Showing 180001 words to 183000 words out of 218703 words
aiko ganinta ne yasa ta buga tsalle cike da matsanancin farin ciki tace.
“Addah Khausy”.
Da wani irin sauri Khausar ta janye hannunta dake cikin nasa ta ruga da gudu.
Atsorace ya sanya tafin hannunsa biyu ya dafe kansa kana ya motsa laɓɓansa tare da faɗin.
“Ya Salam ki daina gudun nan”.
Ina bata saurareshi ba da gudu ta rungume Raudat Raudat kuwa tsalle ta riƙa yi ajikinta tana cewa.
“Oyoyo! Oyoyo Addah Khausy!, Mommy Addah Khausy!! Tazo Addah Khausy!!!,Oyoyo”.
Cike da matsanancin farin ciki Khausar ta ɗaga ta sama ta riƙa juyawa da ita a tsakiyar gida wanda hakan ne yasa baki ɗaya mutanen gida suka san cewa Khausar tazo.
Dai-dai lokacin kuma Haiydar ya fito daga ɗakinsa.
Da gudu Sulaiman ma ya fito daga sashen Hajiya Bunayya atare suka rungumeta suna faɗin.
“Oyoyo Addah Khausy ”.
Khausar kuwa cike da matsanancin farin ciki take jujjuyawa atsakiyarsu ruggume da Raudat tsam a jikinta.
Jin sowarsunw yasa Momy dake zaune falonta ta miƙe da sauri ta fito jin sautin muryansu na tashi cak ta tsaya ta riƙe ƙafan Falon tare da tsirawa Khausar idanu tana kallonta cike da so, ƙauna, bege, kewa irin na uwa da yarta.
Khausar kuwa sai juyawa take dasu tana ƙyalƙyala dariya sai kuma tayi saurin sake su ta nufi Momy tana gudu tare da faɗin.
“Oyoyo Momyna”.
Runtse idanunsa yayi sai kuma ya ɗan ɗaga saitin muryansa yace.
“Dan Allah Momy kice mata ta daina gudun nan zata yiwa kanta Illah fa”.
Murmushi Momy tayi tare da kallon Khausar kallo ɗaya ta mata ta fahimci tana da ciki wanda har ya ɗan tasa ga wani irin kyau da tayi sai ƙelli take zubawa ga ɗan cikinta daya turo gwanin kyau ya zauna a jikinta cib da cib sai ƙugunta da ya ƙara faɗi.
Cikin sauri da bege Minti ta rungumeta asanda ta isa gareta sau kuna tace.
“Ke meyesa bakya girmane. Khausar wannan guje-guje har yanzu baki barshi ba”.
Murmushi tayi tare da sake Momy sai kuma ta sake rungumeta kana ta sake ta ta kuma sake rungumeta ɗan turata Momy tayi tare da faɗin.
“Ni matsa ahanya Bismillah Moddibo shigo".
Sai alokacin Haiydar ya miƙawa Moddibo hannu kana yace.
“Yah Moddibo Bismillah mu shiga”.
Kai Moddibo ya gyaɗa suka shiga bayan sun zauna a falo Momy da kanta ta kawo musu Drinks da Snacks da ruwa ta ajiye musu agabansu.
Raudat kam cike da farin ciki ta kwanta kan Khausar tana ta nuƙurƙusata,
ahankali Moddibo ya riƙo tafin hannunta yace.
“Kiyi haƙuri Aunty Raudiy adaina danne Adda Khausy kar aji mata ciwo”.
Cikin jin daɗi Momy ta kawar da kanta jin yanda yake mata magana cike da kulawa sai kuma ta miƙe tace.
“Bismillah kusha ruwa bari nazo ”.
Ta ƙarashe maganar tana fita kai tsaye bedroom ɗin ta ta wuce.
Acan ɓangaren Hajiya Bunayya kuwa a dai-dai lokacin zaune take aruwan zafi idanu ta tsirawa ruwan tana kallon ƙananun tsutsotsin farare masu jajayen kai wanda ga duk kan alamu sune suke addabar ta da jarabar ƙaiƙayi wanda zuwa yanzu tsakaninta dubaranta da gabanta ya wawake tuni sun fafeta ta kashin ta da gabanta ya haɗe saboda masifar ƙaiƙayi da yanda suke cinta taje asibiti har ta gode Allah abanza kana ta kira matar data haɗa su da Boka Gillaw.
Taje ta faɗawa Boka Gillaw ga abinda yake faruwa yace wannan sakamakon aikin su suke girba babu abinda zai iya kada su sake kiransa, dama shi ya gaya musu idan buƙata ta biya su biya kuɗi idan kuma bai biya ba shikenan suji da kansu.
Matar ta tambaye shi mai zai basu amma yace babu abinda zai basu wannan Sakayyar sune babu wanda ya isa ya kawar da Sakayyar zunubansu ne ya sauka akan su Babu ruwansa suji da kansu shima yaji da kansa.
Tuno waɗanan maganganun ne yasa ta fashe da marayan kuka mai cike da nadama mara amfani, tana cikin kukan ta jiyo sautin muryoyi ana cewa Oyoyo Addah Khausy ahankali ta juye ruwan tana kallon tsutsotsin masu masifar gudu da ƙaiƙayi dole sai ta shiga ruwan ɗumin ne take ɗan jin sauƙi.
Tana fitowa daga Bathroom ɗin ta zaune gefen Amina dake kwance kan gadon wacce ta rame ta zama wata halitta daban kamar ƙwarangwal tana nan tamkar wacce babu numfashi ajikinta kuka ta fashe dashi tare da cewa.
“Amina kinga Sakayyar abinda mukayi ko. Ubangiji ya kama mu tun a duniya Allah ya kamu da Sakayyar tarin zunubanmu Amina ya zamuyi?”.
Araunane Amina ta ɗago kanta cikin muryanta da baki ɗaya ya koma na wata halitta ta kalleta duk ta disashe baki ɗaya kamanninta da siffofinta ya fara zama na maciji ne ko menene dai ho da kyar ta buɗe bakinta tace.
“Umma munemi gafarar wa'anda muka cutar tun kafin dare ya mana ”.
Cikin rauni da zubda hawaye Hajiya Bunayya tace.
“Dole ma mune mi gafarsu su yafe mana nasani wannan Sakayyar abinda nata yiwa wannan baiwar Allah ne, da abinda nayi wa ƴarta da kuma yanda nayi ta zubar mata da ciki sannan nasa aka kashe Ramadan yanzu shine Allah ya jarabceni da wannan abin”.
Kuka sosai Amina ta fashe dashi tana ji kamar adawo mata da lokacin baya ta gyara kuskurenta.
Ita ma Hajiya Bunayya kuka ta fashe dashi Asiya ce ta shigo ta zauna gefen su ta shiga rera kuka cikin rauni da tausayinsu tace.
“Umma ku nemi gafarar Momyn Khausar da Khausar duk wanda ku kasan kun cutar kunemi gafarar su Allah gafururrur rahim ne shima zai yafe muku sai kuma ku nemi gafarar Allah akan shirka da kuka yi Allah ya yafe muku ”.
Cikin raunin Murya da shesh-sheƙa Amina ta gyaɗa mata kai tare da faɗin.
“In sha Allah zamu nema amma Addah Asiya ki taya mu basu haƙuri ”.
Kai Asiya ta gyaɗa tare da cewa.
„In sha Allah yanzu ma mukayi waya da Samira Sani take cemin itama jiya baki ɗaya Momyn ta kwana tayi tana ta ihu acikin gida gaba ɗaya tazama kamar mahaukaciya, ita tana jin tsoro yanzu zata dawo nan ma”.
Atsorace Hajiya Bunayya ta dafe kuncinta tace.
“Yau sun shiga ukunsy Hajiya Lami fa ta haukacene”.
Cikin sanyi da zubda hawaye Asiya tace.
“Haka dai alamu suka nuna Umma Allah ya yaye muku ya dubeku da idon Rahama”.
Cikin rauni da tarin tsoro Hajiya Bunayya tace.
“Ameen”.
Amina kam sai hawaye take tana nadama da danasanin abinda ta aikata.
Acan Falon Momyn kuwa bayan Moddibo yasha ruwa kana yaci Snacks da Drinks Momy ta fito suka gaisa bayan sun gaisa ta kallesa da kulawa tace.
“Ina su Didi kuma?”.
Sake sunkuyar da kansa yayi tare da cewa.
“Momy su Didi suna gida amma sunce zasu ɗan fito zuwa azahar, sannan zasu fara ta gidan su Ummu kafin suzo”.
Dai-dai lokacin kuma Asma'u ta shigo Falon bakinta ɗauke da sallama kasancewar Haiydar ya kirata ya sanar mata Khausar tazo gida.
Khausar na ganinta ta miƙe da tsalle kana ta haɗa da gudu suka rungume juna da Asma'u suka fara juyawa atsakiyaar Falon.
Cikin tsuke fuska Moddibo ya kalli Asma'u tare da faɗin.
“Asmau me haka ki sake ta?”.
Ahankali Asma'u ta sunkuyar da kanta ƙasa sai kuma ta saki Khausar ta tsugunna gefen Moddibo cike da ladabi tace.
“Yah Moddibo sannu da zuwa Ina yini”.
“Lafiya”.
Ya faɗa yana ɗan sake Fuskara sai kuma yace.
“Ke baki ga yanayin yanda ƙawar taki take bane kike mata irin wannan rungumar?”.
Dariyar dake cinta ta danne ganin yanda Khausar ta Cunno baki kana tace.
“Yah Moddibo ayi haƙuri”.
Yana murmushi yace.
“In sha Allah yanzu dai akiyaye”.
Kai ta gyaɗa tare da miƙewa ta riƙe hannun Khausar suka nufi bedroom ɗin ta.
Ganin haka yasa ya miƙe tare da cewa.
“Momy bari in fita dan su Dr Jameel na jirana zamuje gida Abban Jameel ”.
Mommy na gyara mayafinta tace.
“Ayyah ai nima Jameel ɗin nan ina so akawo minshi in ganshi Haiydar yata bani labarinsa”.
Cike da girmamawa yace.
“In sha Allahu Momy za'a kawo miki shi”.
Murmushi tayi tare da faɗin.
“Toh ka gaishe su”.
Amsawa yayi kana ya fita.
A dai-dai lokacin kuma Didi, Lalla Khadijah, Lalla Hafsat, Suna gidan Ummin Jameel duk sun gaisa da ƴan Uwanta wanda suka fara taruwa saboda bikin bayan sun gama suka fito zuwa gidansu Momyn Khausar.
Suna shiga Falon dai-dai lokacin Asma'u da Khausar na kitchen Khausar har mamakin kanta take saboda ƙosai da kunun gyaɗan da taci da safe, kana yanzu kuma Asma'u da kanta ta tuƙa mata tuwan Semovita da miyar ɗanyen kuɓewa aƙaramin dining Dake kitchen ɗin suke zaune.
Khausar kam ta kasa daina mamakin kanta yanda take cin tuwon sosai kallon Asma'u da itama tayi wani irin kyau na ban mamaki tayi ta fito a asalin amarya tace.
“Wallahi Asma'u har mamakin kaina na keyi rabona da abinci hakafa nafi wata huɗu”.
Murmushi Asma'u tayi tare da cewa.
“Ikon Allah baby ɗan albarka yasan yazo garinsu kenan”.
Murmushi Khausar tayi tare da sunkuyar da kanta ta ɗan kalli cikin,
dai-dai lokacin kuma suka jiyo sallamarsu Didi sun shigo gidan cikin wani irin...
By
*GARKUWAR MARUBUTA*
Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/HCji7xLpR1VEJGYcZJMP6k
KAZAURE COLLEGE OF NURSING SCIENCES (KCONS)
Lafiya Uwar jiki, Kuma sai da lafiya ake morar rayuwa. Kazaure College Of Nursing Sciences (KCONS) ta kawo muku ingantaccen tsarin koyar da jinya da unguwar zoma, mun himmatu wajen samar da kwararrun ma'aikatan jinya da unguwar zoma a fadin Nigeria da ma matakin duniya baki daya, a KCONS mun tanadar muku kwararrun malamai, ingantaccen yanayi da tsarin koyo da koyarwa kai harma da tsarin e-learning, ka zalika akwai tabbataccen tsaro a dakunan kwanan dalibai maza da mata, bugu da kari kudin makaranta dai-dai aljuhu, KCONS munanan a lamba 5 layin fadar sarki dake kan hanyar kano zuwa daura a Kazaure jahar Jigawa, za'a iya samummu a shafikanmu na facebook da instagram @KCONsciences domin bayani, za'a iya tuntubanrmu a wadannan lambobin, 07066542055, 08035298851, ko shafin mu na yanan gizo @ http://kcons.edu.ng/admission KCON sciences kan turbar aiki da kwarewa muka shahara.
Zare idanu Asma'u ta miƙe tare da kallon Khausar tace.
“Kamar su Didi ce suka shigo?”.
Kai Khausar ta gyaɗa tare da cewa.
“Ehem sune ya akayi?”.
Yarfe hannu tayi sai kuma ta girgiza kai kana tace.
“Wayyo Allah nikam zan fita ta ƙofar kitchen bana zaton zan iya haɗa ido da ita”.
Dariya ce taso kufcewa Khausar amma sai ta daure bata yiba tace.
“Meyesa?”.
Cikin sauƙe ajiyar zuciya Asma'u ta ɗan kalli ƙofar tare da faɗin.
“Wallahi kunyar su nake ji”.
Baki sake Khausar ke kallonta kafin tace.
“Dallah tafi daga nan muje ki gaishesu idan yaso sai mu tafi gidan Ummi tunda su suna nan”.
Kai ta gyaɗa tare da faɗin.
“Toh shikenan ”.
Kana suka fito Falon Khausar ce agaba Asma'u na biye da ita cike da kunya.
Didi na kallon Asma'u ta miƙa mata hannu tare da faɗin.
“A'a ɗiyata ƴar Albarka Masha Allah fatan mun same ku lafiya?”.
Kai Asma'u ta gyaɗa batare data kalleta ba kana ta gaishesu ɗaya bayan ɗaya.
Anutse Khausar da cikinta ya ƙara bayyana dabida samun cin wadataceccen abinci ta juya jin Lalla Hafsat na cewa.
“Ƙanwata ya dai an samu anci abinci kuwa?”.
Murmushi Momy tayi tana kallon Lalla Hafsat tace.
“Dama bata ci abinci ko?”.
Kai Didi ta gyaɗa cike da tausayi tace.
“Ina kuwa take cin abinci sai dai tai ta shan fruits”.
Mommy na kallon Khausar dake sunne kai kana tace.
“Ikon Allah nan kuwa tunda tazo cikinta bai huta ba haba ashe shiyasa take ta ci ba sausauci”.
Asma'u ce ta karɓi zancen da cewa.
“Yanzu ma tuwo da miyar kuɓewa tana ɗa a kitchen kamar me”.
Khausar kuwa ɗan hararan Asma'u tayi.
Didi kam da mamaki ta kalli Khausar tare da faɗin.
“Ikon Allah Alhamdulillah ai haka akeso”.
Murmushi Lalla Khadijah tayi kana tace.
“Ai dama wani cikin hakane in Kaje unguwa sai kiga Kaci abinci idan kuma agidanka ne ba zaka iya ba”.
Ahankali Khausar ta sake kasa da kanta cike da kunya wani irin masifeffen kunya ne ya mamaye ta jin yanda ake ta maganar tana da ciki.
Batare data ɗago kanta ba ta riƙe hannun Asma'u tare da cewa.
“Mu tafi”.
Miƙewa Asma'u tayi kana suka shiga bedroom ɗin Khausar ta dauko mayafinta kallonta Momy tayi tare da cewa.
“Ina zaki je?".
Tana ƙoƙarin gyara mayafinta tace.
“Zamuje gidan Ummi ne”.
“Toh kin tambayi mijinki ne?".
Cewar Momy.
Murmushi Didi tayi kana tace.
“A Babu Matsala ai taje tunda ziyara ne”.
Miƙewa sukayi suka fita kai tsaye Side ɗin Hajiya Bunayya suka shiga bakinsu ɗauke da sallama.
Falon shiru ba kowa sake sallama Khausar tayi da ɗan ƙarfu.
Asiya dake bedroom ɗin tun ɗazu suna kukane tashin hankali d suke cikine ya hanata fitowa, jiyo muryar Khausar ɗin ne yasa tayi saurin miƙewa ta fito idanunta cike da hawaye ga kumburar da sukatu Khausar ta rungumeta tare da cewa.
“Oyoyo Khausar sannu da zuwa fatan kunzo lafiya? ya gida yasu Didi da kowa da kowa?".
Khausar na sake ruggume ta tace.
“Duk lafiya lau".
Ta ƙare maganar tana kallon idanunta da Fuskanta da suka kumbura alamar taci kuka da damuwa tace.
“Addah Asiya lafiya kuwa?”.
Ɗan Murmushi tayi tare da cewa.
“Lafiya lau Khausar ”.
Kai Khausar ta girgiza tana nazartan yanayinta tace.
“Amma Addah Asiya kamar kuka kika yi fa dan Allah ki faɗa min dakuwarki na tabbatar akwai abinda ke damunki”.
Araunane Asiya ta maida hawayen dake ƙoƙarin zubo mata tace.
“Amina da Umma ce babu lafiya shiyasa hankalina yake tashe”.
Da damuwa Khausar ta kalli Asma'u da itama ita take kallo kana tace.
“Subhanallah me ya sami Aminan?”.
Ahankali Asiya tace.
“Bata da lafiya ne”.
Da sauri Khausar ta ɗan kalli Falon tare da cewa.
“Toh Ina take?”.
Bedroom ɗin Hajiya Bunayya ta nuna mata tare da faɗin.
“Tana ciki”.
Cike da kulawa da tarin tausayi tace.
“Toh mu shiga mana”.
Kai Asiya ta gyaɗa kana tayi gaba Khausar da Asma'u na biye da ita.
Suna shiga Idanunsu ya sauƙa kan Hajiya Bunayya dake zaune gefen gado tana sharɓan Kuka cikin sauri Khausar ta ƙarasa shiga kana ta zauna gefen Amina ta riƙo hannunta acikin nata cikin raunin ganin halin da Amina ke ciki tace.
“Innalillahi wa'inna alaihi raji'un Amina meyesa meki?,me yake damunki?,Ya ilahi ya mujibud da'awati ya hayyu ya ƙayyum meye haka yake damunki?”.
Ƙasa furta komai Amina tayi sai hawaye dake ambaliya saman fuskarta kallonta ta mayar kan Asiya kana ta cigaba da faɗin.
“Addah Asiya meke damunta?”.
Kai Asiya ta girgiza tare da cewa.
“Muma bamu san meke damun Amina ba”.
Muryanta na rawa tace.
“Yaushe taxo to?”.
Kai Asiya ta girgiza tare da faɗin.
“Abin sai ahankali Khausar am”.
Cikin matsanancin Kuka Amina ta damƙe hannun Khausar dake cikin nata kana muryanta cike da rauni tace.
“Khausar ki yafemin”.
Da sauri Khausar tace.
“Ni kuma me kikayi min”.
Cikin rawan murya Amina tace.
“Ai ba abinda ban mikiba na cutar dake arayuwa Khausar ki yafemin”.
Cikin sauri Khausar ta girgiza mata kai Idanunta na zubda hawaye.
Hannunta ta ɗaura akan bakinta ta datake wani irin zaro harshe waje kana tace.
“Ba kiyi min komai ba Amina ki daina kuka Allah Ubangiji ya yaye miki abinda yake damunki Allah ya baki lafiya Amina”.
Kallonta ta mayar kan Hajiya Bunayya jin yanda shesh-sheƙa kukanta ke tashi tace.
“Ummu kema kina kuka toh ita kuma ya zata yi aike zaki ƙarfafa mata guwwa!”.
Amaimakon tayi magana sai ta zame ƙasa ta gurfana gwiwoyinta gaban Khausar tare da riƙe hannunta cikin wata raunatacciyar murya mai sanya tausayi tace.
“Khausar ki yafe min nasan na cutar dake a rayuwata na cutar da mahaifiyar ki nasan kin sani na cutar daku”.
Ahankali Khausar ta cije gefen bakinta kana ta jujjuya kanta still hawaye na bin fuskarta tace.
“Bakomai Umma Allah ya yafe mana”.
Kuka sosai Hajiya Bunayya ta fashe dashi tare da cewa.
“Khausar na cutar daku da cutarwa mafi muni azaman da mukayi nasan ke kina zargina ”.
Kai Khausar ta girgiza tare da faɗin.
“Astagfirullah ai nima zargi nake Umma Allah ya yafe min kan zargin dana miki saboda Manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallama ya ce. _Azzannah Zhambu Walau kana haƙƙun_”.
Araunane Hajiya Bunayya ta girgiza kai tare da cewa.
“Ba zargi bane Khausar dagaske ne tunanin ki akaina, ina cutar daku gashi Allah ya muku Sakayyah alokacin da bakuyi tunani ba ba kuma san ina yiba. Allah yayi muku Sakayyah alokacin da banyi Aune ba don Allah Khausar ki roƙamin gafarar wurin Momynki ku yafemin”.
Asma'u kuwa cikin yanayin tsoro take kallon Amina data kasa tantance yanayin da take ciki.
Hajiya Bunayya kuwa cikin tarin nadama ta cigaba da faɗin.
“Kiga yanda Allah ya jarabceni kiga yanda Amina ta dawo kiga abinda Naseer ya mana Naseer yaje ya cutar min da yarinya.
Jiya da yamma yazo ya wurgar mana da ita ya tafi ko shigowa cikin gidan nan baiyi ba.
Ya juya ya tafi yau ya tafi Indi'a yabar mu da jidali Uwarsa da Ubansa sai binmu sukayi da rashin mutunci”.
Nan ra kwashe duk labarin da Amina ta basu na macijin da yake fitowa yasha nononta da yadda ta kasa faɗawa kowa da kuma yadda yake hanata faɗa ta kara da cewa.
“Ashema shine yake juyawa ya zama macijin yayi ta shan nononta sai jiyan duk yake gaya mata ya aureta ne dan tayi tsafi da ita ya samu biyan buƙatar rayuwar duniyar sa, yanzu kuma buƙatarsa ya biya ya haɗota da takardar saki uku yazo ya wurgar mana da ita”.
Hawayen da yaƙi tsayawa Khausar ta share tare da faɗin.
“Innalillahi wa'inna alaihi raji'un Uncle Naseer”.
Sai Kuma ta juya ta kalli Asma'u da itama ita take kallo Asma'u kuwa cikin sanin muguwar ɗabi'arsa tace.
“Hmmmm Uncle Naseer zaiyi abinda yafi haka ma”.
Hajiya Bunayya kuwa cigaba da cewa.
“Khausar nasan Sakayyar abinda nayi miki ne nayi muku sihiri na biku da bita da ƙulli”.
Daga nan ta tsinke da surutai duk wani abu data aikata musu saida ta faɗa.
Khausar kam baki ɗaya ilahirin jikinta rawa ya fara cikin tsananin kiɗima mamaki da al'ajabi gami sa tsoro.
Duk da cewa tana zarginta bata taɓa tunanin abin nata yakai haka ba.
Hajiya Bunayya kuwa miƙewa tsaye tayi sai kuma ta durƙusa tana ƙoƙarin naɗa zaninta tace.
“Khausar kiga yanda tsutsotsi suke cina yanda na dawo”.
Cikin sauri Khausar ta riƙe hannunta tare da cewa.
“Innalillahi wa'inna alaihi raji'un Umma kada ki nuna min Ummu kiyi addu'a Allah ya yaye miki kuma in Sha Allahu nima zan miki addu'a nikam na yafe miki”.
Idanunta ta mayar kan Amina kana tace.
“Amina Allah ya baki lafiya Ubangiji ya yaye miki zan faɗa wa Yah Moddibo ya miki addu'a Allah yaye miki kuma zan sa Dr Jameel zai zo ya duba ku in Sha Allahu Allah yaye muku ya baku lafiya mai amfani mai albarka Allah ya yafe muku shurkar da kukayi”.
Da karfi Hajiya Bunayya ta fisge hannunta dake cikin na Khausar kana tace.
“Um-um Khausar ki bari in nuna Miki abinda ke cina kiga *Sakayya* data diromin”.
Cikin sauri Khausar ta girgiza kai tare da cewa.
“A'a Umma basai kin nuna min ba wannan bai kamata