Showing 84001 words to 87000 words out of 174305 words
Chapter 29 - Dangina Complete Book 1 Complete Hausa Novel
dai Malam ya amsa cewa yabama Sarki Aminatu su iyayen Sarki suje su shirya sai dai ya kwab'e su akan Sam koda wasa baya son maganar neman auren ya fita waje dan haka dole komai na neman haka suka gudanar dashi a sirance domin Malam ya tabbatar ma kanshi da cewa bayan shedaniyar mata da Allah ya had'a sarki da ita tofa ba tantama akwai na kusa dashi da suke mishi bita da kulli, lokaci yana ta tafiya har ya rage baifi wata d'aya dasu Aminatu zasu fara jarabawar su ta fita ba,
Kai jama'a Malam bazai tab'a iya dena halin shiba, domin dai wannan karan ma a kokarin shi na ganin cewa bai kuntata ma Meenal ba yasa ya yanke hukuncin aurar da Raheenat da y'ar wajen shi Sa'adatu wadanda suke gudanar da rayuwar su cikin kwanciyar hankali ba tareda tsammanin zancen auren su zai taso nan kusa ba domin dai dama duk cikin su Meenal ta girme su sun san ko auren za'ayi sai dai ita amma me?
Kwatsam ranar wata Juma'a kamar yanda suka saba zuwa islamiyar safe kafin a dawo ayi shirin tafiya makarantar boko, suna isowa kofar gidan suka fara ganin cincirin don mutane, iya hasashen su sun gaza gane ko taron jama'ar na menene domin dai ba'aiyi haihuwa a kusan nan ba balle suce taron suna! Basu ga kuma alamun bak'in ciki ko alhini a fuskar mutanen ba balle suce taron mutuwa ake, to me ya faru? Sai dai kuma babu mai basu amsa hakan yasa dole sukaja kafafuwar su suka shige cikin gida.
A farfajiyar ko ba taron komai akeyi ba saina baikon auren Raheenat da Sa'adat wad'anda Malam ya duba a cikin wad'anda suka fito neman auren Aminatu ya musu madadi da kannen ta.
Soyayyar da Malam yakema Aminatu soyayya ce mafi kololuwar girma wanda hakan yasa koshi baya son yazama sanadiyyar k'uncin ta balle kuma wani, sai dai soyayyar ta rufe mishi ido sosai ta yanda baik'i wasu su shiga wani yanayi ba indai ita zata samu sassaucin damuwa a zuciyarta,
Hakan nema yasa shi yanke hukuncin ya hadesu ukun ya aurar sannan a maimakon ita kad'ai a cikin su ta auri mai mata da yara hudu ya yanke hukuncin suma sauran duk masu mata da yaran zasu aura, sai dai a maimakon ita mai yara 4 su nasu mazajen yaran su sun zarta hakan, dalilin shi na kara rufe zancen auren ta tuntuni kuma shine dan kartaji ba dad'i amma yanzun inta samu labarin auren sauran ko nata yazo bazataji damuwa mai yawa a zuciyarta ba, dan zataga cewar ai an aurar da kannen tama balle kuma ita,
Duk yanda suka so suji taron me ake gudanarwa hakan bai samu ba daga karshe ma Ya Sa'eed ne ya kwashe su zuwa Kano a wannan ranar suka kaima Maman Kano ziyara da sunan washe gari zasu dawo, babu wacce tayi tunanin wani abu daban domin dama sun dad'e basu je kanon ziyara ba dan haka tuni suka sake jikin su suka dunga yawace yawace.
''''''''''*******'''''''''''''
Uwar gidan Malam Innan yara ce zaune a falon na Malam sai dai lokaci lokaci takan d'aga kai ta duba agogon dake manne jikin bango domin tasan dai zuwa yanzun tuni su Malam suka tashi a wajen karatun da sukeyi na dare shida magidan tan dake zuwa d'aukar karatun, sai dai kuma gashi shiru har yanzun bai shigo ba har ana neman karfe 10 na dare yanzun.
Jin motsin shi da kuma gyarar muryar shin nan daya zamar mishi (Bakandamiya) littafin Surayyahms🥰.
hakan yasa ta kara gyara zama, domin tabbas yau bata iya bacci saita tattauna da Malam akan batun baikon yaran nan da aka gudanar dashi da safe Wanda su iyayen gidan ko alama basuji kamshin maganar ba sai baiko dasa rana kawai ne ya musu dirar mikiya, domin dai aiko ada can baya kafin baiko sai Malam d'in ya turo mane man sun gana da yaran kafin asa ranar aure,
Da sallama ya shigo.
"Innar yara kece zaune? ashe na barki da jira mun d'an tsaya tat tauna wani batu ne da Sa'eed akan batun nashi auren dan so nike a had'e shi gaba d'aya dana yaran nan ayishi a huta koya kikace? "
Ya Kara she tambayar nashi a yayin da yakai zaune.
"Nima abinda ya kawoni kenan Malam"
"Ah to madallah amma yanzun dai fara zuba min abinci tukun ni kuma bari in d'an shiga daga ciki in canza kayan nan kin san an fara zafi a gari."
"To Malam a fito lafiya"
Har ya kai bakin kofar d'akin shi kana ya waigo gyarar muryar shi yayi wanda hakan ya maida hankalin ta kanshi.
"Nace ina fatan kin tahomin da nawa kason kunnun tamban dan d'azun naji yara na cewa kin dama kunun tamba?
Murnushi tayi tana cigaba da shirya mishi abincin,
shi kuma ya shige ciki yana ayyana cewa mata kenan, wato daga jin batun baikon yayan su shine ta kwaso jiki tazo dan ta tutsiye shi ya fad'a mata dalilin yin hakan, alhalin kosu Adamu da Auta babu wanda ya bude baki cikin su yace mishi mai yasa yayi haka? Mata hooo komin tsufan su dai basa tab'a ganin sun girma, girgixa kanshi kawai yayi ya shige makewayi dan ya watsa ruwa.
Bayan fitowar shi bata tada maganar ba har sai sanda ya kammala cin abincin shi ta gyara wajen sannan ta dawo ta zauna,
"Malam mike faruwa a gidan nan bamu da masaniya haka? "
"Wani abune ya faru a gidan hala? "
Shima ya maida mata da tambaya maimakon ya bata amsa,
"Ah ah ina magana akan baikon da akayi da safe ne nasu Raheena da Sa'adatu, kawai kuma sai mukaga ana taro bamu da masaniyar komai akan hakan! "
"Allah sarki eh wallahi baiko ne akayi harma da sa ranar auren da zarar an samu hutu domin so nike kowa ya samu damar halattar bikin auren koba komai ai mun dad'e bamu aurar da yan mata ba a gidan koh?"
Katseshi tayi da cewa,
"Amma Malam yaran fa"
Hannu ya daga mata yana mai daure fuska shima yace
"dakata Ameenah indai akan batun nan ne zan fad'a miki gaskiya inhar ba Addu'a zakiyi Allah yasa albarkha ya kuma tabbatar da alkhairi ba to ina ganin zaifiye miki alkhairi kiyi shiru da bakin ki, in kuma ban baki zakiyi to zaifi kyau kije kiyi ma iyayen yaran bawai niba domin na riga na yanke hukunci"
"Allah ya baka hakuri Malam amma ni dama gani nayi su yaran suna da mazajen da suka nuna suna bukatar auren su anan cikin gida, kuma koba komai yan magana na cewa gida bai koshi ba aiba'aba dawa nama ba!
Kaga ita Raheena ai Abubakar ke neman ta tun zuwan shi garin nan domin a sashena ma sukeyin zance, ita kuma Sa'adatu Farouq ke neman ta ban fad'a maka bane saboda nasan ba yanzun zaka aurar dasu ba, "
(Abubakar yaron Maman Kano ne aikine ya dawo dashi Zaria yana aikin Banki, shi kuma Farouq yayan Meenal ne)
"To ai gashi nan nauyin bakin naki yaja musu kinga kenan koba komai ni bani da laifi, domin dama ai wani baya auren matar wani sud'in ba matan su bane dan haka sai suyi hakuri su nema a wani wajen domin dai kin san bazai yuwu ince an fasaba tunda na riga na basu, kuma abunda baki saniba shine duk su ukun zan aurar harda uwata suma mazan zan tuntub'esu in akwai wanda ya shirya auren a cikin su duk a had'a ayishi lokaci daya a huta"
"Meenal d'in itama auren zaka mata? "
"Oh bakiji abinda nace da kyau bane hala? To bari in maimaita auren itama zan mata ina kuma fatan cewa baki manta da neman auren nata da uwar gida da Sulaiman suke tamin jele akan shi tsayin shekarun nan ba? To Alhamdulillah yanzun kam lokacin auren yazo dan dazarar sun kammala jarabawa bikin zai gudana, ina fatan kuma yanzun bazaki ce nayi son kai ba? "
Galala Innan yara ta saki baki tana kallon Malam cike da mamaki, lallai hakika yan magana sunyi gaskiya da suke cewa hali zanen dutse to ita kam yanzun me zatace tunda harta da yar gaban goshin shi a wannan karon bata tsira ba,
"Innalillahi Wa'innah Ilaihir Raju'un"
Sai da ta maimata sau uku a cikin zuciyarta tamkar wacce aka aikoma da sakon mutuwa sannan tace,
"Malam Sarki zaka aurama Meenal? Malam Sufyan fa! Wanda kowa yasan yanda matar shi take,
ta gagare shi amma dan bala'i kalli yanda ta zame mishi matar jaraba ta yanda har yanzun ya kasa rabuwa da ita, gashi yanzun har an kai matakin data rabashi da iyayen shi ciki kuwa harda yaranta wanda itace uwar su ba yayan riko ba! Malam Meenal din zaka aurar gidan kishiya mai tsafi?
Dan babu tantama tsafi yarinyar nan keyi shi yasa ta gagari kowa,Malam Meenal din kafa kake neman ka sadaukar a inda baka san kalar rayuwar kuncin da zata gudanar in anyi auren ba domin ko Wanda bai damu da yayan cikin shi dama iyayen shiba ina tabbatar maka itama ba zatayi daraja a idon shiba, Malam na rokeka ka soke batun had'in aure tsakanin ta da Sarki in ma auren nata a yanzun ya zama dole saboda lalurar ciwon ta Malam ka duba koda cikin yaran d'akina ne kona Dije ka hadata da wani, inba haka ba Malam zaka cutar da ita"
Bai bari ya barta ta karasa ba ya katseta a tsawace da kiran sunan ta
"Ameenahhh wai ba nace in bazaki fad'i Alkhairi akan auren nan kimin shiru ba? Ko ke kin san gaibu ne? fad'amin kinsan abunda ka iya faruwa anjima ko gobe? Ah ah koko dan Allah ya had'a shi aure da shaid'aniyar mace shike nan sai mu yanke tsammanin mu akan shi mu sakar mata shi kamar yanda takeso taci gaba da mulkarshi kamar Sarki da Bafade iye? Ko koh dan bakece kika haifeshi ba shi yasa kike kalubalantar auren? Fadamin idan a cikin yaran ki Allah ya jarabta da samun mace irin haka shin komawa gefe zakiyi ki rungume hannu ki zuba ido kina jiran ikon Allah ko koh zaki tashi tsaye ne da Addu'a domin neman ma kanki mafita? Aminatu ban sanki da son kai ba, koba komai uwar yaron nan kawarki ce ta kusa kinga ko inda kara dan kawarki ai nakine! Sannan uban yaron nan fa dan uwan kine tako ina dai Sarki dolen kine dan haka ban son in karajin wata magana a bakin ki sab'anin addu'ar sanya alkhairi domin mu bazamu gaji da fad'ama Allah ya kawo mana d'auki a wannan al'amarin ba"
"Kayi hakuri Malam nima insha Allah bazan k'ara kalu balantar zancen auren ba, ubangiji Allah ya sanya alkhairi ya kuma kad'e fitina,"
"Ameen" Malam ya amsa dashi kana yaci gaba da cewa "munyi magana da yaron ki gobe su Auta zasuje gidan iyayen yarinyar dan haka sai ku fara shiri"
"Malam aini keda shiri nida keda auren yan mata uku ai ba zama kuma Allah dai ya bamu aron rai in mik'asu d'akunan su cikin aminci kamar yanda na mik'a sauran yan uwan su. "
*Bayan wasu kwanaki *
Maryam, Jameela, Aminatu duk sun fara zana jarabawar fita yayin da a gefen su Aisha da Moon suma hakan take duk sai d'auki suke akan su gama su taho Zaria domin yanzun kam ba fashi duk hutu a zaria sukeyin shi, dan yanzun an samu cigaba suma Meenal duk ta jajje gidajen su, dan an samu cigaba sosai ta fannin Meenal din dan yanzun ta sake sosai da yan uwan ta *Danginta* na wajen uwa sosai take jin dad'in yanda suke mu'amalan tarta suke nuna kulawar su akanta,
Sunyi jimami matuka a sanda zancen auren su Raheenat ya fito domin abun ya dake su matuk'a, wai su da koh sakandire basu gama bane za'a aurar, amma ya suka iya biyayya ga Baba Malam wannan kam tilass ne, ba amaren kadai bane sukaji rashin dad'i harda Meenal sai dai koda tajema Malam da maganar amsar daya bata shi yasata dole tasha jinin jikin ta ta koma ba amaren hakuri barin ma Raheenat da suke kwana d'aki daya, sosai tasan yanda Raheena da ya Abubakar suke kaunar junan su Wanda kusan duk jama'ar dake gidan sun san da hakan. Dan sosai ya shiga ciki tashin hankali a yayinda labarin ya iskeshi dan babu wanda koda wasa yayi zaton Malam zai aurar dasu Raheenat din a yanzun, da yasan abinda zai faru kenan da tuni ya gabatar da kanshi a wajen Malam sai dai kuma yanzun kam bakin alkalami ya riga ya bushe sai dai hakuri kawai da zaiyi shi akan dole,
Shirye ² aure fa yana ta kankama su Meenal sune amarori kirjin biki dan itace gaba² akan komai daya shafi amaren.
Duk abunda ke gudana fa nasa rana ku sani hatta da uwar Meenal bata sani ba domin dai Baba Auta gaba d'aya kwarin gwuiwar dazai tun kareta da batun nema ya nema ya rasa, to me zaice mata, ta shirya Malam zai aurar da Meenal nan da yan satikai ko ya zaice mata,
Yaje har wajen Innar yara akan ta taimake shi tazo ta fad'ama Jiddah din abinda ake ciki amma matar nan firrr tak'i a cewarta bata kar zomo ba wallahi baza'a bata rata ya ba, ya koma dai yasan ta yanda zai fad'a mata ai matar shine domin dai yasan aure ba fashi garama ya fad'a matan dan kullum kwanakin kara kusantowa sukeyi...........
Kun daiga yanda na daure na zuba muku tarin Read more saboda ina son yayi sauri koh?
To yasin in banga comment ba shiru zakuji gobe🤨🤨
Aci gaba sa Sharing dinshi please 🙏 .
#Ummiee~Zaria
[8/7, 11:53 PM] Zainabusmanummiee584: ⚜️🔱 FAMILY HOUSE ⚜️🔱
~{{ȶֆɨռȶֆɨʏǟ ʍǟƊǟʊʀɨռӄɨ Ɗǟʏǟ}}~
*©®UZ-2023.*
*👨👩👧👦DANGINA!👨👩👧👦*
_{{ℳℽ ℱᗅℳⅈℒℽ}}_
ⱤɄ฿Ʉ₮₳₩₳.
*ZAINAB USMAN*
_{Uɱɱιҽҽ~Zαɾια}_
*BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM*
*₲₳฿₳₮₳Ɽ₩₳*
_Yabo da godiya da'iman wa abadan na Allah ne. Salati da sallama sune na ɗan gatan Allah fiyayyen halitta Annabi Muhammad (s.a.w),tare da iyalansa da sahabban sa baki ɗaya._
*₴₳Đ₳Ʉ₭₳Ɽ₩₳*
_Gaba ɗaya kacokan ɗin labarin nan sadaukarwa ne gareku ababen alfaharina._
*JAMILA MUSA* {{Meelat Musa}}
*HAUWA MUH'D USMAN*
{{Real Smasher}}
*H UMAR*
{{Admin Beneficial}}
&
*SAJIDA* {{🇳🇪 NIGER}}
*₮Ʉ₭Ʉł₵ł*
_Wannan shafin tukuici ne ga gidaje biyu masu albarka,BENEFICIAL WRITERS ASSO,tare da gidanmu na gado abun alfahari FAMILY HOUSE,Allah ya ƙara haɗin kai ameen.
```Page 27
Tunda ya baro wajen Innan yara yake ta famar sak'a da warwara,
Allah ya sani ba karamin kunyar Jidda yakeji ba dan hakika yasan ba'a kyauta mata ba sai dai koshi da yake matsayin uban Meenal babu wani abunda zai iyayi dan dakatar da batun auren.
Ganin cewa shirun bazai kawo maslaha ba yasa koda ya shigo kai tsaye d'akin Jiddah ya wuce domin gara ayi ta a kare yau kawai.
Waya ya sameta tanayi dan haka ya nemi gefen gadon da take zaune shima ya zauna, sallama tayi ma wanda suke wayar sannan ta juya gareshi,
"Barka da shigowa! yanzun ka shigo ko tun d'azun? na dan tsaya gyara kayane shi yasa banji shigowar naka ba"
Bai iya bata amsa ba illah kamo hannu wanta da yayi duka bibbiyun ya zare wayar dake rike a hannun nata sannan ya runtse hannun a cikin nashi hannuwan yana d'an mur murzasu ta yanda bazata ji zafi ba.
Daga kanta tayi gamida maida kallonta zuwa fuskar shi tana karantar yanayin da yake ciki domin karara ta karanto tarin damuwa kwance a fuskar nashi,
"Abban su me yake faruwa ne? Kasani koda baka fito fili ka fad'amin ba ina lura da yanayin da kake ciki tunda da aka fara maganar auren yaran nan domin nasan damuwar taka tana da alak'a da batun auren! "
Ajiyar numfashi ta sauke tana shafa tafin hannun shi ta d'aura da cewa, "Meye abun damuwa akan abunda ba yau aka fara ba! Naga dai tun tale tale dama haka kuke aurar da yaran ku da kananun shekarun su balle kuma yanzun da su d'in zamu iya kiransu kai tsaye da suna yan mata, gashi Alhamdulillah duka mazajen nasu ai babu yaro balle suyima yaran garaje, ina ganin gara kabar duk wata damuwa kabisu da Addu'ar fatan alkhairi sai kaga nan da wani d'an lokaci mun samu k'arin jikoki a gidan"
ta karasa fad'in hakan tana mai sanya murmushi a fuskarta duk dai dan taga ta rage mishi damuwar dake kwance a fuskar shi.
Duk abinda take cewa kallonta kawai yakeyi batareda yayi yunkurin katseta ba harta kai aya, sannan ya d'an k'ara janyota zuwa kusa dashi sosai yana mai kwantar da kanta akan kafadun shi,
"Hauwa'u Jiddah"ya kira sunan ta yana mai kallon cikin idon ta,
Dago kanta tayi ta kalle shi dan an dad'e rabon da taji ya kira cikakken sunan ta haka, dan ko sunan nata zai kira sai dai yace maman wane ko kuma ya kira ta da Jidda amma yau ya kira ta da Hauwa'u Jidda,
Sai da ya k'ara kwantar da kanta da kyau yana d'an bubbuga gefen kafadarta a hankali sannan yaci gaba da cewa. " da fari ina mai neman afuwar ki akan abunda zai fito daga cikin bakina zuwa cikin kunnuwan ki, Jidda ki sani a kullum ina alfahari da kasancewar ki matar aurena kuma uwar yarana, tsayin shekarun auren mu bazan iya tuna rana guda da kika tab'a b'ata min rai ba, duk da nasan cewa ni d'in lokuta da dama nakan b'ata miki amma baki tab'a