hausa Novel
fada min inda kake ko kuma ka same ni”
“Kana ina?”
“King and his Kingdom”
“Okay gani nan zuwa”
Ya sauke wayar, gabansa na faduwa zuciyarsa na raya masa ko Ameer ya sake shirya wani abun ne, domin King and his Kingdom ba gurin zuwan Mahmood ba ne, it's a very right or appropriate place for rich kids like them amman ba gurin zuwansu ba ne, kara shi ma yana dan taba fita da abokansa sometimes amman Mahmood ya zama Mommy's boy, idan ya dade ya be dawo gida ba har kira take ta ji yana ina, not like Maleek da ta san baya son zaman gida saboda halinsa a can ba, duk da haka kuma ba zata yi bachi ba sai duka yaranta sun dawo gida. Waceaganar ce da ba zai iya fada masa ta waya ba? Shi ne dalilin karin kuzarin Maleek na fice daga asibitin ba tare da jiran kanwarsa ta farka ba...
©Khadeeja Candy
©®Copyright
2023
Ya shiga falon Daddy a wani yanayi da be taba shiga ba, wannan ne karon farko da yake jin wani abu mai kamar kunya da bakinciki saboda zai tunkari Daddy yayi magana da shi, tafiyarsa ma ta banbanta da yadda ya saba yinta. A kofar dakin Daddy ya tsaya ya share hawayen da suke masa zuba sannan ya kai hannu ya kwankwasa kofar ďakin sai kuma ya fasa ya duka a gurin ya dafe kansa hawayen da tsaya suka dawo suna masa zuba. Ganin yake kamar ba gane ba ne ace Daddy ba mahaifinsa ba ne, ya kuma kasa karbar karyar da zuciyarsa take masa. Sai da yayi da gaske sannan ya iya controlling kansa ya share hawayensa ya mike tsaye ya kwankwasa kofar dakin.
“Yes come in”
Gabansa na mugun faduwa ya tura kofar dakin ya shiga, kunyar da bata san ta ina ta fito ba ta lullube ya kasa kallon Daddy har ya zauna a couch, Daddy ya aje wayar hannunsa yana kallon Ameer cikin wani yanayi na tsoron da gargabar rasa ďansa.
“Baka saba kwankwasa min kofa idan zaka shigo dakina ba, kana shigowa ne kai tsaye idan kana so ko da kuwa bana cikin dakin nan, ka dauki abun da kake so, ko kuma ka fadi abun kake so, miyasa yau zaka shigo min tare da kwankwansa”
Ya daga kai ya kalli Daddy sai ya kasa, a take kallon da yake masa a matsayin uwa ya sauya zuwa na maigida da yaronsa. Daddy ya nufi kujerar da Ameer yake zaune ya zauna yana kallonsa.
“Ameer fada min damuwarka me kake so? Fada ka yi da wani? Wani ya taba ka? Ko ka sake kade wani? Mommy ce ta taba ka? Or...”
Daddy na tambaya Ameer na hawaye kuma ya kasa dagowa ya kalli Daddy har lokacin.
“Me ya same ka Ameer? Waya taba ka? Fada min komai kake so a duniyar nan zan maka”
Sauka yayi daga kan kujerar da yake zaune ya zauna a kasa ya kama kafar Daddy ya rike ya dora kansa a cinyar Daddy sai ya fashe da wani irin kuka mai taba zuciya. Daddy ya danne abun da yake ji a zuciyarsa ya cikawa bakinsa iska yana tunanin yadda zai bullowa Ameer domin bayan son ya nuna masa ya yi magana da Hajiya Jamila.
“Babban tashin hankalina a duniyar nan na ga tashin hankalin ďana, ina jure komai a duniyar nan ban da damuwarka, ka fi kowa sanin yadda nake gudun rigimar da kake shiga ko dauko magana, amman ni ne mutum daya da zaka gudu ka boya a bayana kuma na yi maka rumfa, na hana kowa taba ka, fada min Ameer me ka aikata? Wallahi ko rai ka kashe wannan karon na shirya baka kariya”
Sai a sannan Ameer ya samu gwarin guiwar dagowa ya kalli Daddy idonsa sun rine sun yi ja sosai kamar wani mashayi.
“Da rai na kashe da zan fi farinciki fiye da sanin abun da na san shi ne silar ajalina”
“Me kake nufi?”
“Daddy....”
Sai ya kasa furtawa sai hawaye yake kamar ba shi ba.
“Daddy i know it maganar da Mahafiyar Nimra fa fada i talk to Ammy ta tabbatar min da cewar gaskiya ne, and i confront her too ta kara tabbatar min”
Daddy yayi murmushi.
“Baka jin magana ta Ameer, rashin bin abun da nake fada ya jefa a cikin hali da dama, kuma zai sake jefaka a nan gaba, zuciyarka bata raya maka Jamila tana da alaka da Zahra ba? Shiyasa har ta furta sunanta? Saboda ta san zata goya mata baya su rusa tunaninka”
Ameer ya sake kallonsa da mamaki domin be tana sanin sunan matar da take cewa ita uwarsa ba ce sai a yau a bakin Daddy
“How do you know her name”
“Who?”
“Zahra?”
“Oh... Oh... Because a called her Husband kuma na gargade shi akan ya jawa matarsa kunne, ba zan dauki iskancin da take yi ba, ba zan lamuncin ta saka min tashin hankali a gida ba, and i already told my lawyer, idan ma akan hakan ne kakae wannan kukan da tashin hankali ka daina duk wani abun da za su fada maka karya ne”
“Me yasa za su yi karya?”
“I don't know, maybe suna da wata manufa akan hakan, musamman ma Jamila zata iya shirya wannan saboda na ko yarda na maida ita gidana”
“Daddy you can't hide this anymore, Ammy ta fada min komai ciki har da dalilin fitarta a gidanka, ta fada min dalilinka na boye min cewar mahaifiyata ta mutu”
“Kuma ka gamsu ka karya mahaifinka? Wane irin abu ka sha ne Ameer? Da rana tsaka wani zai kalleka yace kai ba dan Bashir ba ne dansa ne kuma ka yarda?”
Ya saka hannunsa aljihu ya ciro takardar yarjejeniyar da Zahra ta ba shi ya mikawa Ummi.
“What about this?”
Dauke wuta Daddy yayi for a seconds yana kallon takardar sannan ya mika hannu ya karba, sai da ya gama karantawa tsab sannan yayi murmushi mai sauti dake nuna be amince da abun da ya gani ba.
“Ina tunanin na haifi ďa mai tsananin basira da saurin gane komai, amman yanzu dan wannan abun zai saka ka karaya? Baka san muna a wani zamani da cigaba zai iya sakawa a yi komai ba?”
Ameer ya ciro hoton mahaifinsa ya mikawa Daddy.
“Wannan fa?”
Wannan karon dariya Daddy yayi.
“Karka ba ni kunya mana Ameer, wannan hotonka ne aka canja saboda a karkata hankalinka ka yarda da abun da suka shirya”
Ameer ya girgiza kai.
“Na san kana kokarin boye min komai ne saboda kai ma baka son karbar wannan gaskiyar mai daci, Daddy ina son ka sani, no matter how you try ko da ka yi nasara a yanzu, bayan mutuwarka dole gaskiya zata bayyana, sanin gaskiya ba zai canja komai a zuciyata ba, sai karin kimarka da daraja a idona”
Daddy ya saka hannu ya shafa kan Ameer.
“Karya suke fada maka Ameer idan baka yarda da ni ba, za mu iya yin gwajin jini tsakaninka da su da kuma tsakanina da kai, ta nan ma za a iya tabbatar da komai, kana yawan janyo min abubuwan tashin hankali, amman wannan da ka dauko ya fi ko wane daga min hankali, cuta kake kokarim haifar min da bana tunanin zata warke min da wuri”
“Daddy, ina son ka kalli cikin idona ka ratse min da Allah cewar Zahra karya take, ba mahaifiyata ba ce, ka karya hoton nan da yake hannunka, kuma ka tabbatar min da cewar kai ne ka haife ni ba sadakata aka baka ba”
“Tsaurin idonka ya kai har ka kalli idona ka fada min haka? Ba ka yarda da duk abun da nake nake fada maka ba? Idan da su kake son zama tashi ka tafi, zan iya hakura da rashinka”
Daddy ya fada a tsawace yana mikewa tsaye ya nuna masa kofa.
“Idan har zan fita daga nan, zan tafi ne a inda kai da ita ba zaku sake ganina ba balle jayayya ta hada ku, zan yi fatar mutuwa ne kai tsaye Daddy, na gode da duk wata kyauta da kulawa da ka ba ni, kuma an yi amfani da wannan damar na roki yafiyarka na abun da na aikata maka tun kurciya har kawowa yanzu dan Allah ka yafe min Daddy”
Ya mike tsaye ya nufi kofar da zimmar fice, gaba daya sa jikin Daddy yayi sanyi zuciyarsa ta karaya sai dai har lokacin be shirya fadawa Ameer gaskiya ba, da gaske baya son tashin hankalin Ameer kuma shi ma be shiryar karbar tashin hankalin cewar shi ba mahaifin Ameer ba ne.
“Ameer”
Daf da zai fice Daddy ya kira shi, sai ya tsaya cak sannan ya juyo ya kalleshi.
“Zo nan”
Ame
“Daddy boye min gaskiya zai kara jefani a cikin wani hali ne kawai, miyasa baka fada min sunan mahaifiyata ba even for once? Baka fada min garin da take ba? Baka nuna min yan'uwanta ba? Baka taba bani labarin dalilin rabuwarka da Ammy ba, baka fada min dalilin da ya saka Ammy take kauna har yanzu ba duk kuwa da kasancewar ta rabu da kai, babu ta inda nake kama da kai, bana kama da danginka, baka taba bani labarin mahaifiyata ba, yanzu kuma kai tsaye ka fadi sunanta, me zai kasa ka boye min gaskiya? Why?”
“Saboda ba gaskiya ba ne, Ameer ni mahaifinka ne? Baka da wani uba sai ni...”
“Wata kila zaka fada min gaskiya a lokacin da gaskiyar ba zata amfanin komai ba, sai dai ka tsaya a gaban gawata kama zubar da hawayen nadamar boyen da kake kokarin yi, Daddy kai da kake ďa kamar ni mai saka ka cikin tashin hankali da fitina da faduwar gaba da ciwon kirji, kake tsoron fada min gaskiya saboda karka rasa ni? Ina ga ni da nake da uba kamar kai? Na san gaskiya Ammy ta fada min amman ina tsoron gaskiyar saboda rasa ka Daddy”
Daddy ya fadi zaune kan kujera idon na sauya launi.
“Innalillahi wa'inna Ilaihiraji'un, Ameer don't force me to do this please”
“Amsa kawai nake so daga bakinka gaskiya suka fada ko ba gaskiya ba?”
Daddy ya mike tsaye a daidai lokacin da hawaye suka sauko masa ya nufi gurin windows din dakinsa ya tsaya ya rungume hannayensa ta baya yana kallon harabar gidan.
“A kowane dare da wuninsa, ina rayuwa a cikinsa da fargabar halin da zaka tsinci kanka idan irin wannan labarin ya zo maka, wannan tunanin yana haifar min da tsoro da bakinciki, sai dai ban saka tsammanin zuwan hakan a yanzu ba? Domin ban yi tsammanin na karya daya daga cikin alkawuran da na daukarwa Zahra ba, ta mallaka min kai bayan na mata alkawarin kula da kai fiye da yadda zata iya, na mata alkawarin baka tarbiya da ilmi, na mata alkawarin baka gata da duk wani kalar jindadin duniya, ban kuma yi tunani a akwai inda na gaza ba, sai dai abun da na gagara ganewa a yanzu shi ne, me zai saka ta saka min da wannan? Me zai saka ta daga min da tsohon ciwon da na yi zaton na warke shi? Akan wani dalili zata tambayi ni ajiyar da ce ta kyautarda zuciya daya?”
Ameer ya tako cikin dakin ya iso gurin Daddy ya rumgume ya fashe da kuka, Daddy ma kuka yake ya kasa juyowa kuma ya kasa barin kukan nasa ya fitarda sauti.
“A kowane dare ina bachi da bakincikin rashin haihu, sai dai saboda son kwanciyar hankalin Jamila a wacan lokacin na kan boye abun na barwa raina, daga lokacin da ta gabatar min da kai a matsayin ďa sai na ji kamar ba ni da sauran kunci a duniyar nan, bayan bayyanar gaskiya sai sonka ya karu, a lokacin ba ni da mafitar da ta wuce na mallaka ka ga mahaifiyarka, duk kuwa da irin kaunar da nake maka saboda na san ta fini bukatarka, domin ita dole ce ta saka ta rabuwa da kai, sai dai bana tunanin dole ce ta saka ta kyautar da kai a gareni, domin ban cilasta mata ba, ban kuma san wani ya cilasta mata ba, sai dai ina kallon abin a matsayin kyautar daban zata ba daga Allah, rahma Allah ce yayi min kyautarka, kuma tun daga lokacin da Zahra ta tabbatar min da kai a matsayin ďa, sai bakincikina ya yaye farinciki ya ninku, musamnan da na sake aure na haifi yaya mata, sai an fahimci hikimar Allah na bani kai kyauta da yayi. A yanzu ma ban san manufar sa, wata kila akwai abun da yake shirya mana, sai dai ina jin kamar ba zan iya jure kallonka a wannan halin ba, saboda ina matukar kaunarka, taso da wannan maganar da Zahra ta yi zata haifar min da damuwar da bata da magani”
Ameer ya sake shi ya fadi kasa ya fashe da kuka, gaskiyar da yake son sani ya santa amman ta haifar masa da karin bakinciki, damuwa da kunci suka bude masa sabon shafi, gaba daya komai ya zame masa ka rubutun littafi, wani abun kuma kamar mafarki. A cikin wuni daya duniyarsa ta juye, rayuwarsa ta sauya, mutanen da yake kallo a matsayin iyayen sun tashi daga iyayensa, wadanda be sani ba be taba mafarkin rayuwa da su ba, su ne iyayensa ta ina zai fara? Kiran wasu da suna da iyayensa? Da girmansa?e yasa wannan abun be same shi a lokacin da yake da kurciya ba? Sai yanzu da girmansa? Har ya mike tsaye ya juya ya fice daga dakin Daddy be juyo ba, Stairs ya sauko be kula da wadanda suke falon ba ya fice zuwa gurin motarsa. Ya shiga yayi mata key yayi reverse, kamin ya isa gate masu aikin kula da gate din sun bude masa. Sai da ya hau titi tunanin ina zai je ya zo masa? Wa zai fuskanta ya fadawa damuwarsa? Damuwace da ba a magani balle a magance masa this is reality. Tafiya mai nisa yayi sannan ya isa unguwar su Humaira, domin zuciyarsa bata raya masa ya je ko'ina ba sai can. Yana shiga unguwar ana kiran sallah Isha'i immediately yayi parking daidai inda Masallacin yake ya fito rike da ruwa ya wanke fuskarsa ya kuskure bakinsa sannan ya rufe motar ya nufi Mallasacin. Second time kenan da yayi sallah a cikin jam'i kafadarsa na taba ta wasu mutanen da be san inda suka fito ba. After gama Sallah ya sake daga hannunsa sai kuma ya rasa addu'ar da zai yi. Sai mikewa yayi tsaye ya fito daga Masallacin ya dawo ta saitin inda gidansu Humairah yake ya tsaya yana ta kallon corner.
Ya dade a haka sannan ya samu wanda ya aika ya fada masa sunanta kuma yayi masa kwatancen gidansu da taba shiga da shi, matashin saurayin ya ce ya gane ta. Takowa yayi ya dawo gurin motarsa ya jingina. Almost 30min sannan ya hango Humaira ta fito, kallonta yake har ta iso inda yake, hakan nan kawai ya ji kamar ya rumgume ta domin yana a cikin damuwar da yake bukatar hug, sai dai ya san Humaira bata cikin irin matan da zai yi ma wannan matukar yana son su kwashe lafiya.
“I thought na ce na aje aiki a gurinku? Miye na sallamo min kuma? Da na san kai ne Wallahi da ba zan fito ba”
Ya dauke idonsa daga barin kallonta ya kalli wani gurin dabam tare da rumgume hannayensa.
“Damuwata ta wuce ta kamfani ko wani gurin aiki, Humaira ban san inda zan je ba, na bata da yawa daga abokaina, some of them ma idan ma fada musu kallon marar hankali zasu min, bana ma son su sani, ban san me zan yi ba, na rufe kaina a daki na yi kuka kamar jariri ko na fito waje na yi ta ihu? Ko kuma na je gurin mutanen da ban sani ba, wadanda suka kira kansu a matsayin iyayena na yi fada da su? Or should I just died?”
Kalamsa sun sanya jikinta sanyi, domin a cikin lafazi mai rauni da neman mafita yake maganar. A wani yanayi na tsoron hantararsa da fadansa ta dago wayarta ta haska fuskarsa. Hawayen da ta gani a fuskarsa ya matukar daga mata hankali, domin duk wani abun da zai iya saka Ameer din data sani kuka to ita zai iya ma kasheta wata kila.
“Me ya faru Ameer?”
“I just need someone to talk to kuma na zo nan na ji kamar bana son magana akan damuwar anymore, I'm sorry for bothering you”
“No... No... No please don't, you need me just tell me me ke damunka?”
Ya sauke kai kasa.
“I'm so weak”
Ya juya ta bude masa motar.
“Shiga ka zauna”
Ya taka ya zauna cikin motar sai ta kwantar masa da seat din, ta rufe motar ta zagaya dayan side din ta shiga ta zauna ta bar nata bangaren a bude saboda idon mutane.
“Do you want water?”
Ya girgiza mata kai, sai ta kalli ruwan dake cikin motar.
“I'm sorry akwai ma ruwa a motar, to zaka ci wani abu?”
Ya girgirza mata kai.
“Ko kana son wani abu? Kana son zuwa wani gurin? Ko kana son shan magani?”
Murmushi ne ya zo masa a lokacin da be yi zato ba, domin ya fahimci so take ta dauke masa damuwa kuma bata san ta inda zata fara ba. Ya juyo yana kallonta sai ta wayarsa ta yi ringing, ya dago wayar yana dubawa sai number Ummi ya gani be hadace number ba amman ya fahimci number ta ne tun a lokacin da ya saka number daga wayar Nimra zuwa wayarsa. Rejected call din yayi a take mood dinsa ya canja.
“Na san bama shiri da juna, and ka tsane ni na sani, amman ganinka a cikin halin ya haifar min da damuwa a yanzu, please fada min meke damunka?”
“Humairah how would you feel idan wata uwar ta fito a matsayin mahaifiyarki, ta ce matar da kike kallon a yanzu ba mahaifiyarki ba ce ita ce mahaifiyarki, and mahaifinki da a kullum kike masa addu'a saboda ya rasu sai wani ya fito yace miki yana raye, yana can wata duniyar yana rayuwa da wasu iyalan da ya fi kauna fiye da ke, ke kuma ya barki duk da yasan shi mahaifinki ne be damu ya baki kulawa da kaunar da kike bukata, and abun da ya fi komai ciwo ya ce kyautar da ke yayi, kuma ya san kina raye