Showing 24001 words to 27000 words out of 218703 words
haka?”.
Kai Innayi ta gyaɗa cikin tsawa tace.
“An faɗa miki wacece ke?Ko kina tunanin nan ma Jauro yaya ne da kike baza ikon ki da mulkinki kina kaɗa kai uwa ƙadangaruwa, kina abinda kika ga dama? to a hir ɗinki ki sani kece kika shigo muhalli na toh ki sani duk da cewa mu muke neman aure a ƙarƙashin ku ba za ki taka muba in barkiba domin mace bata bada Aure dan haka ki ficemin agidana”.
Wani irin dogon tsaki taja kana tace.
“Ko da baki ce in fice miki agida ba dole zan fita, amma kisa Aranki badai.
Ɗai shegen jikanki da tsarkakakkiyar jikata su haɗa Aure ba”.
Tana faɗin hakan
ta ida ficewa daga ɗakin amma still Idanunta na cikin dakin tace.
“Dama ace ansan tushe ansan asalinku sannan ansan jikan ki tsarka kekkene wanda aka haifa ta sunna, to ba komai amma jikanki da yake Najasa wanda aka haifa ta hanyar ƙazanta ba zaiyu abashi auren jikata ba, zaki ga ƙarfin Ikona da isata sannan kuma da Izzata akan al'amarin auren nan”.
Innayi da zuciyarta ke wani irin tafarfasa tace.
“Toh mu zuba mu gani kada ki fasa idan har ke kin cika mai karfin iko da Izzah”.
Ƙwaffa Hajja Nana tayi tare da sauƙa daga barandar ta juya fuuuu kamar zata tashi sama ta nufi waje.
Moddibo kuwa yana shiga falonsa ya maida ƙofar ya rufe, kana ya zame tare da zama aƙasan daɓas ya jingina bayansa da jikin ƙofan Falon lokaci ɗaya yashiga kokuwa da numfashinsa dake ƙoƙarin ɗauke wa.
Atake wani irin azabebben kuka mai gunji ya kufce masa cikin raunin murya da tsantsar tashin hankali ya shiga furta.
_“Allahumma Ajirni fii musibati wa'ahlifli khairan minha Ya wadud³ ya zul'arshil Majeed ya fa'alillima yurid As'aluka bi izzatil lati layura wa mulki kallazi la yurad Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n_”.
Cikin wani irin tashin hankali ya cigaba da karanta duk wata addu'a da tazo bakinsa.
Kana wani azabebben kuka mai sa rawan jiki ya sake kufce masa lokaci ɗaya wani masifaffen zazzaɓi ya rufe sa cikin kiɗima ya fara zantukan zuci. Aransa yace.
Innalillahi Wa'inna ilahi rajiu'n. Shin wannan wace irin Masifa ce? wani irin rayuwa ce take fukantoni! sannan inane tushena.
Ko-ko dai da gaske ne kalmar wannan matar gskyace, cewa bani da asali.”
Sai kuma ya rumtse idanunsa da ɗan karen ƙarfi.
Tare da fara ƙanana mgn a saman lips dinsa dake tsuma.
“Hahhhh da ƙamshin gaskiya acikin kalaman matar nanfa, domin da inada tushe da asali da tuni Innayi ta kaini garesu sannan ta nuna min tushena shin da gskene kenan bata hanyar aure sunnanr Manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallama aka samar da niba Yah salam.”
Sai kuma ya fara mgn cikin rawan murya.
“Ya Ubangiji Allah kada kasa zargina da zatona na tsawon shekaru ya tabbata ta wajen furucin wannan matar.”
Ya ida mgnar tare da kife kansa bisa guiwowinsa.
Domin shi akaran kansa ya daɗe yana tunanin wataƙil shi ɗan shegene shiyasa Innayi bata taɓa faɗa masa Asalinsa ba kuma bai taɓa ganin wani saba dangi na gefen uwa ko uba, ya kuwa san bazai taɓa yiwuwa ace kab duniya bayi da wani ɗan uwa ko ƴar uwa da za'ace nase sai dai in har shi ɗin ɗan Shegen ne, shiyasa Akullum yake tsoron tambayarta wanene shi domin kada yaji abinda zai tarwatsa masa ƙwaƙwalwarsa da kuma lissafin sa sabida tsoron hakanne yasa baya bincike kan tushensa sabida shi kansa ya fara zargan lamarin.
Lumshe Idanunsa yayi hakan ne ya bawa hawayen ciki damar kwaranyowa da masifar zafi suka zubo masa, cikin ransa yace dama nasani dole irin wannan ranan zai zo ranan da wasu mutane zasu fuskance mu gaba da gaba su tuhumi nagartata. sannan su kirani da shege idan har basu samu gamsasshiyar amsaba. Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n”.
Hajja Nana kuwa Afusace ta fita daga gida tare da buga Murfin gate din tana zuwa ta buɗe motar tashiga tana wani irin huci na tsananin ɓacin rai da takaici kallon Baffa Jimeta tayi kana tace.
“Mu tafi baki ɗaya mutanen cikin wannan garin basu da hankali basu san abinda suke yiba”.
Cikin sanyin murya Baffa Jimeta yace.
“Subhanallah Hajja Nana kada kice haka kada kiyiwa baki ɗaya mutanen garin nan kuɗin goro sam hakan be cancantu ba”.
Harara ta watsa masa kana cikin fushi tace.
“Rufe min baki kaja mota mutafi bana son maganar banza”.
Kai ya gyaɗa kana yayiwa motar key suka bar kofar gidan kai tsaye hanyar Jauro yaya suka nufa.
Anutse Malam Liman ya juya tare da kallonta kana cikin sanyin murya yace.
“Kiyi haƙuri Hajja Nana ita rayuwar nan na duniya komai sai da haƙuri ake fuskantar sa, abinda fa hakuri bai warware saba tofa rashin haƙuri ba zai warware saba, dan Allah ki kwantar da hankalin ki koma menene Khausar tayi yarinya ce bazaki sa shi amizani da zai tayar miki da hankali har haka ba”.
Cikin sauri Hajja Nana data tsirawa madubi ido ta juya ta kallesa kana cikin fushi tace.
“Wai Ni Khausar zata dubi tsabar Idona tace bata son Aliyu”.
Anutse Baffa Jimeta dake driving ya dan juya tare da kallonta kana cikin sanyin murya yace.
“Toh Hajja Nana menene aciki dan Khausar tace batason Aliyu ainima kaina bazan yiwa Khausar auren dole ba, duk da cewa Aliyu ya kasance ɗana amma bazan tauyeta in Aura mata shi adole ba tunda bata son shi”.
Afusace Hajja Nana ta buga masa tsawa tare da faɗin.
“Rufe min baki me kake nufi kenan?”.
Ahankali ya sassauta muryarsa cike da girmamawa yace.
“Hajja Nana kiyi haƙuri ki gafarceni Idan har abinda zan faɗa zai ɓata miki rai, amma abinda nake nufi a aura mata wanda take so.”
Sheƙeƙe Hajja Nana ke Kallonsa da Idanunta dake cike da Masifa cike da iko da kuma Izza tace.
“Wannan ne kuma baku isaba ba'a haifi wanda ya isa ya ƙaddamar da wannan abin ba”.
Ajiyar zuciya Baffa Jimeta ya sauƙe tare da kallon Baffa Liman daya tsirawa titi idanu kana ya sake sassauta muryarsa tare da cewa.
“Dan Allah Hajja Nana ki gafarceni Ayiwa yarinya abinda take so”.
“Bafa ku isa ba”.
Ta faɗa a taƙaice.
Kai Baffa Jimeta ya gyaɗa batare da yace Uffan ba ya cigaba da Driving.
Ahankali Malam Liman ya sauƙe Ajiyar tare da juyawa ya fuskanci Hajja Nana da kyau kana yace.
“Adda Hajja to dan tace batason Aliyu shine hankalin ki ya tashi haka?”.
Sake baki Hajja Nana tayi tare da cewa.
“Au don ne ma kake cewa, wato baka ɗauki abinda muhimmanci ba, wannan ɗin bai kai hankalina ya tashi bane?Sannan ma wanda tace tana so ɗin dama ace mutum me tushe ne da asali to ai da sauƙi”.
Dogon numfashi Malam Liman yaja tare da sauƙewa kana yace.
“Toh waye ne tace tana son din ne?”.
Dogon tsaki Hajja Nana taja tare da yin ƙwaffa kana tace.
“Wai wani Malamin Makarantar sune, Moddibo ne ko Momodu ne ohon mata, wannan yaron dai da Malam Arɗo yaje dashi Jauro yaya ashekarun baya sannan akwanakin baya muka je muka sameshi agidan Malam Arɗon tofa wai shi take so”.
Jinjina kai Malam Liman yayi alamun ya gane.
Ita kuwa cike da takaici ta cigaba da cewa.
“Toh Jikan wannan Ƙawar tawa Innare, kuma sanin kanku ne tunda nasha baku labari cewa babu wanda yasan asalinsu, sannan babu wanda yasan tushen su a iya binciken da nayi a iya sanin su da nayi muke zuwa Makka tare yaron nan ɗan shegene”.
Cikin sauri Baffa Jimeta dake Driving ya juya ya kalleta jin furucin daya fito daga bakinta.
Harara ta galla masa kana ta cigaba da faɗin.
“Ɗan shegene bashi da asali ɗane da aka haifeshi ta hanyar zina ta ƙazantacciyar hanya, shin taya zamu haɗa alaƙar aure dashi kalen ya lalata mana sunan zuri'a asamu abin faɗa aciki.
Girgiza kai Malam Liman yayi kana ahankali ya juya da fuskarsa gareta ya fuskanceta sosai yace.
Um-uhum kiyi haƙuri Addah Hajja kada ranki ya ɓaci”.
Girgiza kai tayi tana huci tace.
“Ai dole raina ya ɓaci Liman”.
Gyara Alkyabbar sa yayi kana yace.
“Dan Allah kiyi haƙuri amma kada ki sake aibanta yaron, domin koda maganar ki hakan take, sam bai da ceba duk da cewa kin bada hujjarki akan cewa shi shegene, tofa koda ya kasance shegen ba laifinsa bane, laifin Iyayensa ne da suka haifesa ta hanyar zina”.
Tallafe kunci Hajja Nana tayi tare da tsira masa ido babu keftawa, Malam Liman kuwa cikin sanyin murya da son nusar da ita ya cigaba da cewa.
“Sannan babu inda Shari'a ta hana Auren wanda aka haifesa ta hanyar zina.
Shari'a bata haramta Aurensa da Khausar ba, bai haramta ba a musulunci sai dai idan har akwai wani na ƙasu atare dashi wanda yake aikatawa shine zai zama lalura, sannan dan Allah irin wa'annan kalaman idan zaki furta su ki rinƙa tauna su saboda suna da nauyi”.
Atsawace ta kallesa kana tace.
“Liman Karka fara yimin wannan wa'aze wa'azen'kan nan masu sauya ra'ayi mutum”.
Cike da ladabi malam Liman ya sunkuyar da kansa ƙasa kana yace.
“Dole ne in fara yimi ki wa'azi, domin kada ki faɗa cikin furucin da zai kaiki ga fushin Ubangiji”.
Salati ta rafka tare da riƙe haɓa kana tace.
“Ikon mai duka Fadar gaskiyar ne zesa in fada cikin fushin Ubangiji, ko kuma yana da Uban ne ai tun yana jariri yana cikin tsumma da ka gani kasan cewa ƴarta ce ko ɗanta ya haifo shege ya kawo mata shiyasa ta gudu dashi saboda abin kunya yau tsawon shekara talatin harda ɗoriya kenan bata da wata ƙawa sama dani amma koni bansan tushen suba, bansan asalinsu ba sannan bansan daga ina suke ba”.
Girgiza kai Malam Liman yayi kana yace.
“Kiyi hakuri ki kwantar da hankalinki amma. Duk da haka Addah Hajja baki da hujjar shegan tasa”.
Cikin sanyi ya cigaba da yi mata nasiyya yana nuna mata kuskuren abinda take amma firrr Hajja Nana taƙi sauraronsa. Baffa Jimeta kuwa Uffan bai sake cewa ba har sukayi nisa da tafiya.
Ɓangaren Moddibo kuwa wani irin zazzafan zazzaɓi mai zafin gaskene ya lulluɓe sa wanda gaba ɗaya ilahirin jikinsa ke rawa.
Innayi dake tsaye ɗaki ma baki ɗaya jikinta rawa yake sai Safa da marwa take daga ƙarshe ta zame ta zauna kana ta fashe da kuka cur-cur-cur tamkar ƙaramar yarinya cikin Muryan kuka tace.
“Bansani ba Aliyu bansan wannan abin zai zame maka tabo ba acikin al'amuran kaba, bansan zai zame maka na ƙasu da kuma abin nunawa acikin al'amuran kaba Aliyu”.
Cikin tsanananin tashin hankali da tarin damuwa take maganganu tana zubar da hawaye.
Acan ɓangaren Abba kuwa bayan sun gama waya da Moddibo number Malam Ahmad yayi dearling jin yayi Picking yasa yayi gyaran murya tare da sallama kana suka gaisa bayan sun gaisa Abba ya sauƙe ajiyar zuciya tare da gyara zamansa kana cikin sanyin murya yace.
“Dan Allah Malam idan anyi sallar La'asar ko zan samu ganinka?”.
Cikin daddataku yace.
“Toh badamuwa Insha Allah zanzo, Allah dai yasa lafiya?”.
Jinjina kai Abba yayi tare da faɗin.
“Eh babu komai Allah ya kawo ka lafiya”.
Bayan Malam Ahmad ya katse kiran ya juya ya kalli Ummi dake gefensa kan 2sitter sai kuma Asma'u da Bashir dake kan 3sitter cikin sanyin murya yace.
“Abban Jameelu ne ya kirani”.
Cikin alamun damuwa Ummi tace.
“Lafiya kuwa!?".
Kai ya gyaɗa tare da cewa.
“Lafiya lau”.
Girgiza kai tayi hawaye na taruwa akwarmin Idanunta tace.
“Ka dai ƙara tabbayarsa”.
Ganin bata gamsu bane yace.
“Toh bari in tambayan”.
Ya ida maganar tare da dearling number Abba.
Abba na ɗagawa Malam Ahmad yayi Sallama kana yace.
“Dama na faɗawa Fatima gashi-gashi yanda mu kayi to amma tace wai dan Allah meyake faruwa lafiya kuwa?”.
Kai Abba ya gyaɗa cikin sanyin murya da tarin damuwa yace.
“Eh lafiya lau dama ina so ne kuɗaɗen da suka haɗa na motar ta data saida da kuma na Sarƙoƙinta tunda ga yanda Ubangiji ya ƙaddara to shine kuɗin nake so kazo in baka su sai ka maida mata su, sannan kayi mata bayani tare da kwantar mata da hankali”.
Kai Malam Ahmad ya gyaɗa tare da faɗin.
“Toh shikenan bari zan faɗa mata”.
Ahankali ya juya ya kalli Ummi bayan ya katse kiran kana ya mata bayanin duk yanda sukayi.
Cikin rauni ta sunkuyar da kanta hawaye na kwaranya daga Idanunta Shar-shar-shar suna zuba akuncinta cike da tausayawa suke kallonta musamman Asma'u lokaci ɗaya itama Idanunta suka fara zubar da ƙwalla.
Asanyaye Ummi ta ɗago kanta tare da kallon Malam Ahmad Muryanta na rawa tace.
“Kace masa bana son Kuɗin Na yafe me zanyi da kuɗin da suka kasa ceto min Jameel me zanyi dasu?.
Me zanyi da duk wani kayan ƙawa bana so bana ɓuƙatar su nayafe su duniya da lahira bana ƙaunarsu”.
Anutse Malam Ahmad ya girgiza mata kai cikin rarrashi yace.
“Kada kice haka Fatima kiyi haƙuri Jameelu addu'a zaki yi masa, kuɗin nan kada kice ba zaki karɓaba, idan har kika ce ba zaki karɓa ba zaki sake saka Mahaifinsa cikin damuwa da tashin hankali aransa”.
Kai ta girgiza tare da miƙewa ta nufi Bedroom ɗinta still hawaye na bin kuncinta.
Asma'u kuwa kife kanta da jikin cushin tayi tare da fashewa da sassayan kuka me gunji cikin sauri Bashir ya ɗagota tare da share mata hawaye cikin sanyin murya yace.
“Asma'u Yah Jameel baya ɓuƙatar kukan mu addu'ar mu kawai yake buƙata, dan Allah ki daina yi masa kuka kinji, na tabbata Yah Jameel baya son wannan kukan”.
Kai ta gyaɗa masa still hawaye na bin fuskarta tace.
“Bashir ya zanyi idan na tuna Yah Jameel ya barmu bari na har abada nakan ji zafi da ƙuna acikin zuciyata, nakan ji raɗaɗi mai zafin gaske nakanji.
Tamkar zuciyata zata fashe”.
Cikin sanyin murya Bashir yace.
“Toh ya zamuyi da hukuncin Ubangiji Asma'u haka Allah ya tsara Yah Jameel ba zaiyi tsawon rai ba, koda ace basu sace sa sun kashe ba na tabbata ba zai wuce wannan kwanakin ba mu dai kawai addu'ar mu yake buƙata a hankali kuma waɗanda suka aikata masa hakan zasuga SAKAYYAH mabayyaniya addu'a kawai zakiyi ta masa kinji”.
Jinjina kai tayi kana tace.
“Inayi kuma zan cigaba da har ƙarshen rayuwata da izinin Ubangiji”.
Ummi nashiga Bedroom ta zaune gefen gado tare da fashewa da kuka Malam Ahmad na shiga cikin daƙin ya zauna gefenta kana ya sanya hannunsa tare da janyota ya mannata da jikinsa cikin sanyin murya yace.
“Kiyi hakuri ki daina kuka Fatima, ki yiwa Jameelu addu'a Ubangiji ya masa rahma sannan madadin kice ba zaki karɓi kuɗin nan ba ki sake sakawa mahaifinsa damuwa to ki karɓa”.
Cikin rauni Ummi ta sake manna kanta da ka fadarsa kana ta cigaba da sheshsheƙan kuka.
Tafin hannunta Malam Ahmad ya damƙe acikin nasa kana ya cigaba da cewa.
“Idan yaso idan kika amshi kuɗin sai kiyi amfani dasu wajen yiwa Jameelu Sadaƙatul Jariya.
Kamar Gina Masallaci, Ko kuma gidan marayu, Ko Asibiti,ko makarantar addini, ko kuma yin Bohorle rijiya da dai sauransu da nufin Allah ya kai ladan garesa kinji ko Fatima kada ki butulcewa Ubangiji”.
Ajiyar zuciya ta sauƙe kana yace.
“Kada kice ba zaki karɓa ba Ubangiji shi yabamu Jameelu, sannan kuma shi ya ɗauke Jameelu bamu da abinda zamu yiwa Jameelu sama da addu'a shine kaɗai soyayyar daza mu nuna masa amma idan kika bar kuɗin ya mahaifinsa zaiyi dasu?”.
Jinjina kai Ummi tayi cike da gamsuwa kana tace.
“Shike nan insha Allah zanyi yanda kace Allah yajiƙan Jameelu Allah ya gafarta tamasa Ubangiji ya jaddada rahma agaresa”.
Malam Ahmad na share mata hawaye ya amsa da.
“Ameen”.
Ɓangaren Hajiya Lami kuwa zaune take afalonta cikin sanyi Samira ta fito daga Bedroom ta zauna gefenta tare da tsira mata idanu.
Kallonta Hajiya Lami dake riƙe da wayarta tayi kana tace.
“Lafiya kuwa Samira?”.
Girgiza kai Samira tayi cikin sanyin murya tace.
“Mommy cikina ke ciwo”.
Ahankali Hajiya Lami ta ajiye wayarta tare da tsira mata Ido kana tace.
“Meke damunki ne kwanan nan kina yawan complain din cikin ki yana ciwo”.
Rau-rau tayi da ido still Muryanta na rawa tace.
“Mommy nikam wannan ciwon cikin ya fara damuna,
duk fa lokacin daya Murɗa Mommy wani farin ruwa ne yake fito min ta gaba na.
Mommy har saina sa Path agabana kamar mai yin period kuma ba jini bane kawai ruwa ne yake fito min mai ƙarni da masifar wari”.
Zare ido Hajiya Lami tayi tare da cewa.
“Ruwa kuma?,Ni Lami wani irin ruwa kenan?”.
Cikin rawan murya Samira tace.
“Ruwane kamar Sparm yake fita sannan da yawa da yauƙi yake fita Mommy ga wari da ƙarnin Masifa yanzu bakya jin ƙarnin da na matsoki”.
Da sauri ta jujjuya mata kai alamun a'a.
Ita kuwa Samira cike da damuwa taci gaba da cewa.
“Nifa idan na sunkuyar da kaina ƙasa ƙarnin da warin nakeji”.
Girgiza kai Hajiya Lami tayi tare da haɗiye wani abu mai masifar ɗaci kana ta kalli Samira tare da cewa.
“A'a Samira nikam ban jiba. Amma tun yaushe ya fara miki haka?”.
Kallonta Samira tayi tare da faɗin.
“Yafi kwana biyar idan naji cikina ya Murɗa ya Murɗa, sai wannan abin ya zubo da fari ya fara zubowa kaɗan-kaɗan, to amma yanzu ya fara zubowa dayawa, sannan ciwon cikin yana ƙaruwa baki daya hankalina ya tashi Mommy!”.
Cikin sauri Hajiya Lami tace.
“To bari zan shirya Inje wajen boka Kar'uzu in Faɗa masa halin da ake ciki”.
Suna cikin magana suka ji ƙaran buɗe Bedroom ɗin Abban Samira.
Ganinsa yasa Hajiya Lami wayancewa da faɗin.
“Eh Samira Insha Allah Idan Daddy ki ya bari zanje induba Aminan Hajiya Bunayya dake fama da ciwon ciki”.
Cikin nutsuwar Kamilin Dattijo dake cike da kamala da nutsuwa ya ƙaraso cikin falon tare da kallon Hajiya Lami cike da dattako yace.
“Ayyah Subhanallah lallai dai naji kuna maganar ciwon ciki ashe Amina ce ba lafiya Allah ya sawwaƙa”.
Da sauri Hajia Lami tace.
“Amin dai”.
Shi kuwa yana gwara zaman hular kansa yaci gaba da cewa.
“Shiyasa na kwana biyu ban gantaba ashe ba lafiya ne?”.
Kai Hajiya Lami ta gyar'ɗa tare da cewa.
“Eh wallahi dama so nake idan ka fito zanje in dubata Idan ka amince”.
Jinjina kai yayi kana yace.
“Ayyah to ba matsala ki Gaishe su”.
Acan gidan Lamiɗo kuwa Hajiya Bunayya na shiga falonta ta kalli Amina dake zaune kan 2sitter gyara zama Amina tayi tare da cewa.
“Mommy wai ɗazu hayaniyar me nake jine ina waya da Uncle Naseer ne yana gaya min tsarin ginin gidansa da ake gyarawa a cikin Abuja yace min in anyi aure zamu zauna a nan na wata ɗaya zuwa biyu kafin mu tafi India, shiyasa ban fito ba”.
Cikin jin dadi tace.
“Alhamdullah kice dai abu yanata kankama”.
Kai ta gyaɗa mata tare da cewa.
“ Eh Ummah Amman Hayaniyar me akayi ɗazun”.
Taɓe baki Hajiya Bunayya tayi tare da cewa.
“Ooo Kakar Khausar ce kuma yau tazo tana ta bala'i, banma san bala'in da take ba na dai ji tana cewa Khausar bata da kunya zata kalli tsabar idonta tace batason mijin da ta zaɓa mata