Showing 168001 words to 171000 words out of 212491 words
yadda ka k'ara kyau" shiru kaman bazaice komae ba can kuma yace "kije kiga if he's ready"
"Tk d'in?" ta tambaya, kai ya d'aga mata alamar eh,
"To amman in bai shirya ba zan k'ara kiranka" shiru ya d'anyi sai kuma ya d'age gira yace "bazaki barni nayi bacci ba ko" kyalkyacewa tay da dariya ganin yadda yai mata Maganar tace "to na barka kayi bacci Sweetheart Ya Handsome d'ina, amman fa in muka dawo zan kiraka kaima ka nuna man gayun sallan ka" tay Maganar tana jaddada mashi da kanta, d'an guntun Murmushin gefe yay ya daga mata kai alamar to daga haka ta daga hannu tana yi mashi bye bye shima ya d'aga mata hannu guda kafin ya katse kiran, Lokacin data maida ma Tk d'in wayar yana cikin shiryawa don bayan tafiyarta kwanciyarshi yay ya k'ara yin bacci, cewa tay zata jirashi a parking space yay sauri ya fito yace mata to, bayan wani lokaci tana jingine da Motar Hajiya sai gashi ya fito ya dau wankan voile sai kamshi yake zabgawa, tana ganinshi ta fara kokarin bud'e Motar ya dakatar da ita da fad'in "Yau ba cikinta zamu fita ba"
"To a wacce zamu?" ta tambaya, Corolla S d'in Haisam wadda ranar data fara ganinshi ita ya hau tk ya nuna mata, da mamaki tace "To baya rufe abunshi ba taya zamu hau ta?"
"Ai ya bani makullinta yace ko zamuyi amfani da ita" ya fad'a yana kokarin zura key d'in ya bude Motar,Murmushi ta saki tana jinjina kirkin Haisam a ranta, Bayan sun fita saida suka tsaya suka d'auki Haulat kafin suka wuce.
ALBISHIRUNKU MATAN AFRICA DA KEWAYE SHAHARARRAR MAISAIDA KAYAN MATAN NAN WADDA KUKAFI SANI DA MAMAN HAIDAR TANA YIMAKU ALBISHIR DA CEWA ZAKU IYA SAMUN KAYANTA ADUK INDA KUKE AFADIN NIGERIA DA NIJAR, KARKU MANTA MACE MAI GYARA BATA BORANCI💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃08040448621
Akwai zafafan kayan mata masu matukar kyau da arha cikin sauki zamu aika miki da kayanki cikin aminci da yardar Allah su isa har inda kike ba cuta ba cutarwa karku bari abaku labari.
Muna kawo kalolin ingantattun kaya kamar haka 💥💫💥💫👇👇👇👇
1-Maganin sanyi
2-Maganin gyaran nono
3-Maganin hips
4-Akwai gumba kala kala
5-Maganin matsi masu ciko da gaba ki koma kamar budurwa
6-Kalolin garirrika masu bawa mace ni'ima da jimawa ajiki yana aiki
7-Akwai tsumi sha yanxu magani yanzu
8-Akwai jigidar sirri kala kala
Sannan kuma muna dahuwa kamar haka 💥💫💥💫👇👇👇👇
1-dahuwar kaza
2-yan shila
3-ciccibi
Dadai sauran su.Abubuwa dayawa gaskiya bazasu lissafu bah saboda lokaci maiso ta bini PC don ganin Kalolin kayan da muke dasu 08040448621,
ALLAH YAYI MAKI KIMA DA DARAJA AMATSAYINKI NA MACE👰,KADA KI WOFINTAR DA KANKI A WURIN MIJI SABODA RASHIN GYARA KAI, BURIN MAMAN HAIDAR KO WACE MACE TA ZAMA TAURARUWA⭐YAR LELE AGUN MIJINTA😍 SAI AN GWADA AKAN SAN NA KWARAI🤝
*💖A SANADIN MAKWABTAKA💖*
_*(Love and Destiny)*_
_*BY ZAINAB LALUH📲*_
~(Oumm Imam)~
*DA SUNAN ALLAH MAI RAHAMA MAI JIN KAI*
6️⃣3️⃣
.......Bayan sun gama kallon sallan bazama sukae cikin gari ana yin la'asar Tk yace bari ya maidasu gida don akwae taron da zaije shida abokanshi Fatuu tace to ai basu gama zuwa inda suke so ba yace ta bari gobe tunda ba wani hawan za'a k'ara yi ba sai su fito da wuri suje duk inda suke so sannan ta amince ya maidasu gida, a gidansu Haulat suka sauka sai Magrib ta koma gida ana gama sallan isha taje shago wurin kawu Amadu tace don Allah ya kira mata Ya Handsome, tsawon lokaci ta d'auka tana waya dashi duk da shi ba wata Magana yake ba itace mai surutun wani lokacin tayi Maganar arziki wani lokacin kuma mara kan gado shi dae sai dai yay murmushi ko ya bata yar gajerar amsa har tambayarshi Hajiya tayi yace bai gidan ta kira wayanta, karshe dae saida ya nuna mata zaiyi wani abu sannan ta kyaleshi sukayi sallama, Washe gari ma kaman jiya tunda wuri ta shirya taje wurin tk lokacin ya tashi amman bai gama shiryawa ba tace bari taje wurin Haulatu in ya fito sai ya kirata a gidan harda jaddada mashi kar ya dad'e fa ya dai amsa mata da to, bayan yaje ya d'aukesu sosae sukayi yawo don duk wani wurin shakatawa kama daga park, zoo da sauransu dae har wani had'addan eatery ya kaisu suka ci duk abunda suke so suka kuma dauki wanda zasu tafi dashi duk ya biya kud'in, dama kuma duk inda suka je shike biyan kudin shiga da sauran abubuwan don Musamman Haisam ya bashi kudi saboda hakan, sai Magrib suka koma gida sun gaji likis sun kuma yo guzurin abubuwa sosae sannan duk inda suka je saida Fatuu tasa photographer dake wurin yay mata hotuna za'a turo ma Tk shi kuma sai ya tura ma haisam wad'anda akayi masu kuma da Haulat tace in an turo zata yi ma kawu Amadu magana sai ya tura mashi su,
Washe gari ya kama kwana ukku da salla tk na cikin sharar baccinshi da safe ya jiyo sautin bugun kopar dakinshi koda yace waye Fatuu tace itace har saida gabanshi ya fad'i kafin ya taso ya bud'e mata, bin ta da ido yay bayan ya bud'en tana tsaye taci gayu da shaddar da hajiya ta d'inka mata don jiya voile d'in tasa, tana ganinshi ta turo baki tace "kai Tk wai bacci ma kake yi baka shirya ba kullum sai na jira ka"
"Ina zamu kuma" ya tambaya da mamaki,
"Yawon salla mana" jinjina kai yay yace "yanzu duk uban yawon da muka yi bai isa ba, ko inafa munje ina kuma zamu k'ara zuwa?"
"To ai kayan sallan nawa basu k'are ba, ko sai in sanyasu in zauna gida" ta fad'a tanata faman tura baki, d'an Murmushin yak'e Tk yay kafin ya tambayi kayan sallan nata kala nawane tace mashi kala tara ne yau tasa na biyar yanzu saura kala hud'u, waro ido Tk yay jin har nan da kwana hud'u masu zuwa sai sun fita, ce mata yay ta bari to sai zuwa d'an anjima sai su fitan tunda jiyan sun je wurare da yawa, da farko k'in yarda tay sai daga baya ta amince akan kafin sallar azahar zai zo su fita yace to, tana tafiya ya fara tunanin nemawa kanshi mafita don tsakani da Allah ba k'aramin takura zaiyi ba ace har nan da kwana hudu masu zuwa yana fita da ita kuma dae ba yadda zaiyi dole yai mata yadda yake so in ba haka ba yasan fad'i ma Haisam zatayi shi kuma ba zai so hakan ba koda kuwa haisam d'in ya fahimce shi, Wuraren karfe 12 yaje ya dauketa koda suka biya ma Haulat cewa tai su tafi kawae Innarta tace yau bazata fita ba ita zata kula da gidan don innar tasu ta tafi Unguwa hakan yasa suka tafi,
Gaba d'aya Tk baiji dad'in fitar ba har saida ta k'ule shi don gidaje tasa ya rink'a kaita na yan'uwansu su Zaliha da gidan Baba shehu har gidansu Nana saida taje da gidajen wasu k'awayenta gashi in ya ajeta yace zaije ya dawo sai tace a'a sai dae ya jirata ta fito abunda kuma yafi 6ata mashi rai kenan yadda ta maidashi kaman driver d'inta don ko Hajiya bata ta6a yi mashi haka ba ita iyaka in ma zai jirata in ya kaita wani wuri to baifi suje gida biyu ba, sam bai nuna mata 6acin ranshi ba amman yana ta sak'a yadda zai yi daga yau kar su k'ara fitowa, yau ma dae sai wuraren Magrib suka dawo da daddare bayan sallan isha suna zaune a tsakar gida gwaggo ke ce mata amman dai daga yau sun gama yawon sallan ko tace mata a'a ai bata sanya sauran kayanta ba gwaggon tace yakamata dae ta kyale tukur ya huta hakanan amman sai ta turo baki tace to ai dai Ya Handsome yace ya kaita duk inda take so don haka ita sai tagama sanya kowanne kaya sannan zata gama yawon sallan, washe gari ganin jiya basu fita da wuri ba yasata bari sai kaman lokacin sannan ta nufi gidan Hajiyan bayan taci gayu da d'aya daga cikin atampopin da Babanta ya kawo mata anyi mata riga da skirt ga gyale wanda gwaggo ta siya mata da takalma yauma dae tayi kyau abunta atamfar ta amshi fatarta sosae da yake adon flowers pink gareta, lokacin da ta je bakin Gate bayan sun gaisa da Officer ne yake ce mata anya kuwa Tk zai iya fita yau, cikin rashin fahimta ta tambayeshi dalili,
"Ai jiya kwana yayi ba lafiya don da daddare har saida na kaishi asibiti" cikin rashin yadda take bin shi da wani irin kallo bayan ya gama Maganar tace "Tk d'inne bai lafiya bacin ko jiya lafiya lou muka dawo"
yar dariya Officer yay kafin yace "in baya ga abunki hajiya fatuu ai yanzu yanzu sai Allah ko, ina tunanin wani abu yaci ya lalata mashi ciki shine ya d'ingi gudawa harda amai gaba d'aya yau da safe dana duboshi baida kuzari don ko Magana ma da k'yar yake yi" sototo tay tana kallon Officer alamar kaman dae bata yarda ba ganin hakan yasahi cewa ta shiga ta ganshi, wucewa tay ta nufi cikin gidan yana ganin ta tafi ya d'aga waya da sauri ya kira Tk lokacin yana kwance yanata sharar baccinshi kiran wayar ya tada shi don tana kusa da kanshi, bayan ya d'auka ne da sauri Officer ya sanar dashi ga Fatun nan ai kuwa wata wuntsilawa yay ya saukko daga kan k'atuwar katifarshi ya d'aukko wasu tarkacen Magunguna acikin drawer ya watsasu agefen katifar, bottle water dake saman drawer d'in ya d'aukko ya ajeshi a k'asa kusa da katifar, da sauri ya nufi kopa ya bud'e kafin ya koma kan katifar agurguje ya kwanta hadi da lullu6e jikinshi gaba d'aya da bargo yaba kopar baya, sai bayan d'an wani lokaci ta k'araso don akwae yar tazara daga gate zuwa bayan, tana niyyar kwankwasa kopar ta ganta a bud'e, d'an tura kopar tay ta rafka sallama shiru bai amsa ba ta k'ara yin sallamar sannan ta jiyo muryarshi can kasa yana cewa ta shigo kopar a bud'e take, a hankali ta tura kai ta shiga tana hango shi taja ta tsaya kaman taga abun tsoro ganinshi a kudundune cikin bargo, d'an matsawa tayi ta kira sunanshi shiru bai amsa ba ta k'ara sannan ya amsa da kyar,
"Ashe wai baka lafiya?" ta tambaya tanata zare ido, kai kawae ya jinjina mata ba tare da yayi Magana ba,
"Mike damunka?" shiru kaman bazai bata amsa ba can ya dan fiddo fuskarshi amman bai juyo ba don yasan daya kalleta yana iya yin dariya don dama akwae shi da yawan yin dariya, da kyar cikin irin muryar mara lafiya yace "ina tunanin Food poison ne naci ya lalata man ciki, jiya nasha wahala dakyar na samu na kira Officer ya kaini hospital har saida akai man k'arin ruwa na d'an samu sauki" yadda yake Maganar sai ka rantse da Allah bai lafiyar ita kau Fatuu k'ara zaro ido tai a rud'e jin harda k'arin ruwa akai mashi don ita a wurinta da anyi ma Mutum drip to ciwon yayi tsanani, kaman zatayi kuka ta shiga yi mashi sannu don dama ita badai tausai ba in taga mutum na ciwo duk ta damu, da kai ya rinka amsa mata can tace ya kawo wayarshi ta kira Ya Handsome ta fad'i mashi, da sauri yace " a'a ki kyaleshi kar a tada masu hankali tunda Officer ya kaini asibiti"
"To bari inje in fad'i ma gwaggo, in ta gama abinci kuma zan kawo maka" ta kai Maganar tana nufar hanyar fita da sauri, yana jin k'arar rufe kopa alamar ta fita ya yaye bargon daga jikinshi tare da juyowa yana dariya a fili yace "haka kawae ki nemi maida ni bawanki, ko shi Yaya Haisam d'in nasan da yasan wahalar dani zaki bazai sani kaiki wani yawon salla ba" ya kai hannu ya d'auki wayarshi ya hau yin chat abunshi,
Ko ta kan Officer dake tambayarta ta gano shi bata bi ba iyaka ta d'aga mashi kai kawae tayi gaba, gaban kiosk din Amadu ta tsaya da damuwa ta fad'a mashi Tk bai lafiya don Allah ya kira ya Handsome ta fadi mashi, ganin yadda ta damu ne yasashi tambayarta miya samu Tk din ta fadi mashi, kiran Haisam din ya shiga yi bugu d'aya ya d'aga ya mik'a mata wayar bayan ta gaidashi ne ta kwashe komae game da ciwon Tk din ta fadi mashi a rude tana ta zuzuta ciwon yace zai kirashi daga haka sukai sallama, tana shiga gida ta iske gwaggo cikin kicin itama ta hau fad'i mata, sosae ta shiga jimami har tana cewa ko wannan yawon ai yasa ma mutum ciwo, jin abunda gwaggon tace ne yasa fatun yin wuri wuri da ido jin kaman harda laifinta yake ciwon.
Tk na cikin yin chat kiran Haisam ya shigo har saida gabanshi ya fadi don yasan tabbas Fatuu ta gaya mashi bai lafiya ne, a d'arare ya d'aga kiran bayan sun gaisa ne ya mashi ya jiki yace da sauki sosae jin hakan yasa haisam din cewa Zarah tace har drip aka mashi shiru yay ya kasa cewa eh don mugun jin nauyin yi mashi k'arya yake kuma yasan in yace eh zai iya tada masu hankali ba kaman Hajiya in taji,
"Any problem?" yaji haisam d'in ya tambaya, cikin sanyin murya yace "ba wani abu daman ba ciwo nike ba ita na fad'i ma hakan kawae" shiru Haisam d'in yay kaman bazaice komae ba can kuma ya furta "why", ba tare daya yi mashi karya ba ya kwashe yadda sukae da Fatun na cewa sai kayan sallanta sun kare zasu daina yawon sallan kuma duk inda ya kamata suje sun je, sigh Haisam yay ta cikin wayar jin rikicin Fatun,
"kayi hakuri Ya Haisam in banyi maka daidai ba" Tk ya fad'a cike da girmamawa, gently yace "No, i understand, amman kana ciwon k'arya in ya kamaka fa?",
yar dariya Tk yay yace "ai ya haisam akwae inda dole saida karyar"
d'an guntun murmushi yay ta yadda har saida Tk d'in yaji daga haka yay mashi sallama tare da rejecting call din, cike da murna Tk ya fad'a kan katifarshi don sai yaji kaman wani nauyi ya sauka daga kanshi, yana kwancen Amadu ya turo kopar ya shigo, turus yay ganin Tk d'in kwance yana mashi dariya hakan yasa Amadu murza idonshi don wai ko ba daidai yake gani ba,
"Kaga patient na dariya ko" Tk ya fad'a yana tashi zaune, nufarshi Amadu yay yace "to ai ni waccan burkakkar ce man tayi wai kana kwance magashiyyan fa" k'ara sautin dariyar tk yay "ai hakan ta ganni ne, amman fa lafiya ta garas wllh" nan ya yi ma Amadun bayani dalilin ciwon karyar
"Yarinyar nan fa ba hankali ne da ita ba wllh kai jakinta ne, amman baka ce mata ka gaji sai kayi ciwon karya?"
"Ai hakanne kawae zaisa mu rabu da ita lafiya tunda kaga sani akai yi mata hakan" jinjina kai Amadu yay alamar ya fahimta suka k'ara d'an yin fira kafin ya mik'e zai tafi,
"Amman ya baka kawo man abun ciwo ba to" Tk ya fad'a yana dariya,
"Wake ta wani abun ciwo nida akace ma cikin ka ya lalace kana ta amai da zawo har na fara tunanin ko wucewa zakai" Amadu yay Maganar yana dariya shima,
"to na biyo ka bashi ka aiko man da kayan dubiya" Tk ya fad'a lokacin Amadun zai fita, akan hanya ya had'u da Fatuu ruke da kula zata kai ma Tk Abinci kallonta kawae yay ya d'an girgiza kai ita kuma ta tura mashi baki, tana wucewa ya kira tk a waya yace sai ya shirya ga Boss dinshi nan zata kawo mashi Abinci, koda ya isa bai tsaya shago ba dama wani yaro ya bari ya jire mashi, cikin gida ya nufa ya sanar ma gwaggo game da ciwon Tk din don ta tashi hankalinta har lekowa tay waje bayan Fatuu ta sanar da ita tace don Allah yay sauri yaje ya gano ya jikin nashi yana ciwo shi kadae a gida ya sanar mata dama yanzu yake niyyar zuwa, Salati Gwaggon ta saka ta shiga tafa hannu jin ciwon bana gaske bane,
"Wllh dama nasan dole ya gaji da wannan yawon, ai yama yi kokari kwana nawa suna fita kuma kullum sai wurin Magrib za'a dawo, ai da baiyi ciwon k'arya ba dama ina niyyar taka mata burki tunda ita bata da hankali bata san daidai ba" girgiza kai Amadu yay ya juya hanyar fita yana fad'in Allah ya shiryi Fatuu, tun daga ranar ba'a k'ara fita yawon ba.
**** **** ****
Bayan kwana tara da yin salla ranar Laraba da yamma Fatuu ta dawo daga islamiyya don sun koma tun salla da sati daya wato shekaranjiya litinin kenan, tana shigowa cikin zaure suka yi kacibus da Amadu da ya shigo daukar abu acikin d'akinshi, da sauri taja gefe don tasan yana iya rankwashinta, yar harara ya wurga mata ya nufi waje ita kuma ta nufi cikin gida, har ya fita ya juyo yace "Ke Ya Ugly d'inki ya dawo d'azun nan naga Tk ya d'aukko shi daga Airport" waro ido tai tasa tafin hannunta ta dafe kirjinta alamar mamaki, juyawa tai zata wurga jakar cikin gidan Amadu ya daka mata tsawa "baki da hankali ne ba akwae Alqur'ani ba!"
sai da yay Maganar ta tuna ta nufi cikin gidan da sauri ta ajeta a gefen dakinta kafin ta juya da gudu ta fita daga gidan ta nufi gidan Hajiyar sanata, lokacin data k'arasa part d'in nashi tura kopar Falon tay ta shige cike da zumudin son ganin Ya Handsome saidae bata samu kowa a falon ba