Showing 114001 words to 117000 words out of 271643 words

Chapter 39 - Wani Gari Book 1 Complete Hausa Novel

ciki sai taja tsaki ta dauke kai ta cigaba da tafiyarta, tuka motar yake a hankalin yana binta ganin kamar bata fahimci abun da yake nufi ba ya saka shi mika hannu ya bude mata front seat. Sai ta tsaya kamar zata shiga sai da ta ga shi ma ya tsaya sannan ya kama murfin motar ta rufe da karfi har sai da yayi kara kamar zai cire, ta cigaba da tafiyarta ya sake binta ya bude mata gambun motar.

“Get in”

“Ba zan shiga ba, har ka isa me kake nufi da na shiga an fada maka ni yar iska ce? Ko kuma ni an fada maka ban san ciwon kaina ba? Ko an fada maka tsoronka nake? Ba zan shiga ba, aiki ne daga yau na zan sake yi ba, balle har ka wulakanta ni”

Jan motar yayi ya matsa gaba ya faka yana jiran ta karaso, ita kuma ta ayyana a ranta cewar ba zata shiga motar ba ko da kuwa hankata zai yi. Sai dai abun da bata sani ba ya shirya mata, tana isowa gurin ya bude motarsa ya fito ya zagayo gefen da take.

“Wai Ameer me ka dauki mutane ne? Bayinka? Ka rika juya su yadda kake so kana cilasta kowa yin abun da ka ga dama? Ni abun kunya ne a gareni a gan ni a motarka, domin ni ma zai ayi min daukar yar bariki...kuma... ”

Bata karasa ba ya dago wukar dake boye a hannunsa ya nunata saitin wuyanta.

“Ke idan kika fara zuba baki san ki tsaya ba, idonki yayi tsauri baki tsoron kowa”

“Ina tsoron wuka Ameer dan Allah karka kashe ni”

“Shiga mota or will cut your throat”

“Toh”

Jikinta na rawa ta bude motar tana ta kallon titin ko zata samu wanda zai taimake ta, motoci biyu da suka wice ba su damu da kula da abun da le gafen titi ba balle har a kawo mata dauki, haka ta shiga motar ya rufe sannan ya zagaya, wani bangare na zuciyarta na raya mata cewar ta fita ta gudu kamin ya shiga sai dai ina tsoro irin na masu bakin tsiwa ya hana ta aikata komai har ya shiga motar ya fara tuki fa hannu daya, dayan hannunsa kuma yana rike da zumgurariyar wukar ta yankan nama.

“Dan Allah karka cutar da ni Ameer? Me na maka?”

“Baki san abun da kika yi ba?”

“Toh ka yi hakuri ba zan sake ba, yaushe kuma ka koma yin dabanci ba a san yayan masu arziki da wannan dabi'ar ba”

“Yau na fara, kuma kina yin wasa zan yanka wuyanki ko na fada cikinki kin ga dai ba za ayi min komai ba ko? Idan na kashe ki an kashe banza dan haka ki bini a hankali”

“Toh... Yanzu gida zaka kai ni?”

“Saboda gani direban ki ba”

“Amman Wallahi tallahi na rantse da Allah ni ban taba iskanci ba, dan Allah karka lalata min rayuwa Ameer”

“Ni na taba iskancin, negative mind daman shi ne a ranki, you should be praised kin shiga motata ma ni me zan yi a jikinki?”

“To miyasa zaka dauke ni a motar kana ta tafiya me zaka yi min? Dan Allah karka yi tsafi da ni toh”

“Dodona baya son irin jininki”

Cikin dabara ta kai hannu ta murda gambun motar da zimmar ta bude sai ta ji shi a rufe.

“Na shiga uku na lalace”

Ta fara kuka, hankalinta ya tashi sosai domin bata san manufar Ameer na yi mata haka ba, kai ta zai yi wani gurin ya aje ko ya hukuntata akan abun da ta yi ko kuma wani abun zai mata.

“Ni zan iya baka hakuri a bainar jama'a idan dan abun da na yi maka ne, zai saka ka hukunta ni, dan Allah dan darajar iyayenka ka yi hakuri”

Kallonta kawai yayi ya dauke kai, yadda ta makure a cikin motar ta zama marainiyar gaske duk sanyin ac motar ita gumi take ga idonta ya zurma kamar zuru. Faka motarsa yayi gefe ya bude ya fita rike da wukar da kuma wayarsa da key motar da Daddy ke kira. Yana piciking kiran Daddy ya tambaye shi.

“Kana ina Ameer”

Ya juya kalli inda yake.

“Wani guri Daddy?”

“An fada min ka shiga har gurin da ake dafa abinci ka dauki wuka, me zaka yi da ita?”

“Wani zare na yanke a jikin tayar motata”

“Ameer ba ka min karya karka fara, ni nasan ko me zai faru ba zaka yanke zare a jikin motarka ba”

Yayi dariya.

“Daddy maganar gaskiya wata yarinya na yi ma barazana da ita”

“Subhanallahi barazana da makami Ameer? Kar zuciya ta dauke ka ka aikata kuskure, ka zo ka same ni gida yanzu nan, sai mu ji idan akwai matakin dauka kamata a adauka akan yarinyar kuma na ji abun da ta yi maka”

“Ba wata babbar matsala ba ce Daddy karka damu”

“Na ce ka zo mu tattauna, kuma karka tana yar mutane Ameer dan Allah”

“Okay Daddy gani nan zuwa”

Ya sauke wayar ya nufi motar ya cire key ya shiga ya zauna, tun da suka kama hanya suna tafiya bata ce masa uffan ba sai share hawaye take gabanta na zillo tana ta tunanin inda zai kaita zuciyarta sai sake sake take mata. Tafiya mai nisa suka yi sannan ya shigo umguwar manyan mutane ya fama gaban wani katon gida da gate din gidan ma ya isa bakauye kallo. Wani karamin littafi ya dauko ya fara rubutu, yana yi tana leko har ya gama ya nade takardar ya mika mata sannan ya bude gurin daya aje wayar Nimra ya dauko ya mika mata.

“Shiga gidan nan ki kai wannan wayar tare da takardar nan, amman idan kin shiga ki ce ke kawar Nimra ce kin zo ganinta, sai idan kun kebe zaki bata”

“Wallahi ba wata Nimra yanke min kai za'ayi wannan katon gidan na yan mafiya ne”

“Kwarai kin san mahaifina kudin tsafi yake da su”

Ta lake kafada tana kuka.

“Ni ba zan shiga ba, Allah ya fika”

“Ke look babu abun da za'ayi da katon kan nan naki, yarinyar da kika rika zagina kwanakin baya saboda ita, to gidansu nan, so nake ki shiga ciki ki kai mata wayar nan da wannan takardar, daga nan sai ki duba lafiyarta daman na ga kin damu da ita ai”

“Idan aka kashe ni hakkina yana kanka”

“Idan baki shiga ba, zan saka wukar nan na yanka ki, ko kuma na dauke ki na kaiwa abokaina su yi miki wulakanci son raina, dan haka ki zabi ďaya”

“Ameer me yasa kake mugu ne? Kana ta daukar hakkin mutane da basu maka komai ba”

“Toh bari na zabar miki a cikin ukun”

“Zan tafi, ka bude min motar”

“Idan na bude miki motar kuma ki gudu, na biki da wukar nan ko kuma na aika har gidanku a daukoki ai kin san dai na san gidanku ko?”

Ta daga kai, ta zabi shiga ne saboda shi ne mai sauki a cikin hukuncin abubuwan uku da ya shar'anta mata ta zaba, ta san ko da masu fille kai ne zata musu addu'a, idan kuma abun da ya fada ne a ciki idan ta aikata ga huta. Ta karbi wayar da takardar ta saka a jakarta sannan ya bude motar ya fita ya zagaya bangarenta ya bude mata ta fito.

“Kina yin wani abu kin san sauran”

“Me yasa kai ba zaka shiga da kanka ka bata ba, idan har da gaske gurinta ka zo”

“Ki kwankwasa kofa a bude miki”

Ya koma cikin motarsa ya zauna yana kallonta tana kallonsa, yana ganin ta matsa jikin gate din ya danna mata horn ta koma. Cikin tsoro ta kai hannu ta kwankwasa kofar gidan dake rufe sai da ta yi haka sau uku sannan aka bude kofar ganin mutumen daya fito yana sanye da uniform din police ya saka ta dan ji sanyi a ranta, ta juya ta kalli motar Ameer yayi reverse da ita zat tafi ya barta a gurin.

“Na zo gurin Nimara ne”

Ta fadi sunan a birkice tsabar tsoro da rashin rike sunan da ta yi.

“Ke wacece?”

“Kawarta ce”

Police din ya kalleta kasa da sama, shi dai be san yaran gidan na da kawayen da basa da motoci ba, yanayin mu'alamarsu ya saka ba kasafai suke zuwa gidan kawaye ko kawaye su zo nemansu ba, idan ma sun zo suka zo da manyan motoci ne, sai dai Humarai a kasa ta zo duk kuwa da ya hango motar da ke kokarin juyawa wacce yake kyautata zaton a ciki aka kawota.

“Kun yi da ita zaki zo?”

“Eh ga ma wayarta a hannuna tace na zo mata da shi”

Ta saka hannu a jaka ta dauko wayar tana nuna masa.

“Toh jira a nan ina zuwa, wa a ce mata?”

“Ka ce... Ka ce... Ka ce.. Aisha Humaira ce Ameer”

“Aisha Humaira Ameer?”

Ya maimaita sunan sai ta daga masa shi.

“Yeah”

“Okay shigo sai ki jira nan”

Ya matsa jikin kofar ya samu shiga sai ya rufe gate din ita kuma ta tsaya kusa da inda ya nuna mata jikinta na rawa gabanta na faduwa. Kamin yau idan wani ya zo yace yana son ganin masu gidan kai tsaye masu gadin suke ba shi damar ya shiga domin haka Ummi tace musu, sai dai Umarnin da Abiey ya bada na cewar kar a sake Nimra ta fita gidan ya aaka suka tsaurara tsoro gudun kar wani abun ya faru a dora laifin a kansu.

*Littafin WANI GARI na kudi ne biya ki karanta cikin aminci pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith Bank, then send the evidence to 08036126660*


38


MALEEK POV.

Yana shiga dakinsa ya shiga closet dinsa ya aje jakar ya fito ya sauko downstairs ya zauna a dayan side din da kujeru suke, sosai ya maida hankalinsa gurin plasma dake kunne yana kallon film da MBC 2 suke hakawa. Sai da suka tafi talla tukuna hankalinsa ya kai gurin wayarsa dake kan ďayan set din kujerun tana ringing da hanzari ya isa gurin ya dauki wayar tare da amsa kiran da ya biyo bayan miss calls din dake bayyana a saman kiran.

“Maleek kana ina?”

“Ina cikin gida, bana kusa da wayar ne”

“Ka same ni bangarena zamu gaisa da mijin Namra, na kusa karasowa”

“Okay”

“Kuma ban ce ka zo min da kananan kaya ba”

Yayi murmushi kawai ya sauke wayar yana kallon kansa domin kananan kayan ne a jikinsa. Haurawa yayi sama ya canja tufafin jikinsa zuwa shadda ash color ya fesa turare ya saka kular Zanna bukar yar ubansu, ya canja talkamin kafarsa ya saka wandanda za su dace da shaddar jikinsa be damu da duba madubi ba domin ba yin kyau ko akasin haka ne a gabansa ba burinsa yayi shigar mutunci kamar yadda mahaifinsa ya bukata, be fice dakin ba sai da ya murza wani karamin turare a hannunta ya shafe hannunsa zuwa wuyansa, ya dauki wayarsa ya saka aljihu sannan ya sauko stairs din yana wani irin kamshi na tashin hankali kamar shi ne angon. Kofar fita falon ya nufa tana tafiya kamar mai tausayin kasa.  Entrance din bangaren Ummi ya tsaya yana kallon gate din gidansu, a hankali ya juyo yana kallon motar Shuraim sai ba motar yake kallo kai tsaye ba, kyakkyawar halittar Allah mai matukar burgewa da daukar hankali yake kallo, Waira ce tsaye jikin motar can side din da ace bata mike tsaye ba ba zai iya sanin tana gurin ba, ita ma bata mike tsaye dan sanin cewar shi ne tsaye a gurin ba, sai dan kamshin turaren da ya kaiwa hancinta hari ta kasa jurewa har ta leko a zatonta zata ga Sulem dinta ne sai ta yi arba da abokin fadanta.

Yayi kyau, kyau da ake kira da kyau irin kyaun dake fitar da asalin kyau da siffar kyau a jikin namijin, da haramun ne ka yi masa kallo daya ka dauke ido. Hular kansa ta zauna das kamar sai da aka sauna kalar zaren da girman aka zaka masa domin shi kadai kawai. Shaddar ta haska fatarsa ta kara masa kwarjini da cikar izza irin ta jinin sarauta, daga ita har shi sun dauki lokaci suna kallo junansu, ko wane na tantance kyaun dayan jinsinsa. Waira ce ta fara sulalewa kasa ta zauna tana rike da zomonta, a lokacin da idonshi suka daina ganin kyakkyawar fuskarta sai hayyacinsa ya dawo jikinsa ya dauke kai ya sake maidawa gurin gate din yana hade yawun bakinsa da suka tsinke...
Me kike yi a nan wa kike jira, duk baya bukatar amsarsu, yadda aka yi ta fito daga cikin falon ta zauna a gurin ne abun tambaya a gurinsa, jira ko me take yi a gurin ya san amsarsu, ko da ya tambaye ba zai wuce tace masa tana jiran Sulem ba, domin a gurin motarsu ta tsaya. Yana kokarin zuba hannayensa aljihu ta sake lekowa irin leken da be yi kama da gulma take ba, ta gefen ido yake kallonta rabin idonsa na kan gate din da aka buden ragowar kuma suna kan Waira dake kallonsa, tana ganin motar Abiey ta kunno kai cikin gidan sai ta mike tsaye gaba daya ta bar jikin motar ta nufo hanyar shiga falon inda Maleek yake tsaye. Tana doso inda yake tsaye gabansa ya tsanata faduwa na rashin dalili kuma ya kasa kallonta har ta iso gurin ta ratsa gefensa ta wuce. Sai da ya sauke numfashi mai nauyi sannan ya samu sukuni a zuciyarsa, tun da yake a rayuwarsa be tana jin abun da yaji a yau ba. After Abiey ya faka a compound din gidan ya sauko ya isa gurin motar yana masa sannu da zuwa.

“Maa Shaa Allah, haba ko kai fa yanzu da ban maka magana ba da kananan kayan zaka saka ka fito a matsayinka na yayan Namra”

Murmushi yayi as respond ya karbi jakar dake hannun driver mahaifinsa suka jera a tafe kamar ba uba da ďa ba, kamin su karasa apartment din Abiey yayi masa tambaya uku ya kasa bashi amsar ko daya.

“Ai tun kamin ya zo a matsayinka na dan'uwanta kuma namiji, wanda nake sa ran ko bana raye ko kuma nan gaba kadan zaka iya gudanar da komai ya kamata ace ka mata tambayoyi akansa”

“Abiey ka san ba wani sakewa nake da su sosai ba, so ban cika son shiga rayuwarsu ba”

“Amman ai na ga alakarka da su yanzu ba kamar da ba, ka samu lafiya inji Umminku kasan ita ce kullum take ganin baka da lafiya”

Abiey ya fada yana dariya. Maleek kuma ya kai hannu ya bude babbar kofar falon Abiey ya fara shiga sannan Maleek ya biyo baya. Falon farko babu kowa a ciki hakan ya bawa Abiey da ďansa Maleek damar shiga kofar dake cikin falon wacce zata sada su da corridor dakin Abiey ba sai sun bi ta cikin karamin falon da Namra ta sauki surikinsu ba. Abiey ya fara shiga dakinsa kai tsaye ya zauna tare da Maleek yana fadin.

“Kira Namra ka fada mata ta sanar da bakonta zamu shigo mu gaisa da shi yanzu nan”

“Abiey ba zaka huta ba?”

“Hutun me? Aiki na bari na zo nan fa kuma muna gama gaisawa zan koma”

Maleek ya ciro wayarsa dake aljihu a maimakon ya kira sai ya aika mata da sako. Abiey kuma ya kira Ummi Dr Zainab ta amsa wayar.

“Ka dawo”

“Eh ina dakina tare da Maleek”

“Toh bari idan kun gaisa da shi sai mu fito muma mu gaisa da shi”

“alright”

Ya aje wayar, after like 20 minutes Namra ta shigo dakin ta zube kasa ta gaishe da Abiey kanta a kasa tana mai jin kunyarsa abun da bata saba ba.

“Abiey na fada masa”

Mahaifinta yayi dariyar farinciki yana zolayarta daman ya saba wasa da yayansa ba maza ba matan ba balle kuma Ummi da take matarsa.

“Toh Gimbiya Namra bari mu tafi mu gaisa da Yarima”

Ta rufe ido tana dariya. Shi ma dariyar yake Maleek kam kallonsu kawai yake kamin ya mike tsaye tare da mahaifinsa suka fice daga ďakin. Shuraim na jin an taba kofar falon sai suka kara daidaita natsuwarsu domin Namra ta sanar musu mahaifinta zai shigo ya gaisa da su, kusan a tare Shuraim da abokinsa suka mika tsaye suna amsa sallamar Abiey. Maleek ne ya riga karasa inda suke ya mika musu hannu suka gaisa sannan ya zauna a kusa da inda suka zauna. Shuraim ya mikawa Abiey hannu biyu ya gaisa da shi as well as abokinsa.

“Bismillah”

Abiey ya fada yana nuna masa kujera, tsantsar ladabi da girmama na gaba ya hana Shuraim zama a saman kujera saboda Abiey ya zauna saman kujera yana ganin be dace shi ma ace yana kan kujera ba.

“Sannunku da zuwa”

Sai suka amsa da yauwa suka zauna a kasan Shuraim kansa na kasa kamar wani mace, Abiey kam kamar ya samu tv haka ya rika kallon saurayin mai shirin zama surukinsa.

“Namra ta fada mana zaka zo, saboda mun bata damar zabar wanda take so, mun yi maganganu da ita, sai dai ina tunanin yana da kyau mu kai ma ka gabatar mana da kanka, kuma ka yi hakuri da tambayoyin da zan maka”

“Ba komai Abbah, daman shiyasa na zo ai, saboda mu san juna kuma na yi bayanin kaina, idan na koma sai na sanar da iyayena su same ku da maganar ko a yanzu ma sun san da maganar sun dade da sanin Namra sai dai a yanzu ne magana mai karfi zata shigo”

Abiey ya tsuke ido yana kallon Shuraim tare da murza tsayansa daya da hannunsa kamar mai kokarin tuna wani abu.

“Sunana Muhammad Shuraim, ni likita ne ina aiki a General hospital Katsina, kuma ina dan taba aiki Peach Hospital Katsina sai dai ita Private Hospital ce, mahaifina ma likita ne sunansa Dr Hamid Muhammad iyayena yan asalin garin Kano ne, sai dai zama ya dawo da su a Katsina, na yi karatuna a jami'ar BUK na yi master a ABU zaria, kuma ina shirye shiyen fita waje domin cigaba da karatuna In Shaa Allah, ni na na farko a gidanmu ina kanwa wacce ta yi aure tana Kano akwai kuma dayar tana nan tare da mu ita ma tana kusa da yin auren In Shaa Allah, mahaifiyata tsohuwar malamar makaranta ce, yanzu kuma da ta yi ritaya tana kasuwanci na tufafi da kayan shafe shafe na mata”

“Kai ďan wajen Dr Hamid ne?”

Abiey ya tambaya yana nunashi daman zuciyarsa ta raya masa haka tun shigowarsu ta farko a falon da

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login