Showing 210001 words to 213000 words out of 218703 words
farin ciki tace.
“Hajja Nana Alhamdulillah anyi Theater ancire ɗa namiji”.
Cikin jin daɗi da sauke ajiyar zuciya Hajja Nana tace.
“Alhamdulillah amma tana lafiya ko?”.
”Eh lafiya lau gata nan ma”.
Cewar Momy na miƙa wa Khausar wayar karɓa Khausar tayi suka gaisa cike da farin ciki Hajja Nana tace.
“Ƴar tsele da zaki kasheni azaune”.
Murmushi Khausar tayi cikin rashin jin karfin jikinta tace.
“Yaushe zaki zo?”.
Fuska ɗauke da farin ciki Hajja Nana tace.
“Kwanan nan in sha Allah kafin ayi suna”.
Murmushi Khausar tayi tare da maida kallonta kan Moddibo da idanunsa ke kan Jaririn tace.
“Ayiwa Hajja Nana shiri in Sha Allahu tana kan hanya zata zo”.
Kai ya gyaɗa mata tare da cewa.
“In sha Allahu”.
Akuma dai-dai lokacin Dija da Yah Aliyu suka shigo Murmushi Khausar tayi tare da cewa.
“Dija”.
Cike da farin ciki Dija tace.
“Na'am Khausar ai mu bamu sani ba Khausar baku faɗa mana ba”.
Still da Murmushi afuskarta tace.
“Kiyi haƙuri Dija gaba ɗaya abin ne yazo min atsorace”.
Dariya Yah Ali yayi tare da faɗin.
“Raguwa gaba ɗaya kin gigice kin gigita bayin Allah”.
Langwaɓar da kai tayi kana tace.
“Hmmm ba dole inji tsoro ba Yah Ali abinda ance wasu da yawa idan an musu kafin afito dasu ta can suke wucewa”.
Murmushi yayi tare da cewa.
“A'a ke kam in Sha Allahu kina nan sai kin kawo wasu ƙannensa goma sha ɗaya sun zama Dozen”.
Idanunta ta zaro tare da faɗin.
“Goma sha ɗaya”.
Baki ɗaya ɗakin suka sanya dariya.
Raudat dake zaune gefen Asma'u ta ƙyalkyale da dariya kana tace.
“Addah khausy idan kika haifi Dozen sai ki bani biyun saman na riƙa kulawa dasu kar suyi Miki yawa ai Yah Moddibo zaku bani ko?”.
Ta ƙare maganar tana kallon Moddibo kai Moddibo ya gyaɗa yana Murmushi.
A ranan haka suka yini suna kula da ita.
Bayan sunyi kwana uku aka sallame ta suka koma gida.
Haka Didi da Momy suka cigaba da kula da ita suna bata kulawa na musamman...
Washe gari da safe Misalin ƙarfe 7:30 Asma'u ta zo zaune ta samu Lalla Khadijah, Rahama, na zaune kan lallausan Darduma Yayin da Didi,Momy,Innayi ke zaune gefe ɗaya Hajja Nana kuwa na gefen Khausar da Moddibo dake riƙe da Jaririn yana masa addu'a kana su kuma suna hira.
Ahankali Asma'u ta ɗago fuskarta ɗauke da Murmushi ta miƙa wa Khausar wayarta tare da cewa.
“Kalli wani special abu dana ajiye Miki wanda nake da yaƙinin sai kinyi min kyauta na musamman”.
Ɗan ware idanu Khausar tayi tana kallon Rahama dake cewa.
“Aikuwa dai Addah Asmeey muma dake gefe muna sa ran samun khauta”.
Dariya Khausar ta sanya kana tace.
“Aikam dai zanso gani”.
Ta ƙare maganar tana playing video
Da sauri ta zaro Idanunta waje ganinta kwance kan gado tana surutai.
Moddibo kuwa wani Amintaccen Murmushi ya saki ganin yanda ta zaro Idanunta waje sai kuma tayi saurin ɗaga kanta cike da kunya jin yanda suka ƙyalƙyale da dariya cikin tura baki ta kalli Asma'u tare da cewa.
“Asma'u Ni ko?,Aikuwa kin ci bashi sai na rama”.
Ta ƙare maganar cike da kunya ganin yanda suke maimaita maganar.
Asma'u kuwa Gwalo Asma'u tayi mata tare da cewa.
“Aikuwa sai dai ki rame yarinya dama can abinda ke Ranki kika faɗa”.
Khausar kuwa juyawa tayi jin Hajja Nana na cewa.
“Yoh ai gaskiya Asma'u ta faɗa ke da wannan mijin naki duk ba kunya ne daku idan ke baki cikin hayyacin ki kika faɗa ai shi yana sane bare keɗin ma kina sane”.
Rau-rau da idanu Khausar tayi ta shiga bubbuga ƙafa daga zaune tace.
“Didi kiji fa abinda Hajja Nana ke faɗa wai bani da kunya”.
Murmushi Didi tayi tare da faɗin.
“Rabu da Hajja Nana am Khausar ɗina kina da kunya sosai ai bada sanin ki kikayi ba”.
Momy kam Murmushi kawai takeyi.
Daidai lokacin Jakadiya ta shigo tare da sanarwa Didi tayi baƙi ƴan Barka.
Miƙewa Didi tayi kana tace.
“Toh ganan zuwa”.
Sai kuma ta kalli Momy dake cewa.
“Mu tafi”.
Atare Didi Momy Innayi,Niyna suka fice.
Kallon Rahamah kalla Khadijah tayi kana tace.
“Rahama muje ki tayani haɗa Alawar Madara da gullisuwa tun jiya naso yi kuma ina zirga-zirga”.
Murmushi Rahama tayi tare da miƙewa Lalla Khadijah kuwa har taje ƙofa ta juya ta kalli kana tace.
“Ƙanwata kema zo muje”.
Kai Asma'u ta gyaɗa tare da miƙewa suka fita.
Falon ya rage daga Khausar, Moddibo sai Hajja Nana da itama ta miƙe ta fita falon.
Cikin shagwaɓa Khausar ta kalli Moddibo tare da narke fuska kana ta tura baki tace.
“Yah Mu'allim”.
Murmushi yayi kana ya kwantar da jaririn ya janyota jikinsa bakinsa ya kai saitin kunnenta yace
“Na'am Minha Viddaaaa ya akayi?”.
Ya ƙarashe yana jan sunan.
Cike da shagwaɓa tace.
“Jifa yanda na saki baki naita faɗan magana gabansu Momy da Didi kuma baka hanani ba”.
Murmushi yayi yana shafa bayanta yace.
“Ya za'a yi in hanaki fallasa min sirrin dake Ranki?,Taya kike tunanin bakina zai iya dakatar da zinaren kalaman da suke fitowa daga bakinki suna ratsa kogon zuciyata?,Kin kuwa san farin ciki da shaukin dana kasance alokacin?”.
Ya fesar da sanyayyan numfashi mai cike da zallan so da shauƙi yace.
“A lokacin ji nake tamkar ina yawo a gajimare ji nake tamkar nafi Mazan duniya Sa'a da samun Nagartacciyan mace irin ki kin nuna min so tun baki san menene so ba shin mai zanyi in biyaki”.
Cikin wani irin yanayi na musamman tace.
“Ka ƙaunaceni ka kuma soni fiye da yanda nake son kaina kada ka haɗa ni da kowa atare da kai idan kayi min haka kaga yimin komai Yah Mu'allim”.
Ahankali ya ɗago kanta tare da ɗaura lips ɗin sa asaman nata yashiga kissing ɗin ta...
Alhamdulillah zuwa yanzu jikinta yayi ƙwari bazama ace Thearter aka mata ba kullum Asma'u da Dija anan suke yini ana I gobe suna Dr Zakariyya, Asiya Hajja Nana, Abban Jameel, Lalla Hafsat suka zo.
Hajja Nana da Innayi ce zaune da Khausar aɗaki yayin da Innayi ta zuba mata abinci ta bata taci Momy kuma na riƙe da jiriri tayi masa wankan Yamma ta saka shi cikin wasu fararen kayan sanyu masu masifar taushi pink and white collar.
Anutse Moddibo ya shigo ya same su Kai tsaye bakin gadon ya wuce gefenta ya zauna.
Kallonsa hajja Nana tayi tare da cewa.
“Wai kai kam baka jin kunya ne?”.
Juyawa yayi ya kalleta kana yace.
“Kin iso da sa ido ko? Idon ki be iya gani bakinki yayi shiru ko?”.
Hararansa tayi tare da faɗin.
“Ba dole ba idan bani nake taka maka birki ba babu mai taka maka birki”.
Kallonta yayi tare da cewa.
“Toh sai kiyi mugani in birkin zai taku”.
Anutse Khausar ta kallesa kana ta kalli Hajja Nana tace.
“Yah Mu'allim rabu da ita”.
Murmushi yayi tare da cewa.
“Aima na rabu da ita?”.
Khausar kuwa nutsuwarta ta tattara kana tace.
“Yah Mu'allim gashi har gobe suna in Allah ya kaimu”.
Kai ya gyaɗa kana yace.
“Eh”.
Ahankali ta langwaɓar da kai tare da cewa.
“Kuma banji ka faɗa min sunan yaron ba”.
Murmushi yayi kana yace.
“Kuma tun a asibiti kafin ayi mishi wanka na masa huɗu ba tun kafin ki farfaɗo”.
Murmushi tayi kana ahankali tace.
“Kuma Yah Mu'allim baka faɗa min ba".
Juyawa yayi ya kalli Asma'u kana ya kalli Asiya dake cewa.
“Ai dai kam bamu san sunan yaro ba gashi har gobe Suna”.
Didi kam ido ta zuba mishi tana kallonsa Momy kuwa sunkuyar da kanta ƙasa tayi tana sawa Jaririn safan hannu tace.
“Toh menene sunan”.
Sunkuyar da kansa ƙasa yayi kana ya motsa laɓɓansa tare da cewa.
“Sunan shi Jameel”.
Cikin tsananin jin daɗi Asma'u ta kallesa tare da cewa.
“Allah sarki Yah Moddibo Ubangiji Allah ya saka da Alkhairi Allah yabar zumunci ayyah Yah Jameel ɗina Allah ya raya shi Allah ya mishi Albarka”.
Murmushi yayi tare da cewa.
“Ameen ya Allah Asma'u, Allah yasa ya biyo halin takwaransa”.
Ya ƙare maganar yana Murmushi.
Innayi ce ta amshi zancen da cewa.
“Naji Ibraahim kuna na kiranshi da *Keyan*”.
Kai Modibbo ya jinjina tare da cewa.
“Eh laƙanin kenan. Amman asalin sunan Jameel, Allah ya raya mana shi yayi nagarta irin ta mai sunanshi”.
Cikin tsananin jin daɗi Asma'u tace.
“Ameen ya hayyu ya ƙayyum ”.
Khausar na Murmushi tace.
“Ameen ya Allah yasa ya biyo halin takwaransa Allah yasa yayi Ilimin takwaransa”.
Cikin jin daɗi Didi tace.
“Ka kyauta Babana Allah Ubangiji ya raya mana Jameelu”.
“Ameen ya hayyu ya ƙayyum ”.
Cikin tuno da Jameel Hajja Nana tace.
“Ameen ya Allah ai Jameelu mutumin kirki ne”.
Asma'u kuwa cikin sauri ta ɗauki waya tare da kiran Ummi Ummi na ɗauka tace.
“Ummi albishir”.
Daga ɗaya ɓangaren Ummu tace.
“Goro”.
Cike da farin ciki Asma'u tace.
“Yah Jameel ya samu takwara”.
Murmushi Ummi tayi tare da faɗin.
“Hmmm Asma'u kenan kece baki sani ba amma ainin tun ranan Aliyu ya faɗa min”
Murmushi Asma'u tayi kana tace.
“Ummi shine baki faɗa min ba ranan muna hira ina cewa Ala'andi wani suna za'a sawa yaron kikayi shiru ashe duk kin sani”.
Murmushi tayi tare da cewa.
“Na sani mana tun ranan ya faɗa min”.
Murmushi Moddibo yayi tare da cewa.
“Ai TOH na rigaki yin albishir ɗin”.
Dariya ta sanya tace.
“Wallahi Yah Moddibo Ina sauri in rigaka ashe ka rigani”.
Haka sukayi yinin ranan anata shirye-shiryen suna, nan washe gari suna akayi raɗin suna da hidindimu kamar yanda al'adan masarauta take.
Bayan sallar la'asar manyan Fada ne a zaune saboda Aranar Abualeey yake son yin Murabus ya barwa Moddibo sarauta.
Bayan an zauna an cika a Fada anyi komai an taru Sarkin Al'adun Fada ne ya juya ya kalli Moddibo dake cikin wani irin shiga na alfarma da kawa da yayi masifar fitar da ainihin kyawunsa da ƙwarjinsa kana yace.
“Alhamdulillah kamar yanda al'adun Fada take sarki yana da dama da iko da zai yi Murabus tun yana da rayuwarsa ya danƙa Mulki a hannun ɗan sa da yake ganin zai iya gadon mulkinsa kana zai iya kula da Masarauta yanda ya kamata dan haka Sarki Youseef Mohammed Aliyu Mouley ma yayi alƙawari zai maida Sarauta ahannun ɗan sa Aleeyu Youseef Mohammed Aliyu Mouley”.
Cikin jin daɗi Manyan cikin Fada da Manyan Masarautu na gefe-gefe wanda baki ɗaya sun san da Maganar an samu sa hannunsu tun watanni hudu da suka wuce kowa cikin jin daɗi da farin ciki yake faɗin Alhamdulillah.
Cike da girmamawa Sarkin Fada ya juya ya kalli Moddibo tare da cigaba da cewa.
“Kuma a wannan ranane za'a ƙara wa Sarki Aleeyu Youseef Mohammed Aliyu Mouley mata kamar yanda atsarin Masarauta sarki bai kasancewa da mace ɗaya sai an masa biyu aranan da za'a danƙa mulki a hannunsa”.
Cikin sauri Moddibo ya ɗaga kansa ya kallesu sai kuma ya saki wani Murmushi dashi kaɗai yasan ma'anar sa juyawa yayi ya kalli Abualeey dake cikin matsanancin farin ciki kana ya kalli Sarkin Fada tare da cewa.
“Ina son magana da mahaifina”.
Kai Sarkin Fada ya gyaɗa kana yace.
“Toh shikenan ba damuwa”.
Kana suka shiga ɗakin Sirri Shida Abualeey, Waziri, Galadima Wambai Garkuwa...
A dai-dai lokacin kuma acikin gida Khausar ce cikin shiga ta alfarma sanye take cikin wani lafiyayyan Abaya Pinch colour mai masifar taushi da santsi da yasha duwatsu kana ta ɗaura Alkyabba ta Masarauta fari ƙall mai masifar taushi wanda al'ada ce ta Masarauta wanda ranan da za'a naɗa mijinka a Masarauta zaka sa.
Shima Jaririn sanye yake cikin shiga na alfarma wasu picnh colour kayane tausasa kana aka daura masa ƙaramin Alkyabba fari irin na jarirai.
Sai hotuna suke ta ɗauka dasu Lalla, Khadijah Lalla, Hafsat Asiya, Asma'u, Dija, Rahama, Raudat Asma'u kuwa kai tsaye take turawa cikin group ɗin su na class mate ɗin su da suka gama makaranta.
Nan da nan cikin group ɗin ya kace me da surutu kala-kala kowa na tofa albarkacin bakinsa wata ƙawarsu wacce lokacin da suke makaranta bencinsu ke kusa da nasu Khausar mai suna Hawwa Idris ne tace.
“Ikon Allah wai Khausar ce haka🤔 girma yazo rawan kai ya gudu?”.
Tayi typing da emotion na mamaki dariya Asma'u ta tura mata tare da cewa.
“Gashi kuwa kinga zahiri”
Cikin Mamaki tayi voice dan gani take typing ɗin bai mata sauri kana tace.
“Masha Allah shiyasa akace arayuwa kada ka taɓa wulakanta mutum domin baka san baiwar da Allah ya mishi ba wai yau Khausar ce matar Sarkin Morocco kuma Malam Moddibo?”.
Hoton dariya Asma'u ta sake tura musu tare da faɗin.
“Aikam ikon Ubangiji yafi gaban haka?”.
Wata mai suna Jidda ce tace.
“Aikuwa dai muma Allah yasamu Adamshin ku Asma'u ku kam kunji daɗin rayuwarku”.
Murmushin Samira Sani ta turo tare da cewa.
“Uhmmm kuma ku godewa Allah a yadda kuke ɗin”.
Da sauri Khadijah Sule tace.
“Sosai ma kam Samira am”.
Amin kuwa cikin sanyi da nadama tace.
“Alhamdulillah ai in Allah ya baka lfy ka gode masa”.
Haka dai suka cigaba da hira acikin group ɗin kowa na faɗin albarkacin bakinsa.
_Daga can gefe kuwa su ne Rafi'a,Tutus kitchen, Mom sayyeed&Noor Tatti Dija chiroma, ne da suka halarci wajen sunan ne suke ta Video da hotuna suna turawa cikin Group ɗin SAKAYYA Team Moddibo da Khausar kam baki yaƙi ruhuwa duk farin ciki ya cika su ganin irin gift da Khausar ta bayar akawo musu._
_Daga can gefe kuma ƴan karatun bati siddan na Allah ya isa kenan da basu biya kuɗi ba suke wiƙi-wiƙi da ido duk hakki ya hanasu sakewa da samun nitsuwa..._
Asma'u dake cigaba da hotuna da wayar Khausar wayar ya ɗauki suwwa ganin sunan Yah Mu'allim na yawo yasa da sauri ta nufi Khausar dake tsakiyar Didi da Momy suna hoto tayi saurin isa gareta kana ta tsugunna zata miƙa mata wayar kasancewar azaune suke haka yasa ta fito a hoton da yayi masifar kyau.
Asma'u kuwa cikin raɗa takai bakinta kunnenta tace.
“Gashi fa Yah Moddibo yana kiran ki”.
“Mu gani”.
Cewar Khausar tana karɓan wayar tare da kaiwa kunnenta tace.
“Assalamu Alaikum Yah Mu'allim”.
Cikin wani irin yanayin na musamman yace.
“Minha kizo ki sameni aɗakina”.
Kai ta gyaɗa tare da cewa.
“Toh”.
Sai kuma ta miƙe tare da rungume jaririn kai tsaye ta nufi sashen bakinta ɗauke da sallama ta shiga falon nan ta samu Dr Jameel, Dr Zakariyya, Ibraahim,Yah Ali, da Yah Abba da sauran yan uwansa.
Yah Abba na ganinta yayi Murmushi tare da cewa.
“Mai jego kin sha ƙamashi”.
Murmushi tayi kana tace.
“Ai dai kam”.
Kallonta ta mayar kan Ibraahim tare da cewa.
“Ibraahim Yah Mu'allim fa?”.
Da hannu ya nuna mata bedroom ɗin kana yace.
“Yana ciki”.
Ahankali ta nufi bedroom ɗin kwance ta gansa akan gadon yana ganinta ya saki sanyayyar ajiyar zuciya tare da buɗe mata hannunsa.
Cike da begensa ta zauna kusa dashi miƙewa yayi ya haɗa ta da jaririn ya rungumesu ahankali ya riƙa kissing ɗin goshinta zuwa wuyanta da kuma sassan jikinta baki ta ɗan tura tare da cewa.
“Yah Mu'allim ka matsaneni kuma ɗanka ya matse min wajen Theater na”.
Cikin sauri ya saketa kana ya karɓesa ya kwantar dashi tare da jawota jikinsa ya rungumeta sai kuma ya saki sanyayyar numfashi kana ya ruggumeta tsam cike da kulawa da kuma ganin yanayinsa ta shafo sajensa tare da cewa.
“Yah Mu'allim lafiya meke faruwa?”.
Kanta ya tallofo kana ya kalleta ido cikin ido da mamaki take kallonsa ganin yanda idanunsa suka kaɗa sukayi jawur dasu cike da kulawa tace.
“Yah Mu'allim lafiya?”.
Sunkuyar da kansa ƙasa yayi kana ya ɗago ya kalleta tare da cewa.
“Minha na yiwa Abualeey laifi kuma har yayi fushi dani”.
Cikin sauri ta zare idanunta tare da faɗin.
“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un Yah Mu'allim laifin me kayiwa Abualeey?”.
Araunane yace.
“Minha nayi mishi babban laifi naƙin bin Umarninsa”.
Cikin tsoro da kaɗuwa tace.
“Ya Ilahi Yah Mu'allim akan me baza kabi umarnin Abualeey ba?”.
Langwaɓar da kansa yayi kan wuyansa yace.
“Saboda kece ban bi Umarnin Abualeey ba!”.
Cikin sanyi da rauni tace.
“Ya Ilahi bana son jin wannan maganar sam maganar babu daɗin ji Yah Mu'allim Kabi Umarnin mahaifinka shine abinda ya dace kuma shine *SAKAYYAR* da zamuyi masa”.
Cikin rauni da karyewar zuciya yace.
“Bazan iya ba”.
Cike da mamakin shin wani irin abu ne me nauyi da girma agaresa da yasa har ya yiwa mahaifinsa gardama tace.
“Haba Yah Mu'allim ya za'a yi kace baza kayi abinda mahaifinka keso ba shin wani irin abu ne?”.
Cikin sanyi ya kalleta kana ya lumshe Idanunsa tare da cewa.
“Saboda yau yake so a bani mulkin Masarautar Mouley ahannuna”.
Cikin sauri da jin daɗi kana da Jimamin yanayin da yake ciki tace.
“Toh mene Yah Mu'allim mulkin ne baka son rikewa ko me meyesa zaka yi mishi gardama?Kuma ai nikam ma ina son mulkin nan meyesa baza ka karɓi Sarautar ba? Kawai ka karɓi mulkin shine abinda ya dace”.
Kai ya jujjuya tare da juya ƙwayar idanunsa acikin nata kana ya riƙo hannunta acikin nasa tare da cewa.
“Ba karɓan mulkin bane matsala Minha”.
Cikin rashin fahimtar abinda ke damunsa tace.
“Toh ka karɓi mulkin mana kayi mishi biyayya akai”.
Hannunta ya damƙe kana yace.
“Ki bari kiji ko menene”.
Fuska ta tsuke tare da cewa.
“Nikam babu abinda zanji Yah Mu'allim kawai kayi mishi biyayya akan abinda yake so ka karɓi mulki Allah ya tayaka riƙo ya baka ikon Adalci kai masa biyayya ka samu lada”.
Cikin sanyi da rauni yace.
“Cewa yayi an bani mulki bisa sharaɗin za'a bani Auren wata mata ya zama ina da mata biyu!”.
Da wani irin sauri ta dafe ƙahon zuciyarta da yayi wani irin harbawa cikin rauni da fusgar magana tace.
“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un”.
Atake jikinta ya fara rawa kar-kar-kar tamkar wacce aka watsawa ruwa ƙanƙara atsakiyar hunturun sanyi kana idanunta suka kaɗa sukayi jawur tamkar garwashin wuta lokaci ɗaya taji numfashinta na Up and down alamar yana shirin barin gangar jikinta jawota yayi ya riƙe ta da damuwa atare dashi yace.
“Kee ki tsaya mana ki nutsu me haka!?”.
Gaba ɗaya ta rikice numfashinta sai fusga yake alamun tana gab da suma saboda tsabar masifar kishi, cikin fusgar numfashi da ficewar hayyaci ta dafe ƙahon zuciyarta tare da cewa.
“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un Yah Mu'allim Aure kuma?,Wata matar za'a Aura maka?,ita?”.
Sai kuma ta tsaya da Maganar jin numfashinta na shirin barin gangar jikinta alamar zata iya rasa numfashinta.
Moddibo kuwa cikin matsanancin mamaki tsoro gami da ruɗu yake kallonta tabbas yasan tana da kishi amma bai taɓa tunanin kishinta yakai wannan matsayin ba.
Cikin sauri ya rungumeta tare da riƙo hannayenta kana yana jijjiga fuskarta yace.
“Khausar Khausar ki nutsu mana ki buɗe idanun ki dan Allah ki tsaya ki fahimci abinda zan faɗa miki”.
Da ƙyar ta iya buɗe idanunta.
Cikin sauri da tsoro ya sake tallafe Fuskarta ganin yanda ta zazzaro idanunta sukayi wani irin ja.
Ahankali ya fara bubbuga kumatunta tare da cewa.
“Dan Allah Minha ki nutsu kiji abinda zan faɗa Miki”.
Cikin rauni murya da bugawar zuciya tace.
“Yah Mu'allim yanzu mata zasu ƙara maka innalillahi wa'inna ilaihi raji'un”.
Sai kuma ta kife kanta akirjinsa ta saki marayan kuka mai masifan cin rai da zafi kukan data sakene ya temaka wajen daidaiton numfashinta ya tsaya.
Ahankali ya tallafota jikinsa yace.
“Minha shine laifin da nace Miki na yiwa Abualeey saboda nace masa, in dai har sai an ƙara min mata za'a bani mulkin, ni na yafe bana buƙatar mulki abawa Ibraahim nayi alƙwari zan rayu daga Ni sai ke sai kuma