Showing 108001 words to 111000 words out of 271643 words

Chapter 37 - Wani Gari Book 1 Complete Hausa Novel

kiranshi, ta gwada hakan ya fi a kirga bata shiga ba, daga karshe ta yanke shawarar aika masa da sakon sanar da shi cewar ita ce ya kira ta.
Sakon na shiga kiransa na shigo wayar Umar dake hannunta dariya mai kamar kuka ta amsa kiran ta kara a kunnenta.

“Hello Ameer”

“Nimra how are you?”

Sai ta fashe da kuka.

“Kai ma kansa ba kalau ba, Ameer ina cikin wani hali kamar zan mutu, na rasa ya zan yi na yi missing dinka”

“I miss you too i miss your touch your smell, ina ta tunanin ko a wane hali kike a yanzu, na so na kira Umminki amman ban san me zan ce mata ba, i don't know why ina dai jin kunyarta, wayarki ma tana hannuna i thought zasu kira su karba ba su kira ba”

Ta rike wayar da hannu biyu taba jin kamar ta shige ciki saboda muryar Ameer da take ji.

“Ina kaunar ganinka Ameer, dan Allah ka zo?”

“Ina?”

“Gidanmu, ka zo ka fada musu cewar kana sona kuma zaka aure ni, damar da ka ce min kana jira yanzu ne ya dace ka yi haka, so that mahaifina ya yarda sona kake da gaske, ya yarda aurena zaka yi”

Yayi shiru kamar ruwa ya ci shi.

“Ameer”

“Nimra.. Listen to me let me think about it”

“Ba abu ne da yake bukatar tsayawa tunani ba, a yanzu ya dace ka yi komai Ameer, saboda Abiey yace kasa da wata daya zai mana aure ni da yar'uwarta Namra, ita a yau ma wanda take so zai zo ya gaishe da su Ummi, idan ba ka yi haka a yanzu ba ba za su yarda da gaske aurena zaka yi ba”

“Nimra....”

Sai kuma yayi shiru.

“Nimra.. Ba zan iya yin haka ba, abun kunya ne a gareni ace na zo ina ta hauka akan kanwar abokiya kuma makiyina, bayan iyayenta sun nuna min tsantsar kiyayya, ko baki ji abun da mahaifinki ya fada ba a lokacin da ya zo ya tafi da ke?”

“Ameer karka duba komai, kai da bakinka ka fada min cewar ka shirya fuskantar duk wani kalubale akaina...”

“The things is.... I'm fucking lie, ba gaskiya na fada miki ba, shiyasa na kasa yarda na barki ki sake aikata kuskure, saboda zaki kara jefa kanki da iyayenki a cikin damuwa ne kawai, and maganar Allah na tausaya miki matuka”

“Me kake nufi Ameer?”

“The whole life da muka yi is set up, na shirya haka ne saboda na rama abun da ke da dan'uwanki kuka min, kuma na bakata ran iyayenki kamar yadda nawa ran iyayen ya bace, sai dai yanzu na gane da gaske kin fada so na kuma kin shiryawa komai akaina, sai na ji tausayin amman ni ban taba jin sonki ba even for once, da farkon haduwa dake na dauke ki kamar kawa ne ina jin na sake dake back then na gane komai shiri ne ke da yayanki Maleek sai na shiryawa daukar fansa”

“Karya kake Ameer, wani ya cilasta ka fada min haka saboda a raba mu, kana tunanin yi min wannan karyar zai saka na daina sonka? Nooo”

“I know be kama na fada miki haka a irin wannan yanayin da kike ciki ba, amman dole ne na fada miki gaskiya saboda ki samu natsuwa ki daina wahalar da iyayenki da ke kanki, ina tausayinki Nimra na ji ba dadi a abun da na aikata, and ina gode Allah da baki ban kai ga yin mu'amala dake ba, duk da na yi attempting amman baki ba ni dama ba, you're a good girl, na yaba da wannan....”

“Someone forced you to say this”

“No one can force me Nimra kin fi kowa sanin waye ni, idan kuma baki sani ba ki tambayi dan'uwanki, babu wanda zai cilasta na fadi abun da ban yi niya ba ko kuma ban shirya yi ba”

“Wannan ba kai ba ne, na san waye Ameer dina, ba zaka fadi haka ba, na akwai abun da yake faruwa”

Ta yanke wayar tana kuka zuciyarta kamar zata fashe, gashi jikinta daman babu wani karfi domin bata iya cin komai, fashewa ta yi da kuka sosai ta kwala wani uban ihu da sai da mutanen da ke kasan stairs suka ji. Ummi ta shigo dakin da sauri Namra da Yemin na bayanta kamin Juwairiyyya da Dr Zainab su shigo. Ummi ta zauna kusa da ita ta ta dafa ta.

“Lafiya?”

Ta kasa magana sai kuka take, tun ana rarrashinta cikin dadin rai har suka gaji suka fice. 3pm Namra na dakinta tana shafa hoda wayarta ta yi ringing tana ganin mai kiran ta yi saurin aje powder ta dauka.

“Hello”

“Baby girl anya tafiyar nan zata yi a yau kuwa?”

“Miya faru?”

“Har yanzu jirginmu be tashi ba”

“Amman dazun ka ce min gaku nan zaku shiga jirgi kuma?”

“Eh mun zo zamu shiga sai kuma ta aka fasa”

“Ban gane aka fasa ba, akwai wata matsala ne?”

“Matsalar shi matukin jirgin Kishi yake yi baya son na hadu da matata”

Murmushi ne ya subuce mata.

“Kai dai kullum a cikin zolaya kake?”

Shi ma murmushin yayi mai sauti.

“Ga mu nan bakin gate din gidanku zamu shigo ke nake son na fara gani idan mun shigo”

“Okay i can't wait...”

Ta aje wayar with so much excite a nufi inda mayafinta yake ta dauka ya yafe, ta fice da sauri. Dakin Ummi ta shiga tana murna kamar ba ita ba.

“Ummi gashi nan ya zo”

Ummi dake rike da waya tana nunawa Waira hotuna da dauka na zomonta ta dago ta dube ta.

“Har ha iso, ki fara kai shi bangaren Abiey ya huta tukuna, kim ga gidan na mu da baki kar mu fito tarbarsa ya ji wani iri”

“Shi ma yace ni yake son ya fara gani ai”

Ummi ta girgiza kai tana mamakin yadda abubuwa suka canja ba a ko jin kunyar fadawa iyaye wani abun. Da dariya Namra ta fice daga dakin, sai Ummi ta tashi ta isa gurin Windows din dakinta ta janye curtains din a hankali tana kallon Motar da ta kunno kai cikin gidan, Waira ma ta tashi rike da zomonta tana shafawa ta bi bayan Ummi, daman duk inda Ummi take Waira tana gurin. Da murmushi Ummi take kallon motar tana jindadi farincikin a yau Namra ta kawo musu wanda take so gida. Front door aka fara budewa wani kyakkyawan matashin saurayi mai ruwan fulani ya fito yana sanye da shadda da hula cikin kamala, a take murmushin dake fuskar Ummi ya bace, ta kara daga curtains din tana son tantancewa kama ce ta yi yawa har ta bace haka, ko kuma mutumen da take gani shi din shi ne a zahiri? Amman taya za'ace shi ne har yanzu da kurciya? Waira ma zaro ido ta yi ta saki Zomon dake hannunta a tsaye ya fadi kasa ta taba sarkar wuyanta.

“Sulen...”

Ta kamin ta bar gurin ta nufi kofar dakin ta bude, kamar zata tashi sama haka ta sauko downstairs tana wani tsalle kai ka ce kafafuwanta cirewa za su yi, Maleek dake zaune yana a falon ya bita da ido kamar yace mata lafiya, sai kuma ya ji ba zai iya ba, ta bude kofar falon da karfi ta nufi inda aka faka motar tana kiran sunansa tare da tuna mata da sunan da yake kiranta.

“Sulem... Sulem...Sulem... Babe Girl.. Babe Girl...”

Namra ta juyo tana kallonta, shi ma kallonta inda ake kiran sunansa a birjice yake yana ganin Waira ta ware hannayensa ta iso gareshi da gudu ta daka wani uban tsalle ta fada jikinsa ya rumgumeta....


Waira na barin gurin Ummi ta juyo da sauri tana kallonta jin ta ambaci sunan da take yawan kira a gidan, kamin ta runtse ido tana gani abun kamar almara! Kama ce ko kuma shi din ne? Ko jininsa?

“Ummi me kuka cewa Ameer?”

Ummi ta bude idonta dake cike da tashin hankali ta kalli Nimra dake tsaye hawaye shar a idonta.

“Ba mu ce masa komai ba”

Ummi ta amsa mata cike da nauyin baki, Nimra ta saka hannu ta share hawayen dake taba mata baki.

“Ummi kun cilasta shi fada min cewar shi ba da gaske yake so na ba, kuna tunanin hakan zai saka na daina sonsa? Kuna tunanin hakan zai saka na fasa abun da na yi niya?”

“Ba mu fada masa komai ba Nimra, wata kila Allah ne ya dube ki ya kawo miki abun ta sauki”

“Idan ke baki yi ba, to Abiey yayi, miyasa za ku min haka Ummi? Ba ku son farinciki ne? Me na yi muku? Me Ameer ya tare muku? Ummi ko da zaku yanka ni ku cinye nama ba zan daina son Ameer ba, kuma ba zan fasa aurensa kamar yadda nake da niya ba, ko kun daura min aure da wani ba zan zauna ba, kun san fi kowa sanin addini ya hana auren dole, hakkin da nake da shi akanku ne ku aura min wanda nake so”

“Enough Nimra....! Mind you ina lallabaki ina daga miki kafa ne saboda kar damuwar ta yi miki yawa, amman ba kiji na fada miki ba zaki auri Ameer ba, ko da kuwa shi kadai ya rage a duniyar nan, ko zaki gudu ki tafi wani gurin idan ma wannan ne abun da kike da kuduri har yanzu to ki daina, gurin kowa zaki je ko ki kai kararmu ba za ki auri Ameer ba”

“Saboda me?”

Nimra ta tambaya a tsawace sai Ummi ta daka mata tsawa.

“Saboda Addinin Musulunci ya haramta aure a tsakaninku”

“Ta ina? Ummi kin san me kike fada kuwa? Ameer fa musulmi ne, ba kafiri ba. Duk wank abun da zaki fada ba zai hana aure a tsakanina da shi ba, matukar ba gawata kike son gani ba.”

“Saboda Nonon da Ameer ya sha ya saki shi kika kama kika sha har na yayeki, yadda aure yake haram a tsakaninki da Maleek haka ya haramta tsakaninki da Ameer”

Nimra ta yi murmushin takaici, abun is some how amman ta san wannan duk shiri ne

“Ta nan kuma kuka bullo...?”

Ummi ta dauke ta da mari.

“This is Reality Nimra ki dawo hayyacinki... Wai so kuke ku haukata ni?”

Ta fashe da kuka.... Nimra kuma ta dafe kunci tana kallon Ummi...

*Littafin WANI GARI na kudi ne biya ki karanta cikin aminci pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith Bank, then send the evidence to 08036126660*

36

Kallon da ya fi kama da na ga mahaukaci Namra ta fara yi mata ganin ta zo a guje ta rumgume mata bako.

“Yarinyar nan fa bata da hankali”

Ta fada ta karasa inda suke zata janyo Waira da kafafuwanta ke lake da na bakonta sai Shuraim ya ja baya ya girgiza mata kai yana murmushi kana ganin fuskarsa ka san farinciki a ciki shimfide. Waira ta dago ta kalleta sai ta saka hannunta ya shafa fuskarsa ta ja kumatunsa har sai da ya kyalkyale da dariya mai sauti, ita ma ta fashe da dariyar ta kara rumgume shi kam kam kamar za a kwace mata shi, ta kasa yarda Shuraim din ta ne, mutumen da bata taba tunanin zata sake ganinsa ba a rayuwarta, mafarkin be taba kawo mata zai dawo gareta ba.

“Baby Girl”

Namra ta kalleshi da yanayin mamakin da kuma kufula da kishi a lokaci daya na rumgumar wata macen da bata san alakarsu ba. A zatonta ita yake kira shi kuma da Waira yake ita ma Waira ta san da ita yake domin a zatonta ita kadai ce yake cewa Baby girl. Ta sauke kafafuwanta ta sauko tana rike da hannunsa dayan hannunta kuma tana nuna masa zoben dake wuyanta.

“Sulem... Your ring”

Ta saka hannu ta rika zoben yana dubawa fuskarsa dauke da murmushi. Hakan yayi daidai ta fitowar abokinsa dake cikin motar ya nufo su yana murmushi with confused a the same time.

“Ban taba tunanin zan sake haduwa dake ba, lokuta da dama ina tunaninki na ce yanzu ko ina yarinyar nan take, tana raye ko mace ko wani abun ya same ta, wata kila saboda hankalina ya kara kwanciya Allah ya sake hada mu so that na ga yadda kike rayuwa”

Maganar yake kallon idonta masu matukar daukar hankali.

“Sulem.... Ina son Sulem.... So much so much”

Tana fada tana juya kai wani kalar farinciki da nishadi ne a zuciyarta da baya misaltuwa. Shuraim ya saka hannu ya taba fuskarta gaba daya ta bata masa da masoyiyarsa Namra dake gurin farincikin sake ganinta ya mantar da shi cewar shi suriki ne a gidan.

“Kin yi kyau sosai, kin canja Waira kamar bake ba”

Ta yi murmushi ta sake rumgumeshi, a nan ya dago sai suka yi ido hudu da Namra da fuskarta ke hade sai ya dan rage murmushin da yake yaja baya ta cire jikinsa daga Waira, abun ka da mai dauki sai ta kama hannunsa ta saka cikin nata ta sarkafe.

“Waira”

Ta juyo jin an kira sunanta a tsawace ta kalli saitin katon windows din falon Ummi da aka bude ta kalli Maleek dake tsaye.

“Shigo ciki...”

“Sulem ne...”

Sanin kamar ba zai maimaita mata furucin ba ya saka ta saki hannun Shuraim idonta na cika da kwalla.

“Sulem karka tafi...”

Shuraim da abokinsa sun dauke idonsu daga kallon Maleek, Shuraim ya kalli Waira yayi mata murmushi.

“Ba yanzu zan tafi ba, idan kuma zan tafi zan miki magana je ana kiranki”

“Aa ka zauna duka a nan please Sulem...”

“Shuraim...”

Ya gyara mata, a kokarinta na gyarawar sai ta sake furta sunan a yadda take fada.

“Sulem....”

Yadda ta kira sunan ma ya masa dadi, sai kawai yayi murmushi ya kalli Namra da har lokacin ta saka sakim fuska.

“She's my patient”

“Just...”

Ta tabe baki tana yatsina fuska kamar ta ga abun kazanta. Murmushi kawai yayi ya duba agogon hannunsa kamin ya kalli abokinsa da shi mamakin yake ya ce.

“Ma maybe ka manta ta amman na sha baka labarinta”

Abokin ya dan yi murmushi be ce komai ba sai kallon fuskar Namra yake yana karantarta. Ba dan kar yace ta wulakanta shi ba da a gurin zata barshi tsaye, for which reason zai rumgume wata a gabanta, at first ma ta dauka wata alaka can sai bayan sun gama murzar juna zai ba fada mata cewar patient dinsa ce.

“Bismillah....”

Ta masu ishara da hanyar part din Abiey.

“Na dauka wata alaka ce mai karfi a tsakaninku”

Suna tafiya ta fadi haka sai ya kalli yanayinta ta da ya canja ta kasa sake fuska har lokacin. Murmushi yayi ya juya ya kalli kofar part din Ummi inda Waira ta shiga ya sake juyo suka cigaba da tafiyar.

“Wata kila kina nufin alakar jini, amman a gurina alakar da zaciya zata samu samu kwanciyar hankali idan ta san wanda take tausayi yana cikin koshin lafiya ita ma wata alaka ce mai karfi, da kin san yadda na damu da aka dauko yarinyar aka ce za a zo da ita Abuja, da kin taiyani murnar ganinta da na yi a gidanku, ko ba komai na san zata samu kwanciyar hankali da tsoro a nan”

“Haka ne ina taya ka murna Congratulations Sulem”

Ta fada tana dariyar yake, a badini bakar naganar ce ta yi masa, sai dai shi kuma be fahimta ba domin be fashinci komai ba. Iyakar kokarin da ta yi na danne abun da take ji a zuciyarta ne ta kula da shi yadda ya kamata sai dai duk wani dauki da murnar da take na zuwansa ya ragu a ranta.

Kamar kazar da kwai ya fashewa a ciki haka Waira ta shigo falon da kofarsa take bude tun a fitar da ta yi da gudu bata tsaya rufe kofar ba, maida kofar ta yi ta rufe sai ta tsaya jikin kofar tana taba hannunta ganin fuskar Maleek a hade.

“Ba ki da hankali? Ta yi bako ya zo gurinta kije kina ruining abun da ta shirya, ji yadda kika fita da gudu kafafuwa tsil tsil kamar tsuntsuwa, ku a garinku ba ku da tarbiyar girmama bako ne? Haka ake tarbon bako?”

Yana mata fada tana turo baki daman tuni hawaye ya cika idonta domin bata so rabuwa da Sulem dinta ba, gashi kuma yanzu ya tsare ta da fada. Takawa ta fara yi ta bi ta gabansa zata sai ya daka mata tsawa.

“Ba magana nake miki ba shi ne zaki wuce”

Zabura ta yi ta hawayen dake makalle a idonta ya sauko saman kyakkyawan kumatunta, hakan kuma ba karamin kyau ya kara mata ba, dana da kwarjinin da har kuka kyau yake mata idan tana yi.

“Sulem ne ai”

“Ba Sulem ba sule, ina kika sanshi?”

Ta kai hannu ta rika sarkar wuyanta ta soma magana muryarta na karkarwa irin wanda kuka ke daf da subucewa.

“Ya bani wannan ya saka min”

“Miya faru?”

Mahmood dake saukowa stairs ya tambaya ganin hawaye na sauko mata wasu na bin wasu.

“Wallahi yarinyar nan bata da hankali yau na gani, wanda zai auri Namra ne ya zo sai kawai ta tafi ta rumgumeshi baka ga yadda Namra ta bata rai ba, idan ba hauka ba ina aka taba haka”

“Toh ai Sulem dina ne”

Ta fada tana kuka. Mahmood ta sauko gaba daya ta tsaya inda take.

“Wane Sulem”

“Sulem”

Ta nuna masa sarkar wuyanta.

“Oh na gane kai ta san shi fa, idan bata san shi ba ai ba zata je haka nan ta rumgume shi ba, ka gane Sulem din da take yawan magana, aiko ni ma zan so ganinsa ko dan na ji inda suka san juna tun da bata fada mana ba, waya sani ma ko ďan'uwanta ne”

“You miss the point ko yaya ne be kamatadaga ganin mutum an gayyato shi kije ki rumgume shi ba, wannan ai rashin tarbiya ne da sanin ciwon kai, she's so annoying sai ta rika yin abu kamar wata yar jaririya”

Mahmood ya zauna.

“Maybe daukin ganinsa take kuma ita ai ba musulma ba ce wata kila al'adarsu haka ake tarbon mutum”

Tsaki yayi ya nufi hanyar fita daga falon, Mahmood ya bishi da kallo baki saki, sai a yanzu shi ma yake mamakin sbun da Maleek yayi kamar ba shi ba, da can babu ruwansa da duk wani abun da ya shafi Waira, wata kila saboda kanennsa ba su taba rumgumar wani a gaban idonsa balle ace ya tsawata musu ita kuma ya ga ta yi dole yayi mata fada. Maleek be duba yiyuwar akwai alaka tsakaninsu ba, shi dai abun da idonsa ya gane masa ne be masa dadi ba, domin be ga dalilin rumgume mijin da

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login