Showing 69001 words to 72000 words out of 218703 words
ace akwai wani abinda bai saniba na al'adunmu sai dai abin tambayar shin taya hakan yakasance”.
Kai suka jinjina cike da gamsuwa kana suka cigaba da tattauna maganar daga haka suka tashi daga taron.
Yayin da Didi kam daren wannan ranan haka ta suku-ku baki ɗaya zuciyarta da nutsuwarta ya tafi izuwa ga ɗouki da kuma mararin son ganin yaron da akece yana tsananin kama da Ibrahim ɗin ta koda kuwa abincine ta kasa ci.
Acan ɓangaren Moddibo kuwa yana zaune a inda yake batare daya motsa ba bare kuma yaci abinci baki ɗaya abin duniya ya ishesa abubuwa goma da ashirin sun haɗe masa, tarin tambayoyin a kansa sama da dozin wanda innayi kaɗai yakeson ji da ganin yayi mata su, ahaka ya cigaba da zama kafin daga bisani wata zuciyar ta yanke shawarar ya tashi koda zai iya samun wata ƙofa ta baya da zai fice.
Ahankali ya miƙe tare da kallon gefen daman sa inda ya shiga yayi alwala kana ya kalli falon daga gefe ya hango wata ƙofa ahankali ya fita idanunsa suka sauƙa akan wani falo na daban shima still yana ɗauke da ƙofa hagu da dama murɗa ƙofar yayi ya fita anan yaga wani ƙofa hagu da dama sai kuma wani step daga tsakiyarsu daga can sama shima kofa ce hagu da dama...
Hadimansa kuwa ganin ya fita yasa suka shiga taka masa baya tunda basu da ikon hanasa cikin tsuke fuska ya kallesu, su kuwa cike da girmamawa ɗayansu yace.
“Ranka ya daɗe ko akwai abinda kake buƙata?”.
Girgiza kai kana yace.
“Um-um babu abinda nake buƙata”.
Kai suka gyaɗa tare da faɗin.
“Toh”.
Tunda basu da ikon hanashi tafiya.
Cike da a nitsuwa yake tafiya har ya haura step ɗin yanda ƙasan yake haka zalika saman yake komai na ginin iri ɗaya ne sai dai tsarin Furnitures ɗin ne suka banbanta.
Kasancewar suna saman daga gefen dama komai White & Sky blue kalar Sararin samaniya sai kuma daga can gefen Hagu komai na cikinsa ya kasance Jane da ratsin fari haka nan yakeji kamar anayi ma shi jagorane.
Cikin fesar da numfashi ya koma kan step ɗin ya tsaya a Balcony yana mai cigaba da kallon tsananin kyau da tsaruwan wajen tun da yake a iya tsawon rayuwarsa bai taɓa kallon falo mai masifar girma da kyau irin wannan ba.
Ahankali ya ɗaga idanunsa sama anan ya hango ainihin tsakiyar Fadan.
Babbar Fadace mai masifar kyau da girma akwai wurare daban-daban yayin da Part-part sunfi aƙirga iya inda idanunsa ke iya hangowa Part-part ne ashimfiɗe sai kuma hadimai da yake hangowa suna zirga-zirga wanda bazai iya ƙiyasta yawansu ba, ga wani irin wuta mai haske da ƙyalli daya haske ko ina na cikin fadar tamkar rana kana ga bishiyoyin dabino da mijin gwanda wanda duk ta inda ka cilla ido suke rausayawa sai zurga-zurga Hadimai keyi.
Ahankali ya juya bayansa daga gefe nan idanunsa suka hango wani garden Mai azabebben kyau daga can bayan Garden ɗin kuwa wani Swimming pool ne dake ɗauke da ruwa Sky blue ga wasu fararen kujeru kaman resting Chair dake gewaye da wajen kana daga ƙasa su kuwa Grass Carpet ne da yayi dark blue Mai azabar kyau yayin da wasu irin tsuntsaye masu kyan gani da daɗin sautin murya ke shawagi awajen wanda da alama saboda ƙayatarwa aka ajiye su...
Ya ɗauki tsawon lokaci yana kallon wajen haka nan ya tsinci kansa da son ganin wajen domin kallon wajen yatuno masa da Gembilan sak yanayin tsarin gidansu haka wajen yake sai dai tsarin wannan ba suda yalwan Furanni haka kawai aransa yaji da ace za'a bashi dama zai ƙawata Ilahirin Fadar da Furanni saboda arayuwar duniya babu abinda ke sashi farin ciki kamar yai ta kallon Furanni har misalin 11:30 yana tsaye awajen kafin ahankali ya motsa ƙafafunsa jin sun gaji da tsayuwa kana ya gangaro ya dawo cikin ainihin falon da aka kawo sa...
Yana shiga falon ya zauna akan kujera tare da lumshe manyan idanunsa dake lumshe yana mai sakin ajiyar zuciya akai-akai.
Zaman sa babu daɗe wa kamar misalin 12:00 yaji ƙaran ƙofa an buɗe.
Jin ƙaran buɗe ƙofa yasa ya buɗe Idanunsa dake lumshe kana yabi wajen da kallo...
Da mamaki yake kallon Jabeer bin Jabeer da suka haɗu ajirgi kasancewar shine agaba.
Jabeer bin Jabeer kuwa cikin ƙaguwa ya maida idanunsa kan Didi da Lalla Khadijah da Hafsat ke gefenta, tare da cewa.
“Didi shigo kiganifa, Didi dan Allah ki ganshi da kyau fa”.
Sheikh Jabeer, Sarki Youseep Muhammad Mouleey, Waziri Galadima, Sarkin Dawakai, Jakadiya, Mahaifiyar Sarki Niyna Lalla Khadijah da Lalla Hafsat sai kuma Rahama dake can biya tana biyosu da sassarfa tare da faɗin.
“Didi ku jirani mana”.
Su kuwa cikin nutsuwa suka shiga cikin falon.
Suna shiga Moddibo ya zuba musu ido cike da mamaki yake bin Didi da Abualeey da wani irin amintaccen kallo yana mai jin wani irin yanayi na ratsa mishi zuciya a kansu haka nan ya gaza janye idanushi a kansu sai bugun da zuciyarsa keyi.
Lalla Khadijah da Hafsat kuwa ruggumeshi sukayi tare da sakin wani sassayyan kuka, wannan na gefen dama wannan na gefen hagu,
Rahama kuma na isa, sai kawai ta kifen kanta bisa guiwowinsa tare da faɗin.
“Yah Aleey laisa leeh misluka abadan, ana uhubbuki hubban azeeman”.
wani irin amintaccen nitsuwa ne yaji yana ratsashi, wanda yasa baisan lokacin da yasa tafukan hannunsa yana sharewa Lalla Khadijah da Hafsat hawayeba.
Su kuwa Khadijah da Hafsat sai kuma suka ɗan janye jikinsu tare da ruggume juna cike da tsananin farin cikin.
Ita kuwa Rahama cikin yanayin shogwaɓar ƴan auta take ɗan kuka tare da cewa.
“Yah Ibraahim ina kake kazo kaga Yah Aleey na ya fika kyau daga yauma niba ruwana da kai”.
Dan fesar da numfashi Modibbo yayi tare da sa hannushi yana ɗan shafa bayan Rahama alamun tayi shiru.
Sarki Youseep Mouleey kuwa cikin kamala ya zauna bisa kujera kana Sheikh Jabeer ma ya zauna gefensa yayin da Galadima, Waziri, Sarkin Dawakai, suka zauna a ƙasa.
Amintattun Hadiman dake biye dasu kuwa daga can baya dasu suka zauna.
Jakadiya kuwa idanunta akan Moddibo ta saki yalwataccen murmushi mai cike da zallan farin ciki kana tace.
“Masha Allah nesa ta matso kusa abin nema ya samu”.
Moddibo kuwa idanu ya zuba musu baya ko ƙyaftawa ganin Jabeer bin Jabeer ya zauna aƙasa gasu Galadima sai shima ya zamo daga kan kushin ɗin ya zauna akan Carpet tare dasa hannunsa yana sharewa rahama hawaye.
Yayin da yake kallon Sheikh Jabeer cike da mamaki kasancewar ya masa farin sani domin yasha zuwa wajensa a Adamawa sai dai baya samun haɗuwa dashi cikin tsananin mamaki ya motsa laɓɓansa tare da faɗin.
“Sheikh Jabeer”.
Sheikh Jabeer na kallonsa tare da mamakin kiran sunan sa ya furta.
“Na'am. Ka Sanni ne?”.
Ware idanu Moddibo yayi kana ya jinjina masa kai cikin sanyi Murya da yanayin nutsuwarsa yace.
“Farin sani ma kuwa shekaran Kur'anin dana rubuta na farko kusan uku awajenka wanda na rubuta daga baya kuma yayi cika shekara ɗaya awajenka amma har yanzu ban samu an dubasuba.
Batare da Sheikh Jabeer ya janye idanunsa daga kansa ba yace.
“Menene sunan ka”.
Moddibo kuwa ahankali yace.
“Sunana Moddibo daga Taraba nake tura maka wanda aminina Jameel Bashir Mai Dala yake kai maka”.
Baki ɗaya falon ya sake yin shiru baka jin muryan kowa sai na Moddibo da Sheikh Jabeer yayin da Didi da Sarki Youseep Mouleey kuwa jikinsu ke wani irin tsuma aduk lokacin da Muryan Moddibo ya ratsa kunnensu.
Kai Sheikh Jabeer ya jinjina kana yace.
“Toh menene cikekken sunanka ai Moddibo ba sunan yanka bane?”.
Lumshe idanu Moddibo yayi tare da buɗe su kana ya shafa sajensa a hankali yace.
“Sunana Aliyu Youseep Muhammad Mouleey”.
Cikin matsanancin mamaki daya sake mamaye zuciyoyinsu da tabbatar musu lallai babu haufi jininsu ne, akaro na barkatai suka juya suka shiga kallon junansu da ƙyar Sheikh Jabeer ya furta.
“Kace me sunan ka?”.
Ahankali Moddibo ya kuma motsa laɓɓansa tare da faɗin.
“Sunana Aliyu Youseep Muhammad Mouleey”.
Cike da matsanancin mamaki daya daki zuciyoyinsu suka haɗa baki wajen faɗin.
“Ikon Allah sunan ka kenan?”.
Kai ya gyaɗa yana ɗan ciza lips ɗin sa na ƙasa ya furta.
“Eh sunana kenan?”.
Ahankali Sheikh Jabeer ya furta.
“Ikon Allah toh waye mahaifinka”.
Araunane ya jingina bayansa da jikin Kujeran kana ya girgiza kai tare da lumshe idanunsa yace.
“Babana ya rasu!”.
Da sauri Lalla Khadijah tace.
“Wlh mahaifinka na raye gashi nan a gabansa kusa da kai”.
Cikin Sauri Didi ta katse Khadijah ta hanyar daga mata hannun, kana ta juyo ta kalli Modibbo zuciyarta na cigaba da bugawa da karfi tamkar zai fasa ƙirjinta ya fito ta tace.
“Toh wacece Mahaifiyarka!?”.
Idanunsa cike da rauni ya buɗe ya kalleta kana yace.
“Mahaifiyata ma ta rasu”.
Cikin sauri Rahama tace.
“Ga Didi nan a gabanka a raye waya ce maka baka da mama”.
haka nan yakejin baya son kukan Rahma har ransa, ya kuma lura ta ƙoshi da sakalci cikin sanyi yake jujjuya mata kai alamun kada tayi kuka.
Sarki Youseep Mouleey kuwa cikin sauri yayi gyaran murya tare da faɗin.
“Toh waya faɗa maka Iyayen ka sun rasu?”.
Moddibo kuwa cikin sanyi da fesar da numfashi ya kallesa kana ya gyara zamansa tare da faɗin.
“Kakata ce ta faɗa min”.
Aƙage Sarki Youseep Mouleey ya kuma cewa.
“Shin wacece kakar ta ka?”.
Ahankali ya ɗaga yatsarsa tare da nuna musu hoton dake manne jikin bango kana yace.
“Gata can Kakata na rasa ya akayi nazo na samu hotonta acikin wannan Fadar taku”.
Cikin jin dadi Jabeer bin Jabeer yace.
“Aha bana faɗa mukuba, ai wlh dama na sani wannan daga gani babu tambaya Aliyu ne”.
Da sauri Didi dake kuka ta matso kusa dashi tare rungumesa.
Shi kuwa Moddibo shiru yayi, sai idanunsa daya lumshe yayin da lokaci ɗaya wani irin yalwataccen farin ciki ya lulluɓesa alokacin data rungumesa tsintar kansa yayi da ɗaura tafukansa abayanta ya rungumeta lokaci ɗaya kuwa yaji ruwan hawaye na cika masa idanunsa wanda bai san dalilin zuwan suba kawai dai yasan yanajin wannan matar da yaranta har cikin ƙahon zuciyarsa hakanan yakeji ya aminta da ita fiye da aminci da yayiwa ko wacce uwa a duniya.
Haka zalika rungumar da tayi masa ji yayi kamar Innayi ce ta ruggumeshi amman sai yakejin aminci da son fiye yadda yake ji tare da innayi wannan ruggumar jinsa yayi ruggumace ta mahaifiyar data ɗauki cikinsa tsawon wata tara da kwana tara ce ta kuma yi naƙudarsa so a matsayin uwa zuciyarsa da jininsa suka amshi rungumesa da tayi kamar yadda jikinsa zuciyarsa suka amshi Khadijah da Hafsat da Rahman a matsayin tsotsonshi muharamansa, sabida jini baya ɓuya.
Ji yake tamkar rungumar da yake nemane tsawon shekara da shekaru ne wanda bai samu ba.
Didi kuwa kuka ta saki hadda shesh-sheƙa batare data raba jikinsu ba tace.
“Abeey wallahi wannan ɗana ne. Abba wallahi ɗana ne ku gani taya za'a yi kuce sai kunyi wani bincike? ɗana ne Aliyuna ne fa Abba ɗana ne fa”.
Kalmar da take maimaitawa kenan tana cigaba da kuka.
Da sauri Sheikh Jabeer ya riƙo hannunta kana yace.
“Fatima kada kiyi kuka na gamsu na kuma yadda ɗan kine kuma tsatsonki ne nima ina ji ajikina tabbas tsatsonki ne kuma jikana”.
Ya ida maganar yana share mata hawayen daya ƙi tsayawa a idanunta.
Sarki Youseef Mouleey kuwa cikin sauri ya buɗe wa Moddibo hannunsa kana cikin raunin murya da tsantsar bege yake faɗin.
“Zo ɗana”.
Moddibo kuwa tsintar kansa yayi da gaza yi musu gardama, kana zuciyarsa ta gamsu da kalaman da suke faɗa.
Yayin da yake jin su ɗin wani sashe ne na jikinsa.
Da wani irin bege da shauƙi ya faɗa jikin Sarki Youseep Mouleey ya rungumesa yayin da shima sarki Youseep Mouleey ya ƙanƙamesa ji yake kamar idan ya sake sa tamkar zai sake nesa dashi ne ciki rauni yake faɗin.
“Shakka babu wannan Aliyu nane”.
Kallonsa ya mayar kan Sheikh Jabeer kana yace.
“Abeey wallahi wannan ɗana ne.
Allah sarki rayuwa. Allah ya ɗauki ran Mahaifina yau da yaga jikinsa da zarrar da bai taɓa tunani da zato ba”.
Baki ɗaya kallonsu mutanen falon keyi cike da tarin tausayinsu.
Sarki Youseep Mouleey kuwa cikin rauni da farin ciki ya sake rungume Moddibo tare da kallon mahaifiyarsa Niyna yana faɗin.
“Niyna yau da Abbana na raye da yaga Jikinsa da Zarrar da zata girgiza Maƙiya, Da yaga jikinsa da zarrar da zata sa zuciyoyin maƙiya cikin tashin hankali da firgita tabbas Aliyu ɗana ne Niyna kalleshi fa”.
Kai Niyna take jinjinawa cike da gamsuwa tana mai shafa kan Modibbo.
Moddibo kuwa mamaki da al'ajabi ne ya cika masa zuciya ahankali ya janye jikinsa daga na Mahaifin nasa kana ya koma ya zauna yana binsu da kallo ɗaya bayan ɗaya.
Ahankali ya maida idanunsa kan hoton Innayi kana ya dawo da kallonsa garesu cikin nutsuwa ya furta.
“Wacece wannan awajen ku? Kakata ce wacce da ita nake rayuwa, Kuma ita kaɗai nake da ita a duniyata”.
Cikin sauri Didi ta girgiza masa kai tare da faɗin.
“Kana da kowa aduniya. Kana da ƙanne, kana da Yayu, Kana da Mahaifi, Kana da Kakanni kakan ka ɗaya ne ya rasu Mahaifin Babanka, Kana da zuri'a zuri'arka mai tarin yawa gaba ɗaya wannan masarautar family'nka ne.
Aleey a ina kuke rayuwa?”.
Tun da ta fara magana ya tsira mata idanu yana sauraren ta har sai da tadasa aya kafin yace.
“A Nigeria muke rayuwa acikin Jahar Taraba Gembila” .
Da mamaki ta kallesa tare da faɗin.
“Allah sarki Innayi tana raye?”.
Da sauri ya kalleta jin Sunan Innayin sa abakinta sai kuma ya jinjina kai kana yace.
“Eh Innayi tana raye”.
Still idanunta na zubda hawaye ta furta.
“Allah sarki Innayi tayi min halarci mai yawa ashe wasiƙar data ajiye min da gaske ne ta kular min da ɗana kula mafi kyawu da inganci”.
Zazzafan Ajiyar zuciya ya sauke kana yace.
“Kin santa ne?”.
Kai ta jinjina masa tare da cewa.
“Na santa Hadima tace da aka haɗani da ita.
Jakadiyata da aka haɗani da ita tun daga lokacin da aka kawo ni ƙasar Marocco, ashe data tashi ƙasata ta koma da ɗana kusa da Jahata dan ta kular min da ɗana”.
Sai kuma ta lumshe idanunta akan Moddibo kana ta cigaba da faɗin.
“Sannan sai da tayi sanadin yanda ɗana zai kasance mutumi na gari har Alkur'ani mai girma ka rubuta ka kaiwa Mahaifina ya duba maka”.
Sai kuma ta mai da kallonta kan Sheikh Jabeer kana tace.
“Abeey Ya akayi baka taɓa kallonsa ba?”.
Sanyayyar numfashi Sheik Jabeer ya fesar cike da kamala yace.
“Fatima wannan abubuwane da tattaunawarsu sai ahankali kiyi haƙuri yanzu dai mu fara godewa Allah”.
Kai ta jinjina tana mai yin tasbihi azuciyarta...
Jakadiya kuwa cike da tsantsar farin ciki tace.
“Ai wannan ma babu bukatar wani bin cike ko wani abu tsatso ne na gidan nan, jinine na gidan nan, haihuwa ne na gidan nan,Tarbiyya ce ta gidan nan,Masha Allah”.
Ta sauƙe Ajiyar zuciya tare da cigaba da cewa. _“Fatabarakallahu Akhsanul Khaliƙin_, Halittace ta gidan nan daga gani ma babu tambaya tsatsone namu, ina Ibraahim yazo yaga ɗan uwansa da yake cewa yana haɗuwa dashi acikin mafarkai”.
Haka nan suka ci-gaba da tattaunawa cike da al'ajabi da mamaki wanda mgna ce ta gsky da gsky wacce gskyarce tayi aikin da dole Modibbo yaji zuciyarsa ta gamsu da kalamansu koda suka fara yi mishi tambaya kan yadda ya sarrafa Rinƙas ya shaida musu yasan Rinƙas a mafarkine ga mamkinsu dukkan wasu al'adu ko wani abu na sittin masarautar duk ya sani.
Cike da kulawa Sheikh Jabeer ya kalli Moddibo kana yace.
“Moddibo ka shiga ka kwanta in Allah ya kaimu da safe zamu ƙarasa magana”.
Kai ya jinjina kana yace.
“Wayoyina suna cikin mota ina so akawo min su ina buƙatar mgn da innayi inada tarin tambayoyin da nakeso inyi mata”.
Kallonsa Sarki Youseep Mouleey kana ya girgiza masa kai tare da faɗin.
“Kada ka damu duk abinda kake buƙata ga hadimanka za'a yi maka sannan duk tambayoyinka ka tarasu lokacin amsasu nan tafe”.
Kai ya gyaɗa yana mai cigaba da jin nutsuwa su kuwa sallama suka masa kana suka fice.
Nigeria Gembulan
Dai-dai lokacin kuma Naseer ne, zaune tsakiya falonshi wasu hawaye masu zafin gaskene wani ke korar wani, tunda yaje gidan Lamiɗo, hira wurin Amina da Lamiɗo da kanshi ya sanar masa an daura auren Khausar da Modibbo ya kasa ƙara sawa cikin gidanma ya juyo ya dawo, kuka yayi tayi tamkar mace har yanzu ɗaya gaza bari kife kansa yayi bisa guiwowinsa a fili yake faɗin.
“Khausar ya za'ayi jinin haka, duk wani burina da sha'awata a kanki ne, na soki tun baki san kanki ba, rana tsaka ba zato ba tsammani inji wai an aura miki Modibbo, shike nan na rasaki kenan, domin na sani yafi ƙarfin iyawata, bani da abinda zan iyayi a kanshi, yayi min zarrar rayuwa ya kwace min ke”.
Sai kuma ya ɗan tsagaita kukan tare da kallon wayarsa da kiran Amina ya shigo, cikin tarin takaici ya kashe wayar a fili yace.
“Khausar ne kaɗai a raina Amina zan dai aureki ne dan biyan buƙatar rayuwata, da kuma rage jarabar rashin malakar Khausar ne”.
Haka yaci gaba da surutai kamar zautacce, Allah ya sani baiyi zaton hakaba.
Rabat Marocco
Washe gari tun shida da rabi na safe ƴan uwanshi mata suka shigo a jere, Lalla Hafsat ce riƙe da wani tray mai ɗauke da wasu ƴan ƙaran kwanuka masu kayan gani, Ragama kuwa wayace makale a kafaɗarta. inda yake suka nufa, jawo stoll Hafsat tayi tare da ajiye trayn kana ta fara haɗa mishi tea.
Lalla Khadijah kuwa hannun ta miƙe mishintare da yimishi sallama alamun musabaha takeso suyi.
a hankali ya ɗago hannunsa na dama ya miƙa ta, dai-dai lokacin kuma Rahama ta manna mishi wayar dake hannunta a kunne, tare da cewa.
“Yah Aleey ga Yah Ibraahim daga jiya zuwa yau ya kirani yafi sau goma, wai in ban haɗuka ba yaji muryarka in ya dawo bazai min mgn ba”.
Ɗan murmushin gefen baki yayi tare da sa hannushi na hagu ya amshi wayar.
It kuwa Rahama cikin jin dadi ta kalli askin kan Modibbo tare da cewa.
“Lah Yah Aleey ko askinkafa irin na ahlin masarautar Mouley ne”. sai kuma ta ƙara sunkuyowa kanshi tare da cewa.
“Lah Adda Khadi zoki gani, wlh shima yanada naɗeɗɗen gashin irin na Abualeey”.
Numfashi me ɗan tsawo ya fesar ganin Hafsat na miƙa mishi cup ɗin tea da kuma turo masa stoll din gabanshi tare da cewa.
“Bisimillah Didi tace ka ɗan taɓa wannan kafin ta ƙarasamaka breakfast inka”.
Longwaɓar da kai yayi tare da ɗan yamutsa fuska kana a hankali yace.
“Toh me ɗaya zanyi mgn a waya ko cin abinci ko