Showing 66001 words to 69000 words out of 218703 words

Chapter 23 - Sakayyah 2 Hausa Novel Complete

prblm yajaraba mg's bi'iznillah komai zaizama labari bayan jikinku yy fresh zaisa jikinku yy smooth yadinga glowing, gawanda basa San anfani da Mai zaku iya using mg's batare da kunbukaci wani Mai ba🤗nd wanan new soap din💣ne,😯 bama cika Baki kujaraba kugane ma idanku, domin ance gani yakoriji Kuma siyan nagari maida kudi gida
You can check pic👇for the soap reviews🥰
Soap price:4k
maiso ga number's ɗin da zakuyi mgn bani AYSHA ALIYU GARKUWA, zakuyiwa mgn ba, gaban 👇🏻👇🏻👇🏻Ga ta inda zakuyi magana Whatsapp
08062991549
07046881166
07067210195
Call 08064532391
Instagram:glow_with_mgs
Facebook: mg's skincare

Masu bukatar cream Shima munadashi harda ma complete set nagyaranjiki sannan akwai na amare special Wanda inkinyi using baki Kuma bukatar kiyi Wani gyaranjiki domin keda kanki zaki shaida cewa fatar taki ta wanku tarwai😍08062991549

Munatura Kaya kowani gari dayardar Allah Amma delivery is not free

Be part of the glow team😍karkubari abaku lbr👏


Cike da matsanancin mamaki Moddibo ya tsirawa ƙofar da suka rufe ido, toh shin me hakan yake nufi, gwauron numfashi ya fesar yayin da abubuwa da yawa suka riƙa dawowa cikin ƙwaƙwalwarsa, cikin kasala ya jingina bayansa da jikin kujeran kana ya buɗe manyan idanunsa da suka sauya launi.
Ahankali ya shiga ƙarewa tsarin falon kallo, falone mai masifar girma da kyau tun daga farkon falon yake ɗauke da wasu lumtsa-lumtsan kujeru 4couner tun daga farkon Falon har ƙarshesa kujerune zagaye dashi ya kasance kalan Golden ne da ratsin milk kana da ɗigon Coffe ga wasu trust pillow kalan Golden da suka sake ƙawata kyawun kushin ɗin yayin da ƙasan falon ke mamaye da wani lallausan Darduma kalar Golden da ratsin milk kana da ɗigon Coffe daga can saman P.o.p kuwa wasu irin Gloves ne da akayi musu dising na ƙawa da alfarma, yayin da Labulayen suma suka kasance kalan Golden ɗin, daga tsakiyar Falon kuwa wasu stool ne masu azabar kyau guda biyu ɗaya daga farkon falon ɗaya kuma daga ƙarshe kuma jikinsu duk akwai ƴan ƙananan stoll guda huɗu, wanda za'a iya jansu, iya tsaruwa falon ya tsaru kana sai can gefen daga gefe kuma dinning area ne mai ɗauke da dining table shima komai goldie ne, sai daga gefen dama can wata ƙoface dake da ƙawanyar labule, hakama gefen hagu falo ne na al'farmar kai da ka gani kasan babu ƙaranta a cikin lamarin tsarin komai a fili zai nuna maka anci uban kuɗi a Masaarautar daga can tsakiya wani shunfiɗeɗɗen steps ne mai faɗi wanda ake shimfi tattausan Carpet na al'farmar busa alamun akwai wuri na musamman a saman.

Cikin fesar da numfashi ya riƙa juya idanunsa lungu da saƙo na cikin falon, kafin ahankali idanunsa suka sauƙa akan wasu jerin hotuna masu yawa.
Ware idanunsa yayi ganin wani kyakykyawan Matashi mai masifar kama da shi tamkar an tsaga kara babu abinda ya raba sa dashi yana cikin shiga ta al'farmar dake nuni da rainon masarautar ce.
A hankali kuma ya dire idanunsa bisa hoton dake gefen.
Wannan mutumin daya gani a fada ne amatsayin Sarki sai kuma wata kyakykyawa mata mai matsakaicin shekaru.
Zazzafan Ajiyar zuciya ya sauƙe tare da maida idanunsa dake lumshe kan wasu kyawawan mata su uku biyu daga ciki zasu girmeshi ɗaya daga cikin kuma da alamun itace ƴar auta sai kuma hoton wani Kekkyawan jariri da aka ɗaura saitin cinyar Sarki, sai dai bisa alamu haɗa hoton akayi.
Suna zagaye da iyayen nasu, sai kuma ya maida idanunsa kan hoton dake gaba...
Cikin sauri ya miƙe tsaye murya ɗauke da tsananin mamaki da kaɗuwa gami da al'ajabi ya motsa Pinch lips ɗinsa tare da faɗin.
“Innayi”.
Ganin hoton Innayinsa ɓaro-ɓaro tare dana wannan ahalin duk da kuwa cewa alokacin tana da ƙarancin shekaru bai hanashi ganeta ba, ko dan yasan hoton a wurinta ne, dan tabbas tana da hoton wanda kuma hannunta ke riƙe da jariri fuskarta ɗauke da ƙayataccen murmushi wanda kuma ta sha faɗi mishi shine a hannunta a ranar da anka haifeshi akayi musu hoton.
Yatsunsa biyu na yasa ya murza idanunsa ganin ko mafarki yake.
Cikin bugawar zuciya yace.
“Wannan fa innayi ce ba gizo idanuna kemin ba”.
Cikin tsananin al'ajabi ya furta.
“Ya salam Abun Al'ajabi”.
Kafin ahankali ya ɗaga ƙafafunsa da yaji sunyi masa mugun nauyi ya nufi jikin hoton, yayin da ƙwaƙwalwarsa ke tariyo masa cewa tabbas Innayi nada wannan hoton awajenta.
Da sauri ya dafe kansa tuno kalmarta agaresa da take cewa Kaje sai nazo.
Hannunsa duka biyu ya Sanya tare da dafe kansa lokaci ɗaya abubuwa da yawa suka shiga dawo masa ƙwaƙwalwarsa kama daga abubuwan da yake yawan mafarkinsu, atsawon rayuwarsa wanda tunda ya shigo masarautar nan yake ganinsu ra'anul ayn.
da kuma irin kalaman da Innayi ke masa wasu lokuta kana da tsananin kamanninsa da yaron dake jikin hoton da kuma Sarki wanda Babu bancin dake tsakaninsu wanda zai iya nuna cewa ba mutum ba ɗaya bane, sai dai shekarun da Sarkin yake dashi wanda shi kuma nashi basu kai haka ba kana hatta ƴan matan dake zagaye da hoton suna tsakanin kama dashi.

Zazzafan Ajiyar zuciya ya sauƙe akaro na barkatai kana ya tsirawa farcen hannun mutanen dake jikin hoton idanu wanda baiyi fari tasss ba yayi kalan ruwan ƙasa-ƙasa wanda haka shima nashi yake.
Kansa ne ya shiga juyawa cikin tsananin tarin mmki a zuciya yashiga jada baya yana tafiya da baya da baya har ya isa jikin kujeran da aka ajiyesa da farko kana ya runtse idanunsa kansa ya dafe da hannunsa na dama ya fara tunani.
“Shin me yake faruwa dani? Me hakan yake nufi? Ina ne nan? Toh menene haɗina dasu? Meyesa suka kawoni nan suka rufe ni? Meye nufinsu? Shin ko dai mafarkaina gsky ne?.”
Tambayoyin da yake yiwa kansa kenan.
Cikin sauri ya janye hannunsa dake kansa ya shiga laluma aljihunsa da niyyar ciro wayarsa dan ya kira Innayi. sai yaji wayam iska ya furzar mai zafi tuno cewa ya barsu acikin amota...

Acan cikin gida kuwa wani hamshaƙin falone me masifar kyau da tsari wanda yaji komai na more rayuwa daga can tsakiyar falon kuwa wata kyakykyawar Matace wacce take cikin hoton da Moddibo ya gani Hakimce akan wata kujera ta alfarma.
Yayinda ƴaƴanta ke zagaye da ita a hoton, sunlma suna gefenta sai dai Ba Ibrahim kana babu Rahma, bisa alamu hira suke cike da shaƙuwa.
Cikin nutsuwa Dr Jameel suka kutsa kai cikin falon da sauri yaron da Dr Jameel ke riƙe da hannunsa ya janye kana ya nufi gaban matar tare da riƙo hannunta da cewa.
“Didi kin san wani abu kuwa".
Cikin kula da so irin na kakannin a kan jikokinsu ta girgiza mishi kai tare da cewa.
“Toh Sarkin fada, me ka gano kuma, dan na lura in kunzo dai kana son zaman fada”.
Da sauri ya zauna gefenta tare da cewa.
“Didi wlh yanzu na ga wani mai kama da Uncle Ibrahim sai kingani kamarsa ɗaya da Uncle Ibrahim.
Sai dai shi yafi Uncle Ibrahim tsawo da kyau amma Didi babu abinda ya raba su da ace Uncle Ibrahim zai ɓata toh wlh wannan za'a ɗauka ya maye gurbinsa”.
Cikin sauri da bugawar zuciya. Didi ta kalli Dr Jameel kana tace.
“Jameel waye shi?Akan wayake Hakim ke magana?”.
Ajiyar zuciya Dr Jameel ya sauƙe tare da zama akan Lallausan Darduman dake malale ƙasan tiles ɗin kana yace.
“Kai Didi gsky nima abin nan yaban mamaki.
Didi yau tsawon kwana huɗu kenan yake bibiyata bansan shiba amma tun ranan farko dana fara ganinsa yana min kama da wani sai dai na rasa da waye yake min kama ina ta tunani na rasa ganowa sabida gaba ɗaya lamarin shi ɗauremin kai yadda yake ta nuna ya sanni”.
Sai kuma ya ɗan fesar da numfashi tare da gyara zamansa kana ya cigaba da cewa.
“Na rasa dawa yake min kama baki ɗaya abin ya kwanta min akaina, sai yau da muka zo nan naga na kalli Fuskar Abualeey, sai na ga suna tsananin kama, sai kuma na tuni Ibraahim ashe dasu yake min kama kai kamanninsu da Ibraahim ya ƙazanta Didi shin wanene shi”.
Cikin wani irin yanayi na tsananin al'ajabi da tsuman zuciya. Didi ke sauraransa yayin da ƴaƴanta Lalla Khadijah, da kuma Lalla Hafsat mahaifiyar Hakim wacce take aure a Mexico wanda zuwan kakansu Sheiyk Jabeer Nuruddeen Gwadabe Joɗa, ne yasa su zuwa dan ganawa da kakansu.
Ido suka tsira Dr Jameel cikin son fahimtar wani abu.
kana hadiman Didi kuwa dake can gefe sunkuyar da kansu sukayi

Dr Jameel kuwa ahankali ya cigaba da faɗin.
“Sannan kuma ashe ban sani ba yana bibiyata, har muka shigo gidan nan”.
Nan ya kwashe komai tun daga haɗuwarsa da Moddibo har zuwa yau ya sanar mata...
Kana ya ɗaura da cewa.
“Sannan kuma Didi ɗazun da Abualeey ya kirani kan inzo in duba jikin Rahma ciwon cikinta ya tashi. Ashe ban sani ba yana biye dani sannan kuma shigowar da zamuyi *Rinƙas* ya ƙwace ya shigo cikin Masarauta Didi.
zakisha mamaki idan kika ga yanda yake sarrafa Dokin nan”.
Lokaci ɗaya Lalla Khadijah da Kalla Hafsat suka kalli juna, kana suka juyo cike da mmki suka kalli Didi.
Da bugun zuciyar ta ya sake nunkuwa fiye da kaso tamanin cikin ɗari.
Cikin fesar da numfashi ya cigaba da cewa.
“Kuma kinfi kowa sanin mutum biyu ne ke kaɗai ke iya, sarrafa Rinƙas, ko Ibraahim baya iya zuwa ko kusa dashi.
Amman shifa kai tsaye ya fuskanci dokin. Didi wlh al'amarin mutumin yayi masifar ɗaure min kai fiye da yanda kike zato”.

Didi kuwa tun daga lokacin da Hakim ya faɗa mata yaga mai kama da Ibraahim zuciyarta ke bugawa har zuwa yanzu da Dr Jameel ya dasa ayar mgnar, cikin sauri ta juya ta kalli Lalla Khadija da Hafsat, sai kuma Rahma data fito yanzu ta kwanta gefenta Lalla Hafsat tana damƙe cikinta.
cikin sauri Hafsat da idanunta ke waje ta kalle Didi kana tace.
“Didi”.
Murya cike da sanyi da bugawar zuciya Didi tace.
“Na'am”.
Sai kuma suka shiga kallon juna alamar maganar ta ratsasu.
Dr Jameel kuwa batare daya lura da yanayin da suke ciki ba ya cigaba da cewa.
“Allah Didi kamannin nasu har ya ƙazanta kamanninsa da Ibraahim is too hight har Abualeey da kansa abin ya jijjigasa kin kuwa ga Fada? yana shiga fa sai da kowa ya tashi tsaye”.
Didi kam kallonsa kawai take bako ƙyaftawa shi kuwa Dr Jameel cigaba da cewa.
“Kinga Jabeer bin Jabeer shima sosai yayi mamaki saboda naji yana cewa wai sun haɗu dashi ajirgi, dan sai cewa Abeey yake, Abeey ka ganshi ko babu abinda ya raba shi da Ibraahim kamannin yayi yawa, nacema zan faɗawa Didi kace kar in faɗa mata hankalinta zai tashi, gashi yanzu yazo har inda take Abeey wlh jininmu ne. Haka yake ta faɗa yana can yana ruɗe”.
Cikin sauri da yanayin zabura Didi ta miƙe tare da kallon Jakadiyarta da kanta ke ƙasa kana tace.
“Jakadiya maza je ki duba idan Mai Martaba na nan. Kice Ina son ganinsa cikin gaggawa. In kuwa yanada uzuri a fada, ina fatan ayi min iso”.
Cike da girmamawa Jakadiya ta gyaɗa mata kai kana ta furta.
“Toh”.
Sai kuma ta juya cikin sauri ta juya ta fita Ahankali ta riƙa ratsa tamfatsa-tamfatsan falon har ta isa bakin ƙofar fadan wayam ba kowa alamar duk an watse.
Cikin Sassarfa ta juya ta koma falon domin sanar mata...

Acan ɓangaren Moddibo kuwa jin ana ƙwala kiran sallar Maghriba yasanshi motsa laɓɓansa yashiga bin kiran Sallar kana yayi addu'ar da Manzon Allah (S.A.W)ya koyar sai kuma ya furta.
“Ya Salam, shin Mutanen nan me suke nufi dani, suna nufin ba zanyi Sallah acikin jam'i ba?”.
Ahankali ya juya idanunsa akan wannan Corridor dake gefen damansa cikin nutsuwa yabi hanyar yayi tafiya mai ɗan tsayi ya hango wasu ƙofofi guda biyu gefen hagu da dama ahankali ya murɗa ƙofar dake gefen dama.
“Ya Salam”.
Ya furta asaman laɓɓansa ganin wani tsarerren falo ahankali ya taka ya shiga ciki.
Sai kuma ya ɗan jujjuya kai, ƙofar dake kusa dashi ya nufa.
Wanda bedroom ne a hankali ya murɗa ya shiga.
Ƙofar bathroom ya sake murɗa yashiga, alwala kana ya fitowa.
Jujjuya ya kai yayi cikin sa'a yaga darduma a shimfiɗe a wata ƴar kusurwa awajen alamar ana sallah awajen anutse yayi sallar Maghriba awajen kana ya cigaba da addu'oi har aka kira Isha'i, bayan ya idar ya fito falon farko da aka fara ajiyesa.
Yana isa Idanunsa suka sauƙa akan dining da aka jera abinci kala-kala sai kuma ya juya kanshi hanyar shigowa nan yaga wasu hadimai guda uku maza suna tsaye.
Ganinsa yasa sukayi saurin sunkuyar da kansu ƙasa kana suka ɗaura hannunsu aƙirji alamar Barka da fitowa.
Cike da girmamawa ɗaya daga cikin su yace.
“Ranka ya daɗe ga abinci”.
Numfashi ya fesar kana ya tsira musu ido na second biyu tare da cewa.
“Shin meyesa aka tsareni anan?”.
Cike da ladabi da kuma Mutuntawa suke sake sunkuyar da kansu ɗaya daga cikinsu yace.
“Kayi haƙuri Ranka ya daɗe Umarni ne daga mai martaba yace kada mu bari a buɗe maka ƙofa dukkan abinda kake buƙata akwai shi anan basai ka fita ba”.
Cike da mmki ya kallesa kana ya lumshe idanunsa tare da fesar da iska mai zafi yace.
“Akan me za'a rufeni a hanani fita bayan ina da abubuwanyi”.
Cike da ladabi Hadimin ya sake sunkuyar da kansa wanda da alama shine babban su kana yace.
“Kayi haƙuri In Sha Allah Mai martaba yana nan zai zo wajenka”.
Batare daya sake furta komai ba ya koma ya zauna akan kujeran.
Allah ya sani shi yama rasa shin wani irin tunani zaiyi abu ɗaya dai yana jin wata nitsuwa ta musamman a jikinshi da zuciyarsa.
Anutse Hadimin ya sake biyo sa tare da cewa.
“Bismillah ka matso ga abinci”.
Kai ya girgiza duk da kuwa yunwa da yake ji amma yanayin da yake ciki bazai iya bari yaci abinci ba.
Ganin haka yasa ɗaya daga cikin hadiman ya nufi jikin Frigde kana ya kawo masa Fruits tare da ajiyewa akan stool agabansa.
Sanyayyar iska ya fesar daga bakinsa kasancewar sa mai son ƴaƴan itatuwa yasa ya miƙa hannu ya ɗauki apple ya ɗan fara ci ahankali...
Yayin da hadiman suka koma baya suka ci-gaba da tsayuwar anutse ya ɗago manyan idanunsa dake lumshe ya kallesu kana yace.
“Ku zauna mana”.
Murmushi sukayi tare da faɗin.
“A'a yallaɓai babu matsala kada ka damu wannan ai aikin mune”.
Da mamaki yake kallonsu kana yashiga tunanin wannan al'amarin ya yake.
Yana zaune yaga wani Hadimin ya turo ƙofa ya shigo yayin da wasu hadimai uku mata ke biye dashi hannunsu riƙe da manya-manyan Trolley suna shiga suka gaishesa cike da girmamawa kana suka nufi bedroom ɗin suka buɗe Weldrop suka shirya masa kayan kana suka fito Hadimai matan suka tafi suka bar namijin.
Shi kuwa namijin cike da ladabi ya durƙusa gabansa tare da faɗin.
“Mai martaba yace ayi maka sannu da zuwa, sannan yace afaɗa maka ka kwantar da hankalin ka ka shiga kayi wanka ga kaya an kawo maka ka huta zuwa anjima zai zo kugana”.
Tunda ya fara magana Moddibo ke kallonsa jin ya dasa aya yasa shi faɗin.
“Ina buƙatar wayoyina suna cikin mota akawo min ko kuma suzo muyi duk maganar da zamuyi zan tafi ina da abubuwan yi”.
Cike da girmamawa Hadimin ya furta.
“Kayi haƙuri In Sha Allah zan isar masa da saƙonka”.
Kana ya miƙe ya fita...

Acan cikin gida Side ɗin mai Martaba kuwa Didi ce ke tafiya cikin sasarfa yayin da hadimai biyu ke biye da ita hannu ta sanya ta buɗe ƙofar falon yayin dasu kuma suka tsaya daga gefe.
Cikin Sassarfa ta ƙarasa shiga cikin falon Idanunta suka sauƙa akan Mahaifinta Sheikh Jabeer, Mijinta Sarki Youssef Muhammad Mouley, Waziri, Jakadiyar Sarki, Galadima cikin sauri da girmamawa Jakadiyar Sarki ta miƙa mata hannu alamar tazo ta zauna
Kai ta gyaɗa kana ta zauna tare da kallon Mahaifinta wato Sheiykh Jabeer cikin sanyi da yanayin damuwa ta furta.
“Abiey meke faruwa? Me nakeji? Kufahimtar dani na kasa fahimtar abinda Dr Jameel da Hakim ke faɗa min shin gaskiya ne”.
Cikin sauri Jabeer bin Jabeer ya matsa kusa da ita tare da riƙe hannunta cikin ƙauna da shaƙuwa ta Yah da ƙani yace.
“Didi ina ji ajikina ɗankine kuma tsatsonkine, ina ji ajikina wannan mutumin dana gani ɗankine wallahi domin babu abinda ya raba shi da Ibraahim kamanninsa da Ibraahim da kuma Mahaifinsa har ya ƙazanta.
Didi dai-dai da faratunsa irin na ƴaƴan kine”...

Aƙage ta matse hannunsa dake cikin nata kana idanunta cike da ruwan hawaye tace.
“Toh waye shi? A ina yake? kununa min shi?, dan Allah kuyi gaggawan kaini garesa domin idanuwa sun ƙagu suyi tozali dashi haka zalika kunnuwana su ƙagu suji sautin Muryansa”.
Gyaran murya da Sheiykh Jabeer yayi yasa ta dawo cikin nutsuwarta cike da kamala da tarin nutsuwa ya furta.
“Fatima ki nutsu mana, ai komai yazo da sauƙi Bi'iznillahi ta'ala ɗan da muka rasa tsawon shekaru, in Sha Allahu yazo garemu nima kaina na gamsu wannan ɗankine tsatsonkine”.
Numfashi mai martaba ya fesar tare da muskutawa kana ya furta.
“Nima inaji ajika babu haufi babu shakka ko tsoro wannan ɗana ne jini nane Abeey yaron nan Aliyu nane babu haufi jikina da jinina da zuciyata sun shaida min”.
Sai kuma ya maida kallonsa kan Sheykh Jabeer kana yace.
“Tabbas wannan al'amari ya girmama sai dai kuma yanzu saboda idon Fada da kuma yadda al'amarin yaja hankalin mutane yana buƙatar sirri”.
Kai Jabeer bin Jabeer ya jinjina tare da sake tuno kamannin Moddibo da kuma Ibraahim Sarki Youseep Muhammad Mouleey kuwa numfashi ya fesar kana ya cigaba da faɗin.
“Ga kuma yanda ya shigo ya iya sarrafa *Rinƙas* yaja hankalin mutane gaba ɗaya sannan kuma muna buƙatar tabbatarwa da shi kan al'adun masarautar da sanar dashi dukkan abinda ya dace, dan haka sai zuwa tsakiyar dare yanda hankalin mutane duk ya kau zamu shiga wajensa dan bincike da tabbatar wa”.
Kai suka jinjina cike da gamsuwa da kalamansa sai kuma ya maida idanunsa kan Sheykh Jabeer tare da faɗin.
“Abeey Wallahi wannan yaron ɗanane babu ma wani batun tabbarwa inaji ajikina ɗanane tsatsonane ɗanane da muka rasa tsawon lokaci”.
Cikin fesar da numfashi Sheikh Jabeer yace.
“Ka kwantar hankalinka Youseep na sani amma akwai buƙatar bincike akwai buƙatar mu san wani abu”.
Kai ya jinjina kana yace.
“Toh shikenan”. Kasancewar Sheykh Jabeer abokin Mahaifinsa Muhammad Mouley ne yasa baya iya yi masa musu.
Galadima da tunda aka fara magana bai ce komai ba, sai yanzu ya fesar da numfashi kana yace.
“Tabbas nima inaji ajikina wannan tsatson mune saboda inba haka ba bai isa ya sarrafa *Rinƙas* ba sannan kamannin nan yayi yawa kana ku kalli yanda yake bin taswiran gidan nan tamkar yasan wuraren, wannan yasa nakeda tabbacin da wuya

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login