Showing 84001 words to 87000 words out of 212491 words
ya fara amfani da wannan d'in babanshi Zakee yana can k'asar da ake saida waccan da yake so zan mashi waya in zai dawo zai kawo masa,shine fa nasamu ya shafa man lpy,wai d'azun da nike fad'a ma Feenah zanxo wurinka in na fito yaron nan ashe bai manta ba da yake banzan kai ne dashi kaman naka,bai mantuwa kawae sai yaje ya sanyo takalma wai zaizo ya kar6i kwamfuta d'in shi wurin Baba zakee tunda ya dawo,kasan Allah ni nama manta,dubara ta fad'o man nace mashi wannan wanda zani ba shine baba zakee ba shi H,zakee sunanshi baiji na fad'a ma Momynshi ba,yace shi H,zakeen baida ita,nace mashi eh ai shi tare muka dawo daga Abuja ba shine a k'asan da ake saida computer din ba,shine fa na samu na gudo,feenah nata man Dariya"
Sigh haisam yayi yace"ai da ka siya masa tunda zai masa amfani,from d way kai describing nashi it will help him learn things easily so kudinsa ba abun damuwa bane"
"Uhm kudinsa kam abun damuwa ne,ka kuwa san da kudin zaka mallaki buhun shinkafa harma ka hada da d'an galan d'in mai,koda yake kai fa ba siyan shinkafar kake bama shiyasa zaka ce hakan,kyale sa kawae yanzu ba komai dama ake so akuma samu ba,rayuwan yayi tsada ta abinci ake ba wani abun wasa ba" k'ura masa ido haisam yayi ya cije lip d'insa na kasa kaman ba zai kara cewa komae ba,
"Da kana yaro me ka ta6a nema ka rasa Abbas? shine kai yanzu za kai denying yaro abunda yake so" sosae Abbas ya kyalkyace da daria "wuuuh h,zakee kai fa na manta you don't give up easily,shi yasa ko da muna skul abokan adawan ka na debate ke shan wuya,is hardly ai nasara akan ka,kai baka ganin rayuwan yayi tsada yanzu,"
girgixa kai haisam yayi"kawai dae zaka cutar man yaro,thank God he has another father,ka turo man picture din toy en,akwae computers da za'a turo man next week zan tura masu su bincika masa sai a hado man nasan baza'a rasa ba,koda ba exact irinshi nasan za'a samu mai irin features din shi"
Abbas yace"ah haba ka rabu dashi wllh...."haisam ya katse shi da fad'in"ina ruwanka ne,wait Abbas....,badai so kake ka nuna man iyakata a gun yarona ba..."da sauri Abbas ya daga hannuwanshi alamar ban hakuri yace"Apology baban Abdul "ta6e baki haisam yayi kafin yace"Don ma he's too young ai da ta gasken za'a kawo masa,don so nike ya zama expert tun yanzu don babanshi zai gada shima Computer engineer zai zama insha Allah"
"Allahu yashaa,Hakan nada kyau ai daman kyan d'a ya gaji mahaifinsa"Abbas ya fad'a yana murmushi don kar ya k'ara wani laifin,shi dai Haisam d'an ta6e baki yayi ba tare da yace masa komae ba.
"Wani zaka kawo ma
computers ne? Abbas ya tambaya,
"yeah,wani company ne a lagos suka ban contract zan je nayi masu aiki but sai kayan sun iso"haisam ya bashi amsa,
"Allah ya kawo su lafiya,ya bada sa'a,kaga ba don mun koma aiki ba ai danayi rakiya"
d'an murmushi haisam yayi yace"ai in zanje zan bi flight d'in yamma ne ran friday,inason yin komae within weekend zuwa Monday sai in dawo,kagan just rana d'aya ne bazaka aikin ba" Abbas yace"alright sir,zan dauki excuse,Allah ya kaimu"
"Ameen" ya amsa,daga haka Abbas ya fara kokarin mikewa"bari na wuce Zakee inason zan biya round din Gra ne,Allah ya baka lpy ya kiyaye gaba"
mik'ewa haisam yayi,Abbas na fad'in ya bar rakiyar yace ba matsala ai yasamu sauki sosae suje ya rakashi wajen,suna fitowa waje inda yayi parking motarshi ya tuna da wata magana da yake son yi ma Haisam d'in hakan yasa suka haye saman boot d'in Motar suka zauna don suyi maganar,suna cikin tattaunawa kamar ance haisam ya waiga gefensa ya hango Fatuu na tahowa daga bayansu dayake Motar Abbas din gab da shiga kwanar gate din ya parker ta, bata shiga cikin lungun gate d'in ba,underneath his breath yace"here she comes"kallonshi Abbas yayi"wa?"haisam bai kaiga bashi amsa ba ta zagayo inda suke hannunta ruke da bokitin ruwa,jikinta na sanye da riga da skirt na atampa yayin da ta yafa d'an gyalenta na gado saman kai,kitsonta sun zuba gaban kan,har lokacin ba'a idasa kitson ba don daga baya gashin a fake yake yayi tum,aje bokitin tayi a gabansu ta zuba ma Abbas ido shima bin ta yayi da ido yana kallonta.
*💖A SANADIN MAKWABTAKA💖*
_*(Love and Destiny)*_
_*BY ZAINAB LALUH📲*_
*DA SUNAN ALLAH MAI RAHAMA MAI JIN KAI*
*4️⃣1️⃣*
A hankali ta fara matsawa kusa da Haisam,a gefenshi ta tsaya,kasa kasa da murya tace"Ya handsome bak'o kayi?"kafin ya bata amsa Abbas ya rigashi"ba bak'o bane dan'uwansa ne Mom zarah"waro ido tayi baki bud'e take kallonshi,mamaki ne ya kamata jin yace mata Mom zaraah,nufo inda yake tayi ta tsaya agabanshi tace"kenan Yaya Handsome ya baka labarina?"kai ya d'aga mata"Eh yace wai munyi sabuwar Mom",tafin hannuwanta tasa ta rufe baki tana dariya alamar mamaki,
"To kai ma sunan mamanka gare ni ne?fatuu ta tambaya bayan ta cire hannun,
"Ba kiji nace ni dan'uwansa bane,ai Mom dinmu daya..." tun kafin ya rufe baki ta fara jefa masa wani kallo irin ban yarda ba d'in nan,
"kenan kana nufin kaima Senator babanka ne?"cike da tuhuma tayi tambayar,kai ya daga mata alamar eh,
Juyawa tayi ta kalli Haisam daya sadda kai yana latsa waya kafin ta juyo tana kallon Abbas wanda ya d'an k'ankance ido fuskarsa d'auke da Murmushi yana d'an girgiza kai,ganin hakan yasa ta buga kafa cike da shagwa6a tace"Wllh ban yarda ba,kamm yo ya zanga wake da shinkafa amman kace man wai gidanku d'aya",Sosae Abbas ke 6a66aka dariya jin abunda tace,tsagaitawa yayi"waye wake waye shinkafar"tana turo baki tace"yo kai da kake baki ai kaine waken shi kuma da yake fari shine shinkafar",
"To ai ni Senator na biyo shi kuma sai ya biyo Mom dinmu, ko baki ta6a ganin senator din bane?" shiru tayi tana kallonshi still bata yarda ba"to amman ni ai shi kadai nasani anan,kuma shima baice man yana da wani dan'uwa ba anan,kuma ko gwaggota da hajiya ma basu fad'i man ba",
"To k'ilan dae bakuyi Maganar da zasu sanar dake hakan bane,amman ni dan'uwansa ne Uwarmu daya Ubanmu daya" ya k'arasa yanata Murmushi,kallonshi kawae take ba don ta yarda ba,ganin yanata faman zabga murmushi yasa ta fara bubbuga k'afa tana jujjuya kai sai kace wata yar k'aramar yarinya,murya kaman zatayi kuka tace"bafa kyau k'arya kuma kai babba ne kasani,don Allah ka fad'i man kai waye"a marairaice tayi maganar,karfin halinta ba k'aramin Dariya yake ba Abbas ba,ganin tana ta masa magiya yace"Owk,bari in fad'i maki gaskiya to daman wasa nike maki,ni Amininsa ne tare mukayi Senior Secondary anan garin amman yanzu mu mun wuce abokai yan'uwa ne"washe baki tayi"daman nasan ba gaskiya kake fad'a man ba,kenan kaima kaman Haulatu ne",
"Wacece haka?Abbas ya tambaya,
"nima Aminiya tace yanzu haka makarantarmu d'aya da ita kaman yayata take" jinjina kai yayi,
taci gaba"muna ta yin anko da Yaya Handsome,kaga shima awurin kakarshi yake nima haka,sannan yana da Amini nima ina da Aminiya"ta kai maganar tana ta dariya duk dimples dinta sun lotsa,shima dariyar yake mata,
"To kai ya sunanka?"
"Sunana Abbas", jinjina kai tayi ta kuma cewa"A nan garin kake?" kai ya daga mata alamar eh,
"To ina ne gidanku?"
"Gidana dae,a Fatima shema Estate nike,kinsan wurin ko?",
"Ina dae jin sunan amman ban ta6a zuwa ba,ka ce anan gidanka yake,kana da aure ne?"
Kai ya d'aga"ina da Aure sunan matata Nafeesat kuma inada yaro guda d'aya sunanshi Abdul"hannu fatuu tasa ta ruke ha6a alamar mamaki,a hankali ta juya ta kalli haisam wanda har lokacin kanshi na k'asa yana latsa waya tamkar bai jin ma abunda suke tattaunawa,
D'an matsawa tayi kusa da Abbas kasa kasa da murya tace"to ya akai shi bai yi auren ba?" Abbas na niyyar bata amsa haisam ya d'ago fuska a d'an d'aure yace"Zaraah!"a firgice ta juya ta kalleshi,"ba aiken ki akai ba?"da sauri ta kai hannu ta d'auki bokitin ruwan ta juya zata tafi,Abbas dake guntse dariya yace"Ah Mom ya haka kuma d'anki ne fa shi ai ke yakamata ki bashi umarni ko"juyowa tayi tana mashi wani kallo"da ya baka labarina bai gaya maka akwae yarjejiniyar gidan yari tsakaninmu ba"daga haka tayi gaba,Abbas kau dariya yasa harda dafe ciki,ganin yadda ruwan keta zubowa yana jik'a mata k'asan skirt yasa shi d'aga murya"Mom ki d'aura saman kai mana"bata juyo ba hannu tasa tana nuna mashi tudun gashinta dake afake alamar bazai bari ta d'aura ruwan akan ba,
K'ara daga murya yayi"to Mom zaraah sai yaushe zamu kara had'uwa mu gaisa",d'an juyowa tayi ganin haisam d'in ya maida kan k'asa yasata dakatawa ta aje ruwan"yaushe zaka k'ara dawowa?"ta tambayeshi,
"Kowane lokaci,ina yawan zuwa ai",
"To kaga wannan gidan mai kiosk shine gidanmu,idan kazo kana son ka ganni nan zaka zo,kace a kira maka Fatuu,in kuma ba wanda zaka aika ka shigo ciki kawae,in kaga gwaggota sai kace mata kai Abokin Yaya Handsome ne wurina kazo...." tana ganin haisam yana niyyar d'agowa ta kai hannu da sauri ta d'auki bucket din ta juya,
Sosae Abbas keta dariya don maganar tata dariya ta bashi wai in bai samu wanda zai aika ba ya shigo kawae yace ita yake nema sai kace wani zararre,kallon haisam yayi wanda ya d'ago yana kallonshi don duk maganganun da suke yana jinsu dama shima Abbas din bakinshi sake yake,d'an ta6e baki yayi yana girgiza kai,Abbas yace"yo kai H,zakee ashe Mom d'in naka kwarkwar ce"gaba daya suka sa dariya,
Bayan ya tsagaita da yin dariyar yace"let me take my leave zakee,magrib ma ya kusa",atare suka saukko daga kan boot d'in,Abbas ya zagaya side din driver shi kuma haisam ya tsaya a other side d'in,
"Gaskia Abbas kaci mota,motan ya tsufa,wai a haka yan matan naka suke shiga?" Har Abbas ya kai hannu zai bude kopar motan ya dakata"yo kar yarinya ta shiga in akwae kamarta a gidansu"fuskarsa d'auke da murmushi yayi maganar,
"I thought so,sai dae babun"haisam ya fad'a da murmushi daga haka Abbas ya bud'e motar ya shige suka sake yin sallama yaja Motar bayan ya tafi haisam ya juya ya koma gida.
_____________________
Washegari Juma'a,misalin karfe 11 na safe Hajiya ta kira gwaggo tace mata in Fateema ta dawo daga Makaranta tazo zasu je Unguwa,cike da girmamawa Gwaggo ta amsa mata da toh.
Bayan sallan Juma'a,Hajiya zaune ita da Haisam saman Dining suna cin lunch,Haisam yasha shadda gizner Ash colour hannunsa sanye da wani hadaddan Diamond watch,kafarsa sanye cikin dakakkun takalma na zallar fata suma Ash,Hajjaju ma ansha atamfa babbar Holland kunnanta sanye da yan kunnan zinari harda sark'arsu da zobuna tayi d'aurin kallabi irin nasu na dattawa,kamshi ne kawae ke tashi daga jikinsu,
Bakinta d'auke da sallama ta shigo,gaba daya suka juya suna kallon entry d'in,tana hango su a Dining area ta nufi can,har ta isa idanunsu na a kanta,
"Tubarkallah,maa sha Allah,wannan kwalliya haka Fateema,kice saboda kinci gayu yasa yau ba ayi man irin sallamar da aka saba ba" Cike da jin kunya tasa tafin hannuwanta ta rufe fuska tana dariya,sanye take da riga da skirt na lace brown mai d'auke da kwalliyan fulawoyi Coffee brown,ta yafa gyale coffee yau Allah ya yi ta canza gyale, kafafunta na sanye da takalma masu tudu bak'ake hannunta ruke da yar k'aramar bak'ar jaka,yayin da wuyanta ke sanye da sarka mai kyau da yan kunnanta harda yan hannu,tayi kwalliya harda jan baki maroon,haka kitsonta an ida mata shi ta zubo shi ta gaba har ya wuce kirjinta,cikin kayanta ne na sallan bara tasa,ta Matuk'ar yin kyau,kalan lace din ya hau da fatar jikinta sosae,ganin tana ta tsayuwa Hajiya tace"Zo ki zauna kema kici abincin"cire tafukan tayi daga kan fuskan ta k'arasa wurin table d'in,dama saboda zumudin zasu fita unguwa ita da hajiya lokacin da gwaggo ta sanar da ita yasa ta kasa zama taci abinci,kujera taja ta zauna idonta akan haisam dake cin Abinci a nutse,Saude hajiya ta fara kwala ma kira don tazo tayi serving fatun,A hankali haisam ya cira kai ya kalli side d'in da take,suna had'a ido ta sakar mashi murmushi"Yaya handsome ina wuni"jinjina mata kai kawae yayi don akwae abinci a bakinshi,daga haka ya maido idanunshi kan Abincin,
Fitowa Saude tayi jikinta sanye da doguwar rigar shadda,ba karamin kyau tayi ba sai kace ba mai aiki ba,tsaf tsaf da ita tayi d'aurin kallabi mai kyau,tana karasowa Dining d'in tun kafin tayi magana hajiya tace"ki zuba ma fateema abinci"amsawa tayi da toh,ta kalli fatun"inyee wannan kyau haka fateema"Saude ta fad'a fusakarta da murmushi,itama fatun murmushin take,janyo katuwar Warmer d'in dake kan table din tayi ta bud'e,White rice ce tasha peas da green beans harda carrot gwanin ban sha'awa,Plate ta daukko ta zuba mata sai da ta tambayeta in ya isa Fatun ta ce eh,sannan ta rufe Warmer d'in ta bud'e ta biyu,jar miya ce taji uban nama kitif da ita ta zuba mata a saman shinkafar, sannan ta kuma janyo wata warmer d'in yar babba ta bude,farfesun kaza ne ciki sai uban k'amshi ke tashi,cikin wani d'an bowl ta zuba mata sannan ta rufe,nuna ma fatuu coleslow tayi"gashi nan kisa wanda zai ishe ki"fatuu ta amsa da toh,bayan ta gama zuba mata komae ta tsiyaya mata Ginger Drink a Cup daga haka tace"Aci lafiya"tana shirin juyawa Hajiya ta dakatar da ita"ki d'aukko ma haisam lemu wai ginger d'in tayi mashi yaji"kallon haisam din Saude tayi"Wanne iri za'a daukko?" batare daya d'ago ba ya bata amsa"Coke",amsawa tayi da toh,daga haka taje ta kawo masa,kallon hajiya tayi cikin girmamawa"akwae abunda za'ayi?"hannu ta d'aga mata alamar taje.
Sam fatuu ta kasa sakewa taci Abinci yadda ta saba ci,idonta na akan haisam tana kallon yadda yake tsakuran nashi,hakan yasa itama take ci a hankali,hajiya ta lura da bata sake ba kuma tasan saboda haisam d'inne don taga yadda take ta kallon abincin da yake d'ebowa,
Gyaran murya Hajiya tayi, hakan yasa duk suka d'ago suna kallonta,kallon fatuu tayi tace"muyi yar rigen cinyewa Fateema,wanda ya riga shi yayi nasara"aikam tana fad'in hakan fatuu ta fara yin loma da sauri,itama Hajiyar lomar take sai dai bata kai ta fatun ba,shi kam haisam zuba masu ido yayi cike da mamakin yadda suke tura abinci a baki,kan kace mi Fatuu ta cinye,kyalkyacewa tayi da Dariya tana fad'in ita tayi Nasara,d'an girgiza kai haisam yayi ya fara kokarin mik'ewa,kallon fatuu hajiya tayi"yi maza kisha ginger d'in,dashi wai zaku fita"da sauri ta kalli haisam don ta fahimci inda zasu,a tunaninta hajiyar bata san ina zasu ba,mikewa tayi bayan tasha ginger d'in ta bi bayan haisam da tuni ya bar wurin,
"Don Allah haisam kasa hulan ka an fi ganinka da kamala,akan kabar wannan gashin awaje kasa manyan kaya" d'aga mata kai yayi ba tare daya juyo ba,nufar kujerar da ya aje hulan shi lokacin da suka dawo masallaci yayi ya dauki hulan wadda ash colour ce itama,sawa yayi saman kan ya d'an dannata ta d'an shiga sai dae duk rabin sumar ta fito ta gefe gefe da bayan kan hakan kuma ba k'aramin kyau ya k'ara masa ba,daga haka ya nufi kopar fita daga falon fatuu dake tsaye tana jiransa ta rufa masa baya hajiya na masu adawo lpy.
Yana isa bakin parking spot ya juya yace ma fatuu ta jira,shiga yayi ciki ya nufi wata jeep ash colour sai d'aukar ido take,ba kowace mota bace fa ce Motar da ya za6ar ma Hajiya shekaranjiya har an kawota jiya da yamma yau da safe tahir d'in ya koma,budeta yayi ya shiga ya fara kokarin fiddota waje,fatuu dae sai bin motar take da kallo don sam bata ta6a ganinta ba,sai dae bata yi mamakin ganintan ba don gidan hajiya bai rabuwa da bak'in Motoci,bayan ya fito cikin harabar yasa hannu ya bud'e kopar dake gefenshi fatuu na ganin haka ta matsa gaban kopar tayi tsaye tana kallonshi,
"Sai nace ki shigo ne?" jin haka yasa da sauri ta haye ciki,bayan ta shiga tasa hannu ta jawo kopar a hankali,
"Bai rufu ba,ki bud'e ki sake rufewa da karfi",yin yadda yace tayi,sai dae har lokacin bata rufun ba,rankwafawa yayi don ya rufe da kanshi,da sauri fatuu ta kame jikinta ajikin seat ta runtse idanunta, don sai taga kaman zai had'a jikinshi da nata ne,dakatawa yayi cike da mamaki yake kallonta,a hankali ta fara bud'e idanun,lokaci guda ya fahimci dalilin da yasa tayi hakan,hannunshi ya d'aga yana nuna mata kopan idonshi a kanta yace"bai rufu bane shine zan gyara", jinjina mashi kai tayi,maimakon ya gyaran sai kawai ya juya ya fita daga cikin Motan ya zagaya side d'in da taken ya bud'e kopar ya sake rufewa sannan ya koma cikin motan daga haka ya tasheta,fuu ya tunkari gate din da tuni Officer ya zuge masu shi suka fuce.
G.R.A POLICE STATION
Slowly ya parker motar agaban Station din,hannu ya kai ya d'auki wayarsa dake aje a gefe yayi dialing number din Sp khamis,tana fara ringing yayi picking bayan yayi masa sallama ya sanar dashi yana a waje,
Ba'a dau wani lokaci ba Sp ya fito jikinshi na sanye da Uniform bai dad'e da ya zo station d'in ba,don yanzu a Police headquarter yake aiki, saboda case d'in haisam yazo,haisam na ganinshi ya bud'e motan ya fito,nufo shi yayi yana fad'in"H,zakee d big COE",hannu haisam ya mik'a masa suka gaisa fuskan kowannansu d'auke da murmushi,bayan sun gama gaisawa Sp khamis yabi motan da haisam yazo da ita da ido"H,zakee kune mota,duk wata hadaddar mota da ta amsa sunanta ku ake fara gani da ita,gaskia Motan nan ta tafi da ni Ma sha Allah",haisam dake d'an Murmushi yace"ka shiga kawae,bai da wani tsada..."wani kallo Sp ya bishi dashi"haba zakee ai koda ni makaho ne dana laluba jikin motan nan wllh zan gane mai kudi ce" kafin haisam yace wani abu Fatuu ta fito daga cikin motan ta zagayo inda suke atsaye idonta akan Sp,
"Wow,what a beautiful girl", gaidashi tayi ya amsa yace"ya sunanki?"tace"Zarah",