Showing 3001 words to 6000 words out of 218703 words

Chapter 2 - Sakayyah 2 Hausa Novel Complete

da cewa.
“Alhamdulillah dama yanzu nake tunanin in kira ka dan. Moddibo tun safe daya fita bai dawo ba, duk da cewa dama yanzu bai cika dawowa da wuri ba”.
Ajiyar zuciya Malam Arɗo ya sauƙe kana yace.
“Ki zo mutafi”.
Saurin Kallonsa tayi kana tace.
“Ina zamuje”.
Cikin sanyin Murya Malam Arɗo yace.
“Wajen Moddibo zamuje yana asibiti”.
Da sauri ta dafe ƙirjinta sai kuma ta juya ta nufi cikin gida hijabinta ta ɗauko ta sanya kana ta rurrufe kofofin gidan kafin ta fita.
Bayan sun fara tafiya acikin motar Malam Arɗo ya kalli Innayi kana yace.
“An samo gawar Jameelu fa!”.
Cikin tsanananin ruɗu da tashin hankali ta dafe ƙirjinta tare da faɗin.
“Gawar Jameelu kuma?”.
Kai Malam Arɗo ya gyaɗa kana yace.
“Eh gawar Jameelu aka samu sun kashe sa”.
Atake hawaye suka shiga zubowa Innayi cikin tashin hankali da jimami ta saki sassayan kuka tare da addu'o'i.

A dai daren wannan ranar haka kowa ya kwana cikin ƙunci da raɗaɗi azuciya.
Asp da tawagarsa sun koma gida bayan sun gama dukkan abinda ya dace na bincikensu, haka zalika Lamiɗo ma ya koma gida Abba kuwa kwana yayi da gawar Jameelun sa agabansa batare daya rintsa ba.

Asma'u kuwa Hajiya Turai ta jata zuwa ɗakinta Anan ta kwana duk da cewa ba tayi bacci ba.
Bashir kuwa aɗakin ƙannen M Jameel ya kwana tare dasu Aɓangaren Moddibo kuwa haka ya kwana cikin wani irin yanayi shi ba bacci ba kuma kuma shiba Ido biyu ba ba kuma a sumeba.
Ana kiran Assalatun Farko acikin kunnen Moddibo sannu Ahankali ya fara bude idanunsa da yaji sunyi masifar nauyi har ya sauƙesu akan Ummi dake riƙe da hannunsa Idanunta abushe alamar ko rintsawa ba tayi ba bare kuma bacci.
Cikin wata murya mai cike da karaya da kuma rauni yace.
“Ummi”.
Kallonsa Ummi tayi tare da faɗin.
“Na'am Aliyu”.
Girgiza kai yayi yayinda zuciyarsa ke cigaba da bugawa da masifar ƙarfi yace.
“Ummi J ɗina”.
Cike da tausayawa ta rintse Idanunta kana tace.
“Aliyu kayi haƙuri”.
Cije Lips ɗinsa yayi tare da damƙe hannunta acikin nasa kana yace.
“Ummi J ɗina”.
Jinjina kai tayi tare da sauƙe ajiyar zuciya tace.
“Kayi haƙuri kaje kayi sallah duk abinda kake ji Aranka kana so ka faɗa min ka faɗawa Ubangiji”.

Cikin sauri Malam Ahmad dake tsaye ya ƙara so bakin gadon tare da riƙe hannun Moddibo cikin sanyin murya yace.
“Kayi haƙuri kaje kayi alwala”.
Kallon Malam Ahmad Ummi tayi kana tace.
“Toh ni yanzu zan tafi gida”.
Girgiza kai Malam Ahmad yayi tare da cewa.
“A'a ki bari mu tafi gidan Alhj Bashir yanzu”.
Girgiza kai tayi kana tace.
“A'a mu tafi gidanmu dai”.
Girgiza mata kai yayi kana yace.
“A'a gidan Alhj Bashir zamu je acan fa za ayi jana'izar mu tafi can ɗin!”.

Shiru kawai Ummi tayi ahankali.
Moddibo da har yanzu hannunsa ke cikin nata yace.
“A'a Ummi dan Allah muje gidan Abba”.
Kai ta gyaɗa masa cikin sanyi tace.
“Toh shikenan”.
Batare da an sallamesu ba suka fita Moddibo da Malam Ahmad suka shiga gaba Ummi tashiga baya Anutse Malam Ahmad yayiwa motar key kana yaja suka bar Asibitin kai tsaye gidan Abba suka nufa suna isa Malam Ahmad ya danna hong ta cikin ƙaramin ɓulin. Mai gadi ya leƙa jin ana ta danna hong ganin motar da tazo jiya da safe ne yasa ya koma cikin gida tare da sanarwar Abba yaga motar da jiya tazo yauma ta dawo.
Kai Abba ya gyaɗa kana yace.
“Eh kaje ka buɗe musu Maman Jameel ne yanzu aka sallame su daga asibiti kaje ka buɗe musu”.
Kai ya gyaɗa sannan ya buɗe musu gate din suka shiga bayan Malam Ahmad yayi Parking suka fito kai tsaye falon Abba suka shiga.
Zaune suka samesa shi kaɗai a falon hannunsa riƙe da Carbi ya tsirawa kwalin Gawar Jameel Ido.
Ahankali Ummi ta ƙarasa tare da zama agefen kwalin shima Moddibo zama yayi agefen kwalin Malam Ahmad ma ya zauna agefen kwalin sai ya zamana sun saka kwalin Atsakiyar su.
Moddibo kuwa kallon kwalin yayi kana ya kalli Ummi cikin raunin murya yace.
“Ummi yanzu J ɗinane aciki?.
Ummi da gaske J ɗina ne ya rasu!?”.
Kai Ummi ta jinjina kana tace.
“Da gaskene Moddibo, tabbas Jameelu ne yarasu Jameelu ya tafi yabar mu bari na har abada, ba zamu sake ganinsa ko jin sautin muryarsa ba sai dai ahoto”.
Girgiza kai Moddibo yayi tare da ɗaura kansa akan kwalin ya fashe da wani irin kuka me tsuma zuciya cikin sheshsheƙan Kuka yace.
“Yanzu shikenan J ɗina mun rabu har abada bayan yana burin yin Aure ya zauna gida ɗaya da Ummi da ƙannensa yanzu shikenan wannan burin ya tafi”.
Ya sake Rungume Kwalin tare da cewa.
“Yanzu shikenan J ya tafi ya barni shin dawa zan rayu duk wani farin ciki ne da walwala na J ɗina ne shin waye zai fahimcini a duniya? J ɗina ne kaɗai yake iya fuskarta halin da nake ciki shikenan sun rabani da aminina kuma farin cikina!”.
Wani irin tausayinsa ne ke ratsasu Abba kam kasa daure wa yayi ya sunkuyar da kansa ƙasa hawaye na zuba.

Cikin sheshsheƙa Moddibo ya ɗago kansa tare da kallon Ummi idanunsa cike da ruwan hawaye yace.
“Shikenan Ummu sunyi mai kisan gillah, sun hanashi shan ruwa, ya mutu da kishi da begenmu, yana ganin muna kiransa amma bashida damar ɗauka, Ummi ashe duk kiran da mukewa J yana kallon kiran mu!”.
Sai kuma ya kife kansa akan kwalin hawayen sa na sauka akai yace.
“Ummi J yana ganin kiran mu amma bazai iya ɗagawa ba Ummi sun azabtar da J ya mutu da tsananin begenmu da muradin son kasancewa damu Ummi sun cutar da J mutumin da koda ƙwaro baya iya cutarwa bare bil adam shin wani irin zunubi suka aikata!”.

Jin ankira assalatu yasa Malam Ahmad sauƙe ajiyar zuciya tare da cewa.
“Moddibo kayi haƙuri ku tashi muyi alwala mu tafi masallaci”.
Ahankali Moddibo ya ɗago kansa akan kwalin daya jiƙe da hawayensa cikin ransa yace shikenan J ya tafi yabarni bari na har abada shikenan ni kaɗai zan rayu.
Hajiya Turai ce ta shigo falon tare da jan Ummi suka tafi ɗakinta Anan sukayi sallah.

Dole Gawar M Jameel yanda ya kasance a kakkarye ahaka aka yayyafa masa ruwa madadin wonkan kana aka kaisa makwancinsa na gaskiya.
Jana'izar data samu halarta ɗumbin jama'ar domin kafin gari ya waye mutuwar ta zagaye cikin Gembulan da kewayenta har Taraba Yola da dai sauransu.

Rayuwa tayiwa duk wani makusancin M Jameel ƙunci da zafi musamman Ummi, Abba, Moddibo, Asma'u, Bashir daga Jiya zuwa yau sunyi wani masifaffen ramewa kallo ɗaya zaka musu kasan cewa suna cikin tsananin ƙuncin rayuwa musamman Moddibo baki daya ya fita cikin hayyacinsa duk ya gigice ya sake zama wani shiru.

Misalin ƙarfe biyu na rana bayan andawo daga sallar jana'izar M Jameel Lamiɗo ya koma gidansa kai tsaye falon Mommy ya shiga bakinsa ɗauke da Sallama.
Anutse Mommy da Khausar dake zaune suka amsa masa Sallamar.
Cike da kulawa Mommy tace.
“Sannu da zuwa yinin yau duk baka nan sau biyu ina zuwa sashenka”.
Zama yayi akan 3sitter tare da sauƙe ajiyar zuciya kana ya jingina bayansa da jikin kushin ɗin tare da lumshe idanunsa kana yace.
“Eh yanzu na dawo daga jana'iza”.
Cikin sauri ta kallesa tare da cewa.
“Jana'iza kuma?”.
Kai ya gyaɗa mata tare da cewa.
“Eh”.
Gyara zama tayi tare da faɗin.
“Janaizar waye!?”.
Ajiyar zuciya ya sauƙe tare da dafe kansa kana yace.
“Janaizar Jameelu”.
Cikin sauri Khausar ta dafe ƙirjinta tare da kallon Lamiɗo kana tace.
“Abbah waye”.
Kallonta Lamiɗo yayi kana yace.
“Malam Jameelu”.
Cikin tashin hankali Mommy tace.
“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n Jameelu Yayan Asma'u”.
Kai Lamiɗo ya gyaɗa kana yace.
“Eh shi ɗin dai Allah ya masa rasuwa”.
Cike da kaɗuwa tace.
“Innalillahi Ayyah Ummin Asma'u Allahu Akbar duniya yanzu yaron nan kashesa sukayi”.

Khausar kuwa tunda ta dafe hannunta aƙirji ta kasa koda ƙokƙwaran motsi ne wani irin bugawa da masifaffen ƙarfi zuciyarta keyi.
Atake wani irin kuka mai tsuma zuciya ya kufce mata cikin sheshsheƙan kuka mai cike da tausayi da tashin hankali tace.
“Abba Yaya Jameel ya rasu!? Abba kashe Yah Jameel sukayi? Abba me yayi musu da zasu kashesa, suka rabasa da rayuwarsa”.
Kai ya gyaɗa mata kana yace.
“Eh Khausar sun kashesa kisa mafi ciwo".
Sau kuma ya zayyane musu yanda suka samu labarin har suka je wajen da kuma yanda suka samu gawar.
Cike da tausayawa Khausar ke jujjuya kai tana cigaba da kuka yayinda numfashinta ke sarƙewa.

Kallon Mommy da hawaye ke kwaranya daga idanunta Lamiɗo yayi kana yace.
“Tun jiya ne, ai muka samu gasar, ban dai faɗa muku bane, dan kada in hanaku bacci.
Yanzu ku shirya anjima idan anyi Sallar La'asar zan kaiku gidan kuyi musu ta'aziyya”.
Cikin muryan kuka Mommy ta gyaɗa masa kai cike da rauni tace.
“Ayyah Ummin Jameel ta ɗandani mutuwa me raɗaɗi da ƙunan zuciya”.
Ta faɗa tana tuno Ramadan domin ko Rasuwar Ramadan bata samu tayi kuka haka ba bayan Lamiɗo ya sake rarrashin sune ya miƙe ya nufi sashen Hajiya Bunayya ya sanar mata.
Khausar kuwa Kuka takeyi tamkar zata mace.

Bayan anyi sallar La'asar Lamiɗo ya ɗebe su suka tafi gidan Abba.

Suna zuwa falon Hajiya Turai suka nufa Cikin gidan da falon cike yake da mutane ƴan ta'aziyya duk wanda yaji rasuwar M Jameel da kuma yanda aka samu gawarsa saiya zubda hawaye tare da la'antar wa anda suka aikata masa haka.

Asma'u dake gefen Ummi zaune Idanunta cike da hawaye tana ganin Khausar ta fashe da sabon kuka kana ta miƙa mata hannu cikin sauri Khausar ta kamo hannunta tare da zama gefenta ta.
Rungume juna sukay tare da fashewa da wani irin kuka mai tsuma zuciya.
Mommy da Hajiya Bunayya kuwa kusa da Ummi suka zauna.
Mommy na Kallon Ummi taji wasu sabbin hawaye sun zubo mata cike da tausayawa Mommy tace.
“Ummi Sannu”.
Sunkuyar da kai Ummi tayi cike da dauriya tace.
“Toh ya zamuyi Aysha ya zamuyi da hukuncin Ubangiji.
Jameelu ya riga mu gidan gaskiya ya tafi ya barni da gurbin da bansan ya zai cikeminba”.
Kai Mommy ta gyaɗa tare da cewa.
“Kiyi haƙuri Ummi”.
Kasa ƙara sawa tayi sabida kuka yaci ƙarfin ta kawai saita kife kanta gefen Ummi ta shiga rera kuka.
Ajiyar zuciyar Ummi ta sauƙe cikin sanyin murya me ɗauke da ƙuna tace.
“Kiyi haƙuri Aysha haka Ubangiji ya tsara bamu isa muja da lamarinsa ba addu'ar mu suke buƙata muyi musu addu'a Allah ya gafarta musu”.
Cikin sheshsheƙa Mommy tace.
“Ameen”.
Ahankali Mommy ta juya suka gaisa da Hajiya Turai da Hajiya Karima sannan da ƙannen Abban Jameel Hajiya Maryam da Hajiya Fa'iza suka yi musu ta'aziyya.

Khausar dake Rungume da Asma'u cikin Muryan kuka tace.
“Asma'u yanzu da gaske Yah Jameel ya rasu shikenan ya tafi ya barmu!”.
Kai Asma'u ta gyaɗa tare da cewa.
“Da gaske Khausar Yah Jameel ya rasu shikenan gatanmu ya rasu rufin asirin mu ya tafi garkuwan mu ya barmu Inuwarmu wajen fakewar mu ya gushe, bangon da muke jingina muji daɗi ya fadi ƙasa”.
Kasa ƙara sawa tayi kawai ta fashe da kuka me tsuma zuciya.
Cikin sauri Ummi ta girgiza mata kai Araunane tace.
“Kul Asma'u!,Kada ki faɗi haka kada kiyi butulci ga Ubangiji domin shi ya bamu Jameelu kuma shi ya ɗauke mana shi kuma zai jibanci laluranmu muddin mukayi tawakkali”.
Innayi dake gefe ta matso kusa da Asma'u da Khausar ta janyosu jikinta tare da ɗaura kansu akan cinyarta cikin Muryan rarrashi tace.
“Kuyi haƙuri kuyi masa addu'a”.
Ahankali Khausar ta ɗago tare da kallon Innayi kana tace.
“Innayi yanzu shikenan Yah Jameel ya tafi ya barmu har abada baza ku sake ganinsa ba!? Bazai sakeyi mana nasihaba, bazai sake neman al'farma a wajenaba ashe Yah Jameel Wasiyya yayi ta barmin a wancar ranar”.
Shafa kanta Innayi tayi kana tace.
“Khausar kada kiyi kuka muyi masa addu'a shine abinda yake buƙata awajenmu kana mu cika masa dukkan wasiyar daya bar mana”.
Kai Khausar ta gyaɗa kana ta cigaba da kuka mai ciwo har Idanunta suka kumbura.
Sai Bayan sun idar da Sallar Maghariba kafin Lamiɗo ya ɗebe su suka tafi
A wannan daren ranar baki ɗaya haka suka kwana cikin ƙunci zuciya da alhini Moddibo kuwa baya um bare Um-um ko awajen zaman makoki idan akace masa sannu baya magana saidai kallo sai ance Allah ya jikansa kafin yace.
“Ameen ya Allah Nagode”. Iya abinda yake iya faɗi kenan.

Haka rayuwa tayi musu ƙunci da ɗaci haka aka ɗauki tsawon kwanaki bakwai ana zaman makoki har awannan kwanaki kullum cikin gida da waje a cike yake da masu zuwa ta'aziyya.
Washe garin rana ta takwas da safe Moddibo na fita bai nufi ko ina ba sai gidan Ummi bakinsa ɗauke da Sallama yashiga falon zaune ya sameta hannunta riƙe da carbi ta zubawa waje ɗaya ido.
Jin Sallamar sane yasa ta ɗago kanta tare da tsira masa Ido agefenta ya zauna.
Cikin sanyi tace.
“Babana”.
Ahankali yace.
“Na'am Ummi”.
Cike da tausayawa Ummi tace.
“Babana kalli yanda ka sake dawowa fa yaushe zaka sawa ranka dangana ne? Kadafa muyi abinda Allah bayaso”.
Batare da yace Uffan ba yayi ƙasa da kansa yana jin wani irin zafi azuciyarsa.
Jin muryarsa yasa Asma'u dake Bedroom ta fito tare da zama agefensa kana ta gaishesa.

Ahankali Moddibo ya juya ya kalli Ummi kana yace.
“Ummi yanzu a Duniya babu abinda nake buri daya wuce ingano su waye suka sace J sannan suka yi masa kisan gillah ina so insani. Ummi inaso inyi bincike akai ina so inga lallai a hukunta su kwatankwacin zalinci da suka mana”.
Ajiyar zuciya Asma'u ta sauƙe tare da cewa.
“Aikuwa Yah Moddibo Khausar tana da dan abinda ta sani.
Domin ranan da muka rabu da Yah Jameel na karshe aranan ne ya maida Khausar gida kuma tace mana.
Taga wata mota na binsu.
Ajiyar zuciya Ummi ta sauƙe kana tace.
“Amma Babana Meye amfanin bincike bayan sun kashesa!?”.
Cikin sauri yace.
“To ai Ummi nan nema yake da amfani tunda suka kashesa dama mun biye musu ne saboda munji tsoron kada su kashesa shiyasa mukabi tsarinsu!”.
Girgiza kai Ummi tayi kana tace.
“Toh amma dai ni inaganin barin shi yafi A'ala kada kai ɗinma da ka rage mana su cutar mana da kai”.
Sam Ummi ta rigada ta saki komai na duniya shiyasa duk yadda yaso ayi mgnar a sake buɗe file din binciken taki.
Fahimtarsa bazata yardabane yasa ya nuna mata ya hakura.
Kallon Asma'u yayi tare da miƙewa kana yace.
“Asma'u zamuyi magana”.
Kai ta gyaɗa sannan ya fice.

Yau ya kama sati biyu da rasuwar Ramadan wanda yayi daidai da kwanaki sha biyu da jana'izar M Jameel.
Acan gidan Lamiɗo kuwa da misalin karfe sha biyu na rana Hajiya Ruƙayya da Mommy da kuma Khausar na zaune afalo suna hira kamar daga sama suka jiyo Sallamar Hajja Nana da faɗin.
“Assalamu Alaikum”...!

*Kada kyiwa labarin bahagon fahimta. Wasu abubuwa na cikin Labarin gaba ɗaya gaskiyane ya faru da gaske. Ina mai roƙonku da Allah kuyiwa Jameel Addu'o'i Allah ya jiƙamsa da rahama ya kuma toni asirin waɗanda sunka saceshi suka kasheshi kisa mai muni. Ku sashi a addu'o'i ku, domin Wallahi tallahi rasuwar Jameel gsky ne kuma ya faru, da gaske wanda nasan mafi akasarin mazauna Adamawa zasu san labarin rasuwar Jamilu matashi mai Kekkyawan ɗabi'un sun kashewa sun bar mahaifiyarsa da ƙunshin a zuciya, sun sa mahaifinshi a rauni mai ciwo. Yah Allah ka jiƙan Jamilu kayi masa rahama da gafara, ka tausashi zuciyar iyayensa ka ƙara zamewa mahaifiyarsa Gatan*


🤝🏻KADA KUMA KU DAMU ZAKUSHA MAMAKIN YADDA LABARIN ZAI SAKU FARINCI DA SHAUƘI ZAKUSHA MMKIN YADDA LAMARIN ZAI BADA CITTA, KU DAI KU BIYONI KUSHA LABARI, WACCE BATA BIYA TA BIYA.


By
*GARKUWAR MARUBUTA**SAKAYYAH book 2... Page 2*


Spbnɗettett. Cikin ɗan sakin fuska Mommy ta miƙe tare da cewa.
“Wa'alaikum Salam Hajja Nana sannunku da zuwa”.
Hajja Nana na zama aɗaya daga cikin kujerun falon tace.
“Yawwa Aysha sannunki”.
Cike da farin ciki Khausar ta miƙe tare da riƙe hannun Dije kana ta jata suka zauna akan 2sitter.
Murmushi Mommy tayi tare da juyawa ta shiga kichen.
Ta kawo mu abin taɓa,
Fuska ɗauke da murmushi Khausar dake riƙe da hannun Dije ta juya tare da kallon Hajja data zuba mata Ido, cikin sanyi tace.
“Maraba Hajja Nana ya gida ya Baffa Liman, Baffa Jauro,Baffa Sadu, Baffa, Garga Yaya Sadik? Duk kowa da kowa dai”.
Harara Hajja Nana ta watsa mata kana tace.
“Sai yanzu kika ganni wacce ta dameki ai gashi tun shigowarta kika jata jiki, kuke gaisawa idan kin matsu da sanin yanda suke sai kije ki duba su da kanki”.
Uhum kawai Khausar ce tare da loggobar da kai dan har yau bata dawo dai-dai ba cikin sanyi tace.
“Kai wannan tsohuwa ke dai akwai ki da kishi, da mita ina ce dai yanzu gashi na gaishe ki amaimakon ki amsa shine sai kin cakaleni”.
Riƙe haɓa Hajja Nana tayi tare da maka mata Harara kana tace.
“Yo ki riƙe abinki mana ko wata tsiyar gaisuwar ki zai min?”.
Ta ida maganar tare da sauƙa ta ɗauki Cup ɗin tea da Mommy ta zuba mata kana ta kurɓa”.
Taɓe baki Khausar tayi tare da cewa.
“Oho dai ai ko bazai miki amfani ba kin nema bare ma amfanin zai miki”.

Mommy da fitowarta daga kichen kenan tayiwa Khausar alamar tayi shiru kana ta zauna gefen Hajja Nana cike da girmamawa ta gaisheta tare da tambayar mutane gida.

Miƙewa Khausar tayi tare da riƙe hannun Dije tace.
“Zo mushiga ciki”.
Saurin Kallonta Hajja Nana tayi tare da faɗin.
“Dawo ki zauna”.
Tsayawa tayi tare da kallon Hajja Nana still hannunta na riƙe da Dije tace.
“Toh me kuma zan miki?”.
Sassauta murya Hajja Nana tayi tare da faɗin.
“Ke kam ki dawo ki zauna mana”.

Sake hannun Dije tayi tare da tsare Hajja Nana da ido kana tace.
“To wai mai zan miki zamuje muyi hiranmu irin na ƴan Uwanta kema kuyi hiranku mana ko sai dole na zauna ne?”.
Harara Hajja Nana ta maka mata tare da cewa.
“Wato ke dai daga zuwana sai kinsa mun raba hali, ko ba a isa ace yi kiyiba sai kinyi musu?”.

Kallon Khausar Mommy tayi tare da cewa.
“Ke dai ki dawo ki zauna mana koma menene ai zaki ji”.
Kai ta gyaɗa tare da janyo hannu Dije suka zauna gefen Mommy ya zamana Khausar na fuskantar Hajja Nana.
Hajja Nana kuwa zamanta ta gyara tare da fuskantar Mommy Cike da isa, gadara, taƙama, Iko, kana da Power da take jin tana dashi akan Khausar da kuma rigima irin ta tsofaffi tace.
“Alhamdilillah mun godewa Allah daya nuna mana lokacin da Khausar ta gama karatu lafiya”.
Cikin sauri Khausar ta kalleta tare da cewa.
“An gama karatu lafiya ko kuma anfara taka matsayin karatu? Ko tsakiyar karatu ma naje ne bare akai ga maganar gamawa?”.
Wani kallo Hajja Nana ta watsa mata tare da cewa.
“Karatun ƙa'ida kam nasan angama shi tunda kinyi

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login