Showing 78001 words to 81000 words out of 212491 words

Chapter 27 - Asanadin Makwabtaka Book 1 Hausa Novel Complete

27 Dec 2024

1008

ba,shine za'a kaima Taliya mai daddawa,Haisam yaga ta kanshi😂,

"Wai nikam ko kin daina rashin ji ne Fatuu? Kwana biyu ba wanda ya kawo man k'ararki inata mamaki wllh", gwaggo dake zaune tayi maganar,
Wata yar Isakar Dariya Fatun tayi"Na daina kakus,ance man indae inason in Zama Doctor to sai ma Natsu,don ko inada Kokari indae banda Natsuwa to bazan zama ba",
"waye ya fad'a maki hakan" Fatuu tace"Yaya Handsome na gidan Hajiya",jinjina kai gwaggo tayi"Har shima yasan halinki kenan,ai ni da ina fad'i maki hakan shashasha kika mayar dani shiyasa kika ki daukar maganata...."katseta Fatuu tayi"ai shi mai ilimi ne yasan yanda Abun yake"hannu gwaggo tasa ta ruke baki"ni kuma Jahila ce ko shiyasa baki yarda da maganata ba kenan",

Fatuu dake Dariya tace"to kice Continent sai in yarda ke mai ilimi ce",Juyawa gwaggo tayi gefenta ta rarumo takalmi ta jefo mata,da gudu Fatuu ta fad'a cikin kicin sauran kad'an ta ham6arar da Tunkuyar Taliyan🤣.

*💖A SANADIN MAKWABTAKA💖*
_*(Love and Destiny)*_


Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/D2Y0l2ZoRx8FLdjdi2Te0F

_*BY ZAINAB LALUH📲*_


*DA SUNAN ALLAH MAI RAHAMA MAI JIN KAI*


*39⃣*

Ta cikin Kitchen d'in ta lek'o da kanta,kitson da gwaggo tayi mata gefe da gefe nata reto"Gwaggo Don Allah kiyi hakuri,Wllh ni bance ke Jahila ba ce,ai nasan kwanaki kinje Makarantar yaki da jahilci kuma har d'an turanci kina ji",banza gwaggo tayi mata tana cigaba da Sauraron Radion wayarta da ta kunna,

"Pls Sorry Kakus"Fatuu ta fad'a,
d'aga kai gwaggo tayi tana kallon kanta da ta leko dashi,dan ta6e baki tayi,tasan in ba tanka mata tayi ba haka zatai ta mata surutu,
"bazaki fito ki duba girkin ba sai ta dafe"jin haka yasa Fatun fitowa daga cikin kicin d'in don ta fahimci gwaggon batayi Fushi ba.

*** *** *** ***

Hajiya zaune ita da Haisam a parlor kaman yadda suka saba bayan isha,
"Tahir ya turo man sako yace naki ne" kallonshi hajiyar tayi"Waye Tahir kuma?wane sako?"
"Matsalar kin tsufa da yawa baki gane mutane,Tahir na gidan Mota Kaduna", Dariya Hajiya tasa"Allah Sarki wai Wannan Yaron tahir,rabona dashi tunda ya kawo man waccan 406 d'in kuma mun kwana biyu bamu gaisa ba, kasan Mutane yanzu sunfi gane ma tarkacen chatting d'innan ni kuma ido ba wani isasshen lafiya ba,ban iya inta k'ura ma waya ido shiyasa ba son yin shi nike ba,Miya ce ne?",
"Yace sunyi magana da Dad akan Mota da za'a kawo maki shine ya turo pictures ki Za6a" Yamutsa Fuska Hajiya tayi"Ali ho,ni bansan mike damunshi ba wllh",

Sai lokacin Haisam ya d'ago idanunsa daga kan Wayar dake hannunsa yace"Mi kuma Dad d'in yayi?",
"To wai daga Munyi magana yake tambayana cikin Motoci ba mai Matsala,shine na fad'i masa game da Waccan Vibe d'in da ta lalace yace za'a zo a d'auka,ni ai nayi tunanin gyarota Za'ai kawae Amman shine zai wani ce a turo hotuna in zaba",

Haisam dake d'an kishingid'e ya d'an ta6e baki"Shine har yayi laifi,ke da ba'a maki gwaninta...."da sauri hajiya ta katseshi "To mai Uba kaji nace yayi man Laifi ne,Kawae dai kamata yayi a gyaro Wanccan d'in,ba sai an wani sake ba,Duk ma ga Matoci nan a Gidan,kai kanka akwae biyu naka da kazo dasu ga d'ayar tawa,Sannan acan GRA ma akwae Motoci,to duk miye na sai an Kawo Watan,"

"Ba ruwanki da nawa kowa yayi Amfani da nashi,Kuma na Gra da kike Magana ai Dad yasa Manager d'inshi na nan garin ya kwashe su Saboda anata ajesu ba'a Amfani dasu, in Buk'atar amfani dasu ya tashi zasu yi replacing wanda suka d'aukan,tunda dae so yake a canja maki kawae ki za6a,already i ave selected it for u",

Hajiya dake kallonshi tace"Wacce ka za6ar man?", bai bata amsa ba sai mik'ewa da yayi ya koma kusa da ita ya zauna yana nuna mata pic d'in Motar da ya za6a matan,
"Kai Masha Allah tayi kyau wllh,kuma gata itama yanayin Vibe din gareta inason Mota haka,kamar jeep ce ma ko,Ya sunanta ne,ince dae bata da tsada ko?"

Kwantar da kanshi yayi ajikin kujeran ya d'an zamo"Rav 4,jeep ce,bata da wani kudi sosae just 12 million take..."tun kafin ya k'arasa Hajiya ta waro idanu hannunta d'aya ruke da ha6arta"Million sha biyun ne ba tsada don baka tsoron Allah Haisam,haka kurum jama kai Surutu,aji dadin cewa kudin talakawa yake sata yana kashe man tsofaitsofai dani ko,su Mutane da basa raina abun magana",
"Ina ruwanki da Mutane,let dem say what they want,tunda Allah ya baki iko sai ki denying kanki abunda kike so",
ta6e baki hajiya tayi tace"Uhm surutun Mutane ai abun tsorone haisam,in dae akwae wata wadda bata kai wannan kudi ba in gani",

"Yeah Akwae wasu,ga wata sunanta Venza" yayi maganar yana nuna mata hoton Motar,Hajiya tace"Oh,kaji sunayen Mota iri iri,kuma masha Allah itama ba dae kyau ba,to ita bata kai waccan ba dae ko?"
"Yeah,bata kaita ba,ita 10m take...",
da sauri hajiya ta katseshi tana d'an harararshi "yo miye marabarsu,ni nayi zaton Banzar ce ashe ta kirki ce,kaga nifa banson wadda takai miliyan goma gaskia,in dae akwae na k'asa da hakan to sai in za6a,amman bazan za6i wad'annan ba,ita waccan d'ayan taka d'in nawa take ne?"

"Mercedes kike magana,55m take",Wata Uwar harara Hajiya ta wurga mashi"da Allah ni ba ita nike magana ba,yo ni miya rage man yanzu a Rayuwar da zan rinka hawa Motar Miliyan hamsin harda biyar,d'ayar nike Nufi navy blue dinnan"
Sigh yayi"Corolla S kike nufi,bai da wani tsada 6m yake..."da sauri ta tari numfashinshi"Yauwa to kaga kamar itan ko wadda ma bata kaita ba yar 5 zuwa 4m" Still yayi ya d'an dage gira yana kallonta,
"Kayi man shiru,bakaji mi nace bane?"

Gyara zama ya danyi"Rav 4 da na za6a maki shi za'a kawo period,dama na sanar dake ne don kisan za'a kawo,kina son abu sai ki hana kanki saboda wani Mutane"
A harzuk'e Hajiya tace"To tunda nace banso ba sai akawo man irin wadda nike son ba",banza yayi mata saima latsa wayarshi da ya fara,dama tasan tunda har ta nuna Motar tayi mata to fa sai yasa an kawo ta,
a k'ule tayi kwafa"To wllh da an kawota bada waccan 406 d'in zanyi",d'age gira yayi ba tare da ya kalleta ba yace"as u wish" tana niyyar bud'e baki ta sake yi mashi Magana Muryar Fatuu ta katse mata
hanzari"Assalamu Alaikum,ga bak'uwa daga Makka",

Juyawa hajiya tayi ta kalli entry d'in adai dai lokacin Fatuu ta sake maimaita abunda ta fad'a,d'an girgiza kai Hajiya tayi tace shiryayya kafin ta amsa"Wa'alaikumus Salam Maraba da Mutan Makka ku shigo",shigowa tayi tana Dariya hannunta ruke da yar madaidaiciyar warmer ta yafo d'an bakin gyalenta na gado,da Hijabi ta fito ganin gwaggo zaune a tsakan gida,tana zuwa zaure ta cireta ta sagale ajikin windon Amadu kaman yadda ta saba yi daman ta 6oyo gyalen shine ta yafa kafin ta fito,
Tana shiga haisam ya koma inda yake zaune da farko,hakan yasa ta nufi gefen hajiyan ta zauna tana dariya"Hajiyan Sanata ina wuni",
"Lafiya lou fateema,yau Allah yayi kenan an kitse kan nan",

"Ai ba duka akayi ba iya biyun nan ne,tace sai gobe da yamma tunda ba islamiyya zata k'arasa man sauran",
Jinjina kai hajiya tayi kafin tace"wani abun arzikin nasamu da daren nan" tayi maganar idonta akan kulan da fatuu tazo da ita,janye kulan fatuu tayi gefe"Ba naki bane,Yaya handsome na kawo mawa,naje part dinshi naga bai nan shine na kawo masa nan",
Hannu Hajiya tasa ta ruke baki alamar mamaki tace"iyee, yanzu Fatima ni zaki gwasale,duka yaushe kika san haisam d'in da zaki man tawaye,lalle Nagode da wannan babban dizgin da kika man,amman zamu had'u ne",langa6ar da kae tayi tana ma hajiyan dariya kafin ta mik'e tana niyyar nufar inda haisam d'in yake,kwafa hajiyan tayi tana jinjina kai,ganin dae da gaske haisam d'in ta kawo mawa yasa Hajiya juyawa side d'in kitchen ta fara kwalama Saude kira"Saude,Saude lek'o ki tayani Jimami,yau ni Fateema ta wulak'anta",fitowa Sauden tayi ta tsaya bakin kopar kicin d'in hajiya ta shiga fad'i mata abunda fatuu tayi mata,Dariya ta fara yi daga inda take tsaye,

A gabanshi ta tsaya tana ta Murmushi,shima kallonta yake don duk draman da suke da Hajiyan yana sauraransu,hannu tasa tana d'an kange bakinta"kai na kawo mawa Yaya Handsome"ta fad'a da alamun kunya,kai ya d'aga mata,hakan yasa ta d'aura warmer d'in kan hannun kujera ta kinkimo sofa table kafin ta d'auko kulan ta d'aura,Hajiya dae nata bin ta da ido haka Saude ma har lokacin tana a bakin kicin sai faman Murmushi take,

A hankali Fatuu tasa hannu ta fara k'okarin bud'e kulan,k'amshin daddawa ne ya kaima hancin haisam karo bayan
ta bud'e,da Sauri ya juyar da fuskarshi gefe had'i da runtse Idanuwanshi,waro ido Fatuu tayi ganin abunda yayi,

"Miya faru ne naga Wanda aka kawo mawan ya kauda kai hada rufe idanu??" hajiya ce tayi tambayar,a sanyaye fatuu ta juya ta kalleta"nima ban sani ba,dana bud'e ne sai naga yayi haka",
"Miye kika kawo masa ne?"
Fatuu tace"Taliyan hausa ce mai daddawa",bud'e idanu hajiya tayi hannunta ruk'e da ha6arta"ai baya son daddawa Fateema,kamshinta tada mashi Zuciya yake yi shiyasa bai cin duk wani abu da akayi da ita",
Damm gaban fatun ya buga,juyawa tayi ta kalleshi,ya bud'e idanun sai dai kwata kwata bai kalli bangaren da take ba idanunsa na akan TV,jikinta ba k'aramin Sanyi yayi ba,a hankali tasa hannu ta d'auki kulan,juyawa tayi ta kalli hajiya dake kallonta fuskarta d'auke da Murmushi,a hankali ta nufi wurinta,agabanta ta tsaya ta mik'a mata kulan"gashi to Hajiya ki ci" fuskarta a yamutse tayi maganar,

Dan ta6e baki tayi"saida shi bazai ci ba sannan zaki kawo man,wato ni ga kwad'ayayya ko,to nima bazan ci ba...."fuskarta kaman zatayi kuka ta katse Hajiyan"Don Allah kiyi hakuri ki ci",
"Uhm dama kin daina Wahalar da kanki Fateema bafa zanci ba,har ni zaki ma Wulakanci,wato ke mai Yaya ko,to tunda ba zai ci ba sai ki koma dashi kawae" ba alamun wasa a fuskarta tayi maganar,ganin haka yasa Fatuu d'aga kai ta kalli Saude da har lokacin take tsaye a bakin kicin ta dan d'aga murya"Aunty Saude in kawo maki zaki ci?" kafin Sauden ta bata amsa Hajiya ta amshe"bazata ci ba itama tunda tun farko bamu kika kawo mawa ba,saida aka gwasale ki shine zaki mana neman kai da ita,to ba wanda zai ci"maido kallonta tayi kan hajiya da tayi maganar ganin ba alamun wasa a fuskarta yasa ta fara ta6e baki alamar zata fara yin kuka,ganin haka yasa Hajiyar juyar da kanta gefe alamar ko a jikinta,a hankali ta juya ta nufi hanyar fita idanunta cike tabb da kwalla,sharr kwallan ta fara zubowa,gefen gyalenta tasa tana gogewa yayin da hannunta guda ke rungume da kulan taliyan,

"ZARAH....",Haisam ne ya d'an d'aga Murya ya kirata,a hankali ta waiwaya ta kalleshi,alamar tazo yayi mata da kanshi hakan yasa ta koma cikin parlon tana yi tana goge kwallan dake zubo mata,A gabanshi ta tsaya kanta na kallon k'asa,
"Keep it" yayi Maganar yana nuna Sofa table,a hankali ta d'aura kulan saman table d'in kaman yadda yace,d'agowa tayi bayan ta aje ta saci kallonsa,shima ita yake kallo saidai bazaka iya gane tak'amaimai yanayin fuskarsa ba,
"Go and bring plate with fork" gently yayi maganar,da alamun mamaki ta idasa d'agowa tana kallonsa hakan yasa ya d'an lumshe idanunsa alamar eh,da sauri ta juya don daukko Plate da cokali mai yatsu,suna had'a idanu da Hajiya ta wani sha kunu ta nufi hanyar kicin,hakan ba k'aramin dariya yaba hajiyan ba,tana shiga kicin d'in Saude ta mik'o mata abunda taje d'aukan kallon Sauden tayi fuskarta ba yabo ba fallasa ta kar6a,daga haka ta juya ta fuce,

Ba k'aramin daurewa Haisam yayi ba lokacin da ta bud'e kulan zata fara zuba mashi, don ma ba sosae aka cika daddawan ba sannan ga k'amshin Curry da aka sa hakan ya rage mata kaifi sosae,tana zuba kamar cokali biyar ya dakatar da ita alamar ta isa,maida marfin kulan tayi ta rufe ta d'an ja gefe ta tsaya,Slowly ya kai hannu kan fork din ya d'ebo yar kad'an,lokacin da zai kaita bakinshi har saida ya d'an dauke numfashin shi kafi ya sakata ciki,a hankali ya fara chewing dinta kafin ya had'iye,abunda ya bashi mamaki kwata kwata baiji daddawan ya canja taste d'in abincin ba,kamshinta ne kawae ake ji,k'ara kai fork d'in yayi ya debo har ta dan fi ta farko yawa ya kai bakinsa,bayan ya hadiye ya d'ago fuskarshi ya kalleta a inda take tsaye ta zuba mashi idanu,fuskarshi ad'an sake kaman zai yi Murmushi yace"it tastes good",

Waro idanu tayi"Kenan tayi maka dad'i Yaya Handsome?,
Kai ya d'aga mata da d'an murmushi alamar eh,wata k'arar farinciki Fatuu ta saki lokaci guda ta fara tsalle had'i da juyawa saitin da hajiya take tana fad'in"Yeeee,an gwasale hajiya,an gwasale hajiya....",Sosae take tsalle kitson gaban kanta sai dagawa yake sosae, gaba daya ma gyalen ya zamo k'asa,ita kam hajiya mi zata yi in ba Dariya ba,sosae take tik'ar dariya,hakan ya jawo hankalin Saude ta leko,cike da farinciki fatuu ta tsaya da yin tsallan tace"Aunty Saude Yaya Handsome yaci abincin hajiya taji Kunya",hannu Saude tasa ta rufe baki tana dariya,ita kam Hajiya throw pillow ta d'aukko ta jefo ma Fatun,abunda bata sani ba Hajiyar ita tasa haisam d'in yaci abincin,dama da biyu taki ci lokacin da fatuu ta nufi kopar fita daga falon hajiya ta kalli haisam d'in da kai ta rinka lallashinshi tana magana kasa kasa akan ya daure ya ci abincin,

"To a samman in ci nima tunda wanda aka kawon don shi yaci" hajiya ce tayi maganar tana kallon Fatuu dake zaune a gefen Haisam,mak'e kafad'a tayi"baza ki ci shi ba kuwa,shi zai cinye abunshi"ta k'arasa tana murmura ido,

Dan gyaran murya haisam yayi ta juya ta kalle shi"ki yi hakuri ki bata",
"To ai baka ci da yawa ba fa" a shagwa6e tayi maganar,yace"Owk ki d'an kara man kad'an sai ki bata sauran" mik'ewa tayi taje gabanshi ta k'ara masa kafin ta nufi Hajiya da kulan,a gefenta ta dangwarar da kulan"gashi nan don ba Halin ki ba...."bata k'arasa ba sakamakon damkota da hajiya tayi ta daddage ta d'uma mata dundu tana fad'in"Kin raina ni ko Fateema"Fatuu dake ta dariya tace"to ai ke ba kakata bace ba",Sakinta tayi tace"Je ki d'aukko man fork nima in ci inji in kin iya girkin"cike da Zumudi tace to,har ta nufi kicin ta juyo"banda plate hajiya?"kai ta d'aga mata"eh bani cokalin kawae zanci acikin kulan,

Bayan ta kawo mata cokalin a gefenta ta zauna ta k'ura mata ido tana jiran taji mi zatace game da Abincin,jinjina kai hajiya tayi lokacin da takai lomar farko"Ah Masha Allah, tayi dadi sosae wllh,amman dae nasan dije ce tayi shi....."da sauri fatuu ta katseta"Wllh ni nayi shi na rantse da Allah,ita kawae nuna man yadda zansa abubuwa tayi amman tana zaune nayi har na gama" hajiya tace"lalle kinyi kokari"sosae fatuu ta washe baki alamar taji dadi.

Yana gama cin Abincin ya mik'e don gaba daya jin bakinsa yake yana warin daddawan,Bedroom d'in Hajiya ya nufa fatuu ta bishi da kallo har ya shige corridor kafin ta maido idonta kan hajiya"Wai hajiya da gaske Yaya Handsome baison daddawa?" cinye abincin bakinta ta fara yi tace"Wllh kwata kwata baisonta tun yana yaro,warinta yake ji sosae,wani lokacin har Amai yake yi in yaji kamshinta,shiyasa ma bai shan miyan duk da akasa ma daddawa yanzu haka da kika ga ya nufi dakina na tabbatar Brush zai je yi",
Jinjina kai fatuu tayi a sanyaye tace "ai da bai ci ba tunda bai so,ni fa koda nayi kuka saboda ke kinki kici ne", dariya hajiya tayi" karki damu,yaji zai iya ne shiyasa yaci,nima kuma dama don yaci d'in tunda shi kika kawo mawa yasa nace maki bazan ci ba,yanzu da yaci ba gashi nima ina ci ba"gyad'a kae fatuu tayi sai faman fara'a take ba k'aramin dadi taji ba da suka ci,

Fitowa yayi yana goge face d'inshi da tafin hannunshi da alama ruwane a fuskar,hanyar fita ya nufa don duk da yayi Brush d'in still jin bakinsa yake ba dai dai ba,Part dinsa zaije Don ya fesa had'addan Mouth spray dinsa ko zaiji daidai,
"in fita zaka yi don Allah ka d'an raka Fateema dare nayi"hajiya ce ta katse mashi hanzari,kai kawae ya d'aga ba tare daya kallesu ba,
"To Fateema tashi ki bi shi sai kuma Allah ya kaimu,Nagode duk da bani aka kawo mawa ba", mikewa tayi ta dauki kulan don tuni hajiyan ta gama ci,
"Sai da safe Hajiya" kai ta d'aga"Allah ya tashe mu lafiya",
har Fatuu ta nufi hanyar fita cike da tsokana hajiya ta dan d'aga Murya"Gobe ki kawo ma Yaya Handsome Tuwo da Miyan kuka",a sukwane fatuu ta juyo ta kalli hajiya dake ta dariya,ganin haka yasa itama tayi dariya tace"ai bazan k'ara kawo masa abu mai daddawa ba",daga haka ta juya tabi bayan haisam wanda tuni ya fice,

Da sauri ta isko shi don a hankali yake tafiyan,jerawa tayi dashi ta d'ago kae ta kalleshi"Yaya handsome don Allah kayi hakuri nasa kaci abunda baka so,wllh ni bansan baka sonta ba"d'an juyawa yayi ya kalleta da dan Murmushi calmly yace"Don't worry ur self,naji dadin abincin ai,thanks",jinjina kai tayi tana ta zabga uban Murmushi daga haka suka fuce daga Gate din gidan,

Fatuu na ganin har sun wuce katangar gidan Hajiya bai tsaya ba tace"Yaya handsome yau har gida zaka rakani ne?"kai ya daga mata alamar eh,taci gaba"ko dae don kar na sake zuwa kangon nan ne,ai bazan k'ara zuwa ba duk da ma an kamasu,oh lemunana ko suna can ko wani ya d'auke su"tayi maganar hannunta ruk'e da ha6arta,

"Ko zaki je ki duba ne" haisam yayi maganar idonshi akan hanya,dariya kawae tayi don ta gane gatse ne yayi mata,gab da kiosk d'in kawu Amadu Haisam ya ja ya tsaya,hakan yasa itama ta tsaya tana kallonshi"kije sai da safe"fatuu tace"to bari inma kawu Amadu magana ku gaisa,bata jira cewarshi ba ta juya tana kwala ma Amadu kira"Kawu Amadu ka lek'o ku gaisa da Yaya handsome",
lek'o da kai ta cikin kiosk d'in Amadu yayi tun kafin yayi magana Fatuu ta nuna masa haisam dayake an maido da wuta akwae haske sosae,,Haisam na ganin Amadun na k'okarin fitowa

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login