Showing 45001 words to 48000 words out of 218703 words
Lamiɗo yayi cikin yanayin dattako da kamalarsa yace.
“Eyyy sosai ma ai ba'a bori da sanyin jiki”.
Abba dake tsaye jikin mota yace.
“Aikam dai ba'a Bori da sanyin jiki”.
Baffa Garga da fitowarsa daga masallaci kenan yace.
“A masha Allah harda Alh Usman mai Dala ne a Lallai sannun ku da zuwa maraba maraba ku karaso?”.
Ya faɗa tare da shigewa gaba kasancewar yanzu shine ƙarami tun bayan rasuwar Baffa Umaru yana shiga ciki yace.
“Addah Hajja abamu taburmai munyi baƙi”.
Miƙewa tayi daga zaune da take da murmushi afuskarta ta ɗauko taburmai ta miƙa masa karɓa yayi kana ya shimfiɗa musu Abaranda.
Daga ciki tace.
“Aaa baƙi mukayi sannunku da zuwa sannunku”.
Tana ƙoƙarin fita Khausar da Mommy Kuma na kokarin shiga Atake fara'ar dake fuskarta ya gushe Harara ta watsawa Khausar sai kuma ta maida kallonta kan Mommy tace.
“A Aysha kune atafe?”.
Kai Mommy ta gyaɗa kana tace.
“Eh”.
Sannan suka shiga cikin dakin mazan kuma Baffa Garga ya shimfida musu taburmai daga waje.
Koma ciki Hajja Nana tayi tare da ɗaukan ƙwaryar nono da ƙorron soyayyan Zabbi da aka yiwa Baffa Jimeta na zuwansa ta kalli Khausar dake gefen Mommy zaune haɗe fuska tayi babu walwala atare da ita tace.
“Toh fitsararriya uwar fitsararru zoki kai musu abin taɓawa kin zauna kina zare ido sai kace wata ta Allah rasa kunya ɓerar tanka”.
Uffan khausar bata ce mata ba ta miƙe ta ɗauki Ƙorran ta fita ta kai musu sannan ta dawo wani ƙorron Hajja Nana ta miƙa wa Mommy kana tace.
“Aysha Bismillah”.
Kallon yanda tayi kicin-kicin da fuska Khausar tayi taɓe baki tayi cikin tsira mata ido tace.
“Hajja Nana Ni kar inci ne?”.
Harara ta watsa mata kana tace.
“Duk yanda kika ga dama kiyi”.
Ware ido Khausar tayi ta kalli Hajja Nana data kawar da kai gefe murmushi tayi cikin sanyin Murya tace.
“A'a Idan kada inci sai inbar miki kayanki”.
Baki Hajja Nana ta taɓe kana tace.
“Oho cikin ko nawa fitsararriya Mara kunya mai ido atsakar ka”.
Fuska Khausar ta ɓata ta buɗe baki da niyyar magana Mommy tayi saurin ɗaga mata hannu alamar kada tace komai hakan yasa ta tsuke bakinta Mommy kuwa kindirmon ta ɗaga ta burga kana tasa sugar.
Daga waje Lamiɗo yace.
“Khausar fito mana ki burga mana Nonon”.
Kai Baffa Garga ya Girgiza kana yace.
“Ba matsala bari na burga muku”.
Murmushi Lamiɗo yayi kana yace.
“A'a bari dai ita ɗin tazo ta burga mana”.
Miƙewa Khausar tayi tare da ɗaukan goran zuwa ta fita ta burga musu Nonon kana ta zuba musu zumar sannan ta miƙe ta koma ɗaki bayan sun gama taɓe taɓe an sake gaisawa Lamiɗo ya kalli Baffa Jimeta cikin sassauta murya yace.
“Toh Alh Muhammadu Hausawa sunce maso ɗan tsun-tsu shike binsa da jifa, mun zo wajenku neman yafiya, afuwa da kuma alfarma sannan da neman iri domin nima ina cikin ƴan neman Auren ne”.
Cikin sauri Baffa Jimeta yayi dariya kana ya girgiza kai tare da kallon Lamiɗo yace.
“Haba Lamiɗo ba zamuyi haka da kaiba ai kai mai bada Auren Khausar ne baka cikin masu neman aure kana cikin masu bada Auren Khausar ne”.
Murmushi Lamiɗo yayi cike da jin daɗin karancinsu yace.
“Nagode da karamci”.
Gyara zama Baffa Jimeta yayi da murmushi afuskarsa yace.
“Ka cancanci fiye da hakan Lamiɗo”.
Jinjina kai Baffa Liman yayi cike da kamala yace.
“Ai mu saidai muyi addu'a da fatan alkhairi amma kaine mai bada Khausar”.
Cikin jin dadi yace.
“Nagode da kawaici Allah yasaka da alkhairi”.
Gyara zama Malam Arɗo yayi da murmushi afuskarsa yace.
“Toh mu mun yarda mun amince mune masu neman Aure”.
Abba dake Kallonsu ya faɗaɗa Murmushin fuskarsa kana yace.
“Mune masu neman aure da kuma neman iri agareku bisa cika wasiyyar da ɗana ya bari ina fatan zan samu sauki da haɗin kanku wajen cikawa ɗana burinsa koda bayan ransa kamar yanda ya faɗa min”.
Ya ida maganar cikin rauni idanunsa na tara ƙwalla.
Ajiyar zuciya Baffa Jimeta ya sauke cike da tausayawa yace.
“Bakomai Alh Bashir Insha Allah babu abinda zai gagara aida mu daku duk mun zama ɗaya Lamiɗo yamin bayanin duk abinda ke tafiya kan cewa wasiyya ce daga wajen danƙa marigayi Jameelu”.
Ahankali Abba ya sunkuyar da kansa hawaye na cigaba da taruwa akwarmin Idanunsa.
Cikin sanyi Baffa Jimeta ya cigaba da cewa.
“Insha Allah bazai gagara ba zamuyi ƙoƙari amma yanzu kuyi haƙuri da al'amarin tsohuwa in Allah ya yarda babu abinda zai gagara”.
Ajiyar zuciya Lamiɗo ya sauke tare da gyara zamansa yace.
“Allah Ubangiji yasa haka mukam ma da gwaɓin mu muka zo duk da cewa akwai tsoro atare damu amma muna da kyakkyawan yaƙini akanku hakan yasa kafin muzo muka taho da gishiri da goro na neman izini”.
Murmushi Malam Liman yayi yana kallon Lamiɗo yace.
“Lallai kuwa zamu barku da Hajja Nana ku fafata”.
Zare da ido Lamiɗo yayi tare da sanya dariya kana cikin sauri yace.
“Na tuba ayimin afuwa ai Hajja Nana saiku zakuji da ita”.
Gyara zama Malam Liman yayi cike da nutsuwa yace.
“Insha Allah itama munyi ƙoƙari mun samu ta ɗan sauko amma duk da haka akwai karin ɗan lokaci da za'a bayar”.
Anutse Mommy ta gyara zamanta tare da kallon Hajja Nana cikin sanyin murya tace.
“Dan Allah Hajja Nana kiyi haƙuri abinda ya kawo mu nazo ne in baki haƙuri naga kin tafi ranki aɓace abinda Khausar ta aikata ba laifi na bane ba kuma da yawuna bane”.
Ta ida maganar Muryanta na rawa tamkar zata fashe da kuka.
Hajja Nana kuwa jin yanda Muryan Mommy ke rawa yasa tayi saurin Kallonta har ranta take Jin Mommy domin alokacin zamansu tasan bata da matsala cike da kulawa tace.
“Kar kiyi kuka Aysha aina zauna dake nasan halinki fitsaran Khausar ba daga gareki bane kuma ba daga Allah bane halitta ce da tayiwa kanta”.
Cikin sauri Khausar ta ɗago kanta ta watsa mata Harara cikin ƙasa da murya tace.
“Inma tsiwarce ai awajenki na gada”.
Harara Mommy ta watsa mata hakan yasa ta tsuke bakinta.
Ahankali Mommy ta sauƙe Ajiyar zuciya kana ta fuskanci Hajja Nana cikin sassauta murya tace.
“Itama kanta Khausar al'amarin yazo mata adolene”.
Baki Hajja Nana ta taɓe kana tace.
“Bangane yazo mata adole ba inace soyayya take da wani can yasa ta kalli tsabar idona tace bata son ɗan Uwanta”.
Kai Mommy ta Girgiza kana ta kwashe duk yanda Khausar ta faɗa mata sunyi da M Jameel aranan da aka sace sa kana ta daura da faɗin.
“Sannan kuma yaron shine ƴan Kidnapping suka sace sa suka ɗauresa har ya rasu”.
Ahankali Khausar tayi ƙasa da kanta hawaye na taruwa akwarmin Idanunta.
Cikin sanyi Mommy ta cigaba da cewa.
“Sai maganar tasa ta zama kamar wasiyya kuma ya roƙi alfarma ya faɗawa kakar Amininsa Moddibo kana Ya faɗawa mahaifiyarsa da mahaifinsa yanzu ma haka da mahaifinsa muka zo kuma yace alfarma yake nema ko bayan ransa acika masa wannan burin nasa, jin haka yasa nima baki ɗaya jikina yayi sanyi”.
Numfashi Hajja Nana ta fesar kana tayi ƙasa da kanta cikin sanyin murya tace.
“Allah sarki shine akace ansace sa a daure sa ya rasu ko?”.
Asanyaye Mommy ta gyaɗa mata kai tare da faɗin.
“Eh shine aka sace aka ɗaure har ya rasu”.
Jinjina kai Hajja Nana tayi tare da watsawa Khausar Harara ta kalli Mommy cikin raunin murya tace.
“Ayyah Allah sarki Allah yajiƙan sa da rahma ina ma ace yana raye dashi zan bawa Khausar ya aura wallahi koda Khausar bata auri Aliyu ba bazan damu ba”.
Cikin raunin murya Mommy tace.
“Gashi kuma shi ɗin Ubangiji bai nufa za ayi dashi ba, babu gatan da zamuyi masa sai dai addu'a”.
Jinjina kai Hajja Nana tayi cikin sanyi tace.
“Sosai ma”.
Mommy kuwa sassauta murya tayi kana tayi ƙasa da kanta tace.
“Kuma inda hali mu samu mu cika masa wasiyyar daya bari”.
Gyara zama Hajja Nana tayi tare da kallon Khausar da kanta ke ƙasa kana ta kalli Mommy nunfashi ta fesar cikin sanyin murya tace.
“To aini bani da tacewa acikin wannan maganar sai abinda iyayenta suka faɗa tunda annuna min bani da iko da ita”.
Dai-dai lokacin Baffa Jimeta ya shigo Anutse ya zauna gefenta ya tanƙwashe ƙafafunsa kana ya fuskanceta da kyau yace.
“Kina da iko da ita mana muma kam mu aike kike da iko damu amma ana neman alfarma awajenki gacan Baban yaron ma awaje sai hawaye yake zubarwa yana neman alfarma acikawa dansa wasiyyar sa”.
Daga waje ta jiyo sheshsheƙan Kukan Abba cikin sauri ta miƙe ta nufi ƙofa ta fita kusa dashi ta zauna cike da tausayawa tace.
“Kuka kuma kake Alh Bashir?”.
Cikin sheshsheƙa Abba yace.
“Ya za ayi ba zanyi kuka ba burin da Jameeluna da kuma fatan da yake so yana tangarɗa koda aranan da muka rabu na ƙarshe yace min shine babban burinsa daya rage aduniya”.
Cikin zubda hawaye ya cigaba da cewa.
“Yace babban burinsa yaga Moddibo yayi Aure kafin nasa Saboda Aliyu yana buƙatar mace yana buƙatar ayi masa Aure sai dai Allah bai nufa Jameelu na zai gani ba ina tsoro saboda bani da damar da zan cika masa wasiyarsa”.
Gyara zama Hajja Nana tayi kana ta gyara ɗaurin dankwalinta ta sunkuyar da kanta ƙasa kana ahankali ta ɗago Muryanta na rawa tace.
“Na amince ina dai dan nice. To acikawa yaron nan burinsa Allah yajiƙan sa da rahama na amince Ayi aure...
Littafin SAKAYYAH na kuɗine ƴar uwa ki biya ki karanta cikin Aminci da salama 1k ne kacal 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP NUMBER'N 09097853276.
By
*GARKUWAR FULANI**SAKAYYAH book 2... page 9*
Na
*Aysha Aliyu Garkuwa*
Alamomin infection sune kamar haka. Rashin sha'awa. Ƙaiƙayin gaba Kiji idan ya fara miki ƙaiƙayi kamar zakiyi hauka. Warin ko ƙarnin wurin. Fitar farin Ruwa mai fatsi-fatsi. Ƙurajen su ɗan fetso ƙananan ko ƴan manya, melewar fatar wurin, Tusan gaba. Bushewar gaba, Rashin ni'ima. Buɗewar gaba, domin har budurwa infection na iya buɗata. Ciwon mara ko ciki mai tsanani yayi al'ada, rashin haihuwa, domin har baƙin mahaifa take toshewa. Ko kirinƙajin wani abu na miki yawo ƙasan mara, ko jin zafi yayin yin fitsari, da kuma saduwa, da dai sauran abubudann ban lissafa. Sune manyan alamomin infection.
Shin kin kuwa san illar da infection keyi miki, amman kinajin ɗaya daga cikin alamominta kinyi bulum buƙui da ita a jikinki. To bari kiji illolin infection wato cutar sanyi.
Rashin haihuwa, ƙyara da hantara a wurin miji domin muddin kina tare da ita baki da wata daraja a idanu nai, sabida ƙyamas kike ba damshi bare wata ni'ima mai Taste, Kinga kenan shinfida ta lalace, in kuwa shinfiɗa ta lalace dole kiga sauyin fuska, domin su maza dole sunason wurin da kwatanta Zaki kasance baki da wani daɗi da ɗumin da mai gida ke buƙata. Kinga duk tsabtarki da kyanki da iya girkinki shinfidarki ta zama lami. Kiyiwa Allah ki nemawa kanki lafiya ki samawa mijinki da ke kanki nitsuwa.
KADA KUJI IYA WANNAN DOMIN AKWAI MUGUN INFECTION WANDA BAYA BAYYANA KANSA. Wanda kawai sai dai kijiki, kamar kwalta kin bushe ƙyamas ya dauke miki dukkan sinadaran ni'imomin ki, da sha'awarki, duk kayan matan da zakisha a wofi zadai kiji ƴan uwa da abokan arziƙi da ƙawayenki na yaba miki magunguna GARKUWAR MA'AURATA, amman ke in kinsha jiya I yau, duk nacin oga da yi miki wasannin bazaki ji sha'awa ba, toh wlh muguwar infection ce, wacce bata bayyana kanta har sai ta gama yi miki rugu-rugu. Ta lalata miki zaman aure. Lokacin da zata bayyana sai kiji Doctor's suna kira miki, ovarian cyst, ko kuma fibrod duk a cikin chronic infection ne yar uwa.
INFECTION set ɗinmu na kowa da kowane Mata, Maza, Bazawara, Budurwa, Maijego, Yara, Ke yar uwa Wlh har maiciki zatasha, bashi da matsalar komai na Gargajiya ne mai rakake INFECTION ya fito miki dashi, wlh duk nacin infection koda na cikin mahaifane bi'izinillahi ta'ala zaki rabu dashi, cutar infection cutace mai masifar naci, so yar uwa kana dole ki nace masa da maganin set ɗin na 10k ne kuma maganin kala biyarne nasha da kala uku na tsarki ɗaya na shafawa ɗaya. Yar uwa idan har kin saya to kiyi ƙoƙarin kisha da mijinki, in akwai abokiyar zama, kisa miji ya saya mata, domin ko kin rabu da shin dai ita tana dashi tofa kin kashe macijine baki cire kaiba, ma'ana zai sake dawo miki, idan kuna da yara suma a saya musu, domin tsoron kada ya riƙa a jikinsu musamman ya'ya mata ya buɗa miki ƴa tun tana ƙaramarta, ki aurar da ita miji na muku kallon lalatattun iyaye da baku iya bada tarbiyaba. Saboda yamayin garin yasa ina raba rabin set ɗin in sa miki komai rabi-rabi 5k amman set ɗin 10k ne. Idan kin san a shirye kike ga account number na nan 0005388578 Jaiz bank AISHA ALIYU GARKUWA, ki turo kuɗinki kafin kiyi min mgn ta WHATSAPP NUMBER'N na 09097853276 sai ki turo min shaidar biyanki, domin akwaishi Available ko yau kika tura kuɗinki, gobe kayanki zai taho, ina bada sari ko sayan ɗaɗɗaya. Farashin Sari da sauƙi daga kan mutum 3 ko 6 ko 12. Kai ko na mutum 24 kikeso in Sha Allah zaki samu. Please dan Allah in dai kinsan baki shirya sayaba kada kimin mgn ki bari sai kin shirya. Taku ce dai GARKUWAR MA'AURATA.
Shiru Hajja Nana tayi kafin ahankali ta ɗago ta kallesu ɗaya bayan ɗaya tace.
“Shikenan ni babu abinda zance acikin wannan al'amari zira ido da kunne nawa duk abinda yaje ya dawo Khausar ita tajawa kanta”.
Ƙwaffa tayi kana ta cigaba da cewa.
“Tunda kuma iyayenta kuce kun amince, to ni dai babu abinda zance bare inyi baƙin jini”.
Kallon Baffa Jimeta daya sunkuyar da kai ƙasa tayi taɓe baki tayi kana tace.
“Yo ni me zai da meni tunda uban daya haifi Aliyu bai damuba yanuna ayi mata yanda take so ai shikenan, tunda bata illar tsintacciyar mage bata mage ba, ɗan da ba'asan Asalinsa ba ba'a san tushensa ba duk abinda ya faru ita tajawa kanta”.
Anutse Lamiɗo ya ɗago kansa ya kalli Hajja Nana cikin sauri yace.
“Insha Allahu ma babu abinda zai faru sai Al'khairi”.
Abba kuwa karɓan maganar yayi ta hanyar cewa.
“Insha Allah Moddibo zai riƙe ta da amana da gaskiya da Izinin Ubangiji Khausar ba zata tozarta ba yanda Khausar ta amince tayi niyyar cikawa Jameelu na wasiyyar sa”.
Ahankali Khausar dake can cikin ɗaki ta lumshe Idanunta zuciyarta na bugawa da Masifaffen ƙarfi.
Cikin sanyin murya Abba ya cigaba da cewa.
“Insha Allahu Ubangiji bazai tozarta taba Allah zai cika mata burikanta na rayuwa insha Allah zata kasance cikin kwanciyar hankali da nutsuwa”.
Kallonsa Hajja Nana tayi kana ta jinjina kai tace.
“Haka kake gani kk? Hmm ta yaro kyau take bata ƙarko, kai yanzu Alh Bashir tunda kuke kasan asalin yaron ne?”.
Ahankali Abba ya sunkuyar da kansa ƙasa batare da yace Uffan ba.
Ƙwaffa tayi kana tace.
“Hmm ka buɗe baki kai tsaye kace baka sani ba shine magana”.
Kallonta ta mayar kan Malam Arɗo tace.
“Malam kai da suke aiki a ƙarƙashin ka kasan Asalinsa?, kasan waye Ubansa? Kasan inane Ƙasar da suka fito kasan inane Jaharsu? kasan menene tushensa? Waye ubansa waye Uwarsa?”.
Ajiyar zuciya Malam Arɗo ya sauƙe kana ya kalleta Anutse yace.
“Ai a al'amarin Aure wannan duka ba magana bane”.
Kai ta girgiza cikin tsira masa ido tace.
“Yanzu ina magana da Malam Liman zai miƙe yace min Allah yace Annabi yace amma ai Aure abin bincike ne ko”.
Cikin sanyin murya Lamiɗo yace.
“Dan Allah Addah Nana kiyi haƙuri wannan tone-tonen basu da Amfani”.
Baki ta taɓe tare da Kallonsa kana tace.
“Eh basu da amfani Ni tunda dai aka samu antsira ba ɗan Mayun bane zata aura, aishikenan sai inzira mata ido ni naɗan ji sauƙi ma akan abin”.
Kallon ƙannenta tayi kana tace.
“Yo ai gaskiya ne na fada da kuka wani tsareni da ido, kuma dole idan gaskiya ta taso a faɗeta da ace ta auri ɗan mayu jikan Mayu ai gwara ɗan shegen tunda taji ta gani tana so ta bone dai tayiwa ƴaƴanta da ahalinta”.
Kai Baffa Liman ya girgiza tare da sunkuyar da kansa ƙasa cike da takaici Hajja Nana ta cigaba da cewa.
“Tunda ta yiwa kanta tabo ita tasani amma Ni dai babu ba kina babu hannu na babu ƙafana na suje can su ƙarata sanda ƴaƴanta zasu ce ina dangin Ubansu ta nemi abin faɗa musu”.
Ahankali Mommy da Lamiɗo suka sunkuyar da kansu ƙasa Khausar kuwa hannunta riƙe da kofin madaran da bata shaba bata ajiye ba ɗumin na ratsa tafin hannunta ta tsirawa waje ɗaya ido ba ƙeftawa.
Ajiyar zuciya Malam Liman ya sauƙe tare da girgiza kai kana cike da ladabi da nutsuwa yace.
“Dan Allah Addah Nana ya za'ayi ana kitse gaba kina warware baya dan Allah wasu furucin ki riƙa sanin abinda zaki riƙa faɗa saboda Manzon Allah (SAW)
_Falyaƙun Khairan Auliyastumu”_.
Baki ta taɓe kana tace.
“Naji naji Liman aini zuwa yanzu ko ƙwaƙwalwar kifi ne dani yaci ace in haddace Hadisai sama da dubu tunda duk motsin da nayi sai kace min ga abinda Allah da Manzonsa suka faɗa”.
Sunkuyar da kai Malam Liman yayi cikin taɓe baki ta cigaba da cewa.
“Ni dai na faɗa ba bakina ba hannu na babu ƙafana kuje duk abinda kuka ga ya dace kuyi. Kai kuma”.
Ta nuna Baffa Jimeta da kansa ke ƙasa kana tace.
“Tunda kaine madadin Uba agareta kace kaji ka gani ko? Sannan kaima”. Ta nuna Lamiɗo daya ɗago kansa cikin haɗe girar sama da na kasa tace.
“Kai kuma kaine wakili kuma Uba data tashi agabansa kai kace kaji ka gani ai shikenan na cire bakina aciki amma dan Usmanu na baya raye bazan bari jinjinsa ya cuta ba”.
Ajiyar zuciya Baffa Jimeta ya sauke kana yace.
“Insha Allahu ma ba zata cutuba da izinin Ubangiji zai riƙe ta da Amana”.
Baki ta taɓe cike da takaici ta juya cikin ɗaki.
Takalli Khausar da har zuwa lokacin hannunta ke riƙe da kofin madaran Harara ta watsa mata kana tace.
“Ke kam kinyi asara gaki mace har Mace Bafulatana tsayayyar mace Kyakkyawa zubin zamani ƙirar masu tsada amma ace wai ke zaki buɗe baki kice kina son Namiji”.
Cikin sauri Khausar ta ɗago kai ta kalleta.
Harara Hajja Nana ta watsa mata kana tace.
“Ki ɗauke wannan tsayayyun idanun naki akaina Ke zakice kina sonsa wanda baisan dake bama sannan baice yana sonki ba bai damu dake ba wai kice kina sonsa shi zaki Aura”.
Fuska Khausar ta ɓata kana ta kawar da kanta gefe tare da murguɗa mata baki