Showing 168001 words to 171000 words out of 218703 words
By
*GARKUWAR MARUBUTA**SAKAYYAH book 2... Page 32*
Na
*Aysha Aliyu Garkuwa*
*Masu son Maganin infection da maganin mata, ku marmatso wannan account no in ne naku ta ciki zaku turo kuɗin ku 0005388578 Jaiz bank AISHA ALIYU GARKUWA, Sai ki turo shaidar biyanki ta WHATSAPP NUMBER'N na 08069423567. akwai sabbin kaya masu zafi suna nan bisa hanya, ki turo kuɗinki a saki cikin lissafi. Kayanen mata masu zafi sadidan daga Chadi akwaisu Garukan daka, gumbunan, Tsumummuka, cida Ciccibi Abodi cida kaza ci da jan nama kwanon ƙasaitacciyar mace biyar sirri, furar mata, gumbar madara Gumbar kolli mai ƙyallin al'khairi gumbar uku al'khairi, gumbar da ba'a baiwa mai kishiya, gumbar riɗi, garin maɗi garin melɗamhi garin ilanwaddihi garin mallaka, tsumin riɗi tsumin tsirtai tsumin kinfi budurwa, tsumin riɗi, tsumin ta baje Sabaya, matsin maliƙi mai masifar matse mace matsin daɗi har maɗiga, mai ɗan kare kyau. Kullacar sirri al'ajabu shu'umar Humra, da duk sauran kan ƙamshi. Haɗin amarya budurwa ko bazawara haɗin mai jego ko uwar gida, akwaisu Available set ɗinmu hawa hawane akwai manya akwai ƙananan, ƙanan daga 40k ne 35k 30k 25k 20k 15k 10k shine ƙarami haɗina na karshe sai kuma haɗin kwanon ƙasaitacciyar shi 7k ne shine ƙarshen haɗina kenan... Manyan set ɗin kuma daga 50k 60k 70k 80k 90k 100k ke zaki faɗi haɗin nawa kikeso anyi miki kana kimin bayanin yadda kikeso da matsalarki ni kuwa nasan abinda zan haɗa miki, ina araha kam amman ina hana bashi*
Amai kamar ba gobe, wasa wasa dai amai yaƙi tsaya, ganin hakane gaba ɗaya Modibbo ya birkice kawai sai ya rungumeta a jikinshi tanata kakarin wanda ba abinda take hararwa sai miyau da ɗan ruwa kaɗan sabida ba abinda taci shiyasa gaba ɗaya ta galabaita.
Cikin sauri Didi ta shiga ɗakinta alƙyabbata ta sako kana ta dawo tare da cewa maza.
“Maza ɗauketa mu tafi asibiti”.
Cikin ruwan jiki ya ɗauketa suka fito harabar side din Didi suna fita hadimai na buɗe musu mita Didi da Innayi mota ɗaya suka shiga shi kuma mota ɗaya da Rahama da tazo shigowa ne ta gansu.
Kai tsaye Mouldy hospital suka nufa.
Wanda tuni Didi ta gayawa Abualeey da kanshi ya gayawa Dr Jameel shiyasa tun kafin su isa an shirya komai.
Suna isa aka amsheta tare da bata taimakon gaggawa wani ɗan karamin ruwa suka ɗaura mata da allurai kana suka nufi ɗakin gwaje-gwaje da ita.
Wanda duk inda sukayi Modibbo na biye dasu a baya.
Cikin iyawa da ƙorewa Dr Isha ke ɗan jujjuya na'urar dake saman cikin Khausar yayinda Dr Jameel kuwa yana ɗaya gefen yana haɗa ruwan allura.
Cikin murmushin Dr Isha ta kalli Modibbo fuska cike da jin daɗi tace.
“Alhamadullah Mrs Aliyu Youssef Mouldy nada ciki na tsawon kwanaki arba'in da biyar”.
Ya Salam shine abinda Modibbo yayi ya faɗi a fili da kuma ƙarfi sai kuma ya juya da sauri ya fuskanci alƙibla yayi sujudushukur, yana ɗagawo kuma ya dawo bakin gadon da sauri ya yasa hannunsa da nufin zai ɗagota sai kuma ya kalli Dr Jameel da ya riƙe hannunsa tare da cewa.
“Malam barta bakaga bacci tayiba”.
Kawai sai sunkuyo kanta bisa goshinta ya sakar mata amintaccen kiss sai kuma a kunatu daga nan sai haɓarta kawai sai ya rinƙa bin duk jikinta da sumbatar dake nuni da tsananin farin cikine ya gigita shi, ita kuwa Khausar bacci takeyi cike da wahala.
Ganin alamun Modibbo zai takura tane yasa Dr Isha cewa.
“Afwan a barta tai vacci”
Jin hakane yasa ya juya da sauri ya fita.
Yana fitowa ya nufi Didi itama ɗin shi ta nufa, yana isa inda take kawai sai ya rungumeta cikin tsananin farin ciki jin daɗin mara musaltuwa na yadda labarin yazo mishi a bazata yace.
“Didi Minha vidaa nada ciki Didi ciki nanefa a jikin Khausar Didi ɗa nane a jikinta fa”.
Cikin tsananin jin daɗi Didi da dama ta daɗe da fahimtar cikine da Khausar kanshi ta fara shafawa tana cewa.
“Kayi sujja ka godewa Allah”.
Da sauri yace.
“Didi nayi”.
Sai kuma ya saki Didi ya kama Innayi da yanzu ta ɗago kanta daga yin sujjadar godiya ga Allah ruggemeta yayi yana cewa.
“Innayi kinji ko?”.
Kai ta gyaɗa mishi dan da alamu yama rasa me zauce.
Sai kuma ya kamo hannun Rahama dake rawa da juyi da waya a kunneta da alamun Lalla Khadijah take gaya cikin jin daɗin yace.
“Kinji kin kusa zama Goggo ko”
Sai ta ruggumeshi.
Kan kace kobo Abualeey da Waziri Galadima da Niyna suna sunzo.
Haka dai ranar suka wuni a asibiti wanda ita kam Khausar batama san meke faruwa ba dan bacci ta wuni.
Nigeria
Ana kiran sallan Magrib Hajiya Bunayya dake kwance tayi zumbur ta miƙe tsaye tare da sakin ƙara ta rugawa a guje ta nufi bathroom sabida wannan azabebben ƙaiƙayin da ta kwana dashi daran jiya da tayi ya dawo.
Ai kuwa susa takeyi harda hawaye data fito bazata wuce 15 minute ba ƙaiƙayin zai dawo sai kuma ta koma ciki.
Kafin zuwa lokacin sallan Isha har jini ke zuba sabida masifar
Kaikayawa datake.
Ganin Jini na zuba yasa ta mike azabure,
ruwan dumi ta hada a Baho kana tasa gishiri ta shiga ahankali tafara Jin masifar kaikayin na raguwa zaman minti goma tayi kana ta fito falon kan 2sitter ta zauna tana Maida numfashi wayarta ta janyo tayi dealing number Hajiya lami ringing biyu ana uku ta dauka tare da sallama cikin matsanamcin tashin hankali gami da tsoro Hajiya Bunayya tace.
“Hajiya Lami nifa nashiga cikin Masifa ƙaiƙayine yake addabata na faɗa Miki jiya kwana nayi banyi bacci ba da asuban farine na samu sauƙi yanzu gashi Maghiba nayi ƙaiƙayi ya dawo”.
Zazzafan Ajiyar zuciya Hajiya Lami ta sauƙe tana gyara zama ta girgiza Kai tare da cewa.
“Ke dai bari Hajiya Bunayya nima Ina cikin tashin hankali tunda muka dawo yarinyar Nan ta fara Shan magani wannan abu guda² suka fara fitowa kamar masu Rai”.
Aruɗe Hajiya Bunayya ta dafe ƙirjinta da hannunta na hagu sai Kuma ta ɗago ta yarfe tare da faɗin.
“Yau mun shiga Uku wannan wace irin masiface ta tun kuramo?”.
Zazzafan Ajiyar zuciya Hajiya Lami ta sauƙe kana tace.
“Hmmmm ni nama rasa kalar tunanin da zanyi Baki ɗaya hankali na atashe yake”.
Haka dai suka cigaba da tattaunawa.
Morocco Acan ɓangaren Khausar kuwa bayan an idar da sallar Isha'i Moddino ne da Dr Jameel cikin sauƙe numfashi Dr Jameel yace.
“Ruwanta ya ƙare yanzu zan sallameku ku koma gida sannan zan haɗa maka magungunanta”.
Numfashi Moddibo ya fesar tare da cewa.
“Toh shikenan Babu laifi”.
Sai Kuma ya juya Inda su Didi ke zaune Ganin Basu nan yasa ya Maida kallonsa Kan Dr Jameel yace.
“Ina su Didi?”.
Ɗan gyara tsayuwa Dr Jameel yace.
“Ni nace su tafi tunda zan sallameku”.
Kai ya gyaɗa tare da faɗin.
“Ok”.
Ya Ida maganar tare da tura ƙofan ɗakin da take kwance yana shiga Idanunsa suka sauƙa akanta tana zaune kan sallaya bisa alamu ta idar da Sallah Dr Ishaa na gefenta sai Kuma Rahama yayin da Dr Ishaa ke riƙe da Plate ɗin Indomie Wanda yaji yajii Dr Ishaa na miƙa mata kanta ta kawar gefe alamar bata so.
Kallonsa Rahama tayi kana tace.
“Yah Aleey kaga yanzu abinci kusan kala huɗu muka kawo mata Kuma duka taƙi taci”.
Ta ƙare maganar suna miƙewa ita da Dr Isha ɗin suka nufi ƙofar fita.
Shi kuwa Modibbo
Zama yayi gefenta tare da rungumeta aƙirjinsa sai Kuma ya manna Kansa a wuyanta yana shaƙan ƙamshin wajen yayin da ya Sanya hannunsa na dama yana shafa cikinta cikin wata sanyayyar murya Mai cike da aminci, tausayi jin ƙai gami da shaƙuwa yace.
“Minhaa cikin nan yana wahalar min dake sosai, nayi alƙawarin duk randa yazo duniya saina sumbacesa kana na Sanya mishi Albarka sannan nayi mishi adduar shiriya saboda wahalar min dake da yake yi”.
Jin haka ne yasa Dr Ishaa da Rahama saurin fita.
Bayan sun fita ta ɗaga kanta ta kallesa cikin wata kasalalliyar murya Mai sanyi tace.
“Waye ɗin Kuma?”.
Amintaccen murmushi ya sakar mata Wanda ya fito daga ainhin ƙoƙon zuciyarsa still Kuma hannunsa na cikinta yana shafawa yace.
“Minhaa kina da ciki fa”
Fuskanta ɗauke da mamaki ta kallesa sai Kuma ta lumshe Idanunta cikin kasalar daya game jikinta tace.
“Ciki Kuma?,Dama Ina da ciki ai”.
Ɗan shafa cikin yayi sai Kuma ya sassauta murya cike da matsanancin farin yace.
“Ba irin wannan cikin ba,Ciki na Haihufa”.
Cikin mamaki ta buɗe Idanunta dake lumshe ta kallesa giransa ɗaya ya ɗaga mata da faɗin.
“Wallahi dagaske”.
Cikin wani irin yanayi ta faɗa jikinsa hannunsa duka biyu yasa ya rungumeta itama hannunta tasa ta rungumesa tana Jin wani irin yanayi na tsananin farin ciki sai Kuma ta ɗaura hannunta asaman cikinta tana shafa muryanta ɗauke da farin ciki tace.
“Yah Mu'allim da gaske?”.
Kai ya jinjina tare da cewa.
“Eh Wallahi da gaske”.
Ahankali ta Kuma ɗago Kai ta kallesa cikin sanyi tace.
“Allah yasa mu samu Mai kama da Ramadan idan ya girma sai mu bawa Momyna shi ya maye mata gurbin Ramadan”.
Sake rungumeta yayi ajikinsa tare da faɗin.
“Allah ya sauƙeki lafiya Allah ya ingantashi ya masa Albarka Amma Khausar bazan iya bada gudan jininmu ba kiyi haƙuri ba zan iya ba.
Ya karashe maganar cikin tabbatarwa da Kuma gaskiya da gaskiya ahankali tace.
“Baza ka iya ba?”.
Kai ya gyaɗa yana shafa cikinta ya fesar da numfashi tare da faɗin.
“Bazan iya ba,bazan iya ba kiyi haƙuri ban Miki alƙwariba kada ma in Miki ƙarya”.
Ɗan ware Idanunta dake lumshe kamar na Mai jin bacci tayi sai Kuma tace.
“Ido da ido?”.
Ɗan murmushi yayi Jin yanda tayi maganar cikin shaƙan ƙamshin ta yace.
“Um kada in Miki ƙarya ne”.
Tana sake shiga jikinsa ta ɗan cunno Baki tare da cewa.
“Ni Kuma Ina so idan na samu Mai kama da Ramadan in bawa Momy ya maye mata gurbinshi shiyasa naji daɗi”.
Cikin fahimtar har yanzu rashin Ramadan na ranta yasa yace.
“Toh shikenan in kin dage kin Haifa mana Dozen Mai yuwa in bawa Momy ɗaya”.
Zare Idanunta tayi tare da faɗin.
“Har Dozen?”.
Kai ya gyaɗa kana yace.
“Eh mana”.
Cikin sauƙe numfashi tace.
“Wannan ɗayan ma ga yanda nake ji”.
Cikin Jin taisayinta ya tallafe fuskarta kana ya motsa laɓɓansa tare da faɗin.
“In Sha Allahu zanyi Miki addu'a Kuma Ubangiji zai kawo Miki da sauƙi ”.
Sai Kuma ya tallafo ta tare da miƙar da ita yace.
“Tashi mu tafi sai mu biya restaurant idan akwai abinda kike so in siya miki”.
Kai ta girgiza cikin sanyi da game mata jiki tace.
“Nikam ma banajin yunwa cikina aƙoshe yake”.
Dai-dai lokacin Dr Jameel ya shigo Idanunsa akan Moddibo yace.
“Eh ko bata ci abinci ba bazata damu ba saboda ƙarin ruwan da aka mata zai taimaka.
Kuma in Sha Allahu duk bayan makonni zanke ɗan ƙara mata ruwa tunda dai bata samun cin abinci”.
Ya Ida maganar tare da miƙa masa ledan Magungunan kana ya ɗaura da cewa.
“Rahama tana jiraku amota”.
Ahankali Moddibo ya tsugunna ya tallafo ta kamar Baby muryanta cike da sanyi tace.
“Yah Mu'allim kabarni zan iya tafiya naji ɗan sauƙi fa”.
Kai ya girgiza tare da cewa.
“Um-um fa bana so”.
Ya faɗa yana gyara mata zama ajikinsa.
Baki sake Dr Jameel ke kallonsa tare da faɗin.
“Ikon Allah”.
Harara Moddibo ya watsa masa kana yace
“Ɗan sa ido”.
Murmushi Dr Jameel yayi tare da bin bayan sa suna Isa jikin Motar Dr Jameel ya buɗe masa gidan baya yasata kana Shima ya shiga Rahama na ɗaya gefen ya zama sun sata tsakiya kana Driver yaja.
Suna ƙoƙorin fita cikin asibitin Moddibo yayi saurin Kallon Driver tare da cewa.
“Kai ya kake gudu irin haka da ƙarfi?”.
Cike da girmamawa Driver yayi ƙasa da Kansa tare da faɗin.
“Kayi haƙuri”.
Kai Moddibo ya girgiza Idanunsa akan Khausar Dake lumshe Ido yace.
“Um-um bani baza ka iya ba”.
Murmushi kawai Rahama tayi al'amarin Yah Aleey da Khausar na masifar burgeta.
Kai Drive ya gyaɗa tare da fita Moddibo kuwa mazaunin driver ya koma har ya shiga sai Kuma ya fito yana Kallon Khausar ya miƙa mata hannu kana yace.
“Fito ki koma gaba”.
Kai ta gyaɗa, tare da miƙa mishi hannun a gefensa ya ajiye ta.
Yana ƙoƙorin saita Motar kan kwalta ya janyo Khausar ya ɗaura kanta kan kafaɗarsa ahankali yake driving tafiyar da zasuyi cikin minti talatin Saida suka dauki awa ɗaya da ƴan mintuna sunayi.
Sunzo dai-dai wani restaurant ya fara ƙoƙorin parking yana cewa.
“Mushiga in siya Miki duk abinda kike so?”.
Idanunta ta buɗe ta kallesa sai Kuma ta girgiza Kai tace.
“Ni Babu abinda nake so kawai mu koma gida inyi wanka in samu in huta”.
Rahama kuwa tana gyara zamanta ta Kalli Khausar da duk jikinta Babu kuzari tace.
“Lalla Khausar idan akwai abinda kike so ki faɗa min ko meye idan munje gida zan dafa miki”.
Kai ta girgizawa Rahama tare da cewa.
“Ayyah Rahama ni Babu ma abinda nake so bana Jin yunwa”.
Moddibo kam ahankali yaci gaba da driving har suka Isa gida yana parking ya fito ya ɗauketa Kai tsaye ya side ɗin Didi ya wuce da ita.
Didi na ganinta ta sauƙe Ajiyar zuciya tare da cewa.
“Sannun ku da zuwa
Ɗiyata ya jikin?”.
Murmushi Khausar tayi ahankali tace.
“Da sauƙi".
Sai Kuma ta juya dinning abinci kala-kala ta ɗebo ta jere mata agabanta tace.
“Toh Maza sauƙo kici”.
Langwaɓar da Kai tayi muryanta asanyaye tace.
“Ayyah Didi na ƙoshi fa bana Jin yunwa”.
Da damuwa Didi ta kalleta tare da faɗin.
“Wannan al'amari yana damuna Khausar am duk laulayi laulayine Amma Wallahi laulayin dake hana cin abinci yafi jikkatarwa da wahalar wa”.
Cikin sauƙe numfashi da tarin tausayinta Moddibo ya fesar da numfashi Idanunsa akan Khausar yace.
“Yanzu Didi Babu abinda za taci Kenan?”.
Kai Didi ta girgiza tace.
“In dai jininka ya ɗauka zaiyi wuya, taci abinci sai dai Ina tunanin in Sha Allahu akwai abinda zan dafa mata zata ci Dan haka nayita fama lokacin da cikin ka”.
Ajiyar zuciya ya sauƙe tare da cewa.
“Toh Didi menene?”.
Tana ƙoƙarin miƙewa tace.
“Toh ba matsala bari in shiga kitchen”.
Kai ya gyaɗa tare da faɗin.
“Toh kafin ki gama bari tayi wanka”.
Kai ta gyaɗa tare da shiga kitchen shi Kuma ya ɗauketa ya haura samansu wanka tayi da ruwan ɗumi kasancewar lokacin har goma yayi kafin ta fito.
Ya fito mata da kayan bacci masu masifar taushi Pink color da ratsin farin da Kansa yasa ka mata kana ya cusa mata gashin kanta a hular net ruwan da aka ƙara mata yasa jikinta ya ɗanyi ƙarfi sai dai fuskarta tayi fayau alamar rama sai dai Kuma ta sake haske sosai yana gyara mata gashinta cikin hular yaji ana knowking ajiyeta yayi bakin gadon kana ya tafi ya buɗe ƙofan Didi da kanta ya gani tsaye iso ya mata suka shiga falon tana kallonsa tace.
“Ina Khausar ɗin”.
Yana ƙoƙarin karban warmer dake hannunta yace.
“Tana ciki”.
Kai ta gyaɗa tare da bin bayan sa suka shiga bedroom ɗin stool ta janyo ta zauna tare da faɗin.
“Sannu Khausar”.
Murmushi tayi tare da cewa.
“Yawwa na warkefa”.
Didi kuwa Warmer ta buɗe Dambun Shimkafa da yaji zogale da gyaɗa kana yaji Vegetables sosai sai tashin ƙamshi yake.
Khausar na gani taji yawunta ya tsinke Didi na kallonta tace.
“Zaki ci ko?”.
Kai ta gyaɗa murmushi Didi tayi Khausar kuwa ahankali ta ɗan gyara zamanta tare da faɗin.
“Didi asamin kadan”.
Kai ta gyaɗa kana ta zuba mata da ɗan yawa ahankali Khausar ta karba ta faraci murmushi Didi tayi tana kallon Moddibo tace.
“In Sha Allahu Zata ci da yawa”.
Murmushi tayi tare da ci gaba da cin dambun Alhamdulillah kuma taci kusan cokali tara kana a hankali ta
ta miƙawa Didi plate ɗin tare da faɗin.
“Na ƙoshi”.
Didi na Kallon Plate ɗin tace.
“Kin ƙoshi Kuma?”.
Moddibo kuwa ahankali ya kalleta tare da sassauta murya yace.
“Ki ƙara mana”.
Kai Didi ta girgiza kana tace.
“A'a barta tunda taci wanna an samu ya zauna acikinta ya Isa kaima haka nayi ta fama da Kai”.
Cike da rauni ya kalleta yana Jin ƙaunarta Aransa yace
“Oh Didi Kiya femin haka nayita wahalar dake”.
Murmushi tayi tare da cewa.
“Na yafe maka tuntuni Babana.
Kai ma bari na Saka maka kaci”.
Bata Jira cewarsa ba ta ƙara masa akan plate ɗin Khausar anutse ya karba ya fara ci ba laifi yaci da yawa Dan sosai ya masa daɗi bayan ya gama Didi tayi musu sallama kana ta ta dauki warmer da kanta ta tafi dasu.
Bayan ta tafi Moddibo ya Mike tare da komawa gefen Khausar ya zauna ya jawota jikinsa ya rungumeta....
*Dan Allah in dai kinsan baki shirya sayaba kada kimin mgn, masu cewa wai sun goda suga number'n nayine, ko kuma a'a bari dai in na shirya zan sake miki mgn, ko kuma yanzu dai kuɗin bai cikaba tukun sai sun cika, ko kuma a wanne gari kike, kai munyi nisa, toh in ba iyayiba ai duk nisan state da kike ba ruwan mota ba inda bazai kai mikiba, nake turawa ƴan ƙasashen wajema. Kuyiwa Allah da Manzonsa in dai in kinsan Baki shirya sayan kaya ba ku daina min mgnar ku bari sai kun shirya,kada kizo ki ɓata min lokaci a banza, wlh ni na tsani harkar karanta, duk bayani na gamayi in dai saya zakiyi ga kuɗin kaya ga account no ga numberta ai sai ki biya kawai kafin kimin mgn. Tunda dai ga alamominshi da duk illar da yakeyi na faɗi in kina dashi faƙat in babu kada ki wani zo kice min bayani dan ko kinzo iya bayanin da zan miki kenan*
Alamomin infection sune kamar haka. Rashin sha'awa. Ƙaiƙayin gaba Kiji idan ya fara miki ƙaiƙayi kamar zakiyi hauka. Warin ko ƙarnin wurin. Fitar farin Ruwa mai fatsi-fatsi. Ƙurajen su ɗan fetso ƙananan ko ƴan manya, melewar fatar wurin, Tusan gaba. Bushewar gaba, Rashin ni'ima. Buɗewar gaba, domin har budurwa infection na iya buɗata. Ciwon mara ko ciki mai tsanani yayi al'ada, rashin haihuwa, domin har baƙin mahaifa take toshewa. Ko kirinƙajin wani abu na miki yawo ƙasan mara, ko jin zafi yayin yin fitsari, da kuma saduwa, da dai sauran abubudann ban lissafa. Sune manyan alamomin infection.
Shin kin kuwa san illar da infection keyi miki, amman kinajin ɗaya daga cikin alamominta kinyi bulum buƙui da ita a jikinki. To bari kiji illolin infection wato cutar sanyi.
Rashin haihuwa, ƙyara da hantara a wurin miji domin muddin kina tare da ita baki da wata daraja a idanu nai, sabida ƙyamas kike ba damshi bare wata ni'ima mai Taste, Kinga kenan shinfida ta lalace, in kuwa shinfiɗa ta lalace dole kiga sauyin fuska, domin su maza dole sunason wurin da kwaranya, zaki kasance baki da wani daɗi da ɗumin da mai gida ke buƙata. Kinga duk tsabtarki da kyanki da iya girkinki