Showing 72001 words to 75000 words out of 218703 words

Chapter 25 - Sakayyah 2 Hausa Novel Complete

gaisuwar ku, ko kuma kallon kaina zan bari Rahama tayi tayi”.
Ya ƙare mgnar da amsa sallamar da yaji anyi mishi da muryar da ta kasance irin tasa sak.
Sai kuma ya ɗanyi murmushi jin Ibraahim na cewa.
“Yah Aleey ka koresu in ba hakaba bazasu Barka ka huta ba fa more especially Rahama Bata da aiki sai suru”.
Cikin sanyi yace.
“Kana ina yanzu Ibraahim kai ban gankaba”.
Cikin jin daɗi Ibraahim yace.
“Ina Istanbul, nima jiya na tafi da safe kai kuma ka isa da yamma”.
Kai ya gyaɗa tare da kallon Hafsat dake miƙa mishi tea ɗin amsa yayi da hannunsa na dama. Ya lura kusan halinta iri ɗaya ne da nashi bata da yawan surutu da fara'a sosai sai dai kuma tana da kula.
Lalla Khadijah kuwa miƙewa tayi tare da cewa.
“Bari inje in taya Didi aiki”.
Kai ya gyaɗa mata kana ta fita.
Daga nan yaci gaba da mgn da Ibraahim, tare da kallon Hafsat dake ƙara mishi siymil wani abinci su ne na larabawan can da fulawa akeyishin sai dai ya wadatu da nama.

Cup din ya miƙawa Rahama tare da kallon Hafsat kana yace.
“Alhamdullah na ƙoshi, kai ta jinjina kana ta tattara wurin tare da cewa.
“Toh kaje ka ɗan kwanta ka huta, ke kuma Rahana zomi tafi".
Kai jinjina mata, daga nan suka fita suka tafi.

Sai misalin ƙarfe 9:30 Didi ce da Sarki Youseep Mouleey suka shiga falon suna shiga suka ji falon shiru alamar baya nan yayin da suka fara jiyo wani sautin murya mai daɗi da sanya nutsuwa na karatun Alkur'ani na ratsa kunnensu.
Cikin nutsuwa Sarki Youseep Mouleey ya fara bin direction ɗin da yake jiyo sautin karatun Yayin da Didi ke biye dashi.
Akan darduma suka hango sa da alama Salatul duha ya idar kana idanunsa na lumshe yana karatun akansa.
Daga gefensa suka zauna lokaci ɗaya hawaye ya shiga bin kuncinta cike da farin ciki ta ɗaga hannunta sama kana tace.
“Alhamdulillah Innayi kinyi min duk kan gatan duniya kin bawa ɗana Ilimi mafi girman ilimi mafi tsada da daraja wanda zai amfanesa duniya da lahira sannan zai amfanemu”.
Sai ta kuma kalli Moddibo still hawaye na kwaranya daga idanunta ta cigaba da faɗin.
“Wannan ɗana ne yake karatun Alkur'ani tamkar acikin harami wanda koda acikin harami sai an jinjina masa”.
Moddibo kuwa jin sautin Muryanta da kuma motsin Mahaifinsa yasa ya buɗe Idanunsa jin tana cigaba da cewa.
“Innayi Allah ya biya ki da mafificin Al'khairi Ubangiji Allah ya sadamu inyi miki *SAKAYYAH* da mafi kyawun abinda ki kayi min sannan inyi miki godiyar da ban san da wani irin baki zan miki ba”.
Ahankali Moddibo ya shafa addu'a kasancewar yazo ƙarshen surar da yake karantawa.
Anutse ya juya ya kallesu haka nan zuciyarsa ta aminta da cewa Tabbas suɗin wasu ababene na jikinsa da Zaran ya kalli Mahaifinsa zai ga tsananin kamanninsa dashi babu abinda ya raba su shi kansa kamanninsa da mutumin yana bashi mamaki babu abinda ya rabasu sai dai shi Modibbo yawan shekarun sa bai kai nasa ba zuwa yanzu ya gama gamsuwa iyayensa ne su.
Cike da ladabi ya gaishe su kana suka amsa cikin sakin fuska da tarin ƙaunarsa.

Didi kuwa ahankali ta janyo basket data shigo dashi ta ajiye agabansa, tare da fitar da kulolin, kana ta ɗauki plate ta zuba masa abincin da ta dafa mishi da kanta, kana ta kalleshi cike da so da ƙauna tace.
“Wannan abinci da kaina na shiga kitchen na dafa maka dan kaci da kyau”.
Cikin gamsuwa da kalamanta ya jinjina kai ya tabbatar nutsuwa da kamalarta da kuma kimarta tafi ƙarfin tayi masa ƙarya maganganun da take faɗa daga zuciyarta ne kuma gaskiya ne babu shakka ko haufi aciki shi kanshi ya gamsu mahaifiyarsa ce ita Abualeey kuwa mahaifinsa ne masarautar Mouley kuwa tabbas mahaifarsace...
Fuska ɗauke da yalwataccen murmushi Sarki Youseep Mouleey ya janyo Cup tare da faɗin.
“Ni kuma da kaina zan haɗa maka tea in baka duk kan kulawar daka rasa atare damu na tsawon shekaru, in Sha Allah sai mun haɗa ta mun baka a iya tsawon sauran Rayuwar da Allah ya ƙadddara mana anan gaba”.
Cikin wani irin tattali da kulawa suka ci-gaba da faɗa masa maganganu masu sanyi da ratsa ƙwaƙwalwa wanda ko wani ɗa yake fatan saurara daga iyayensa.
Moddibo kuwa tamkar amafarki haka yake jin abubuwan sai dai wani lokaci wani abu ya taɓa ganinsa amafarki sa.
Haka suka cigaba da kulawa dashi suna hira da kara fahimtar yasan komai ma masarautarsu, yinin wannan rana suna tare dashi koda motsi yayi zasu tambayesa me yake so ko kuma me yake buƙata sai gab Azahar suka yi masa sallama suka fita suna tafiya aka kira sallar Azahar...
Anan yayi Sallar Azahar ɗin sa yinin wannan ranan ma ba'a buɗe sa.
Haka yayi kwanaki biyu anan batare daya fita koda ƙofan falon ba sai dai akawo masa abinci sai dai kuma su shigo suyi hira dashi...
Yau ta kasance Asabar inda ya zama kwanakinsa uku kenan a Masarautar Mouleey bayan fitar Mahaifiyarsa, Mahaifinsa da kuma Sheikh Jabeer yana zaune a falon kamar daga sama ya fara jiyo shesh-sheƙan kuka.
Cikin sauri ya juya ya kalli Hadiman dake tare dashi sai kuma ya kauda kansa ganin basu bane cikin yanayin mamaki da al'ajabi ya juya gabas da yamma kudu da Arewa yaga dai duk basu bane keyi kukan. Bisa alamu kuma kamar su basujiba, ahankali ya miƙe ya nufi Corridor har ya isa falon nan ma ba kowa sai dai yana jin shesh-sheƙan kukan daga cikin bedroom cikin sassarfa ya nufi bedroom ɗin yana shiga ya hangi Jalaluddeen ne zaune agefen gadon yana kuka tamkar ransa zai fita.
Cike da matsanancin mamaki gami da al'ajabi yace.
“Jalaluddeen k...”.....



LITTAFIN SAKAYYAH na kuɗine ƴar uwa 1k ne kacal 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP 09097853276 in tura miki kisha karatunki.

GAREKU masu son Maganin infection duk maiso ta biya yau in Sha Allah jibi saƙonku zai taho.


By
*GARKUWAR MARUBUTA**SAKAYYAH book 2... Page 13*

Na
*Aysha Aliyu Garkuwa*


Tallah !! Tallah !!

Shahararriyar Marubuciyar nan Ikilima Adam (kyauta daga Allah) wacce ta nishadantar daku a littafin ta mai suna *Kanwata* , yau ta sake dawo muku Domin tallata muku Littafin mai Suna ( Rai Daya Jan Zaki) littafine mai kunshe da Butulci , cin amana ,zagon Kasa , soyayya irin ta gani kasheni , aminci da saura n su basai n'a cika Ku da surutu ba Hausawa sukace Gani yakori ji.

Farashin wannan littafin Naira Dari biyar ne 500 kacal postin biyu a arana banda ranar Juma'a .
Domin Karin bayani Ku tuntubeni a lambata kamar haka (09069080725 ko Kuma + 22953726162 ) wacce Bata shirya Siya ba kada mu batawa juna lokaci.
Domin aikawa da kudi kai tsaye . 3115484026 ikilima Adam first bank
Turo shaidar biya akan wannan 09069080725 sai najiku.

Jalaludeen kuwa cikin rauni ya ɗago idanunsa wanda suka zama tamkar garwashin wuta, saboda yanda sukayi ja-jawur yayin da baki ɗaya ilahirin jikinsa ke rawa kar-kar tamkar wanda aka jona masa Shorking kuka yake mai shiga jiki tare da ratsa zuciyar duk wani mai imani daya saurara.
Da sauri Moddibo ya ƙara sa kusa dashi gefenshi ya zauna cike da matsanancin rauni da kuma famewar mikin dake zuciyarsa na rashin J ɗinsa ya shiga rera wani irin raunataccen kuka tamkar ransa zai fita, kukan wanda bai samu yayi shi ba a lokacin rasuwar, baka jin sautin komai acikin ɗakin, face Shesh-sheƙan kukan su dake cigaba da wanzuwa aƙalla sun ɗauki kimanin minti goma sha biyar suna kuka batare da wani yayi yunƙurin rarrashin ɗan uwansa ba.
Cikin dauriya da ƙoƙarin son hana kansa kuka kana da shesh-sheƙa Jalaludeen ya ɗago tafin hannunsa mai masifar sanyi tamkar wanda aka ciro acikin dusan ƙanƙara ya manna aƙirjin Moddibo daya ke jiyo bugun zuciyarsa, cikin rauni yace.
“Kayi haƙuri Mouley haƙiƙa munyi rashi mai girma.
Munyi rashi mafi ciwo azuciyarmu. Kayi haƙuri Aliyu kaya femin tsawon lokaci baka ganni ba ina cikin haramine! shiyasa baka ganniba”.
Lumshe idanu Moddibo yayi wasu hawaye masu masifar zafi suka zubo akuncinsa yayin da sanyin tafin hannu Jalaludden ke ratsa zuciyarsa Jalaludden kuwa cikin raunatacciyar murya ya cigaba da faɗin.
“Saboda na shiga inayin I'itiƙafi tsawon lokacin nan shiyasa kuma koda na fito munyi tafiya nida Kakana munje ƙasar Sin shiyasa baka ganni ba bansan Jameelu yashiga wannan hali ba bansan Jameelu ya rasuba Mouley”.
Sai kuma ya fesar da numfashi mai zafi tare da cigaba da faɗin.
“Sai jiya Juma'a ne naje Taraba domin kai muku ziyara, kasancewar na daɗe ba muyi magana ba yasa na shirya muku Surprised sai dai kawai ku ganni, toh ina isa gidan innayi na nufa, naje gidan Innayi na samu babu kowa sai na wuce gidan Ummi”.
Kallonsa kawai Moddibo keyi hawaye na cigaba da silala daga idanunsa.

Cikin rauni Jalaludden yace.
“Acan na samu Innayi suna hiran. Jameel ya rasu kuma na tsinkayi cewa kana ƙasar Morocco, nazo ƙasar Morocco na bibiyi al'amarin ka har na gane cewa kana cikin Fadar Rabat!”.
Kuka ne yaci karfinsa cikin kuka kamar ƙaramin yaro ya cigaba da cewa.
“Mouley munyi rashi.
Jameel ya tafi ya barmu Allah yajiƙan Jameel Allah yayi mishi rahma!”.

Cikin sanyin murya Moddibo yace.
“Amin Ya Allah. Amman nayi mamaki rashin jinka Jalaladdeen ina ka shiga, tsawon lokaci ba ɗuriyarka. Na shiga matsanancin damuwa Jameel ɗina ya ɓace tsawon lokaci, bamu sameshi ba.
Naso ace kana kusa damu kayi mana amfani fiye da amfanin da kayi mana abaya ka faɗa mana inda J.yake”.
Kai Jalaludden ya girgiza still hawaye na kwaranya daga idanunsa ya riƙe hannun Moddibo kana yace.
“Bana kusa Aliyu, sannan kuma koda ina kusa muma kanmu jinnu. Ubangiji bai sanar damu gaibu ba Aliyu,
da ace Allah ya sanar damu ilimin gaibu ko a inda nake zan iya sani da zan faɗa maka, amma Allah bai sanar damu gaibu ba.
Sanin gaibu sai Allah kaɗai bansan haka zai faru da Jameel ba.”
Numfashi Moddibo ya fesar kana ya dafe goshinsa da hannunsa na dama tare da faɗin.
“Tabbas munyi rashi mafi girma ban taɓa sanin ya ɗaci da zafin mutuwa yake azahiri ba har sai da na rasa J ɗina, mutuwar J mutuwa ce da bazan taɓa mancewa ba. Sannan bazan daina jin zafi da raɗaɗinsa ba har sai ranar dana koma ga Ubangiji na!”.
Kai Jalaludden ya gyaɗa kana yace.
“Sosai ma kuwa Aliyu, amman haƙuri zamuyi, domin babu abinda Jameel yafi buƙata agaremu yanzu face addu'a addu'ar mu”.
Kai Moddibo ya jinjina tare da cewa.
“Zan cigaba da yiwa J ɗina addu'ar samun rahamar ubangiji har zuwa numfashina na ƙarshe”.
Haka suka kwana suka yini suna hira.

Washe gari da safe koda Sarki Youseef Mouley da Didi suka shiga wajen Moddibo suna tare da Jalaludden sai dai su basu da ikon ganinsa kasancewar bai bayyana musu kansa ba,
ko Moddibo ba ma asiffar mutum yazo masa wanda sukayi karatu dashi.
Bayan fitansu ya kalli Moddibo yace.
“Kana kama da Mahaifinka”.
Da mamaki Moddibo ke kallonsa kafin ahankali yace.
“Mahaifina ko?”.
Kai Jalaludden ya gyaɗa Fuskarsa ɗauke da murmushi yace.
“Eh Mahaifinka mana, shin ban taɓa faɗa maka cewa kai ba ɗan Nigeria bane, har kaita dariya kana tambayata to kai ɗan ina bane?”.
Kai Moddibo ya jinjina tuni lokacin suna Jami'atul Madina bayan sun fito daga darasi suna shan shayi Jalaludden ke sanar masa.
Still da murmushi afuskarsa ya cigaba da faɗin.
“Har kace min kai ɗan ina ne nace kai ɗan Morocco ne, kace ba haka bane.
Amma ni nasan hakane saboda nayi bincike ne akan Innayinka na kuma fahimci haka”.
Zazzafan ajiyar zuciya Moddibo ya sauƙe cikin tsira masa idanu yace.
“Kenan kana nufin nan ƙasatace?”.
Murmushi Jalaludden yayi ta gyaɗa masa kai kana yace.
“Sosai ma kuwa ƙasar kane, tsatsonkane, Mahaifarkane. Wa'annan kuma Mahaifanka ne”.
Cikin girmamawa lamuran Ubangji mabuwayi gagara misali Moddibo yace.
“Ya Salam shin taya akayi wanna al'amarin yakasance ya akayi abin ya faru a haka, abin ne yazo min tamkar amafarkaina na yau da kullum”.
Gyara zama Jalaludden yayi tare da faɗin.
“Kada kayi mamaki,Ka cire al'ajabi da mamaki acikin lamarin Ubangji ya wuce mamaki. Kai dai kawai kayi godiya ga Allah”.
Ahankali Moddibo ya motsa laɓɓansayace.
“Alhamdulillah Allah kulli halin”.

Kai Jalaludden ya jinjina haka suka cigaba da hira kafin daga bisani Jalaludden ya kalli Moddibo da murmushi afuskarsa yace.
“Sannan kuma akwai al'amarin da naje na samu ranan juma'a ya kasance amma bazan faɗa maka ba sai ka ganin da idonka”.
Ware idanu Moddibo yayi kana ya langwaɓar da kai tare da cewa.
“Jalaluddeen nawa dan Allah ka faɗa min mana”.
Ƴar dariya Jalaludden yayi wanda ya bayyanar da fararen haƙoransa yace.
“Ok naje na samu Ummi ta shiga damuwa sosai akan tsawon kwana uku kenan tana kiran wayar ka amma bai shiga har Abban Jameel yazo da kanshi dan Maganar dana samu suna tattaunawa da Innayi kenan”.
Lumshe idanu Moddibo yayi yasan dole hakan zai kasance rashin jinsa awaya zai ɗaga musu hankali musamman Innayi da Ummi shima Abba sai dai kawai yayi dauriyar maza.

Da murmushi Jalaludden ya cigaba da cewa.
“Ya faɗawa Innayi shima ya kira wayarka baya shiga tsawon kwana uku kenan, amma kuma Innayi sai dariya take tana ce musu kada su damu kawai afara shirin kawo maka”...
Sai kuma yayi shiru tare da yin mgnar zuci. Alhamdulillah gwara da ban faɗa masa ba saboda naji suna faɗin cewa Moddibo bai san anyi masa Aure ba..

Ɗan ware idanu Moddibo yace.
“Ana shirin kawo min me?”.
Buɗe hannu Jalaludden yayi kana yace.
“Kai dai ana shiri kawai abinda naji sun faɗa kenan”.
Langwaɓar da kai Moddibo yayi cikin Muryansa mai cike da sanyi yace.
“Kai dai Jalaludden baza ka faɗa min ba kawai”.
Kai Jalaludden ya girgiza kana yace.
“Um-um iya abinda naji kenan, kasan na faɗa maka bansan gaibu ba Allah ne kaɗai mafi sanin gaibu”.
Kai Moddibo ya jinjina cikin gamsuwa da maganarsa yace.
“Toh shikenan”.

Washe gari Litinin ya kama kwanan Moddibo biyar kenan acikin Masarautar Mouley.
Misalin ƙarfe tara na safe Moddibo ne zaune acikin tangamemen Falon kamar yanda ya saba ko yaushe yaji an buɗe ƙofar falon anutse ya ɗaga kyawawan idanunsa tare da kallon ƙofar.
Idanunsa suka sauƙa akan.
Didi da Sarki Youseef Mouley sai wani kyakykyawan Matashi mai masifar kama dashi kallo ɗaya ya masa ya fahimci shine Ibraahim ƙaninsa ne da Didi ke yawan bashi labarinsa duba da kamannin dake tsakanin su. Sai kuma Lalla Khadijah da Lalla Hafsat, sai ƴar auta Rahama.
Ibraahim kuwa yalwataccen murmushi ya sakar masa domin shi yakasance mutum ne mai fara'a da son Mutane kana da abin dariya

Suna haɗa ido da Moddibo ya ƙara fara'ar fuskarsa kana ya tafi cikin sassarfa ya rungumeshi yana mai jin farin ciki da nutsuwa agaba ɗaya ilahirin jikinsa cike da shauƙi ya ɗago kansa kana yace.
“Yaya zance maka? Ko kuma Usaini? ko kuma Hassan ɗina?”.
Moddibo kuwa lokaci ɗaya ya tsinci kansa da ƙaunar yaron aransa rungumesa yayi kana cikin ɗan sakin fuska yace.
“Koma me ka kirani dashi zan amsa”.
Sai kuma suka sake rungume juna yayin da ƙaunar junansu ke ratsa ko wani lungu da saƙon dake jikinsu...
Cikin tsanananin so da ƙauna Lalla Khadijah tace.
“Kai Ibraahim ka sakeshi haka mana”.
Kalla Hafsat dake ruggume da ɗiyarta ce tayi dariya tare da zama tana kiciniyar bawa baby nono, tace.
“Ai dai kam ya maƙaleshi kamar ya fimu sonshi”.
Didi da Abualeey kam kallonsu kawai suke cike da jin daɗi mata misaltawa.
Rahama kuwa cikin tura baki ta harari Ibrahim cikin yanayin tsamar saƙo-da saƙo tace.
“Ai shi haka yake ga yadda ya maƙaleshi kamar shine auta”.
Cikin jin daɗi Abualeey yace.
“Toh mu zauna dai kafin ai ta yiwa Ibraahim ƙorafi”.
Shiko Ibraahim signal yayiwa Rahama tare da cewa.
“Ai shi nawane ni kaɗai ba dama cewa kike nine bani da ɗan uwaba toh Allah ya dawo min da ƴaƴana dama yafi Yayunki kyau”.
Lalla Khadijah ce ta ɗan zuggure ƙayarsa.
Ɗan tsalle yayi tare da
ɗago kansa ya kallin Moddibo kana yace.
“Kaga abinda suke minko ko Yah Aleey”.
Murmushi Modibbo yayi tare da ɗan janye jikinshi gefe yana mai kallonsu ɗaya bayan ɗaya yakejin sonsu da ƙaunarsu na ratsa mishi zuciya.
Shi kuwa Ibraahim baki ya ɗan tura tare da cewa.
“Kayi haƙuri ɗan uwana”.

“A kan me?”. Modibbo ya jefa mishi tambayar.
da sauri yace.
“Sabida rashin dawowata da wuri, sabida ranar da kazo ranar na tafi Turkiyya dan daga nan muke kai musu dabino, toh nike wakiltan lamarin, koda Lalla Hafsat ta gaya min ji nayi kamar inyi fiffige in dawo gashi naga dan ban dawo da wuriba kamar kafi sonsu a kaina”.
Dariya sukayi baki daya.
Sai kuma duk suka tsagaita tare da zubawa Modibbo ido ganin yadda yake dariya tare da shafa kan Ibraahim dan ganinshi yake kamar Bashir.
Didi kuwa da su Kalla Hafsat murmushi dukeyi ganin yadda ya jawo Ibraahim ya ruggumeshi yana mai cewa.
“Waya ce maka nafi sonsu, suda zasu koma gidajensu su barmu tare”.
Cikin dariya yayi musu gwala.
Rahama kuwa ɗan rawa tayi tare da faɗin.
“Ni dai muna tare”.
Shi kuwa Ibraahim
juyowa ya kalli Didi da Abualeey tare da cewa.
“Dan Allah Didi ku aurar da ita ta bar mana gida mu sake".
Baki ta tura tare da cewa.
“Ba ruwanka da ni”.

Didin kuwa fuskarta ɗauke da ƙayataccen murmushi ta kallin ƴaƴan nata dake zaune reras agabanta kana tace.
“Alhamadullah Allah na gode maka da ka cika min farin cikin ahlina”.
Kai Abualeey ya jinjina tare da faɗin.
“Masha Allah”.
Ibraahim kuwa
janye hannunsa dake cikin na Modibbo yayi kana ya juya tare da kallon Alƙibla yayi Sujudur Shukur.
Kana ya ɗago tare da komawa gefen Moddibo ya zauna still fuskarsa ɗauke da ƙayateccen murmushi ya kalli Sarki Youseef Mouley tare da faɗin.
“Abualeey Addu'ar mu ta karɓu Ubangiji ya dawo mana da Yah Aliyu alokacin da bamuyi zato ba sannan ba muyi tsammani ba sai nake ji kamar gaba ɗaya burikana na duniya aka gama cika min dan ganin ɗan Uwana kuma gudan jina”.
Kai Sarki Youseef Mouley ya gyaɗa kana yace.
“Tabbas kuwa domin babu abinda ya gagari Ubangji Allah da kansa yace mu roƙeshu zai amsa mana. Domin shi addu'a ba'a gaggawa dashi”.
Moddibo kuwa cike da tsananin so da ƙaunarsu dake ratsa ko wani magudanan jinin jikinsa yace.
“Tabbas kuɗin kun kasance min. Garkuwa ne atare dani ina jin ajikina babu abinda zanyi face godiya ga Allah daya haɗani daku kafin na koma garesa”.
Haka suka cigaba da hira tsawon lokaci ganin suna shirin tafiya yasa Moddibo ya sunkuyar da kansa ƙasa kana yace.
“Ayyah Abba dan Allah Ina bukatar wayoyina akawo min su”.
Murmushi Sarki Youseef Mouley yayi kana yace.
“Kada ka damu za'a kawo maka wayoyinka dan suna

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login