Showing 177001 words to 180000 words out of 218703 words

Chapter 60 - Sakayyah 2 Hausa Novel Complete

cikin Sabgoginmu yana hana mu Kidnapping yanda suke a yankin, dan da in sun sato mutane a nan cikin tsaunukan dake zagaye dasune suke zuwa su ɓoye mutane, sai an biya su kuɗi wanda in za'a samu mutane a wurin kai tsaye cewa za'ayi Fulani wurin ne suke satosu.
saboda haka ne in sunje sunyi kidnapped shi yake hana su sakewa, kuma basu isa su ɗauki dabbobi yanda suke so saboda kasancewar mutum mai sa ido da kuma Jarumta”.
Cikin tafarfasan zuciya Sheikh Jabeer ya dasa masa bindiga akansa kana yace.
“Shi kuma Malam Jameel meya muku?,”.
Cikin haki da fusgar numfashi yace.
“Shima Malam Jameel manyan mune suka bamu kwangilar kashe sa Saboda shine mutum na farko daya buwayi al'ummar mu da wa'azi wanda yake zama sanadin da matasanmu da yawa suke Musulunta shiyasa manyan mu suka bamu umarni shi da Moddibo mu haɗa su mu kashe su shine abinda zai fi mana sauƙi da kwanciyar hankali idan ba haka ba zasu janye mana ra'ayi da tunanin matasan mu”.
Dafe kai Sheikh Jabeer yayi tare da cewa.
“Innalillahi wa'inna alaihi raji'un”.
Cikin tashin hankali Moddibo ya dafe kansa tare da faɗin.
“Hasbunallahu wani'imal wakin".
Sai kuma ya koma ya zauna yana dafe kansa da hannun ɗaya yayinda ɗaya hannun kuma ke tallabe da Khausar cikin kaɗuwa yace.
“Ana zaton wuta amaƙera sai gata a masaƙa ina zaton kashe J akayi tunda aka kamasa na tabbatar cewa magautane acikin kashe sa amma duk atunanina akwai sa hannun ɗaya daga cikin Yadikkonsa ashe babu su Astagfirullah Allah na tuba ka yafe min da zargin da Nai ta yiwa Hajia Turai da Karima Allah na tuba”.
Cike da rauni da tausayinsa Khausar ke zubda hawaye, shi kuwa Modibbo cikin rauni ya cigaba da cewa.
“Manzon Allah (S.A.W)da kansa yace _Azzhana zhambu Walau kana haƙƙun_ sai naje na nemi yafiya da gafarar Hajiya Karima saboda duk tunanina ko ita ko Hajiya Turai akwai sa hannun ɗaya daga cikinsu aɓacewan J ashe suma ba abinda suka sani waɗan nan kafiran maƙiya Allah da Manzonsa suka sa aka kashe min J ɗina”.
Sosai Sheikh Jabeer yasa aka azabtar dasu suka faɗi duk laifinsu daga nan aka tura su waje na daban aka killace su domin jiran yanke musu hukunci.
Jalal kuwa nan take ya tura Modibbo video da yayi musu na cikekken bayanansu da sukayi.

Sheykh Jabeer kuwa da kansa ya tara su Abualeey yayi musu cikekken bayanin, ya ƙara da cewa, sai yazo ɗaurin auren su Dr Jameel shi da kansa zai yiwa Ummi da Abban Jameel dukkan bayani.

Aranan ƙarfe goma dai-dai na safe suka kama hanyar tafiya Membila da rakiyar motoci na musamman.

Ƙarfe huɗu dai dai ya musu acikin garin Gembilan...





By
*GARKUWAR MARUBUTA*

KAZAURE COLLEGE OF NURSING SCIENCES (KCONS)
Lafiya Uwar jiki, Kuma sai da lafiya ake morar rayuwa. Kazaure College Of Nursing Sciences (KCONS) ta kawo muku ingantaccen tsarin koyar da jinya da unguwar zoma, mun himmatu wajen samar da kwararrun ma'aikatan jinya da unguwar zoma a fadin Nigeria da ma matakin duniya baki daya, a KCONS mun tanadar muku kwararrun malamai, ingantaccen yanayi da tsarin koyo da koyarwa kai harma da tsarin e-learning, ka zalika akwai tabbataccen tsaro a dakunan kwanan dalibai maza da mata, bugu da kari kudin makaranta dai-dai aljuhu ne, KCONS munanan a lamba 5 layin fadar sarki dake kan hanyar kano zuwa daura a Kazaure jahar Jigawa, za'a iya samummu a shafikanmu na facebook da instagram @KCONsciences domin bayani, za'a iya tuntubanrmu a wadannan lambobin, 07066542055, 08035298851, ko shafin mu na yanan gizo @ http://kcons.edu.ng/admission KCON sciences kan turbar aiki da kwarewa muka shahara.

https://chat.whatsapp.com/HCji7xLpR1VEJGYcZJMP6k


Ajere-Ajere motocinsu suka fara shiga harabar gidan Innayi. Moddibo kuwa sassayan numfashi ya fesar a hankali ransa cike da mamakin, shin meyesa Abban Jameel yace su sauƙa anan duk da yasan cewa ba wasu wadatattun ɗakuna bane a gidan, kasancewar daga ɗakin Innayi sai Side ɗin sa dake da 2 bedroom sai single room a bakin ƙofar falon, yace wa Abba su sauƙa a hotel daya musu booking Amma yace a'a yaƙi masa musu ne, saboda bai san mai ya shirya ba duk da yafi tunanin Abba yace hakane ko sai sunci abinci kafin su tafi Masauƙinsu.

Akuma dai-dai lokacin motocinsu sukayi Parking a farfajiyar gidan.
Daga can waje kuma cikin sassarfa Haiydar da Bashir suka nufo gidan wanda har sun dauki hanyar komawa gida kasancewar sun jira su basu zoba sai kuma suka hango motocin su.

Acan harabar cikin gida kuwa cike da matsanancin mamaki da al'ajabi Moddibo ke bin baki ɗaya ilahirin gidan da kallo wanda aka tsara shi yayi masifar kyau wasu dan ƙara dan ƙaran Side ne akayi su guda biyu wa ɗan da kusan komai nasu irin nasa ne sai dai basu da wadatan flowers kamar nashi cikin fesar da numfashi da mamakin dake kwance saman fuskarsa ya ziro ƙafarsa na dama kafin ahankali ya gama fito da gangar jikinsa daga motar, hannunsa na riƙe cikin na Khausar still Idanunsa na bin harabar gidan da kallo.
Akuma dai-dai lokacin Idanunsa suka sauƙa kan Abban Jameel, Lamiɗo da Malam Ahmad suna sauƙa daga kan barandar ɗaya daga cikin Sabon Side biyu da aka gina still da mamaki ya maida kallonsa kan Innayi data fito daga Motar da suke.
Murmushi Innayi tayi ganin kallon mamakin da yake bin gidan dashi kana tace.
“Bismillah ku shiga side ɗinka”.
Kallon yaushe akayi wannan ginin yayi mata, fahimtar kallon da yake mata yasa ta jinjina masa kai tare da cewa.
“Tun kwanaki ai aka fara ginin saboda sanin cewa zamu zo Auren su Jameel, kana lokaci zuwa lokaci zamu buƙaci zuwa nan tunda ni da kai dai ba zamu manta garin Membila ba”.
Sanyayyar ajiyar zuciya ya sauƙe kana yayi murmushin gefen baki sosai yaji daɗin hakan saboda bawai ya tsani garin Membila bane saboda ya samu nasa garin, kawai dai Membila ta fita a ransa ne saboda rasa amininsa, Amman duk da haka yasan gari Membila garine wanda yake da tarihi arayuwarsa yana jin Membila na cikin garin da yake tamkar tsagin jikinsa, ya sani bazai manta garin arayuwarsa ba, ko ina yaje a duniya watara zata faɗo masa arai kuma dole zai buƙaci jin yana son zuwa cikin garin.

Anutse Didi ta fito kana Lalla Khadijah, Lalla Hafsat, Sai Rahama tana fita ta nufi gefen Khausar fuskarta ɗauke da murmushi tace.
“Woww Lalla Khausar haka garinku yake daɗi?,Masha Allah kina jin weather Mai daɗi haka Masha Allah i like it”.
Murmushi Khausar tayi kana ta gyaɗa mata kai da faɗin.
“Aikuwa zaki sha sanyi”.
Idanu Rahama ta lumshe sai kuma ta buɗe tace.
“Aikam akwai sanyi kam, duk da muma A Morocco ana mana sanyi but time to time ne amma bai kai wannan ba sanyin nan daban ne”.
Ta ƙarashe maganar tana ƙanƙame jikinta waje ɗaya jin yanda sanyi ke ratsata.

Kallon Khausar dake ɗan lumshe idanu Didi tayi kana ta maida kallonta kan Moddibo cike da kulawa tace.
“Aleeyu ku shiga ciki yarinyar ta gaji da zaman motar nan ”.
Kai ta gyaɗa Tare da cewa.
“Toh”.
Sai kuma ya damƙe hannun Khausar cikin nasa tare da ɗan janyota jikinsa suka nufi Side ɗin sa.

Gaba Innayi tayi tana mai cewa.
“Didi, Lalla Khadijah Lalla Hafsat Bismillah”.
Kai suka gyaɗa tare da bin bayanta suka nufi ɗaya daga cikin Side ɗin.
Akuma dai-dai lokacin Ummi ta fito daga Side ɗin fuskarta ɗauke da farin ciki da mamakin ganinsu tace.
“Masha Allah sannunku da zuwa, sai yanzu kuka iso, da naji ku shiru-shiru har nake cewa barin tafi wata ƙil zaku kai dare”.
Ta ida maganar tare da rungumar Didi itama Didi rungumeta tayi tana cewa.
“Masha Allah fatan mun sameku lafiya”.
Kai Ummi ta gyaɗa tare da riƙo hannun Lalla Hafsat tace.
“Alhamdullah. Bismillah mu shiga daga ciki”.
Cike da farin ciki suka bi bayanta...

Abban Jameel kuwa shi yayi wa Abualeey, Waziri, Galadima, Baffan Zakariyya, Dr Jameel Zakariyya jagora zuwa Side ɗin da suka fito ko wanne yana ɗauke da 3bedroom manya,-manya wanda aka shirya su da kaya na alfarma da kawa ɗaya daga cikin ɗakunan Dr Jameel, Zakariyya da Ibraahim ne aciki.
Sai kuma na biyun Abualeey ne da Waziri, Sai kuma Baffan Zakariyya, Galadima.
Acan Side ɗin su Ummi kuwa Didi da Rahama ta nunawa ɗakin farko inda zasu zauna kana bedroom ɗin gaba ta kai Lalla Khadijah, Lalla Hafsat,da Niyna.
Sai da ko wannensu yayi wanka kana suka canza kaya zuwa mai ɗan nauyi amma ba can ba saboda yanayin sanyin garin kafin suka gabatar da sallolin suka ɗan huta tare da taɓa hira sai kuma suka fito Falo Ummi da kanta tayi musu iso zuwa dining.
Didi na murmushi ta shaƙi sanyayyar Iskar garin da kuma wanda bishiyoyi da flowers ɗin gidan ke kaɗawa tace.
“Kai Alhamdulillah Masha Allah weather garin nan akwai daɗi ”.
Murmushi Ummi tayi tare da cewa.
“Aikam sai dai akwai sanyi”.
Sai kuma tayi serving ɗin su da lifiyayyan abinci iri iri na alfarma da suka musu.
Akuma dai-dai lokacin Haiydar da Bashir suka shigo bayan sun fito daga ɓangaren su Abualeey Haiydar na bin Falon da kallo yace.
“Ummi ina Addah Khausy?”.
Ɗan Murmushi Ummi tayi tare da faɗin.
“Tana side ɗin Moddibo”.
Cikin sassarfa ya juya da niyyar fita sai kuma yayi saurin juyawa ya kalli Didi cikin girmama ya ɗan rusunar da kanshi yace.
“Ayyah Didi kuyi haƙuri na manta bamu gaisa ba ina yininku fatan kunzo lafiya?”.
Dariya tayi tare da faɗin.
“A' lafiya lau anyi kewar ƴar uwa ko?”.
Dariya yayi tare da kama hannun Bashir da yake gaida su daga nan suka ficewa kai tsaye Side ɗin Moddibo suka nufa.

Acan Side ɗin Mazan ma haka ya kasance Abban Jameel da kansa yagabatar musu da abinci na alfarma da girmamawa sosai Abualeey suka jinjina mutunci da karramawarsu...

Haiydar da Bashir kuwa tun daga kan step ɗin Side ɗin Moddibo suke ƙwalawa Khausar kira suna cewa.
“Addah Khausy! Addah Khausy!!, Addah, Khausy!!!”.
A kuma dai-dai lokacin Khausar da Moddibo ne tsaye Dining hannunsa na cikin nata cikin taushi ya ranƙofa kanta tare da sassauta murya yace.
“Me zaki ci?”.
Kanta ta langwaɓar tare da tsirawa jerin abincin dake dining ɗin ido lumshe idanunta tayi tare da fara buɗe womers ɗin cikin yanayin jin sanyi ta motsa laɓɓanta tare da cewa.
“Ga nan tuwo miyan kuka kasa min kaɗan zanci ”.
Ajiyar zuciya ya sauƙe tare da faɗin.
“Masha Allah zauna toh bari na zuba miki”.
Da dan sauri ta juya jin Bashir da Haiydar na cewa Addah Khausy Addah Khausy hannunta dake cikin nasa ta janye ta juya cikin sassarfa ta nufi ƙofan anufinta tayi gudu.
Da wani irin sauri Moddibo ya riƙo tsintsiyar hannunta yace.
“Kiyi haƙuri Minha na tuba dan Allah kada kiyi gudu”.
Ɗan ware idanunta tayi tare da faɗin.
“Su Bashir da Haiydar ne fa”.
Kafin ta ƙarasa suka ƙara so cikin falon tare da rungumeta shima Bashir cikin sauri ya rungumeta ta gefen Haiydar.
Murmushi Moddibo yayi tare da harɗe hannunsa aƙirji yana kallonsu da tattausan murmushi bisa kekkyawar fuskarsa.

Khausar kuwa kallon Bashir tayi tare da cewa.
„Bashir ina Asma'u?”.
Murmushi yayi kana yace.
“Ba tazo ba wai ita kunya Amarya baza ta zo ba”.
Dariya mai tauri ta sanya tare da faɗin.
“Don Allah yanzu baza tazo ba haka zata min kenan?”.
Kai ya gyaɗa tare da cewa.
“Wallahi fa taƙi zuwa tun safe taƙi zuwa ayi shara da ita wai Ummi tayi haƙuri”.
Dariya Khausar ta sanya tace.
“Lallai dai kam”.
Haiydar kuma hannunshi yasa cikin nata.
Cikin mamaki ta kamo hannun tare da kallon faratunsa hararansa tayi tare da cewa.
“Me haka zaka wani tare farce kamar mace?”.
Cikin lingwaɓar da kai yace.
“Na gaza koyan yanke wa nefa, Mommy kuma tace in dai bazan koyaba bazata yanke minba”.
Murmushi tayi tare dasa hannunta ɗaya ta dungure ƙeyarsa tare da cewa.
“Shine daga isowata zaka haɗani da aikin yankewa”
Ta ƙareshe mgnar tana jawosu suka zauna bisa kujerun Dinnin table ɗin.
Moddibo kuwa a kujerar dake fuskantar Khausar ɗin ya zauna, yana maiyi mata wani arin amintaccen kallo ya fahimci akwai tsananin shaƙuwa da so tsakaninta da Haiydar duk da yawan faɗan da suke a da.
Anan sukaci abinci tare.
Kana sukayi ta hira kiran sallan Magrib ne yasa duk mazan sunka tafi masallaci.
Kana basu dawoba saida sukayi sallan Isha sannan suka dawo nan kuma suka sake dasa sabon hira.
Hakama Abban Jameel dasu Abualeey.
Suma su Didi da Ummi haka ta kasance a wurinsu.

Misalin sha ɗaya su Lamiɗo suka yiwa su Abualeey saida safe kana suka tafi.
Su kuma duk sukayi shirin bacci suka kwanta.

Ummi dake tare da Malam Ahmad ta nufi sashen Khausar tana faɗin.
“Bari in je in jawo su Haiydar dan na lura su yau in zasu samu a nan zasu kwana”.
Kai ya jinjina mata tare da jingina jikin motarsu ya tsaya jiran fitowarta.

Ummi na shiga ta kalli Haiydar dake zaune gefen Khausar tace.
“Ku tasa mu tafi”.
Da sauri Khausar ta miƙe tare da cewa.
“Toh Ummi bari in ɗauko mayafina mu tafi”.
Juyawa Ummi tayi jin Moddibo na cewa.
“Ina zaki je?".
Idanunta ta narkar kana tace.
“Zanje gida mana”.
Yana tsuke fuska yace.
“Da Izinin wa?".
Murmushi Ummi tayi tare da kallon Haiydar da Bashir tace.
“Haiydar kuzo mu tafi dare yayi mu barsu su huta”.
Saurin kallon Ummi Khausar tayi tace.
“Ayyah Ummi dan Allah ku jirani ya za'a kuma ace bazan jeba don Allah kayi haƙuri”.
“Da Izinin wa?”.
Ya maimaita tambayar yana mai tsuke fuska.
Kamar za tayi kuka tace.
“Da Izinin ka mana”.
Kai tsaye yace.
“Toh ban bada Izini ba”.
Ummi kam hannun Haiydar da Bashir taja suka fice.

Sai da suka sauƙe Haiydar agida kafin suka wuce.

Haiydar na shiga Falon Momy ya shiga da sauri ya zauna gabanta kan lallausan Darduma da take bisa alamu shafi da witri tayi.
yayin da ta jingina kanta jikin kushin cike da matsanancin farin ciki yace.
“Momy".
Cikin tsira nasa ido ta gyara zamanta tare da cewa.
“Na'am”.
Murmushin fuskarsa ya faɗaɗa tare da faɗin.
“Kin ga yanda Addah Khausy ta dawo kuwa Momy?”.
Kai Momy ta girgiza kana tace.
“A'a ya ta dawo?”.
Zama ya gyara yace.
“Wallahi idan kika ganta zakice Balarabiya ce Masha Allah Subhanallah, tayi wani irin fari mai masifar kyau farinta har wani ƙelli takeyi”.
Ɗan ware idanu Momy tayi tare da faɗin.
“Allah ko?”.
Kai ya gyaɗa yace.
“Wallahi fa”.
Daga nan suka cigaba da hira.

Acan ɓangaren su Moddibo kuwa cikin tura baki Khausar tace.
“Haka kawai ahanani zuwa gidan mu yanzu Fisabilillahi muna ƙasa ɗaya gari ɗaya ace bazan ga Momyna ba?”.
Kansa ya ɗaura bisa kafaɗarsa yace.
“Na isa? Ai ban isa in hana ki ganin Momyn kiba? waya isa ya raba uwa da ɗa? ban isa in ra Baki da Momy ba.
Kawai dai nima bana so ara bani da ɗana akusa dani ne shiyasa”.
Cunno baki tayi tana kallonsa cike da shagwaɓa hanci ya lakace mata kana ya cigaba da cewa.
“Kuma ina so ki huta nasan in kunje hira zaku tayi baza ki huta ba kiyi haƙuri ki kwanta kiyi bacci ki huta gobe da kaina zan kai ki muje mu gaida Momy”.
Ajiyar zuciya ta sauƙe tare da cewa.
“Da sassafe”.
Kai ya gyaɗa cikin tabbatar wa yace.
“In sha Allah in dai mun karya”.
Lallausan murmushi ta sakar mishi tare da riƙe tafin hannunsa tace.
“Toh shikenan”.
Bedroom suka wuce sosai tsarin ɗakin yayi kyau komai yayi yanda ake buƙata kana agyare tsaf-tsaf sai tashin ƙamshin roomfteshner yake, zama tayi kan gadon tare da jingina kanta da jikin gadon.
Moddibo kuwa gefenta ya zauna yana ɗan matsa mata ƙafafun yace.
“Kinga tafiyar nan da akayi mai ɗan tsawo sai nake ga kamar ƙafarki ta kumbura”.
Idanunta dake lumshe ta ɗan buɗe ta kalli ƙafan sai kuma ta gyaɗa masa kai tace.
“Eh dama Ni haka nake in dai na ɗanyi tafiya mai tsawo amota Normal haka yake min, zuwa safiya zaka ga ya watse”.
Ajiyar zuciya ya sauƙe tare da faɗin.
“Kuma ahaka kike so ki tafi kije ki zauna ba kiyi bacci ba”.
Ya ƙare maganar yana jan yatsun ƙafar tata tare da ɗan mammatsa mata su, sassayan numfashi ta fesar tare da muskutawa, da sauri ya ɗan tallabota tare da gyara mata kwanciyar saboda ganin duk ta sake alamun bacci mai nauyi takeji.
Ahaka ya cigaba dayi mata massage suna hira jefi-jefi har bacci ya ɗauketa.
janyota jikinsa yayi ya haɗa hannunsa waje ɗaya ya tofa musu addu'a ajikinsa ya fara shafawa kana ya shafa mata.

Washe gari bayan sun kammala breakfast da duk wani abu da za suyi Kai tsaye sashen su Didi suka shiga bakinsu ɗauke da sallama suka shiga bayan sun gaigaisa Moddibo ya kalli Didi tare da cewa.
“Didi zamu je wurin Momy”.
Kai Didi ta gyaɗa kana tace
“Ok sai munzo muma yanzu Ummin Jameel zata zo mu taho tare”.
Kai ya gyaɗa yana ɗan matsa hannun Khausar yace.
“Toh shikenan sai kun zo”.
Daga nan suka miƙe suka fito da kansa ya shiga mazaunin driver, kana ta shiga gefen mai zaman banza, cikin nitsuwa yaja suka tafi anutse yake driving yana Jin wani yanayi na daban.

Titinan garin ya zubawa ido lokaci ɗaya kuma tunanin J ɗinsa ya faɗo masa sai kuma yake tuna Lokuta da dama Idan yana tuƙi J na gefensa ko kuma J na tuƙi shi yana gefensa jikinsa ne yayi sanyi, tafin hannunta ya riƙo tare da mannawa kan cikinta yayi shiru kwayar idanunsa na tsats-tsafo da ruwan hawaye.
Tuni ta fahimci yanayin da yake ciki cikin sanyi da rauni tace.
“Allah ya jiƙan Yah Jameel Allah ya mishi Rahma Allah ya gafarta masa”
Araunane yace.
“Ameen Ya Allah Minha”.
Tana matsa hannunsa dake cikin nata tace.
“Yah Jameel yanzu baya buƙatar kukan nu addu'ar mu yake buƙata”.
Cikin ƙoƙarin hana hawayen sa zuba yace.
“Nima haka nakeso ina ta ƙoƙarin hana zuciyata da Idanuna kuka akan J sai dai muyi ta mishi addu'a Amman wasu lokutan ina gaza hana kaina hawaye a kanshi saboda nayi rashine da har yau ban samu madadinsa ba”.
Cikin tausasawa tace.
“Na sani Yah Mu'allim to Amman Allah ya fimu sonshi, kuma dama shi ya bamu shi dan haka addu'a kawai zamuyi ya mishi”.
Cikin sanyi yace.
“In sha Allah za muyi masa”.

A kuma Dai-dai lokacin mai gadi ya buɗe musu gate ɗin gidan Lamiɗo Parking yayi kana suka fita da sauri ta nufi harabar gidan da nufin gudu,
saurin riƙo hannunta yayi cikin tsira mata idanu ya langwaɓar da kai yace.
“Kar kiyi gudu mana wai ke bakya jin tsoron ki faɗine”.
Kai ta ta gyaɗa tace.
“Toh ai sauri nake inje inga Momy".
Sake langwaɓar da kai yayi yace.
“Ai zaki ganta Minha ba sai kinyi gudu ba tun da gaki cikin gidan”.
Ko gama rufe baki baiyi ba ta hango Raudat riƙe da Comb da kifiya bisa alamu kitso zata tafi.
Da sassarfa ta nufeta tana kiranta,
Ita kuwa Raudat jin muryar Adda Khausy tane yasa ta ɗago kanta

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login