Showing 135001 words to 138000 words out of 212491 words
ta d'aga mashi hannu suna cewa Allah ya tsare Fatuu na fad'in wayyo babana ya tafi harda yin baya kaman zata fadi haulat ta tareta tana mata dariya,
(To Baban Fatuu, muma muna yi maka Addu'ar Allah ya kiyaye hanya,Allah yasa a sauka lpy,Amin)
Ana gobe za'a fara Azumi Tk ya kai uban kayan abinci gidansu Fatuu, dama duk azumi Senator Ali na aiko da kayan abinci masu yawan gaske a rarraba gida gida sai dae wannan karon kayan da aka kai gidansu Fatun sunfi na baya yawa sosae sakamakon Haisam da ya kara masu, bama su kadae ba harda sauran mutane saidae nasu yafi yawa don babu abunda babu wanda mutum zaiyi lafiyayyan buda baki da sahur, bayan d'anye da ake rarrabawa anayin lafiyayyan dafaffen abinci na sadaka agidan hajiyar, musamman ma'aikata masu yin girkin duk azumi ke akwae, a can bayan part d'in hajiyar ake kafa rumfuna ana yin aikin, bayan abinci ana yin kunu da kosai da kuma abunsha kamansu zo6o kunun aya wani lokacin harda fruit acikin wanda ake kaiwa masallacin gidan alokacin bud'a baki,
**** **** ****
An fara azumi lafiya gashi yau in an kai na bakwae kenan wato sati guda da farawa,Misalin karfe sha daya na safiyar ranar wadda take Asabar Fatuu ta shigo gidan hajiya ta Gate don tunda aka fara azumi ta rage zuwa part d'in Haisam don da safe yana wurin aiki ko tazo bai nan dayake ita an basu hutu in ya dawo da rana kuma mafi yawancin lokutta ko taje bacci yake da yamma kuma in aka gama sallar la'asar tsayawa yake wurin tafsir hakan yasa basu cika haduwa ba sai a part din Hajiya, tana shigowa ta hango shi acikin parking space ya bude boot d'in mota ya d'an dukar da kanshi da alama wani abu yake yi, wurinshi ta nufa ta tsaya daga gefenshi ganin alamar mutum yasashi d'agowa ya kalleta, gaidashi tayi tana d'an d'age baki tana yamutsa fuska,
"Miya faru?" ya tambayeta,kaman zatayi kuka tace "ba azumin ne ke bani wahala ba" jinjina kai yayi yace "tunda wuri haka" tana ta faman yamutsa fuska ta d'aga mashi kai, dama kullum in sun hadu haka take complain d'in Azumin wuya,
"Ki shiga ciki sai ki kwanta ki huta",
amsa mashi tayi da to ta nufi part d'in Hajiya, lokacin da ta shiga cikin parlon ba kowa amman an gyara shi tsaf sai dan sanyayyan kamshi ba mai karfi ba ke tashi don tunda aka fara azumi aka rage sa turare da yawa, kitchen ta nufa wurin Saude don tasan war haka Hajiya bacci take, tana shiga ta isketa tana yin wanke wanke,
"Aunty Saude ina kwana",
da fara'a ta juyo ta kalleta "lafiya lou Fateema har an dawo daga islamiyyar" kai ta d'aga mata alamar eh,
"Ina fata dai yau kina yin azumin?"
tana tura baki tace "banyi,ni wllh wuya yake bani shiyasa nike karyawa" jinjina kai Saude tayi tace "ki rink'a daurewa kina yi ta hakane zaki saba" d'aga mata kai tayi alamar toh tana dai atsaye can ta matsa tace bari ta tayata, d'auraya ta fara yi mata suna cikin yi sauden tace "Don Allah jeki part d'in Yayanki ki d'aukko man basket d'in kayan sahur da aka kai mashi da asuba na manta ba'a d'aukko su ba",
amsa mata tayi da to ta juya ta fita, lokacin data fita harabar gidan bata hango shi a cikin parking space d'in ba hakan yasa tayi tunanin ya koma part din nashi, da sallama ta shiga lokacin data isa saidai bai amsa mata ba don bai cikin parlon, k'ara yin sallamar tayi wai ko zai jiyo ta don kilan yana cikin Bedroom ne amman bata ji ya amsa ba hakan yasa ta nufi center table don d'aukar basket d'in da ta gani a samanshi cikinshi dauke da kayan tea da warmer, maimakon ta d'auka din sai takai hannu ta bud'e warmer dake ciki nan take ta zare ido ganin soyayyan dankalin turawa mai d'an yawa aciki, shiru tayi tana kallonshi ta fara hadiye miyau,d'an d'agowa tayi ta kalli kopar Bedroom d'in nashi jin bata ji wani motsi ba yasa ta kai hannu ta d'ebo dankalin mai yawa ta tura abaki tana taunawa idonta na a corridor d'in Bedroom din, tun tana ci atsaye har ta duk'a tayi ruku'u tana yi tana kallon corridorn don kar ya fito ya ganta,
"Can't u sit properly, haka zai iya shake ki ai" taji daga bayanta ya fad'a aikuwa a firgice ta juya ta kalleshi baki cike da dankali, ashe bai cikin d'akin kuma da ta shigo bata kulle kopar falon ba hakan yasa bata ji shigowarshi ba, can 6arin L-shape ya nufa ya zauna ya d'aura abunda ya ruko ahannunshi saman c-table wanda da gani wani abun computer ne, ci gaba da duba abun yayi alamar gyara yake yi ajikinshi,
shin wai ina Fatuu????
ALBISHIRUNKU MATAN AFRICA DA KEWAYE SHAHARARRAR MAISAIDA KAYAN MATAN WADDA KUKAFI SANI DA MAMAN HAIDAR TANA YIMAKU ALBISHIR DA CEWA ZAKU IYA SAMUN KAYANTA ADUK INDA KUKE AFADIN NIGERIA DA NIGAR KARKU MANTA MACE MAI GYARA BATA BORANCEππππππππππ08040448621
Akwai zafafan kayan mata masu kyau da arha cikin sauki zamu aika miki da kayanki cikin aminci da yardar Allah ba cuta ba cutarwa karku bari abaku labari
Muna kawo kalolin kaya kamar haka π₯π«π₯π«ππππ
1-Maganin sanyi
2-Maganin gyaran nono
3-Maganin hips
4-Akwai gumba kala kala
5-Maganin matsi masu ciko da gaba ki koma kamar budurwa
6-Kalolin garirrika masu bawa mace ni ima da jimawa yana aiki
7-Akwai tsumi sha yanxu magani yanzu
8-Akwai jigidar sirri kala kala
Sannan kuma muna dahuwa kamar haka π₯π«π₯π«ππππ
1-dahuwar kaza
2-yan shila
3-ciccibi
Dadai sauran su.Abubuwa dayawa gaskiya bazasu lissafu bah saboda lokaci maiso tabini PC don ganin Kalolin kayan da muke dasu 08040448621
*πA SANADIN MAKWABTAKAπ*
_A heart touching story of Love and Destiny_ π
*Mallakin*
β¬οΈ
*πΉZAINAB LALUH*π²β
_~(Oummu imam)~_
*DA SUNAN ALLAH MAI RAHAMA MAI JIN KAI*
5οΈβ£5οΈβ£
.......tsaye tayi tanata binshi da ido gashi ta kasa k'arasa cinye dankalin bakinta ta d'an d'age hannun da take ci dashi kamar mai shanyayyan hannu, saida ya d'an d'auki lokaci sannan ya d'ago ya kalleta, ganin yadda ta k'ame yasashi d'an ta6e baki yay mata alamar ta zauna da kanshi, zaunawa tayi idonta akanshi shima kallonta yake ya dan 6ata fuska,
"Har yanzu baki daina k'arya ba ko?" da sauri ta girgiza mashi kai kaman zatayi kuka,
"Miya hana ki yin fasting ko karya shi kikai?",
sai lokacin ta idasa cinye dankalin bakinta ta fara Magana murya kaman zatayi kuka,
"a'a dama bana yi, wllh dana d'auka in rana tayi sai inji kirjina ya fara ciwo numfashina har d'aukewa yake kaman zan mutu",
" guda nawa kikai?" zaro ido tayi jin tambayar da yayi mata gashi ya kafeta da ido tasan da ta yi k'arya zai ganeta,
" Banyi ko d'aya ba" buda ido yayi alamar mamaki ya d'an jinjina kai kafin yace "ita grandma d'in naki ta kyaleki baki ko daya ba?"
"A'a tana tada ni inyi sahur to in rana tayi bata nan sai in karya, in kuma tana nan naga tana yin bacci sai inje kicin in karyashi ko kuma in shige toilet in ci wani abu", k'ara bud'a idon yayi ya d'an yamutsa fuska jin abunda tace,maida kanshi yay yaci gaba da abunda yake yi ganin hakan yasa tace "in ci gaba da ci?" da hannu ya bata amsa, ta kai hannu ta fiddo warmer d'in dankalin ta d'aurata asaman cinya taci gaba da ci har wani jujjuya kai take tana lilo da kafafunta, can ya d'ago ya kalleta tai saurin kame kanta,
"A islamic school naku ba'a fad'i maku hukuncin wanda ya karya azumi da gangan ba?" cakk ta tsaya jin tambayar da yayi mata tace "an fad'i mana,ance Mutum sai yayi kaffara duk azumi guda sai ya rama sittin harda guda d'ayan da ya karya",
jinjina kai yay a kausashe yace "shine kuma kike karyawa!"
" To ai ance sai wanda ya balaga ne ya zamar ma dole nikuma fa ban balaga d'in ba tunda ance sai mutum ya fara wai jinin haila shine ya balaga nikuma har yanzu ban fara ba, da bamma gane abunda ake nufi ba dashi saida na tambayi Haulatu tayi man bayani dayake ita ta fara ko wanccan azumin duka tayi, tasha wuya kuma saida ta rama wanda tasha, nan gidanma take biyoni ta lalla6o shan Ac, ni dae Allah yaso ni har yanzu bai zamar man dolen ba shiyasa ma nike karya shi" ta tura dankali abaki tana yar dariya lokacin da takai k'arshen Maganar, still yay yanata binta da ido, ba yau ta fara kwa6o Magana ba amman yayi Matuk'ar mamakin yadda ta gaya mashi wannan batare da taji komae ba duk da tasan mi abun ke nufi, d'agowa tayi suka had'a ido ganin kallon da yake mata yasa tayi tunanin ko bai yarda da Maganarta bane hakan yasata cewa "Wllh da gaske nike fa ban fara ba, ba kasan shekaruna ba, ko kwanaki wasu Mutane sunzo Makarantarmu suka raba mana panties da pad da turare harda sabulu mai kamshi acikin yar jaka, suka koya mana yadda wai zamu tsaftace kanmu in muna yi to nidai pad din sai dai naba Haulatu ita,nasan kai baka san miye pad d'inba tunda kai Namiji ne, ita wai ake sawa a pant sai ta tar......",
"Enough Zarah!!!" ya daka mata tsawa har saida ta firgita ta k'ame tana kallonshi idanu waje Jikinta na yar kerma.......,
fuska a matukar d'aure yace " ke baki san ba komai ne Mutum ke sakin baki yana fada bane,did i ask u all dat!",
a tsorace tace "naga kai yayana ne shiyasa na fad'i maka amman ba wanda na fad'i ma wannan",
ganin ta d'an tsorata yasashi d'an sakin fuska yace "nima ba komae ne zaki fad'i man ba cos wani abun yakamata ki barshi as a secret and kowa da kike gani yana da sirrinshi wanda bai fad'a ma Mutane ko ni ina fad'i maki abu game da kai na ne?" da sauri ta girgiza mashi kai alamar a'a,
"To ki daina fad'i man abu irin wannan, ko matsala gareki data shafi kanki ki fad'a ma grandma d'inki, kingane mi nike nufi?" ya d'age mata gira,kai ta d'aga tace "eh kaman jikina kake nufi ai ko" kai ya d'aga mata daga haka ya maida kanshi kan abun da yake yi,
"In sha tea d'in" kai ya k'ara d'aga mata alamar eh, mik'ewa tayi ta aje warmer dankalin don ta cinyeshi ta fara kokarin had'a tea,
D'an kallonta yay yace "zaki had'a ba tare da kin wanke cup ba" jin hakan yasa ta d'auki cup d'in ta nufi washbasin dake can gefen fridge d'inshi don ta wanko shi, d'agowa yay ya bi bayanta da kallo kafin ya d'an girgiza kai, sam baiyi mamakin jin bata fara menstruation ba duk da baiyi zaton hakan ba amman yasan ba wata babba bace kawae dai tana da d'an jiki ne da zai iya sawa ai tunanin takai matakin yi, lokaci guda ya fad'ad'a Murmushinshi don hakan ya tuna mashi da wani abu wanda shi kadae yasan ko minene ya maida kanshi kan abunda yake yi,
tea mai kauri ta had'a ta zauna kan kujera tana sha idonta akan tv tana kallon Mbc Bollywood, tallar man gyaran gashi aka fara wata mata nata juya gashinta da ya zuba a gadon bayanta,
"Ina son nima gashina ya koma haka wllh amman ni banzan nawan nad'ewa yake" ta fad'a tana kur6ar tea, can aka nuno wata kuma mai gashi brown tace "lah, ga mai irin gashin wannan yar'uwan taka ta India" sai lokacin ya d'an d'ago ya kalli tv d'in kafin ya maida kan k'asa, cigaba tayi da santin gashin tana fad'in Allah yasa nata ma ya koma haka liya liya yabar nad'ewa,
" baki mai abunda ya kamata bane" taji ya fad'a ba tare da ya kalleta ba,
" To ai man farming ake sawa, waccan sallar da aka saka ma haulatu nace nima inaso sai gwaggo tace baza'a saman ba gashin wai lalacewa zaiyi" jinjina kai yay sai kuma yace "ba dole sai ansa relaxer cream ba ai",
tace " to mi za'a sa yayi liya liya ya mik'e?"
d'agowa yay hannunsa guda yana d'an shafa beard d'insa calmly yace "in kina so sai a kai ki" da sauri tace "inda ake maida shi hakan?" kai ya d'aga mata alamar eh,
" To kai zaka kaini?" shiru ya danyi kaman bazai bata amsa ba sai kuma ya d'an d'aga mata kai don wani lokacin gajiya yake da tambayarta bata iya dunk'ule tambayoyinta tayi at once,
" To yaushe zamu ko sai Salla ta kusa?" ta sake tambaya cike da zumud'i,
" i wll talk to u" haka kawae yace tare da maida bayansa ya jingina sosae da kujerar ita kuma taci gaba da yin kallo tana shan tea d'in fuskarta d'auke da murnar za'a kaita inda za'a maida mata kai liya liya har wani d'an jujjuya kai take, duk wannan abun idanun Haisam na akanta kaman yana nazarin wani abun,
" Zaraah" taji ya kirata, amsa mashi tayi "uhhuym" tare da juyowa, on a serious note ya fara magana " daga yau ki rinka yin azumi!" cike da bada umarni yay Maganar, tana jin hakan ta tsaya cakkk kaman an latsa mata pause,
" did u hear me" yace fuskarshi ba alamun wasa, marairaice fuska tayi tace "to amman ai bai zaman man dole ba ko"
" who told u bai zaman maki dole ba? Shima malamin da yayi maku bayanin kan hakan baki fahimceshi bane sosae dole zaki rink'a yi ko ba wannan abun da kika fad'i ai cos kin girma ko bake kikace ke matashiyan budurwa bane?" ya d'age mata gira alamar ta amsa mashi,
(ya fad'i mata hakanne donta rink'a yi, duk da a ilimin dake gareshi kan hakan yasan bai zamar mata wajibi ba sai dae dole arinka sata tana yi as ladab kuma ta hakane zata saba kan yazaman mata dole), hannu tasa tana d'an sosa gaban kanta ta d'age baki,
" ki rinka yi sai kina hutawa like in kika yi 3 sai ki huta one day" zaro ido tayi a rud'e tace " har sai nayi ukku zan huta, gaskiya ai yayi yawa sosae" takai Maganar kaman zatayi kuka,
Sigh yay yace "Owk mu barshi biyu to" tana tura baki tace "kadai k'ara rage man kabar man d'aya in nayi sai in huta" yadda tayi Maganar sai kace suna ciniki,
girgiza kai yayi strictly yace " 2 days zaki rika yi ki huta 1 day" ganin zata k'ara magana ya dakatar da ita da fad'in "Zarah dat's my final say, kinyi 7 days batare da kinyi fasting ko guda ba and shine bazaki iya yin 2,2 days ba, even yara younger than u suna yi kullum ko kunya ma baki ji",
kwa6e fuska tayi tana mommotsa baki saidae ta kasa yin magana don ba alamun wasa a tattare dashi, mik'ewa tayi dama ta gama shan tea d'in ta saka cup d'in acikin basket ta d'auka zata tafi, har zata bud'e kopar ya kirata ta juya,
" ki fara tomorrow, kuma kada kice zaki shiga kitchen ko toilet tunda ke kazama ne kici wani abu, in kika yi hakan mi zai faru?" ya kafeta da kaifafan idanunsa, baki a kumbure tace "kana zaune zaka gani a Computer" jinjina kai yay yayi mata alamar ta tafi, d'an girgiza kai yay bayan ta fita ya mik'e ya nufi Bedroom.
Lokacin da ta koma sashen Hajiya, Saude har ta gama wanke wanken tana ganinta tace sai yanzu ni harma na manta dana aike ki, anan take fad'i mata kamata Ya Handsome yayi tana cin abinci kuma yace dole ta rink'a yin azumi kwana biyu kafin ta huta kwana daya kuma wai daga gobe zata fara, fuska a tur6une take gaya mata hakan yasa saude yin yar dariya itama tasan dama yakamata ace tanayi ko don ta saba, in ba haka ba wuya zata sha nan gaba in ya zamar mata dole karshe ma ta rink'a karyawa don ko shekarar data wuce bazata manta ba karyawar ta rinka yi don batama tunanin tayi cikakken azumi sai dae wani lokacin tana kaiwa azahar sannan ta karya wai intayi na gobe sai yazama d'aya, bata wani dad'e ba tace gida zata tafi Saude nace mata ko ta samar mata wani abu ta k'ara ci tace ta k'oshi, a haka ta nufi gida ranta a jagule don ance tayi azumi kuma dai ba damar tayi yadda ta saba don ta yarda Haisam d'in zai gani.
Da Asuba lokacin da gwaggo ta tada ita sahur dagewa tayi ta ci uban abinci wai don karta ji yunwa bata san in kaci Abinci da yawa bama kafi jigatuwa, da gari ya waye ko islamiyya k'in zuwa tayi wai in taje taya zata dawo cikin rana tana azumi tai wucewarta gidan hajiya lokacin batama tashi ba sai Saude dake gyaran gidan, bayan sun gaisane tace zata je d'akinta ta kwanta sauden ta tambayate ba islamiyya zataje ba tace bata iyawa Azumi take, Maganar har saida taba saude dariya, daga haka tai wucewarta d'akin Saude. Bacci sosae tayi don sai wuraren sha biyu ta farka tana jin wata irin yunwa saukinta ma acikin Ac take, tana cikin juye juye Saude ta shigo d'akin, ganin ta farka ne yasa tace masu Azumi antashi kenan, tambayarta Fatuu tayi wai an kusa kiran Magriba don taga tayi bacci sosae, Dariya saude tayi tace to dama ta k'ara kwantawa don ko karfe sha biyu bata yi ba, sosae gaban Fatuu ya fad'i jin hakan, bayan fitar saude duk yadda taso ta koma bacci abun ya gagara sai faman juye juye take tana yin tsoki dakyar ta samu ya d'an dauketa amman sama sama, shigowa saude ta k'ara yi lokacin an fara kiran Sallar azahar, ganin Fatun ta motsa