Showing 1 words to 3000 words out of 218703 words
*SAKAYYAH book 2... Page 1*
Spndeɗɗ. Baya Moddibo ya koma. Suuuuuu ya faɗi a sume, cikin sauri Lamiɗo ya tarosa, ya faɗa jikinsa cike da tashin hankali Lamiɗo yace.
“Innalillahi ya suma fa Subhanallah!”.
Cikin sauri Malam Arɗo ya ƙara sa kusa da Lamiɗo idanunsa akan Moddibo ya shiga kiran sunan sa yana faɗin.
“Moddibo!, Moddibo!!, Moddibo!!!”.
Ina tuni Moddibo ya sume babu alamar numfashi atare dashi.
Abba kuwa kansa ya ɗaga tare da kallon fuskar skeleton M Jameel kana ya maida Idanunsa ƙasa kan takalmin dake sanye aƙafarsa ahankali ya leƙa bayan idanunsa suka sauƙa akan guntun rigarsa da bai gama sauƙa daga jikin skeleton ba jinjina kansa yayi cikin wata dakakkiyar murya ya juya ya kalli Moddibo dake sume kai ya girgiza tare da sakin murmushin da yafi kuka ciwo murmushi da yafi ihu zafi, murmushin da yafi ciwo, Ciwo murmushin da yafi raɗaɗi zafi, ya saki kana ya juya ya kalli sauran mutanen dake tsaye sai ya kuma kalli fuskar skeleton tare da maida kallonsa kan yatsun hannunsa.
Cikin wata dakakkiyar murya me ɗauke da tarin raɗaɗi da ƙuna yace.
“Uhmmm Jameelu na ne”.
Kallonsa ya mayar kan Moddibo da har zuwa lokacin yake. Rungume a jikin Lamiɗo taune lips ɗinsa yayi tare da cewa.
“Kai kam Aliyu kahuta, inama ace nima zan sume ko kuma in mace ma gaba ɗaya da hakan yafi min sauƙi”.
Cikin sauri ɗaya police ɗin ya juya tare da isa gefen Abba ya riƙe sa cike da alhini da tarin tausayawa yace.
“Alhj Bashir kayi addu'a kaji”.
Kai Abba ya gyaɗa cikin wata dakakkiyar murya yace.
_“Innalillahi wa'inna Ilahi rajiu'n lahaula wala ƙuwwata Illah billahil aliyul Azhim Hasbunallahu wani'imal wakil Allahumma Ajirni fii musibati wa'ahlifli khairan minha La'ilaha Illah anta subhanaka Inni kuntu Minal Zhalimin”_ sune Adduo'in da yake iya maimaitawa afili da kuma ransa.
Ori dake tsaye ciki ruɗu da tausayawa yayi saurin ƙarasawa gaban skeleton gawar M Jameel ya ɗauko goran ruwan kana ya dawo tare da miƙawa Lamiɗo yana mai cewa.
“Lamiɗo gashi ayayyafa masa”.
Karɓa Lamiɗo yayi kana ya buɗe tare da yayyafawa Moddibo dake kwance jikinsa amma ko kaɗan Moddibo bai motsa ba.
Kallon Buba Lamiɗo yayi kana yace.
“Ori taimaka min mu saka shi cikin Mota”.
Kai Buba ya gyaɗa.
Ɗaya daga cikin Folisawan ne yace.
“Ranka shi daɗe bari mu saka shi”.
Ya faɗa tare da kallon ɗan gidansa da Ido ya masa alamar yazo su kama Moddibo ƙarasawa yayi sannan suka ɗauki Moddibo suka sauƙa kasan dutsen, tare da sanya shi abayan Motar Malam Arɗo.
Folisawan kuwa ƙara sawa sukayi suka shiga ɗaukar hoton gawar skeleton M Jameel.
Bayan sun gama ɗauka tare yan dube-dubensu, da Babbansu da sauran suka saka handglove suka ƙarasa gaban gawar da niyyar sunjanye gawar Babbansun najan Igiyar da aka ɗauɗaureshi ƙasusuwan suka kakkarye tare da zubewa a ƙasa babu ta yanda zasu iya daukarsa Babban su ya umarci Coustable yaje ya ɗauko musu kwali abayan mota kana suka tattara gawar suka zuba acikin kwalin kana suka kwashe takalmansa da wayoyinsa suka saka awata leda.
Abba kuwa cikin wani irin yanayi ya nufi cikin jejin yana tafiya ba tare da shi kansa yasan inda ya nufaba.
Cikin sauri Lamiɗo ya nufesa tare da riƙe hannunsa cike da tausayawa yace.
“Alhj banan zamu bi ba can baya ne, hanyar kazo innu na maka hanyar da zamu bi”.
Kai Abba ya gyaɗa tare da bin bayan Lamiɗo baki ɗaya baya cikin nutsuwarsa ya kasa gane shin mafarki yake ko kuma azahirance komai ke faruwa.
Bayan sun isa Lamiɗo da kansa ya buɗe masa mota yashiga sannan shima yashiga.
Folisawan kuwa kwalin da gawar M Jameel ke ciki suka ɗauka tare da sawa abayan motarsu suka tafi gida.
Abba kuwa kallon hanya kawai yake baki ɗaya baya cikin hayyacinsa ganin yanayin da yake ciki ne yasa Malam Arɗo ya fara yi masa Adduo'i yana tofa masa kana yana faɗa afili.
Ahankali Abba ya fara sakin Ajiyar zuciya kana yashiga maimaita Adduo'in sannu Ahankali ya fara jin hankalinsa ya fara dawowa jikinsa.
Motar da Moddibo ke ciki Ori da police ɗaya ne aciki direct Asibiti suka nufa dashi.
Yayin da Motar dasu Abba da kuma gawar M Jameel ke ciki kai tsaye gida suka wuce, suna isa kai tsaye falonsa suka wuce police ɗin ne ya ɗauko kwalin Gawar M Jameel ya shigo dashi kana ya ajiye agabansu.
Hajiya Turai dake sashenta tana jin tsayuwar motoci ta fito zuwa falon Abba.
Ganin Abba zaune tare dasu Lamiɗo yasa ta nufi gefen Abba cikin yanayin damuwa tace.
“Alhj lafiya ya ake ciki Gawar waye kuka samu?”.
Ahankali ya ɗago Idanunsa da suka kaɗa sukayi jawur ya kalleta kana yayi ƙasa da kansa cikin raunin murya yace.
“Gawar Jameelu na ne!”.
Arazane Hajiya Turai ta kallesa zuciyarta na bugawa da masifar ƙarfi Idanunta akansa tace.
“Gawar Jameelu kuma!?”.
Kai ya gyaɗa mata Cikin tsananin tashin hankali da ruɗu ta fashe da kuka me tsuma zuciya tana furta.
“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n ina gawar yake?”.
Da hannu ya nuna mata kwalin dake gabansa.
Da kallo tabi kwalin cikin sauri ta sake Kallonsa Idanunta cike da ruwan hawaye tace.
“Gawar Jameelu ne acikin kwali haka?”.
Kai ya gyaɗa batare daya ɗago kaiba yace.
“Shine”.
Wani sabon kuka ta fashe dashi tana Girgiza kai Kukanta ne ya fito da Hajiya Karima itama ganin abinda ke faruwa yasa ta fashe da kuka.
Acan Asibiti kuwa ana kai Moddibo likitoci suka shiga bashi temakon Gaggawa saidai koda wasa bai farfaɗo ba ganin haka yasa suka dauƙo wani na'ura mai kama da Iron akafara danna masa aƙirji.
Amman ina babu alamun zai motsa, sosai likitocin suka dugufa wurin ganin sun cetoshi, a karo na biyu suka kuma danna mishi a ƙirjunshi, amman ina, Dr Lukman ne ya karɓi aikin tare da goggoga jikin na'urar ya manna masa a kirjinsa da ƙarfi.
Cikin ikon Allah yaja wani dogon numfashin sake dannawa yayi da karfi wani irin maraitaccen numfashi ya sake ja amma still bai farfaɗo ba sake dannawa sukayi akaro na biyar ne yaja wani dogon numfashi tare da buɗe idanunsa kana yace.
“Jyyyyyyy”.
Malam Arɗo da bai daɗe da dawowa daga gidan Abba bane, yayi saurin riƙe hannunsa tare da cewa.
“Moddibo kayi addu'a”.
Duk da cewa baya Cikin nutsuwarsa hakan bai hanashi maimaita duk wata addu'a da tazo bakinsa ba ahankali ya ɗago kansa tare da kallon Malam Arɗo yace.
“Malam J ɗina nefa!”.
Jinjina kai Malam Arɗo yayi cike da tausayawa yace.
“Eh shine Moddibo Allah ya karɓi Jameelu muyi masa addu'a Allah ya karɓi shahadarsa”.
Girgiza kai Moddibo yayi tare da cije lips ɗin sa duka biyu, kana ya runtse Idanunsa cikin wani irin yanayi mai wuya yace.
“Malam Arɗo mutuwar azaba suka masafa, ɗaure sa sukayi suka ajiye masa goran ruwan agabansa ta yanda yana ji yana gani bashi da damar sha sun barshi da azabar ƙishi”.
Kallonsa Malam Arɗo keyi cike da tausayawa yana ganin yanda zuciyarsa ke bugawa da ƙarfi.
Cikin wata raunan'niyar murya Moddibo ya cigaba da cewa.
“Malam ɗaure sa sukayi suka ajiye masa wayoyinsa agabansa ta yanda yana kallon muna kiransa bashi da damar ɗauka bare yace mukawo masa ɗauki”.
Sai kuma ya rintse idanunsa da masifan ƙarfi zuciyarsa na cigaba da buguwa da masifaffen ƙarfi kana yace.
“Ɗaure sa sukayi ta yanda yana ganin ga hanyar tsira sai dai bashi da damar kiran wani ya kawo masa ɗauki ɗaure sa fa sukayi ta yanda yana ganin kiran mu amma bashi da damar ɗauka”.
Jujjuya kansa ya farayi kamar zautacce hawaye na bin gefe da gefen idanunsa har suna shiga kunnensa cikin Muryan kuka yace.
“Ɗauresa fa sukayi ta yanda yana ganin kiran Abbansa bashi da damar ɗauka,Mutuwar azaba da raɗaɗi suka masa da ƙishi fa suka kasheshi”.
Kasa ƙarasa maganar yayi kawai ya fashe da matsanancin kuka mai tafiya da numfashi Atake numfashinsa ya ɗauke ya sake sumewa!.
Cikin sauri Malam Arɗo ya miƙe tare da kiran likitoci kana ya sanar dasu ya sake suma taruwa likitocin sukayi akansa kana suka shiga bashi temakon Gaggawa da kyar da temakon Allah suka samu ya farfaɗo ganin ya farfaɗo yasa Dr ya masa Alluran bacci Atake baccin wahala ya ɗauke sa.
Ajiyar zuciya Malam Arɗo ya sauƙe tare da miƙewa ya fita kana yayi dearling number Lamiɗo yana ɗauka yace.
“Ranka shi daɗe yaron nan fa gashi agigice yake baki ɗaya da zaran ya farfaɗo sunan Marigayi Jameelu yake kira, yana kiran sunan kuma zai sake suma!”.
Acan gidan Abba kuwa zaune yake afalonsa hannunsa riƙe da waya tunda suka dawo yake zaune awajen ya kasa koda motsawa se kwalin Gawar Jameelu daya zubawa Ido yana jujjuya wayar hannunsa ajiyar zuciya ya sauƙe tare da kiran number Ummi Yana Jin tayi picking ya fesar da numfashi kana yace.
“Fatima”.
Cike da mamaki Ummi tace.
“Abban Jameel”. Jin muryansa.
Cikin raunin murya ya sake cewa.
“Fatima”.
Anutse Ummi ta amsa da.
“Na'am”.
Runtse Idanunsa yayi kana yasake cewa.
“Fatima”.
Cikin dakiya Ummi da taji zuciyarta ya tsinke da Masifar ƙarfi tace.
“Na'am Abban Jameel ka faɗa min me yasamu Jameelu na sun kira ne ko kuma yaya!?”.
Cikin rauni yace.
“Hmmm”.
ya faɗa tare da katse kiran kana ya fito da Number Malam Ahmad.
Malam Ahmad na ɗagawa Abba yace.
“Malam kazo da Fatima da yaranta!?”.
Cikin tsinkewar zuciya Malam Ahmad dake Bedroom ɗinsa ya miƙe tare da cewa.
“Meya faru Alhj Bashir ka faɗa min”.
Girgiza kai Abba yayi tare da taune lips ɗinsa kana yace.
“Ga gawar Jameelu na agabana”.
Cikin tsanananin tashin hankali Malam Ahmad ya dafe bango tare da faɗin.
“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n Allahumma Ajirni fii musibati wa'ahlifli khairan minha”.
Katse kiran Abba yayi cikin sauri ya fito falon tsaye ya samu Ummi riƙe da waya a hannunta cikin ƙoƙarin ɓoye tashin hankalin sa yace.
“Fatima Lafiya!?”.
Ahankali Ummi ta juya ta kallesa tare da cewa.
“Yan zun nan Abban Jameel ya kirani, to kuma ya yanke gashi kuma ina ta sake kira naji line Busy”.
Da ƙyar ya haɗiye wani abu mai masifar ɗaci kana cikin ƙoƙarin ɓoye damuwarsa yace.
“Toh kada ki damu kizo muje muji meke faruwa”.
Kai ta gyaɗa tare da cewa.
“Toh”.
Sannan ta nufi hanyar fita.
Kallon Bashir da Asma'u dake tsaye yayi kana yace.
“Kuma kuzo mu tafi”.
Kai suka gyaɗa kana suka bi bayansa suka fita.
Suna isa falon suka samu Hajiya Turai da Hajiya Karima da ƴaƴan Hajiya Karima na kuka cikin sauri Ummi ta ƙara sa shiga falon tare da tsayawa agaban Abba kana tace.
“Abban Jameel meye faru?”.
Ahankali ya ɗago ido ya kalleta, sai alokacin yaji kuka ya kufce masa ganin Ummi agabansa baki ɗaya ta gigice jikinta na rawa.
Cikin rawan murya tace.
“Abban Jameel meyafaru!?”.
Kasa cewa komai Abba yayi sai kuka da yake tamkar ƙaramin yaro.
Da sauri Ummi ta juya tare da kallon yanda su Hajiya Turai ke kuka cikin rawan murya da yanayin tashin hankali tace.
“Ku faɗa min mana meke faruwa!?”.
Tayi tambayar baki ɗaya ilahirin jikinta na rawa.
Asma'u da Bashir dake tsaye Atare suka fashe da matsanancin kuka ganin yanda ƙannen M Jameel ke kuka.
Ahankali Malam Ahmad ya matso kusa da Ummi tare da cewa.
“Fatima ki zauna”.
Girgiza kai tayi kana tace.
“Ni bazan zauna ba kafaɗa min abinda ke faruwa”.
Cikin sanyin murya Lamiɗo yace.
“Maman Jameel kiyi haƙuri ki zauna”.
Kallon sa tayi tare da cewa.
“In zauna?”.
Kai ya gyaɗa mata kana yace.
“Eh”.
Cike da tausayawa Malam Ahmad ya janyo hannunta tare da zaunar da ita.
Abba kuwa kallonta yayi cikin tsanananin fargaba da tashin hankali yace.
“Fatima”.
Cikin rawan murya da raunin zuciya tace.
“Na'am Alhj Bashir”.
Cikin sauri Abba ya kalleta wannan shine karo na farko arayuwar sa da yaji ta kira sunan shi kai tsaye.
Jinjina kai tayi Idanunta tsaye akansa tace.
“Eh Alhj Bashir ka faɗa min menene? kafaɗa meke faruwa”.
Rintse idanunsa yayi yana jin kansa na sarawa Araunane yace.
“Fatima Jameelun mu”.
Kai ta gyaɗa kana tace.
“Eh nasani akan Jameelu ne to Menene ya faru?”.
Kasa cewa komai Abba yayi kawai sai ya fashe da matsanancin kuka yayin da hawaye ke bin kuncinsa Shar-shar-shar.
Cikin raunin murya yace.
“Fatima ga Gawar Jameelun mu”.
Atake maganar ya daki dodon kunnenta kana ya ratsa ƙwaƙwalwar ta zuwa zuciyarta saurin kallon Abba tayi tare da sakin Murmushi kana ta juya tare da kallon su Hajiya Karima dake kuka cikin wata dakakkiyar murya mai cike da ƙuna tace.
“Toh kukan me kukeyi!?,
Juyawa tayi tare da kallon Abban M Jameel kana tace.
“Har kaima kuka kakeyi!?Haba Alhj Bashir Addu'a ya kamata ka masa amma ba kuka ba!, Su mata suyi kuka kaina kayi Yanzu ina yake?”.
Cikin sheshsheƙan Kuka Abba ya nuna mata kwalin da ya tsarsa kana yace.
“Gashi can”.
Saurin Kallon wajen tayi Zuciyarta na bugawa da masifar ƙarfi still Muryanta adake da wani irin bushewa da hurawar zuciya tace.
“Gawar ne kuma acikin kwali”.
Cikin wata raunan'niyar murya ya Girgiza kai kana yace.
“Kiyi haƙuri kiyi ta maimaita Addu'a”.
Ajiyar zuciya ta sauƙe tare da rintse Idanunta kana tace.
“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n Hasbunallahu wani'imal wakin La'ilaha Illah anta subhanaka inni kuntu Minal Zhalimin Allahumma Ajirni fii musibati wa'ahlifli khairan minha³”.
Ahankali ta gyara zamanta tare da naɗe ƙafafunta tare da sakin murmushi kana ta fuskanci gabas yayin da Idanunta suka kaɗa sukayi jawur jikinta na wani irin tsuma na tsananin tashin hankali cikin raunin murya tace.
“Ya Allah kaine ka bani Jameelu, kai kasa ya zamemini Garkuwa, ya Allah kajiƙan sa da rahma, ya Allah kasa ya huta Alfarman Annabi da Alkur'ani, Allah kayi mana SAKAYYAH akan dukkan waɗanda suka cutar damu ya Allah kayi mana SAKAYYAH”.
Kusan a haɗe baki daya mutanen falon suka amsa da Ameen.
Wani irin kuka mai tsuma zuciya ne ya kufcewa Asma'u da Bashir musamman Asma'u numfashinta har fisga yake baki ɗaya Falon kaurewa yayi da koke cikin rawan murya Ummi tace.
“Ina gawar yanzu Jameelu na ne haka acikin kwali?”.
Jinjina mata kai Abba yayi tare da cewa.
“Eh shine”.
Still Muryanta adake tace.
“Wani irin mutuwa yayi da har gawarsa zata ƙankace ya zauma acikin kwali”.
Asp dake tsaye ya kalli Ummi cike da tausayawa yace.
“Hajiya kiyi haƙuri ya riga daya bushe, shiyasa ana taɓa shi ya kakkarye!”.
Ahankali ta juya ta kalli Asp kana tace.
“Toh ya akayi kuka tabbatar Jameelu na ne?”.
Cike da tausayawa Asp ya ƙara sa gaban Kwalin kana ya buɗe mata ahankali Ummi ta tsirawa jerarrun gabɓan gawar dake cikin kwalin ido ahankali ta sauƙe Idanunta akan zara-zaran yatsun, hannunsa da suka bushe kana ta tsirawa zoben hannunsa ido.
Cikin wani irin yanayi na ƙunan zuciya da sadaukarwa tace.
“Hmmm!”.
Ahankali Asp ya sake nuna mata takalmin M Jameel dake cikin leda da kuma wayoyinsa cikin sanyin murya yace.
“Ga takalmansa da kuma wayoyinsa duk agabansa muka samu sun ajiye masa da goran ruwa.
Ajiyar zuciya ta sauƙe tare da fesar da numfashi kana tace.
“Tabbas Jameelu na ne”.
Ahankali ta matsa jikin kwalin sosai tare da sanya tafin hannunta ta rufe kana ta sunkuyar da kanta akan kwalin cikin Muryan ta daya fara karaya tace.
“Babana bazan yi maka kuka ba, sannan baza zubar maka da hawaye ba, kana bazan yi maka Ihu da kururuwa ba, amma zan ƙarashe baki ɗaya sauran rayuwata ina maka addu'a, zan ƙare rayuwata da ƙunan rashinka zan ƙare rayuwata babban giɓin rashinka”.
Wani irin tausayinta ya ratsa baki ɗaya jama'ar dake falon ahankali Malam Ahmad da Lamiɗo suka sanya hannu tare da share hawayen da suka saƙƙo musu.
Cike da rauni Ummi ta cigaba da cewa.
“Babana zan ƙare baki ɗaya sauran rayuwata ina maka addu'ar Ubangiji ya karbi shahadarka Allah ya maka SAKAYYAH tun daga nan duniya akan wa anda suka zalince ka har zuwa ranar tashin Alkiyama. Allah Ubangiji yajiƙan ka da rahma Allah ya gafarta maka yasa kahuta”.
Cikin sauri Hajiya Turai ta ƙarasa kusa da ita tare da Rungumeta ajikinta kana cikin Muryan kuka tace.
“Kiyi haƙuri Hajiya Fatima kiyi shiru”.
Kallonta Ummi tayi still Muryanta adake tace.
“Idan banyi haƙuri ba Hajiya Turai ya zanyi. Ubangijin daya ɗauke Jameelu shi yabani shi kuma shi ya ɗauke sa kana ya fini sanin wanene Jameelu agareni, sannan ya fini sanin Jameelu Allah ya masa rahma”.
Ta ida maganar tare da janye Jikinta daga na Hajiya Turai tare da juyawa ta kalli Abba kana tace.
“Ina Moddibo!?”.
Tana gama fadar haka tayi baya tare da sumewa.
Cikin sauri Hajiya Karima ta mike tare da ɗauko ruwa ta yayyafa mata dogon numfashi Ummi taja tare da buɗe Idanunta kana tace.
“Ina Moddibo yake?”.
Cike da tausayawa Abba yace.
“Moddibo yana asibiti asume tunda abin ya faru daya farfaɗo idan ya kira sunan Jameel zai sake sumewa, yanzu ne da aka samu ya farfaɗo aka masa Alluran bacci”.
Araunane tace.
“Ku kaini inga Moddibo sannan kada aje abinne Jameelu abari sai Moddibo ya farfaɗo yaga J ɗinsa na ƙarshe ya tabbatar cewa J dinsa tafi ya barsa bari na har abada, idan yaga haka zai dangana ya sawa ransa haƙuri amma yanzu dan Allah ku kaini wajen Moddibo”.
Abba ne yace.
“Yanzu zaki tafi can?”.
Kai ta gyaɗa tare da cewa.
“Eh ku kaini wajensa”.
Ahankali Malam Ahmad ya miƙe tare da riƙe hannunta suka tafi.
Asma'u da Bashir kuwa kuka suka sake fashewa dashi har muryarsu baya fita saboda tsananin tashin hankali.
Rintse Idanu Abba yayi cike da tausayawa ya kallesu kana yace.
“Ku daina kukan nan kuyi masa addu'a babu abinda Jameelu ke buƙata awajenmu yanzu kamar addu'a.
Acan asibiti kuwa Ummi da Malam Ahmad na isa a reception suka samu Malam Arɗo tsaye ganinsu yasa ya ƙara sa kusa dasu kana yace.
“Maman Jameelu kiyi haƙuri. Ubangiji Allah ya jikansa da rahma Allah ya gafarta masa Ubangiji ya amshi shahadarsa”.
Cikin sanyin murya tace.
“Ameen Malam Arɗo ina Moddibo?”.
Ahankali ya gyara tsayuwar sa kana yace.
“Gashi can yana ciki”.Ya faɗa tare da shiga gaba Ummi da Malam Ahmad na biye dashi.
Suna shiga ɗakin Ummi ta zubawa Moddibo idanu dake kwance plat Fuskarsa tayi fayau duk da bacci yake amma tashin hankali da fargaba ne kwance asaman fuskarsa.
Ahankali ta riƙe hannunsa acikin nata kana tace.
“Moddibo munyi rashi, rashin da baza mu maimaita gurbinsa ba, munyi rashi rashin da har abada ba zamu mance shiba, munyi rashi rashin da saidai namu mutuwar ne zai mantar mana dashi”.
Moddibo kuwa duk da Alluran baccin dake jikinsa hakan bai hana shi jiyo sautin muryan Ummi ba. So yake ya farka domin kunnuwansa na sauraronta haka zalika yana iya motsa gaɓɓansa sai dai koda ya buɗe idanunsa baya ganin komai cikin wani irin yanayi ya damƙe hannun Ummi acikin nasa, yayinda zuciyarsa ke cigaba da bugawa da masifar ƙarfi.
Kallon Malam Ahmad Malam Arɗo yayi kana yace.
“Toh tunda kunzo bari na wuce na faɗawa Kakarsa halin da ake ciki”.
Jinjina kai Malam Ahmad yayi tare da cewa.
“Ya kamata kam aje afaɗa mata sannan itama ataho da ita”.
Kai Malam Arɗo ya gyaɗa kana ya juya ya fita kai tsaye gidan su Moddibo ya nufa yana isa yayi Parking ɗin motarsa kana ya shiga gate din farko ya daga sautin muryarsa tare da yin sallama.
Cikin sauri Innayi ta fito ganinsa yasa ta saki Ajiyar zuciya tare