Showing 150001 words to 153000 words out of 218703 words
da Manzonsa sannan kuma keda kanki kikace zaki rayu dashi a ko wanne yanayi.
Dan haka babu yanda za'a yi adawo dake kin taɓa ganin anyi Auren ƴa mace ta koma gidansu?”.
Cikin matsanancin kuka ta girgiza mata kai Momy kuwa cikin nutsuwa ta cigaba da faɗin.
“Hakkine da iko da matsayin miji duk inda yaga dama ya ajiye matarsa ya za'ayi Kice ya dawo dake hauka ne akanki?.
Haka Ummi da muka yi waya take faɗa min Haiydar nata kuka kamar ransa zai fita saboda ya tafi ya barki kina kuka duk hankalinsa ya tashi zaki sa yaro adamuwa kisa ya dawo min da zazzabi shi kansa mijinki kin tayar masa da hankali”.
Cikin faɗa ta cigaba da cewa.
“Har mijinki zai riƙa rarrashinki yana cewa kiyi haƙuri amma ki ƙi kiyita kuka kamar ibada”.
Khausar kam shesh-sheƙa ta cigaba dayi so take ta hana kanta kuka amma kukan yaƙi haɗiyuwa.
Cikin damuwa Momy ta cigaba da cewa.
“Ok zakici gaba da kukan kenan?”.
Kai ta girgiza tare da faɗin.
“A'a Momy na dainaaa”.
Irin yanda take kukan har numfashinta na yankewa.
Momy kuwa cikin damuwa ta cigaba da faɗin.
“Mijinki yaita rarrashin ki ki ƙi rarrashuwa hauka ne akanki, Kiyita kuka kina cewa zaki da kowa ba ganan Maman mijinki ba ai zata zame miki madadina in dai kika mata biyayya zata maye miki gurbina mijinki kuma dole ki masa biyayya sannan ki bishi sau da ƙafa domin shine komai na rayuwar ki a yanzu saɓa mishi kamar saɓa umarnin Allah da Manzonsa ne da suka ce Ayiwa miji biyayya”.
Kuka ta cigaba dayi tana jan ajiyan zuciya.
Moddibo kuwa ganin Momy nayi mata faɗa sannan bata daina kukan ba yasa ahankali yasa hannu ya zaro wayar daga kunnenta kana ya mayar kunnensa cikin sanyi da ƙasƙantar da kai murya a raunace yace.
“Kiyi haƙuri Momy rarrashinta za'a yi ba faɗa za'a yi mata ba”.
Yana maganar kamar zaiyi kuka.
Kai Momy ta girgiza kana tace.
“Khausar baza taji rarrashi ba idan ta fara kuka batasan bari ba kafita harƙanta ka barta idan tayi Kukan tagaji da kanta zata bari ka barta na lura Khausar rigima ne da ita”.
Sake ƙasƙantar da muryarsa yayi yace.
“Momy kiyi haƙuri In Sha Allah zan rarrasheta za tayi shiru Mommy bayan iya barinta tana kukaba zai cutar min da ita”.
Kai Momy ta gyaɗa tare da cewa.
“Toh shikenan sai anjina”.
Ahankali ya sanya hannunsa kan kumatunta ya fara share mata hawaye kana cikin sanyi da taushin lafazi yace.
“Kiyi haƙuri ni ba mugu bane bazan miki mugunta ba, nifa Mijinki ne ba kyau kada ki sake cewa mijinki Mugu bakya tsoron Allah ya ƙona kine?”.
Cigaba da kuka tayi wanda yake fitowa daga ƙasan ranta cikin rauni tace.
“Aini ban ce maka mugu ba amma dai kana cin zalina shekaran jiya kusan kasheni kayi kuma Allah zai sa kamin”.
Sake ƙasa da murya yayi cikin taushin lafazi yace.
“Kiyi haƙuri In Sha Allah bazan sake ba ki yafe min kinji ki yafewa Yah Moddibonki Minha”.
Kafaɗa ta maƙale tare da tura baki da juya kumburarrun idanunta tace.
“Ni dai ban yafe ba sai Allah ya saka min daga duniya har kiyama bazan taɓa yafe maka ba”.
Zare idanunsa yayi sai kuma ya langwaɓar da kansa yace.
“Ayyah Khausar am ki yafemin kiyi min duk horon da zaki min amma kiya femin”.
Cikin shesh-sheƙan kukan ta kallesa kana ta tura bakinta tace.
“Da gaske?”.
Cikin sauƙe numfashi yace.
“Yess kimin duk hukuncin da kikaga ya dace da laifina, Amman banda kuka kuma banda cewa bana sonki da kuma cewa zaki koma”.
Cikin sauƙe numfashi shesh-sheƙan tace.
“Toh nima yanda kake cin zalina sai na rama ka kaɗe ɗankwali”.
Ba zato yaji murmushi ya sufce masa sabida mgnar tazo mishi a bazata.
Ya kuma lura yadda tayi mgnar kamar hakan shine babban burinta, ɗan ware idanunsa yayi tare da cewa.
“In kaɗe ɗankwali kuma?”.
Cikin tura baki ta gyaɗa kai tace.
“Eh kaima ba haka kake min duk abinda nayi kaima mugunta da kayi min ka kaɗe ɗankwalin kaji abinda nake ji”.
Numfashi ya fesar cikin tsira mata ido yace.
“Idan na kaɗe ɗankwalin zakiyi shiru?”.
Da sauri ta gyaɗa masa kai tare da faɗin.
“Eh”.
Sassayan ajiyar zuciya ya sauƙe kana yace.
“Toh kawo ɗankwalin in kaɗe sau nawa zan kaɗe?”.
Kallonsa tayi ta wani tura bakisai kuma tace.
“Da gaske zaka kaɗe?”.
Girarsa ɗaya ya ɗaga mata.
Cikin jin dadi tace.
“Toh Sau hamsin zaka kaɗe”
Ware manyan idanunsa dake narke yayi tare da yarfe hannu da faɗin.
“Wayyo Allah na Ni Aleeyu”.
Sai kuma ya zauna ya kifa kansa akan cinyarta cikin langwaɓar da kai yace.
“To ai zaki kashe mijinkeeh”.
Ya ƙare maganar cikin shu'umar muryar da tasa jukinta mutuwa,
Ƙyafƙyafta idanunta tayi kana tace.
“Ba nima kana sani ina kaɗewa sau 30 ko sau 20 ba?“.
A hankali yace.
“Toh ai ke 50 kikace inyi”.
Cikin sharce hawayenta tace.
“Toh kasan Ai laifin da kayi yafi nawa yawa da zafi ko?”.
Numfashi ya fesar kana yace.
“Toh shikenan kawo ɗankwalin In kaɗe”.
Ɗankwalin abayar kanta ta cire ta miƙa masa karɓa yayi yana ɗan buɗawa.
Baki ta tura tare da cewa.
“Ai wannan ma bashi da nauyi bari In ɗauko maka ɗan kwalin Less”.
Saurin riƙo hannunta yayi ganin ta yunƙura yace.
“Ainima wanda nake saki kike kaɗewa bana Less bane kin manta?,Na Uniform ne na Uniform kuma be kai wannan kauri ba”.
Baki ta tura tare da faɗin.
“Toh ka kaɗe”.
Cikin tsira mata idanu yace.
“Ina idan na kaɗe zakiyi shiru?”.
Gira ɗaya ta ɗage cikin jin dadi tace.
“Eh mana kai dai ka kaɗe na gani”.
Murmushi yayi kana yace.
“Toh ki share hawayen ki”.
Ba musu ta sanya hannunta ta share hawayen yayin da take sakin murmushi tana tuna yanda take jin azaba ahannunta idan ta kaɗe sai kuma ta ɗan ɓata fuska da faɗin.
“Toh kaje ka kaɗe mana”.
Kai ya gyaɗa tare da cewa.
“Toh muje”.
Kallonsa tayi da kumburarrun idanunta tace.
“Ina?”.
“Muje mana kiga yanda zan kaɗe”.
Ajiyar zuciya ta sauƙe tare da cewa.
“Ok”.
Hannunta ya riƙe suka shiga bedroom ɗin kana suka wuce Bathroom.
Bocket ya jawo ya sa ɗankwalin kana yasa ruwa.
Juyawa yayi ya kalleta tana tsaye bakin ƙofa tana murmushi kuma har zuwa lokacin tana sauƙe ajiyar zuciya na kukan da tayi amma kuma fuskarta ɗauke da murmushi ya lura kaɗe ɗankwalin zai sata farin ciki ganin itama yau ta samu ƴanci zata sashi aiki cikin langwaɓar da kai ya kwaikwayi muryarta yanda take roƙon sa abaya yace.
“Ayyah Yah Mu'allim a kiyi haƙuri mana In cire rigar jikina kar in jiƙe”.
Ka faɗa ta maƙe kana ta tura bakinta tace.
“Ai kaima lokacin da kake sani kaɗewa harda hijabi ma ajikina da kuma Uniform ɗina haka kuma nake kaɗewa”.
Sake langwaɓar da kai yayi tare da narkar da murya yace.
“Kenan yanzu bazan cire Jallabiyar ba?”.
Kai ta gyaɗa tana murmushi tace.
“Yesss Of Course kayi ahakan”.
Ta ƙare maganar tana cilla girarta sama fuska ɗauke da murmushin mugunta.
Kai ya gyaɗa tare da tsugunnawa ya matso ɗankwalin acikin bokitin”.
Cikin sauri ta wani tura baki tace.
“Ai ba'a matse ɗankwalin sosai kaɗan ake matsewa”.
Ta faɗa tana karasa shiga cikin Banɗakin abakin Bathtub ɗin ta zauna shikam cikin wani irin yanayi na musamman ya fara kaɗe ɗankwalin na farko, hammm ya ja numfashi sabida sanyi ruwan daya watsu a jikinshi,
sai kuma ya kaɗe na biyu kana ruwan ya watsu a fuskarsa sake kaɗewa yayi Still ruwan ya sake watsuwa afuskarsa tuni sajensa ya jiƙe.
Ido ta tsirawa Sajensa tana sakin murmushi Allah ya sani sajensa na masifar yi mata kyau musamman yanzu da fuskarsa ta jiƙe da ruwan sai ƙyallin sajen keyi murmushi kawai take tafi kowa sanin yanda zaiji a hannayensa idan ya kaɗe.
Moddibo kuwa sau bakwai ya kaɗe sai kuma ya tsugunna zai mayar cikin Bokitin.
Cikin sauri ta kamo hannunsa tace.
“Wallahi sai ka sake kaɗewa ai bai bushe ba”.
Lumshe idanunsa yayi tun lokacin da hannunta ya sauƙa kan nasa jin tsikan jikinsa na tashi saboda laushi da kuma santsin hannunta haka nan ya tsinci kansa cikin wani irin farin ciki da shauƙi da kuma nishadi ɗan marairaice fuska yayi kana yace.
“Toh shikenan”.
Sai kuma ya ƙara uku kafin ya kalleta yace.
“Toh yayi In tsoma”.
Cikin jin daɗi ta gyaɗa masa kai sake tsomawa yayi ya matse zuwa lokacin baki ɗaya Fuskarsa ta gama jiƙewa har ruwan na ɗiga tal-tal-tal kana gaban Jallabiyarsa ma ya jiƙe ahaka dai har ya tsoma sau biyar ya kaɗe sai kuma ya ajiye ɗankwalin acikin Bokitin ya riƙe ƙugunsa tare da cewa.
“Wayyo Allah ƙuguna”.
Still sajensa na ɗigar da ruwa til-til-til.
Dariya ta ƙyalƙyale dashi harda dafe ciki.
Tsayawa yayi yana kallon yanda dimples ɗin ta ya lotsa da kuma yanda fararen haƙoranta suka bayyana suna sheƙi duk da cewa ga yanda fuskarta yayi ja da kuma idanunta suka kumbura cikin ƙyalƙyala dariyar tace.
“Madallah ka dai ji yadda nake ji. Allah ya ƙara ai nima haka nake ji kuma wallahi saura arba'in da biyar”.
Ta ƙare maganar tana mishi signal ɗin daya sashi jin wani irin fitinenne abu na zirya daga tsakiyar kansa har zuwa tafin sawun shi.
Karya kai yayi tare da langwaɓar da murya yayi kalar tausayi kamar yanda da take masa yace.
“Dan Allah Malama kiyi haƙuri arage min yawansu yayi yawa hannuna ciwo yake”.
Cike da farin ciki ta kuma fashewa da dariya kana ta miƙe ta riƙe ƙugu tace.
“Haka nake ji kaima kayi”.
Sai kuma ta zuba wa sajensa idanu tana kallon yanda ruwa ke cigaba da ɗiga tal-tal-tal.
A hankali yasa babbar yatsarsa na hannunsa na dama ya kwantar da gashin giransa tare da zira mata idanu.
Ganin ta kifi tafin hannunta kan sanjeshi tana ɗan katse ruwa tare da cewa.
“Bari in gogema maka ruwan”.
Sai kuma ta ƙare maganar da yin murmushin da zuba idanunta kan sajen da kyau.
Ya lura batama sanin lokacin da take kai hannunta kan sajenshi, ganin yadda ya tsira mata idonsa ne yasa tai saurin janye hannunta.
Shi kuwa Modibbo cikin wani irin fitinenne flenings ya ɗan sake matso ɗan kwalin Abayar ya sake kaɗewa dake ta miƙe tsaye tana kusa dashi haka yasa ruwan ya jiƙata.
A tare suka saki ajiyar zuciya.
Ita kuwa gira ta kuma ɗaga mai tare da cewa
“Ya akayi?”.
Cikin fitinenniyar murya can ƙasan maƙoshinsa yace.
“Zaki kasheni“.
Murmushin mugunta tai tare da cewa.
“Ba wani mutuwa sai wuya dai, ci gaba, tunda ban mutuba in sha Allah kaima bazaka mutuba”.
Cikin narke fuska yace.
“Uhmmm bayan wuya kuwa zamsha daɗi ba“. Sai kuma ya sunkuya ya cigaba da kaɗewa har yayi na takwas Kallonta yayi tare da faɗin.
“Wayyo Didi na hannuna ciwo Allah hannuna zogi yake min Minha”.
Dariya ta ƙyalƙyala kana tace.
“Allah ko goma baka yiba kuma sai ka ƙara”.
Juyawa yayi ya fuskanceta kafin yace.
“Kiyi haƙuri ni koma me kike so ki sani amma banda kaɗe ɗankwalin nan yana da wahala”.
Ware Idanunta tayi tace.
“Kaima haka kake yimin ba haka kake sani ba dan haka kaima sai kayi,yau kam sai kayi”.
Yana yarfe hannu yace..
“To ai nayi amma arage min kingani kin ninka min yayi yawa ki bari sai gobe In ƙarasa,in yaso yau inyi 25 gobe inyi 25”.
Ɗan shiru tayi kamar mai nazari sai kuma tace.
“Toh kayi 25 ɗin, kayi na yarda”.
Shafa sajensa yayi tare da cewa.
“Kuma nima ai ashirin nake saki”.
Ƙugu ta riƙe kana tace.
“Toh aini laifina kaɗan ne”.
Kwaikwayon maganar ta yayi yace.
“Toh nima ki bari idan na sake miki lefin sai ki sani”.
Da sauri tace.
“Zaka sake laifinma kenan?”.
Cikin sauƙe numfashi yace.
“Yess sosai ma kullumma kuwa,bai kema kullum sai kin maimaita laifi dan haka nima banyi alƙawari bazan ƙaraba”.
Cikin kwaɓe fuska tace.
“Wlh komawa zanyi”.
Sai kuma ta kalleshi jin yana cewa.
“Kiyi haƙuri wasafa nake, wanda nayima na tuba ki yafemin”.
Cikin jin dadin cewa yau ita kesa Moddibo irin punishment ɗin da yake sata kuma yanayi harda ƙaramar murya yake mata cikin jin dadi tace.
“Toh ka kaɗe, Ka kaɗe”.
Kai ya gyaɗa kana yasa ita kam dariya ta cigaba dayi yayin da yake jin wani irin farin cikin ganin murmushin ta da kuma yanda idan yace ya gaji take dariya yasa duk kaɗewa ɗaya sai yace.
“Wayyo hannuna”.
Ita kuma sai ta fashe da dariya ahaka dai har akayi ashirin tana ƙyalƙyala dariya kamar ba ita ke kuka ba yanayin yanda ruwan ke sauƙa a fuskarta sai ya zama fuskar ta wanku fes juyawa tayi kan abin alwala ta wanke fuskarta sai ta juya ta kallesa lokacin daya kade na 25 yana ƙoƙarin maida bocket ɗin inda ya dauka tare da sanya ɗankwalin acikin kana yace.
“Wayyo Hannu na ya mutuuuuu”.
Dariya ta sanya tare da faɗin.
“Nima haka nakeji duk randa aka sani kaɗe ɗankwalin nan na koma ko rubutu bana iyawa sai dai Haiydar ya min kaima yau kaji yanda nake ji”.
Juyawa tayi ta nufi hanyar fita.
Da sauri ya tsaya gabanta yace.
“Toh Ni yanzu ko rigana ma bazan iya cirewa ba gashi duk ya jiƙe ki taimaka min ki cire min”.
Kafaɗa ta maƙale tace.
“Um-um nima ai idan ka sani da kaina nake cirewa kacire ka gani kaima idan zaka iya ka dai ji yanda nake ji”.
Cikin langwaɓar da kai yace.
“Toh shikenan”.
Sai kuma ya tsugunna ya kamo ƙasa Jallabiyar ahankali ya zaro tare da faɗin.
“Wayyo hannuna”.
Cikin sauri Khausar da takai bakin kofa zata fita ta juya jin maganarsa dariya ta ƙyalƙyala dashi.
Yana cire Jallabiyar ya saƙale ahanga dake ban ɗakin.
Ita kuwa ahankali ta zubawa sajensa dake ƙyalli ido sai kuma ta maida idanunta kan gashin ƙirjinsa dake kwance luf-luf.
Ahankali ya matsa kusa da ita.
Yayinda ita kam baki ɗaya idanunta na kan ƙirjinsa.
Yana isa jikinta ya janyota kana ya rungumeta aƙirjinsa yana saki wani sanyayyan ajiyar zuciya kanshi ya cusa tsakanin wuyanta da kafaɗarta a hankali ya kai bakinsa saitin kunnenta yace.
*“Minha vidaa* Kin huce ko? Kinji daɗi kinsa mijinki wahala?”.
Kai ta Jinjina tace.
“Eh amma dai zaka ƙarasa saura guda 25”.
Cikin sauƙe numfashi ya shaƙi ƙamshin ta yace.
“In dai zakiyi dariya kaɗewan zai saki farin ciki ko guda dubu kike so zanyi miki *Minha vidaa*”.
Lumshe idanunta tayi.
Shikam ahankali ya riƙa cusa yatsun ƙafansa ƙarƙashin ƙafanta wanda yasa dole ta daura tafin ƙafan ta akan rumfar ƙafansa yana jin haka ya manna kanta da ƙrjinsa ahankali ya fara ɗaga ƙafansa yana takawa har suka fito yana tafiya da ita, ɗin yaja ƙofan ya rufe...
Suna shiga tsakiyar bedroom ɗin ya matsa da ita bakin gado akunnenta ya raɗa mata
“Kijifa kema kin jiƙe”.
Baki ta tura cikin kasala tace.
“Uhm toh ba kaine ka jiƙani”.
Yana lumshe idanunsa yace.
“Bake bane kika tsaya kina min dariyar mugunta ba”.
Dariya ta sanya Amma batace komai ba.
Akasalance yace.
“Yanzu ma dariyar kike min ko Minha”.
Cikin lumshe idanu tace.
“Eh mana kaima ba dariyar mugunta kake min ba”.
Yana fesar da numfashi yace.
“Ni na taɓa yi miki dariya ne?”.
Tana tura baki ta ɗan gyara tsayuwar ta akan ƙafarsa tace.
“Baka min dariyar, tunda kasan kayi min Mugunta ai kai kaji daɗi ma nayi maka dariya kai ban taɓa ganin haƙorinka bama”.
Sanyayyan murmushi ya saki tare da cewa.
“Aikam naji daɗi kiyi min dariya nayi farin ciki, kuma ke yanzu ai ba haƙorina bama, ba gashi harda ƙirjina da duka jikinama kike kalloba shekaran jiya har kusan tsinkemin lips nafa kikayi Minha vidaa da kyar na tsira dasu”.
Cikin sauri ta runtse tare da cusa kanta a ƙijinsa.
Sai kuma tayi saurin buɗe idanunta jin ya zuge zip ɗin rigarta yayi ƙasa da ita.
Cikin tura baki tace.
“Sanyi fa”.
Muryansa ashaƙe yace.
“Badole kiji sanyi ba rigar ta jiƙe ki bari In cire miki shi kiji ɗumi”.
Kafaɗa ta maƙale tace.
“Um-um nikam ka barmin rigana”.
Numfashi ya fesar yace.
“Zai saki mura Ni kuma bana son abinda zai cutar *Minha* ”.
Shuru tayi jin yanda ya zuge rigar sannan yayi ƙasa da hannunta ya cire acikin rigar runtse idanunta tayi lokacin da taji ya zare ɗaya hannun rigar ya zama ta gaba ne kaɗai ya rage baya yaja kaɗan rigar ya faɗi runtse idanunta tayi.
Cikin sauri da bugawar zuciya ya rumtse Idanunsa jin tudu da taushin Breast ɗin sun sauka kan ƙirjinsa ga sanyi daya ratsa fatar jikinsa wani sanyayyan ajiyar zuciya mai ƙarfi ya saki atake jikinsa ya fara sharking Kamar anjona masa Shorking.
Cikin wani irin sauri tasa hannu ta zagaye ƙugunsa da ƙarfi yayin da take jin wani irin abu yana game jikinta mai cike da shauƙi.
Shikam wani irin abune ya tsiga masa tun daga tafin ƙafarsa har ƙwaƙwalwar kansa yayin da idanunsa suka sauya lips ɗin sa suka hau rawa hannunsa dake rawa ya ɗaura akan skintied ɗin ta ya fara murzuwa yana ƙasa dashi.
Da sauri ta tura bakinta ta riƙe kana tace.
“Wayyo Allah ka bari bana so”.
Ahankali ya zauna bakin gado da ita tare da jingina bayansa da jikin gadon ya ɗan ware ƙafafunsa yasata atsakiyar ƙafansa blanket ɗin ya ware ya rufe su cikin mayatacciyar murya yace.
“Ai kin san ba kyau fa tauye haƙƙin miji, haka zaisa ki faɗa cikin fushin Allah, kina son Allah yayi fushi dake?”.
Cikin sanyi take girgiza mishi kai tare da lafewa a jikinai tana shaƙan.
Wani irin ƙamshin blanket da taushinsa da kuma sanyinsa ɗakin suka haɗu suka sauƙar mata da kasala da mutuwar jiki ahankali ta manna kanta da jikinsa dai-dai kan maransa.
Cikin sauƙe numfashi yasa hannunsa duka biyu ya ɗago ta kana ya manna ƙirjinta da ƙirjinsa ya zamana kanta na dai-dai ƙasan gemunsa yana shinshinan kanta ahankali ya fara shafa bayanta sai kuma ya sauƙe hannunsa kan skintied ɗin ta yana ɗan tura hannunsa kan mazaunanta.
Da sauri ta runtse idanunta kana tasa hannunta ta rungumo bayansa ɗaya hannun kuma yana kan sajensa tana shafawa ahankali ya matso da bakinsa kan kunnenta cikin wata kasalalliyar murya yace.
“ *Minha* ”.
Lumshe idanunta tayi zuwa yanzu ta fahimci wani sunane da yake kiranta dashi wanda batasan me manufar saba may be wani abune daban sai wata zuciyar kuma tace waya sani ko ƴar Iska yake nufi tunda yace min Fattanah Rigimammiya yanzu kuma yana ce mata *Minha vidaa* wata ƙil ƴar Iska yake nufi dan yaga yayi abu da ni kuma Allah ya sani nidai ba ƴar Iska bace ta ƙare maganar zucin tana ƙoƙarin tashi.
Da sauri ta koma ta faɗa jikinsa ganin lokacin data tashi yasa hannu ya tallafe ƙirjinta da hannunsa ɗaya kana ya kamo hannunta ɗaya kuma ya ɗaura kan mararsa......
By
*GARKUWAR MARUBUTA**SAKAYYAH book 2... Page 29*
Na
*Aysha Aliyu Garkuwa*
*Masu son Maganin infection set ɗin 10k half 5k sai kuma masu son maganin mata na gani na faɗa na kece raini da baza ƙamshi na alfarma, ku marmatso kusa wannan account no in ne naku ta ciki zaku turo kuɗin ku 0005388578 Jaiz bank AISHA ALIYU GARKUWA, Sai ki turo shaidar biyanki ta WHATSAPP NUMBER'N na 08069423567. akwai sabbin kaya masu zafi